22
22
Sakiyyyy fa kace wallahi baka isa ba ,ka isa nema yar ka ta dakeni sannan kazu kasakeni ,,yace eh din banza inba iskanciba mace da aurenki kina kallon blue films ,tace na kallan din aykai ne baka biyamin bukatu ne ,yace to ya isa jeki dai ki auri jarababbe irinki ,,,
Haka hajar tafito tanata zage zage har dakin hajiya ,tana shiga tasa kuka hajiya kinga umar yasakeni ko ,munafukar matarsa ta zugashi,
Hajiya dama akule take ,cewa hajar tayi to ay sai kiyi hakuri hajar kema bake jin mgn ,,hajar tace kice dama da hadin bakinki ,tshowar banza da wufi wato kinsa danki ya mayarni bazawara kamar ke ko ,bakar azzaluma ,,,hajiya tace hajara ni kike gayawa mgn haka ,nafada din ,hajar tas tayiwa hajiya, sannan tafita hajiya sai kuka take ga ciwo ga takaici ,
Umar yana shiga gurin husna yana hada gumi da haki, husna ,da sauri husna ta tareshi tace my me ya faru haka kake ta gumi,ruwa ta mikamar mai sanyi tace cool dawng ,shuru yayi bayan yasha ruwan sannan yace husna ,tace naam yace nasaki hajar ,salati husna tayi tace haba my kai da nagayamaka abinda melat ta mata maimakon kamata hakfita kuma sai ka saketa ,,haba dan Allah kaifa uban ya,ya, matane abin da kayi shi zaamaka,,tsawa ya daka mata yace dakata husna dan na haifi ya,ya, mata baizama hujjar da zan zauna yarinyar na tanamin halin banza agidah ba,nan yabata lbr abun da hajar takeyi,durkusawa husna tayi tace kayi hakuri na dauka akan fadansu da melat ne fah ,bansan kana da naka dalilin ba ,,,,
Yarima kullum tunanin lema ya hanashi sakat ,bashi da ayki sai saurarun karatunta ,inda ya kudura atansa yau zaije yasamu waziri akan mgn yaje ya naima mishi izini ,ganin leema,,,
Tare da sultan sukaje basu sha wahalar fahimtar da waziriba ,sbd leema sananneyace duk wani mai fada aji a garin yasan ta sbd fita musabaka ,sosai waziri yayi murna yace zai samu mai martaba da zance ,,,
Haka kuwa akayi yaje da maganar mai martaba ma yayi murna sbd ya dade yana saurarun magnar aure daga bakin yarima ,,haka aka shirya zuwa naiman aure ,ta hannun malaman mkrtrsu leema,inda kafin suje aka sanar da umar,shikuma ya gayawa yayunshi ishaq da hamza sai babban abukinshi ,salim,
Jamaar gidan sarki sun iso naiman izinin auren leema ,kuma anbasu ,,har antsayar da sadaki maganar aure da girma,saura sa rana,,,
Yarima kam murna kamar zaiyi yaya inda sultan ke tsokanarsa wannan shine cinkin biri a sama kaida bakaga fuskartaba ,,,yarima yace ita nakeso ba fuskartaba ,kuma yau zanga fuskar insha Allahu,
Haka suka shirya sai gidansu leema ,suka ayka suna sallama, daker husna tasa ,leema tafita har tafita ta dawo tace momy me zance in naje ,husna dariya tayi tace ki gaishesu ,sannan tafita a dakin zaure aka saukesu ,da sallama tashiga ta gaida su ,inda duk su biyun suka lalace a kallonta ,yarima ne ya dakawa sultan duka suka sa 😃 leema dai kanta a sunkuye ,sultan ne yace hajiya leema ya gidah ,haka dai aka taba hira ,sultan ya fita yabasu waje nan yarima ya baje kulin soyayyah ,lema ma atake taji duk duniya ba wanda take so sai shi,haka suka dau lkc kafin yarima yayi sallama da leema yabata waya da sauran kayan da ya kawo mata ,wannan kenan
Abubuwa sun taru sunyiwa hajiya yawa ga ciwo ka rashin mai kula da ita dan rahama sai tayi sati batayiwa hajiya wankaba ,,haka uwar hajar tazo har gidah taimata rashin mutumci ,sannan sahal bai daina kumai ba bayazuwa mkrt ga sata daga yaga kudin hajiya zai dauke haka abinci ,,,
Yau surayya ce tazo daga yobe kasancewar taji lbr auren leema tazo tayasu murna dumin leema tayi babban kamu wato yarima sadik,
Sun dade suna hira sannan surayya tace ke husna yau ina hajiyarki take ne naji shuru gidan ,,,husna tace ay hajiya ta karye har sau biyu,surayya tace amma baki da kirki shine baki gayamin ba maza muje in dubata,,,da sallama suka shiga dakin hajiy daker suka samu gurin zama ,kacaca dakin ,ga wani wari dayake tashi ,rahama ko tayi ficewarta,kasancewar surayya nus ta duba kafar hajiya ,tace ay wannan kafa bata gyeruba ,nan fa tafara fada ,haba husna kina gidan nan da ya,yanki ace hajiya tazama haka ,maza leema dauramin ruwan zafi ,kafin kace an gyre hajiya da dakinta sbd tsbar datti kasan katifarta harda tsusa ,hajiya sai godiya take tana hawaye,
Surraya takira umar tace lalle gobe Monday akai hajiya asivity kashi dan kafarta ta lalace ,,,kafin surayya tabar gidan saida tayiwa husna nasiha sosai akan kula da hajiya ko ita baza tayiba tasa su leema su dunga gyrata kullum ay ko a lahira wani yana cin albarkacin wani,,,,
Washegari zaakai hajiya asivity ,akayiwa lami mgna tace suje zatazo matar ishak kam ko bude kofa takiyi ,,,hawaye umar yafara zubarwa shidai yana jin kunyar husna bazai iya sata doleba ,haka ya kuma dakin hajiya ,abin farin ciki husna yagani da leema da melat sun gyera hajiya ,husna tace ya mu futune yace eh muje ,aransa kuma yace Allah yasakawa surayya da alheri har inda take,
A asitvty ma albarkaci melat akaci dan tana practical agurin ,da sauri aka duba hajiya ina likita yayi ta fada yace lalle ne sai an yanke kafar dan ta baci sosaiiii
Takuce dai uwar farhana ,love u fans😘
*BRILLIANT WRITTES ASSO*
👱🏻♀👱🏻♀👱🏻♀👱🏻♀👱🏻♀
*YA,YA, MATA*
Abin Alfahari ne
👱🏻♀👱🏻♀👱🏻♀👱🏻♀👱🏻♀
*BY UMMU FARHANA*
*DEDICATED TO MY FANS LOVE U ALL*❤
COMMENTS