MA'AIKACIYAR GOMNATI Complete Hausa Novel

  COMPILED BY  ESHATT SMILER HOM OF HAUSA NOVLS DOCUMNTS WASAPP 08066360176           MA'AIKACIYAR

 


COMPILED BY 

ESHATT SMILER HOM OF HAUSA NOVLS DOCUMNTS

WASAPP 08066360176



          MA'AIKACIYAR

              GOMNATI

              ⓂⓂⓂ


                   1



        By

Asmabaffa



      Masoyana naga sakonku sosai na yabo da jinjina kan novel dina na maraicin rahma,ban San Kalmar da zanyi amfani da ita ba wajen gode muku,na gode kwarai Allah ya bar kauna,Allah ya biya muku dukkanin bukatunku na alkhairi.





         LONDON na nufa a 80 jirgi ya saukeni da kyar na hada kudin zuwa ma sabo da jin dadinku readers bazan bari ya wuce Ku ba,wani gida Wanda ya amsa sunansa gida ko a kasar ba duk gida ba,ko ina ya tsaru wani handsome na hango narke a 3seater yana latsa wata dankareriyar iPad ga wata computer new design itama iPad a gefe yana ta aiki ciki hade da danna waya,tun daga yatsunsa nasan kudi da Hutu hade da jin dadi sun ratsashi,don guy karshene wajen haduwa da kyau  OMAR MOHD OMAR kenan dan kimanin 35yrs sunan kakansa yaci.Baban sa mohd  Omar  Ibrahim shahararren dan boko ne kuma dan kasuwa kuma dan siyasa,shi kadai tilo iyayensa suka Haifa kafin rasuwarsu,yan asalin jahar gombe ne,fulanin gombe,babansa ya tsaya masa yayi karatu kafin rasuwarsa,yanzu kam mohd Omar sai yan uwa da suke gombe kawai suka rage masa,yana musu alheri da ziyartarsu, dattijon kirki yayi aikin gomnati kala kala,ya rike mukamai da dama ta fannin siyasa,yayi mulkin siyasa state rep sau daya,house of rep a abuja har sau uku,senator sau daya,ya rike minister sau 2,yanzu haka ambassador ne na Nigeria a Russia.ga kamfanoni da yawa,harkar business iri iri,ya Tara dukiya kadarori barkatai,a takaice dai hamshakin me kudine na gasken gaske dake zaune a abuja birnin tarayya.yana da mata biyu hajia amina itace uwar gida tana da yara uku dan Allah bai bata haihuwa da yawa ba,Omar shine na farko,sai abdullah dan 18yrs sai autarta suleim yar9yrs.matarsa ta biyu hajia rahina yaranta duk matane guda 5 sadiya 27yrs,Aisha 25yrs,zainab 23yrs,naja 21yrs sajida 15yrs autarta.hajiya amina yar kauyen gombe ce,dan haka batayi karatu ba iyakacinta secondary shima bayan mohd Omar ibrahim ya aureta ya sata tayi.ita bata aiki bata zuwa ko ina ta rike yaranta ta basu tarbiya tare da mijinta,


Rahina kuwa da yaranta uku manya duk suna aikin gomnati sunyi degree,kullum sai iyayi a hau mota fuuuuuuu ko wacce ta tafi aiki,in salary yazo ai ta gasa da juna. Baffa yayi yayi su fito da miji tunda sunyi degree amma sunki,shi yasa gidan ya Tara mata rida rida.gashi na bangaren amina sune sukafi kowa kyau,musamman Omar,shi yasa suka kara tsanarshi.


        Basa zaman lfy ko kadan, dan hajiya rahina bata kaunar hajia amina da yaranta,dan amina tana da maza ita bata dasu,ganinta zata fita cin gado,gashi alhaji mohd yafi son amina da yaranta musamman Omar,da wannan yasa rahina dagewa lallai yaranta mata baza suyi aure ba sai ko wacce tayi degree tana aikin gomnati,suma yaran nata a akidar haka suks taso kuma halinta kaf suka dauko,ga karya,rashin mutunci da nuna su wasu ne,a junansu ma basa zama lfy,daga munafunci sai fada a titi,sai gasa da junansu ko wacce naso taga tafi kowa,gasu da bin malamai uwarsu ta dorasu,ita kuwa Allah sarki haj amina mutuniyar kirki ce mace ta gari,abin duniya bai dameta ba,ga hakuri da addini.addua kawai take zabgawa kanta da yaranta musamman Omar dan sunfi kishinsa,shi kam Sam baya shiga harkar kowannensu sai iya nasu dan yaga kannen nasa ba tarbiya.


     Kyakyawa ne na karshe ko shi yayi Kansa iya yanda zaiyi kenan,omar fari ne amma ba kal ba,dan baza ace masa chocolate ba dan ya wuce yakai fari za a kirashi,dogone amma ba zankaleleba dai dai,ba ramamme ba kuma ba me kiba ba,a tsakiya yake da kirjinsa me fadi normal,hancinsa me kyau da tsari kuma baiyi tsini can da yawa ba,gashin kansa Wanda ya tarashi luf dashi baki ga santsi da laushi kamar na India,girarsa me yawa ga kyau,idanu dara dara farare kal,habarsa me dan tsayi,bakinsa das dan daidai lips dinsa su ba pink ba amma kamar light pink.baza Ku sha mamaki ba readers sai danaga yayi daria kusan sumewa zakuyi yanda hakoransa suke yar yar farare kal kal,ga wani dimple nasa,skin dinsa sumul luwai sai taushi laushi da sheki,tana sulbi,kafarsa da yatsu hannayensa duk abin kallo ne da birgewa,cinyarsa da kaurinsa gashi kwance masu kyau,kirjinsa kuwa da sauran jikinsa das suke ba komai luwai luwai.duk inda kuke kallon da tunanin kyau na Omar ya wuce nan.kowa sai ya kalleshi,hattana fararen fata dake London yaba masa sukeyi wajen tsaruwa da kyau,


    Ta bangaren halaye kuwa Omar kusan 95% yake,baya shan komai,baya ko saurarar mata duk yanda suke rubibinshi, yama tsani yan mata shi,basa gabansa,baya shiga harkar kowa,bai damu da matsalar wani ba,sai in ka nemi taimako wajensa zai baka,matsalarsa akwai zucia da saurin fushi,ga girman kai,da rashin fara'a dan baya daria ba komai ke sashi murmushi ba.yana da tausayi in yaganka cikin masifa amma shi baya shiga rayuwar wani bare ya kai masa agaji sai ka nema zai maka,baya son surutu da hayaniya.yayi karatunsa na degree a London ya karanta economics,yanzu yayi masters tuni.bangaren addini kuwa ba a cewa komai yana da haddar ya kai izu 40,banda sauran wasu littafai na addini daya haddace,kuma ba laifi yana aiki da ilminsa,yana kuma addini sosai,baffa ne ya matsa masa kan lallai sai yayi aure,yana 30yrs ya nemo masa auren yar gidan wani governor wato sahar,yar boko ce itama dan medicine ta karanta tana aiki a wani babban hospital dake abj,tana da private nata guda biyu..


   Sahar kyakyawace ba laifi chocolate ce amma tsabar body cream ta dawo fara tas,ga daukan wanka ammafa in zataje aiki.bata ganin kowa da mutunci ganin tana juya naira,motocinta 4 laba laba,duk ma'aikantan gidansu tsoronta sukeyi,sabo da cin mutunci,bata da tarbiya,ba kamun kai,dan a wurin aiki har tafawa take da maza,give me five saleem bam kaji sun kashe.


Haka maza suyi ta yaban kyanta da turarenta gaskia kin hadu,mijinki ya more,tayi ta zancen batsa da mazan aiki.wasu kamilallun matan ma'aikata sunsha bata shawara amma taci musu mutunci,


   Tsiyar sahar bata tsaya nan ba har kan mijinta Omar bata ganinsa da gashi ko kadan,bai San mene aure ba,bai San dadinsa ba,bai San love ba bai tabayi ba,dama baffa ne ya lika masa dole,


     Sahar addini bai dameta ba,ita kawai kudi da aikin gomnati,ga kawaye marasa tarbiyya,a rana sai ta fita sau biyar kullum bata gida,da anyi magana tace aikinta.


Taki yarda ta haihu Sam tace ina bata shirya ba,bataso ta lalace,Omar ma sabo da kudinsu ta yarda ta aureshi,dan ita burinta kudi.Omar gajiya yayi da bakin cikin halinta ya tafi London ya huta,ita kuwa ko a jikinta,ya mata fada da nasiha taki ji,bata bari ya kusanceta sai in bukatarta ce,ko tana son karbar kudi wajensa,shi kuwa baya sonta bashi da feeling a kanta yanayi ne don sauke hakkin dake kansa,shi yasa ma yake tunanin anya yana da lafiya kuwa danshi bai taba jin sha'awar matarsa ba Sam,mata kuma ko inda suke baya kalla bare ya gano matsalarsa.



    Amma babban abokinsa sultan yace dan baya son matarsa ne shi yasa,duk ranar daya hadu da real love dinsa zatayi busting dinsa sanannan zai tabbatar lfy yake.Omar kuwa gani yakeyi karyane kawai.yaki yarda kwata kwata,yaje hospital da dama a turai sunce lfy lau yake. Wannan kenan kadan daga the most handsome and sexy OMAR.



     Ku biyoni readers yanzu akafara Taku har kullum 


Asmahbaffa.

[5:06PM, 3/10/2018] ‪+234 808 522 6395‬: ⓂⓂⓂ

        MA'AIKACIYAR

            GOMNATI

             ⓂⓂⓂ


                    2


By

Asmabaffa



          Nigeria na dawo abuja garin da ake ji da naira.wajen gari na fita gidajen masu rangwamen gata,wanda suke kaiwa da kyar suna yar sana'a,da suke haya a wajen abuja Kafin a karasa cikin garin abuja,dai dai gefen titi na hango wata yarinya tana saida apple da dafaffen kwai,a titi take bi tana mikawa ta window na mota,apple and egg tana bi mota mota a round tana dagawa masu mota domin su siya,


Kallonta nayi sosai yarinya ce yar kimanin 15yrs ta hada gumi sakamakon ranar da ake zabgawa,sanye take da wata yar doguwar Riga ja da kadan ta wuce gwiwarta,rigar taji jiki ta kode ta jeme,ta fita daga hayyacinta da dankwalinta baki,amma kana kallon yarinyar fes da ita rigar kar kar ba dirty,da gani gidansu da tsabta,


       Yarinyar na kurawa ido na kasa dauke idona  sabo da tsananin kyau da tsarin sura na wannan yarinya,kerarriyar yarinyace me cikar zati,dan kana kallonta Kazan ta hada jinsi da larabawa basai an fada ma ba,da gani nan gaba za ayi mashahuriyar budurwa,duk motar data wuce sai ta kalleta wasu har tsayawa sukeyi suce suna sonta,


  Santala santalan kafafunta na kalla na jinjina kai,sama nayo naci karo da makeken hips dinta da tudun mazaune wasu das dasu,nan nace to fa yarinya karama kenan nan gaba fa za asha kallo,ina yin gaba naga idon garin wato boobs dinta suma dai basu girma ba kananu yanzu suke tasowa nan gaba suma uhmmm...wuyanta na kalla naga wasu yan digo digo baki sun kai biyar Wanda ake Kira tawadan Allah, wuyanta mul dashi kadan ake ganin kashi,


       Fuskarta na tafi sawa ido,bakin nan na hango light pink dan cut,lips masu matukar kyau,hakora kanana tas farare,hancinta na kalla me kyau da tsayi gami da tsini amma ba mai yawa ba,da digon baki dis a kan hancin Wanda ya kara kawata fuskarta,idanu dai dai ba manya ba ba kanana ba farare tas kamar madara,


    Gashin kanta Wanda yayi luf har gaban goshinta ga saje kadan yala yala baki sidik,bata da girman goshi lol,gashinta ta tubke jelarsa har ya wuce tsakiyar bayanta,


Sa idona bai tsaya nan ba readers sai Dana kai kallona wajen kunnenta kanana masu kyau,fara ce kar,rana da wahala ma yasa ta danyi duhu a hakan.tallanta kawai takeyi a titi bata sauraran kowa,wasu dan kyanta suke siya,wasu dan ta kulasu su sami damar lalata mata rayuwa,shi yasa bata kulasu sam,dan haka tana zuwa talla take siyarwa,


      Wata yar yarinya na gani baza ta wuce 9yrs ba me kama da me tallan apple da egg ita amma sai dai a kirata da light chocolate dan ba fara kar bace,hannun me saida apple ta kamo tana anty IKLAS kizo inji ummi tallan ya isa,wai yunwa mukeji ki dafa mana abinci,


   Hannun yarinyar iklas ta rike tana murmushi ok suhaila dama yanzu zan dawo gida,ya schl?normal anty,ance ban biya kudin books din da akace mu siya ba,ranar Friday za a rufe.


     Sorry baby akwai kudin zan baki gobe never mind,botikinta ta dauka dan tuni egg ya kare apple saura Leda biyu,gida suka wuce ita da kanwarta,nima na rufa musu baya,tafiya sukayi ba wani nisa da titi wani gida suka shiga Wanda zai iya zuwa na 3 a lalacewa kaf gidajen dake unguwar suna cikin mafi rangwamen gata.


      Gidane na bilon siminti amma kamar kango tsabar lalacewa,daki biyu ne,sai toilet Wanda rabin katangar toilet din na karfen langa langa ne,sai kitchen dinsu suma na langa langa ne,gidan ko ina da simintinsa a dabe yake,dakinsu kuwa duka ledar tsakar dakice kusan sabuwace ma,abin mamaki wani bed na gani na gaske kalar na kasar waje yasha katuwar katifa,ga wata spare katifa jingine a bango,gefe guda wasu kayan kitchen ne dana cin abinci na gaske masu tsada a katon kwali har biyu,gefe can wata sip ce itama kalar bed din da gani ansha wuya wajen shigarta dakin,rabin sip din kayan sawarsu rabi kuma suke boye kayan abincincinsu da sauran tarkace,Duk a daki daya,daya dakin kuwa Leda ce da center carpet me kyau kuma da gani me tsadar gaske ne,nayi mamaki,wasu kujeru na gani na alfarma 3 seater 2 seated da 1seater,da badan ginin marar kyau ba da palon yafi haka kyau,wata TV na gani katuwa me kyau kamar plasma tsarinta girke a kan wani glass TV stand,


     Gidan ko ina kal kal yake sai kamshin turaren wuta ke tashi,wata dattijuwa na hango a zaune tsakiyar tabarma tana fere doya,na kare mata kallo wannan sai dai a kirata kakarsu amma ba ummi ba da naji sun fada,jikinta suka zube wash ummi tsohuwa me ran karfe,mun gaji,ko wacce tana ta dakuna tsohuwa tace dalla Ku dagani zaku karasani,sai warin rana kuke,ke faratu tashi ki mana girki,kiyi wanka ki huta,gashi na rage miki hanya.na fere doya,na miki jajjage,to ummi na gode,bari nayi sallah tukun.


Sallah tayi ta shiga kitchen.faten doya ta yi musu sannan sukaci,wanka tayi ta shirya kanwarta suhaila ta rike hannunta sukawa ummi sallama ummi mun tafi islamiyya daga can zamuje kasuwa domin saro apple zamuje ma gidan gona siyo kwai sabo da siyarwa gobe,addua ta musu suka wuce.


      Wai wace IKLAS NE


      Babansu abdurrahman saddiq dan asalin kasar libiya ne,balaraben libiya a can wani kauye a yankinsu,ruwan sama aka musu mai matukar yawa Wanda ya haddasa ambaliyar ruwa a yankin,da kyar aka samu aka ceci mutane ba Sufi 10 ba,wasu kuma mutum biyar suka taimakawa Kansu da rakuminsu suka yo hanyar Nigeria,su kwana su tashi a sahara har Allah ya kawosu Nigeria,har suka sauka a jigawa state da rakumansu,maza ne su biyar,haka suke fadi tashi a kauyukan jigawa,ciki harda abdurrahman saddiq babansu iklas kenan,ana haka har mutum biyu suka rasu suka rage saura 3,sauran biyu suka koma libiyansu suka bar abdurrahman a Nigeria,yasha wuya yasha talauci a kauyuka,har ya fara Aron gona yana noma,da haka yaci gaba har ya fara samun kudi,ya mallaki gonaki, a wani kauye dake cikin roni nan ya hadu da abu bafulatana wato Babar su iklas,kishiyar babar abu ce ke gallaza mata kasancewar kafin Baban abu ya rasu sun rabu da babarta,shi yasa ya kwace yarsa abu ya bawa matarsa riko,


      Nan abdurrahman ya fada sonta ya tausaya mata,da haka ya dage saida aka aura masa abu,bayan aurensu arzikin abdurrahma ya shahara ga kauyen ana masa sharri dan mafiya,haka abu ta haifi iklas wacce sak babanta ta kwaso,daga nan ya kwashesu suka koma abuja da zama tare da Babar abu wato hajia asmau,wacce yanzu suke hannunta kenan,suke kiranta da ummi tun tasowarsu sukaji mamansu da abbansu suna kiranta ummi shi yasa suka saba suma.har yau suke ce mata ummi,


      Abdurrahman sai da ya mallaki gida a abuja ga har noma ta haka ya biya musu aikin hajji sannan ya ziyarci kasarsa ya nunawa matarsa yan uwansa maza guda biyu da suka rage a duniya,haka gaj asmai ummi kenan,duk ya hada musu hanyar da ko sabo da halin rayuwa zasu iya Neman yan uwansa,


      Bayan suhaila Nada shekara 7 da haihuwa abu maman su iklas da mijinta abdurrahman Baban su iklas suna hanyar dawowarsu daga jigawa zuwa abuja suka tafka hatsari inda Allah yayi musu rasuwa,dukansu,anyi jaje da jimami,yayinda kakarsu ummi ta kira yan uwansa ta sanar musu,har Nigeria sunzo,kuma sun bawa su iklas nasu gudunmuwar,dan suma ba yan uwansa na jini bane,dangi ne kawai sama sama shi yasa basu dauki su iklas ba suka koma kasarsu,


       Ummi kakarsu iklas ce taci gaba da kula dasu,tana sana'ar saida kayan miya,irin su citta,maggi,manja,wake,barkono etc,har abincinsu ya kare,kudin hannunsu ya kare,komai nasu ya kare kat hattana kudin makarantar su babu,lokacin iklas tana ss1,suhaila na primary 2,da haka suka yanke shawarar saida gidan da suke ciki,haka suka siyar da gidan Ganin matane yasa aka cucesu sosai aka siyi gidan arahar banza,


Da haka suka tashi suka koma wajen abuja gidajen dake kusa da garin abuja kafin a karasa cikin city,anan suka sayi wannan gidan da suke ciki,an musu tsada sosai anan kudin ya kusa karewa,shi yasa suka ebo wasu kayan na gidansu da suka siyar Wanda zasu iya amfani dasu suka zuba a gidan da suka siya,


Sun biyawa suhaila kudin makaranta tun daga primary 2 zuwa jss3 gudun kar a sami matsala,abinci suka jibge  komai da suke bukata sai da sukayi dai dai kudinsu,har da jarin kwai da apple,ita kuma ummi takeyin sana'ar siyar da kayan miyarta a gida,


     Islamiyya ma sun biya kudinta na shekaru,iklas ma an canja schl me saukin kudi,ta biya daga jss2 har zuwa ss3.ga saida apple da egg,tana dawowa daga schl zata wuce tallanta, zuwa 4 su tafi islamiyya,haka suke rayuwa har yanzu sun kwashe 2yrs.


    Yanzu komai ya dagule musu,da tallan da iklas ke zuwa da sana'ar kakarsu ummi suke ci suna sha,da sauran abubuwan rayuwa Wanda ya zama dole.


     Iklas bata da burin da ya wuce tayi karatu me zurfi tayi aikin gomnati dan ta tallafawa kanwarta da ummi,bata da burin da ya wuce tayi aikin goMnati,gashi aikin gomnati na burgeta, ita ko me aikin gomnati ta gani a titi to birgeta takeyi,ko ji tayi ma'aikata na labarin wajen aikinsu to sai ta tsaya ta saurara.


     In tana tuno aikin gomnati ita kadai zaka ga tana daria,idan kana so kaga dariarta ko jin dadinta to ka mata adduar Allah sa ki zama ma'aikaciyar gomnati ko ta company,dan haka duk layinsu in ta wuce ko abokanan tallanta zakaji ana gomnati gomnati wasu suce ma'aikaciya,arnan ko gwarawa da marasa jin Hausa da suka Santa sai kaji suna kiranta the manager.murmushi take musu sosai,


Indai kana so a nuna ma gidan su iklas to kace gidan su gomnati ko ma'aikaciya,ko gidansu  manager.


  Ya halayen iklas sukene



Asmabaffa

[5:06PM, 3/10/2018] ‪+234 808 522 6395‬: ⓂⓂⓂ

       MA'AIKACIYAR

            GOMNATI

             ⓂⓂⓂ


                    3


By

Asmabaffa




     Readers kar Ku gaji da hakuri da typing error sometimes ba time na editing.tnx




         IKLAS nutsatsiyar yarinya ce kamila,ga addini hankali da sanin ya kamata,ga kamun kai,tsabta da son kwalliya,bata so ace taci baya sai gashi talauci yasa ta zama sai a hankali,gata da kokari ita da suhaila,gaskia iyayensu sun iya tarbiya kuma Allah ya amsa adduarsu ya basu yara nutsatsu,ga yarda da kaddara,Sam basu dau duniya da zafi ba.


     Iklas bata da tsoro,tana da hakuri amma indai ka tsokaneta ko ka rainata to fa ba mutunci,bata kyalewa,gata tana da surutu amma ba me yawa ba,itama akwai zucia,gata da fara'a da mutunci da karrama dan Adam shi yasa kaf yankin da suke kowa ya Santa kuma ana sonta maza da mata,komai nata a nutse,ita sam bata son raini,Suhaila ita bata fiye son surutu da hayaniya ba. In dai kaje unguwar su iklas baka isa ka nunata da yatsa ba yanzu matasa yan unguwar zasu hada ma jini da majina,shi yasa suke zaune gidansu lfy.


      Ummi ma tana fitowa za kaga ana kwasar gaisuwa sabo da iklas ta siyo musu mutunci.wannan ne asalin da tarihin iklas .



          Ci gaban labari


      Baffan su Omar ne ya kirashi a waya,Omar na daga wayar baffa ya fara fada haba Omar kasan ina Russia na bar ma komai na business dina a hannunka ga iyalinka can na jiranka amma ka tare a London kaki dawowa,bayan Kaine babba wa zai kula da harkata in ba kai ba,kasan kannenka basu da hankalin da zan dorasu kan harkata,pls ka koma gida nan da 3days.cike da ladabi yace alright baffa insha'allah zan koma yanda kace,dadi baffa yaji that's my son,yana son Omar sosai.


     Omar kuwa nazari ya shiga yana tunanin yanda zai je ya hadu da mahaukaciyar matarsa wacce take bata masa kullum wato sahar.amma ba yanda zaiyi dole yabi umarnin baffansa ya koma Nigeria,


      Yana cikin wannan tunani sahar ta mako masa kira,tsaki yayi hade da daga wayar dan yasan kudi zata roka ko wani shirmen,ba ko gaisuwa kawai ya London tace sannan tace baby wlh kudin da ka bani sun kare kuma gashi za muyi bikin wata yar wajen aikin mu,


   A hankali yace yace OK zan miki transfer,yanzu ke sahar baza kiyi hankali ba,yanzu haka ake kula da miji.ganinki kinyi dai dai,tunda na bar gida ko kirana bakiyi ba,kiji tsoron Allah sahar,kiyi amfani da damarki kafin ta wuceki,kunkuni ta fara yanzu ya kake so na maka,kullum bani da time fa busy nake,kasan aikin mu ba daga kafa,ke kullum Aiki aiki baki da wani abu sai aikin gomnati.


      To ni kaga karka dameni dan ka samu na kiraka,da bukatarki ta taso ba,ae hakkinkane ai taja tsaki hade da kashe wayar.omar sarkin zucia har zucia ta kawoshi wuya,take idonsa ya canja,sai bacin rai da huci yakeyi.


       Mama ya kira a waya suka sha hira ta hadashi da kannensa suleim da abdullah sun sha labari.yau ne ranar da omar zai dira a Nigeria,karfe 4:30pm mama,suleim da abdullah suka dauko handsome daga airport,sai murna sukeyi cike da kasaita ya bisu suka wuce gidansu na alfarma.tunda yaran hajia rahina wato umma sukaji labarin saukar Omar suka fara gulmace gulmace,hassada da bakin ciki,ko wacce part dinta daban amma su umma wato rahina sun dami rayuwarsu sabo da mugun halinsu.


    Sadiya ce ta parker motarta kuuuuuuuu ta fito dawowarta daga wajen aiki kenan,direct part dinsu ta wuce,duka yan matan kannen nata da umma suna zaune suna gulma da zage zage,sadiya ma zama tayi dabar kasancewar ita ce ba,umma kice tsinanne ya dawo kasar,Aisha tace na tsani yaya omar wlh waishi dole me kyau,me kudi,umma tace duk Ku saurara shi din banza wlh sai nayi maganinsu gaba daya har uwar tasu,


      Zainab tace wlh umma karki daga musu kafa,naja tace har mu zai nunawa kudi aikin banza wai wannan sahar din matarsa har ta isa ta ganni tamin kallon banza,yanda take ji ita me kudi ce muma haka,domin aikin gomnati ne muma shi mukeyi,


      Sadiya tace hmmm umma zatayi maganin ogan nasu ai,haka suka kai har dare suna zage zage,a karshe suka yanke zasu je masa sannu da zuwa don sugano kwakwaf,


    Ita kuwa baiwar Allah mama tasa danta gaba yaci ya koshi dan tasan matarsa ba matar kirki bace,addua take Allah masa canjin alkhairi,amma ita kam wulakancin sahar ya isheta,nasiha ta masa sosai tare da Jan kunne wajen dagewa da addini,sannan ta turashi kan dole yaje ya gaida hajiya rahina umma,


Badan yaso ba bayan sallar isha ya isa part din,da zuwansa ya gansu a Palo rida rida a kwance ko wacce na latsa waya,umma na gefe,suna ganinsa dukkansu gabansu sai daya fadi dan mugun tsoronsa sukeyi,ga kwar jini da yake musu, Sam baya musu ko murmushi,dama duk zaginsu a bayan ido sukeyi,risunawa yayi ya gaida umma,da kyar ta amsa tana masa kallon harara,su kuwa yan matan kowacce yaya sannu da zuwa ka dawo lfy,lfy kawai yace ya ficewarsa cike da kasaita 

    Yana fita suka dasa gulmarsu kunga maye yanda ya kara kyau ga iya daukan wanka,ko wanne kaya yasa kyau suke masa.wurin mama ya wuce ya roketa kan ta barshi ya kwana gobe sai ya tafi gidansa,kyaleshi tayi dan tasan matarsa ba kula take dashi ba,


       Suleim tana manne a jikinsa sai bacci takeyi,washe gari da safe uban yan daukan wanka omar sakkowa yayi daga sama yana zuba kamshi,sanye yake da wani yadi fari Sol ya matukar masa kyau,hattana takalminsa fari ne,ba hula a kansa sai gashi kwance luf.sallama yawa mum bayan ya cika tumbinsa ya basu tsaraba,wucewa yayi gidansa dake zone 11princess suit,gidan ya tsaru,


     Driver ne ke tukashi har gidansa,tun daga compound yake jiyo hayaniya sama sama,a nutse ya shiga palon da sallama,frnds din sahar ya hango arna da musulmai maza da mata suna jin kida hade da hira,ga kayan ciye ciye nan,


    Ran omar ne yayi mugun baci suna masa magana amma ko kallon su baiyi ba ya wuce room dinsa,ita kuwa sahar baki ta tabe hade da Jan tsaki,


    Saida wata kawarta zuby tace sahar kije wajen mijinki kinga kamar ransa ya baci,tsaki sahar ta ja to sai me yanzu akansa zaku tafi haba mana frnds,next time zamu dawo yanzu kije wajen mijinki cewar wani saleem abokin aikinsu,bata so ba suka tafi ,yar aikinta ta bugawa tsawa kan tazo ta gyara wajen,direct dakin Omar ta nufa tana cika tana batsewa,sanye sahar take da T-shirt baka da skert din atamfa sun kamata kam,kanta ko dan kwali babu,


     Tana shiga ta ganshi kwance kan gado yana latsa waya,baki ta turo ta kare masa kallo gaskia mijinta me kyau ne,ga iya wanka,a nan take sha'awar Omar ta motsa mata ba abinda takeso sama da ya biyaa mata bukatarta,gashi tasan fushi yake yi yanzu bare ya mata abinda take so,


       A gefen gadon ta zauna sannu da zuwa baby ya hanya?tunda yaji haka yasan tabbas sahar wani abun take so ya mata,dan bata aikin banza sai da dalili,ko kallonta baiyi ba,sha'awace ta kuma lullubeta tace baby kayi hakuri nasan na ma laifi,kallonta Omar yayi tabbas yasan da dalili,sahar baza ta taba bashi hakuri ba tare da kudirin wani abu ba,a hankali yace ya wuce,in mutum yayi da kyau shima ya sani in ya bata ma ya sani,kisani ke baki isa ki sani bacin rai ba,Wanda ka damu dashi shi ne in ya bata ma rai kake damua,sahar taji haushin kalamansa amma sabo da tana neman wani abu tayi shuru ta kara cewa am sorry hade da hayewa kan bed din,yana kallonta  ya gano me take nema,sha'awa ya hango zalla a idonta,kwancia tayi a kirjinsa,dan sahar ita bata da kunya ko kadan.


       Shafashi ta fara tana wani shagwaba,babyna I missed u alot,tabe baki yayi yana kallonta ta fara cire masa Riga,baya son ya wulakantata,kuma yasan hakkinta a kansa musamman da ya tafi London ya Dade bai dawo ba,sabo da wannan  dalilin ya biye mata yayi manage ya biyamata bukatarta,sahar tana jinta zam zam dan Omar gwarzon maza ne ya tsaya ya biya mata bukatarta sosai taji dadi har jinjina iya sex na Omar takeyi,guy ya hadu ta fannin romance da sex,ni kuwa nace danma ba zabinsa bace ke,bashi da feeling akanki.


      Sahar tana jin zam zam ta mike tayi ficewarta,shi kuwa Omar baiji wani dadinta da yawa ba dan sahar ko dan gyaran da mata keyi na shan tsumi bata yi Sam,ita fa indai ba aikin gomnati ba to bata ganewa komai.washe gari Omar ya shirya tsab cikin suit baka yayi kyau yana baza kamshi ya sakko cike da takama da kasaita,dakin sahar ya shiga tunda ya tashi bai ganta a bed dinsa ba,room dinta ma wayam bata nan,Palo ya zo ba kowa sai hindatu me aikinta,ina sahar take cewar Omar,har kasa hindatu ta duka ta gaisheshi da sakin fuska ya amsa,yanlabai ta tafi wajen aiki tun 6am wai tana da tiyata,


   Tsaki yaja ya fice gaba daya daga gidan ko dining bai kalla ba,yana mamakin yanda sahar ta rainashi ace matarka ta fita ko fada ma baza tayi ba,tsaki yaja hade da ci gaba da karanta jaridarsa yayinda ya kame a bayan wata luntsumemiyar motarsa Wanda takai milyan 40,driver ke gaba yana tukashi,shi Omar Sam bai damu da driving ba yafi so a tukashi kaji manya fa readers.


    Hadadden gidansu yace a kaishi direct wajen mama ya nufa,a Palo ya sameta tana turaren wuta rungumeta yayi hade da gaisar da ita,mama kintashi lfy?lfy babanmu ya gida,great mama,to alhmdllh.mama breakfast fa?juyowa tayi da alamar tambaya gidanka ba a baka ba,wlh mama kin San dai komai,yan aiki keyi ni kuma kin San bana son kazanta,kuma yau mama inaso naje na duba gidan gonarki da kike kiwon kaji,kinga an Dade ba a duba ma'aikatanba da sauran abubuwa,murmushi tayi yawwa babana Allah maka albarka,da har na yanke shawarar zuwa da kaina,haba mama da raina da lafiyata na barki ki wahala.to Allah maka albarka.su abdallah suna schl ae ai ka sani.OK.


     Haj amina tana da shahararren gidan kiwon kaji dake wajen garin abuja,baffan su Omar ne ya gina mata ya bata kyauta ganin haj rahina na aikin gomnati shi yasa ya bata wannan kyauta.

Haj rahina umma ta tafka bala'i akan wannan kyautar ta baffa,haka ta hakura.


    abinci yaci ya koshi yawa mama sallama ya wuce office,karfe 2pm ya bar office ya wuce gidan kajin mama.


   Asmabaffa

[5:06PM, 3/10/2018] ‪+234 808 522 6395‬: ⓂⓂⓂ

      MA'AIKACIYAR

           GOMNATI

            ⓂⓂⓂ


                   4


By

Asmabaffa



      1:30pm iklas ta shigo gida ta dawo daga tallanta,domin schl din da ta koma 8to12 ce ta irin manyan mutane ce Wanda basuyi karatu da wuri ba,irinta ta koma sabo da tallan da take zuwa domin da shi suka dogara,dan haka 12 tana dawowa zata tafi talla kan titin kwalta,1-1:30pm ta dawo,tana cin abinci zata shirya ta tafi saro apple da egg,tana dawowa sannan suhaila ta dawo sai su shirya su tafi islamiyya,Saturday Sunday kuwa da safe take zuwa talla zuwa 3 to 4pm ta dawo,haka take rayuwa kullum ba Hutu,gashi watarana har girkin gida ummi take sata dan bata so iklas tayi aure bata iya girki da sauran ayyuka ba,dan haka take sata dole,shi yasa ta iya komai dama gata jaruma,


     Wanka tayi ta shirya cikin wata yar rigarta doguwa itama wata Igbo ce ta bata ita,light blue ce me ratsin ja ja da digo digon baki,daga sama ta dan matseta kasa ta bude amma itama da kadan ta wuce gwiwarta,basu da kayan kirki,dan ma waiyayenamure na taimakawa su basu kayan da suka musu kadan,wasu kuma har sabo suke basu,ita ma suhaila tana samun na yaransu,wasu kuma iklas na kokarin sai musu gwanjo,shi yasa kusan kayansu gaba daya English wears ne,tsangalallu ne badan suna sa dankwali ba sai ka dauka arnane suma saboda rashin wadata.to daya suke samun na ci ma.


     Bakin gyale siriri ta yana kanta,batayi kwalliya ba powder ta shafa kawai sai Vaseline da ta shafa a lips dinta,tayi kyau dama me kyau ko ba kwalliya me kyau ne,wani takalmin roba me igiya baki ta saka,shima wani ne da yake siyarwa ya bata kyautarsa yaga tana da hankali,ga babu ta zauna musu.tayi kyau sosai a nutse ta dauki botikin saro kwai da ledar siyo apple ta yiwa ummi sallama ta wuce,a kofar gida suka hadu da suhaila ta dawo daga schl,anty har kin shirya?yeah iklas ki jirani muje tare mana,no je kici abinci ki huta ki shirya zuwa islamiyya kafin na dawo OK.OK anty sai kin dawo,Allah tsare shafa kanta tayi ameen suhaila,tana matukar kaunar kanwarta.


      Tafiya tayi da dan nisa ta isa gidan kaji domin siyo kwai da apple,mutane da motoci birjik sunzo sarin kwai da apple suma,gaskia kowa ya kalli gidan gonar yasan an kashe dukiya,part part ne wurin kaji da kwai daban,part din fruits daban,kifi daban,ga sauran tsuntsaye da abubuwa kala kala.


    Da araha suke bada sarin shi yasa ake cika gidan gonar,shi yasa iklas ke saro nata can dan ba karamin riba take ci ba,ratsa ciki tayi ta shige,ma'aikatan ciki sai fara'a suke mata suna gaisawa,dan sun saba da ita,gashi sun karanci nutsatsiya ce me mutunci da kamin kai,suna tausaya mata mace kamar ta tana sa'a irin wannan,da gani suna cikin talauci,shi yasa suke Mata arha fiye da kowa.


          Tana tsaye tana jiran a sallami Wanda suka rigata, wata arniyar mota ta shigo cikin wurin,kowa bin motar yake da kallo,babu Wanda ya taba ganin kalar motar,har jira ake aga waye me motar,


    Ita kanta iklas duk tsaiwarta a titi bata taba ganin mota irin wannan ba,su kuwa ma'aikatan gidan sun San bazai wuce Omar ko mama ba.sun San irin wannan babbar harka sai iyayen gidansu Wanda suke jin dadin aiki karkashinsu,shi kuwa Omar tun shigowarsu kansa na kasa yana duba jarida,driver ne ya fito da sauri ya bude masa kofa,subhanallah shine abinda iklas ta furta a ranta ganin takalmi da kafafuwan Wanda ke fitowa,


     Basu gama sumewa ba sai da Omar ya fito gaba dayansa daga mota,wani daddadan kamshi ne ya mamayesu gaba daya,iklas tana kallonsa gabanta ya fadi ji kake daram dam,sunga zallar baiwar kyau da kwarjini da cikar zati,iklas tace tab yau ga Wanda ya takeni a kyau,ido ta lumshe hade da bude kafafen hanci tana shakar ni'imantaccen kamshin Omar, shi kuwa Omar iklas ya fara hangowa da tsangalalliyar rigarta,kasancewar fara ce kar sai ta haske gidan. Gonar gaba daya,kallo daya ya watsa mata shima gabansa yayi mugun bugawa,bai taba ganin dan Adam me kyanta ba,duk kyansa sai yaga ga wata yarinya ta fishi,shi bai taba jin faduwar gaba ba sai akan wannan tatsitsiyar yarinya,


     Fuska ya yatsina kamar yaga kashi yayi mata kallon kaskanci ya wuce ta gabanta,da mutanen wajen maza ya gaisa ya mika musu hannu,sannan suka dan kebe da babban me kula da wajen suna magana.


   Iklas kuwa ta cika fam sabo da irin kallon banzan da ya mata,bata son raini,dan suna talakawa shine zai yatsina mata fuska,hmm duniyace a ranta take wannan magana,ana haka har akazo wajenta aka cika mata botikinta ta mika kudi,lokacin Omar ya gama da wajen kwai ya wuce wajen fruits,da kyar take daga bokitin ta karasa wajen fruits itama ta mika kudi aka cika mata katuwar ledarta da apple,ta juya zata wuce sukayi karo da  da botikin kwanta tayi karo da mutum gwaraf,amma batafi saman cikinsa ba,botikin kwai ya tuntsire wajen guda ashirin sun fashe,shi kuwa take yaji wani mugun shock a jikinsa zirrrrrrrrrrr wanda bai taba ji ba,sakamakon haduwar jikinsu,daurewa yayi ya dawo hankalinsa,tsaki yaja ya furta psycho kawai,haushi ta karaji ya mata abu maimakon hakuri sai zagi,ledar hannunta ta apple ta ajiye gefe,gabansa ta sha ta rike kugu hade da harara,malam kamin laifi da barna ka kasa bani hakuri sannan ka zageni,da nayi niyyar yafe ma amma wlh tunda ka zageni ka kasa bani hakuri to ba kira ba abinda zaici gawayi,sai ka biyani each and every egg da ya fashe,dan akanka bazan dauki asaraba,


      Daria yace ta kamashi ya danneta,bai taba haduwa da funny girl haka ba sai yau,yar yarinya da Karin magana haka,ga masifa har wani jijjiga takeyi gaban katon namiji kamarsa.


      Allah ya taimakesu ba wasu mutane wurin sai masu shirya fruits,tasowa sukayi daya daga ciki yace haba gomnati basai kinyi fada ba za a biyaki,shine me wajen,a fusace tace dama haushinsa nakeji ni time din daya shigo yamin kallon Tara saura kwata,dan haka wlh sai ya biyani,tofa wannan yarinya da kuruciya sosai kanta ga tsiwa cewar Omar aransa. Wasu ma'aikatanne suka zo wajen suna haba gomnati ikon allah bamu sanki da haka ba,wani ciki yace the manager wannan oganmune fa,murmushi ta saki jin an kirata da sunan da tafi  so wato gomnati, Wanda ya tafi da imanin Omar, tace to na yafe masa sabo da Ku


      Gefe ta matsa tana gyara bokitin kwanta hade da kunkuni kawai an cuci mutum,wannan days fashe ni haushina ma daya asararsa da akayi,yanzu wannan ya ishemu mu soya muci da su ummi har na 5days,ko mu soya doya da kwai ta kwana biyu,ai kuwa da munci dadinmu.duk surutun nan da takeyi Omar na jinta,sai daria yakeyi a zuciyarsa,yarinyar so funny,ya dade rabon da yayi nishadi irin na yau,kwai aka kawo mata guda 100 a Leda,kallon mutumin tayi laaaa ai nace na yafe masa wlh,ai oga ne yace a baki gashi guda 100 ma aka baki kinci riba...no na yafe ai,fafur iklas taki karban kwan nan,,sunyi sunyi taki karba,Omar ne ya karba hade da daka mata tsawa karba ban son shirme,tsoro ne ya kamata,taf aka cika botikinta da kwai,aka kara mata apples da yawa sannan aka mika mata kudinta,mamaki tayi sosai ta kalli Omar a tsorace na gode oga Allah kara arziki,sosai yaji dadin adduar ta matarsa bata taba masa ba,sai wata a titi,it's OK zaki iya tafiya, uhm....uhm.....dama oga dazu kaga fadan Dana ma,nayi ta masifa rainane ya baci kanwata na aika taki zuwa,shine raina ya baci,amma maganar gaskia bada kai nake ba,da kanwata nake.


    Murmushi Omar yayi Wanda yasa iklas sandarewa ganin kyau da dimple na Omar,shi kuwa a ransa yace yarinyar nan da wayo take.a fili hade rai yayi ya tabe mata baki ya shige mota driver ya ja suka wuce.itakam taji haushin tabe mata baki da yayi,ya rainata.anyway sun sami kudin abinci lallai yau tazo a SA'A.


     Yau taga lailatulqadari sunan da ta lakabawa Omar kenan kayanta ta dauka da kyar ta nemi taxi,kayan sun mata nauyi,ga murna an vata komai kyauta,shi yasa yau ta shiga taxi,ta matsu ta koma gida ta bawa kaka ummi labari.



Asmabaffa

[11:56AM, 3/11/2018] ‪+234 803 630 0627‬: ⓂⓂⓂ

     MA'AIKACIYAR 

          GOMNATI

           ⓂⓂⓂ


                  5


By

Asmabaffa



   

         Har kofar gida me taxi ya sauketa da kayanta,da sauri ta shiga da kayan ta fara kwalawa ummi kira tsohuwa kaka ummi...ummi...tsohuwa wai kina ina haka,ke lfy kike rafka min kira haka kamar kina bina bashi cewar kaka ummi,iklas ce ta rungume ummi tana ummi lailatul kadari na gani yau,kinga yau komai kyauta aka bani kwai da apples ummi sai nayi 1wk banje sari ba,duk na kyauta zan siyar,kinga kudin yanzu zamu tafi kasuwa dama abincin mu saura na kwana daya,


      Kaka ummi ce ta kalleta da murmushi tana mai cike da farin cikin kalaman iklas,to iklas wai waye lailatul kadari naga ta kaina yar nan karfa kiyi mana sabo,ummi oga ne me gidan kajin ya bani komai kyauta,nan ta kwashe labari ta fadawa ummi,ummi taji matukar farin ciki,dama basu da abinci ba kudi,


To alhmdllh iklas kece wacce ta iya tsari da lissafi sai muyi shawara,ai ummi yau baza mu islamiyya ba,dan kasuwa zamuje da suhaila,Biro da jotter ta dauko suka zauna a tabarma nan iklas ta fara planning,dama iklas akwai iya planning din rayuwa,nan ta rubuta abubuwan da suke bukata ta tsara komai,ta bawa ummi na cefane taja hannun suhaila suka wuce kasuwa.


     Omar direct gidansu ya wuce wajen mama,cike yake da tunanin yarinyar da yaji ana kira da gomnati ko manager sunan ne ya bashi daria,ya kara nanatawa a ransa bai San sanda ya saki murmushi ba,nan take ya shiga tunanin yanda take masa tsiwa a gidan gona,a haka ya karasa palon mama


    Zaune ya sameta suleim na gefenta suna game ita da abdallah,sallama ya musu ya kwanta Shana Shana cinyar mama yana shagwaba sai shafa masa gashi mama keyi tana wani lallabashi,dining ta jashi ta zaunar dashi,da kanta take bashi a baki har ya koshi,


      Mama sosai take tausayin dan nata sabo da yanda tasan halin matarsa bata da hali.adduarta kullum Allah masa chanjin alkhairi.Omar yayi aure amma kullum a gidansu yake rayuwarsa,kullum babu Wanda zaice ya taba aure,Rabin kayan sawarsa gaba daya  yana room dinsa a part dinsa bangaren mama.bashi da banbanci da gwauro.mama kuwa bata hanashi.


   Direct room dinsa ya wuce,wanka yayi hade da sallah ya kwanta sai bacci.iklas kuwa Niki Niki suka shigo gida dauke da kayan abinci dai dai kudinsu.ummi ta kawo musu farar shinkafa da miya hade da salat harda kifi,dan iklas duk talaucinsu bata yarda aci fara da yaji ba sai in suna sha'awa ko da dalili,dan gaskia tana da son cin dadi,ita ta yarda su rasa komai suci abinci me kyau,tunda suna Sana'a kuma suna samu ba laifi shi yasa take musu cefane me kyau na talaka.Rabin rayuwar gidan kaf a hannun iklas take


    Wanka sukayi suka zauna hira kafin magrib ta karasa,bayan sunyi sallar isha iklas ta shiga kitchen ta dafa musu indomie da dankalin turawa harda kifi,a baki ta bawa suhaila taci ta koshi,sannan suka ebo littatafansu sukayi karatu,nafila sukayi sannan suka haye gadonsu suka kwanta,kaka ummi kuwa dama a katifa take kwana,wai gadon ji takeyi tayi sama dogogo.suhaila da iklas a katon gadonsu,

 

     Haj rahina tana ta kulle kullen mugunta kawarta na hango suna zuba hirar mugunta a zaune a palon umma,ita da babbar kawarta hajiya  binta suna shirya tuggun da zasu kullawa Omar da mama,rahina tace binta ko wajen bokaye zan je ne?daria binta tayi tace share bokaye watarana aikin baya ci,kin San munafukar akwai addua,mufa mata ne ba irin tuggun da baza mu iya kulla musu ba Wanda zai jefa su cikin wani hali,ke in ta kama har gidan nan sai sun bari,tsabar iya tuggu da sharrinmu,haba rahina kin manta mu ne, tun muna yara kin San tsiyarmu.daria da shewa sukayi hade da tafawa, su sadiya yaran rahina sunaji sai murna suma sukeyi suna tafawa,dasu ake shirya komai.sai kara zugasu sukeyi,


Iyaye da dama na kuskure manya manya duk wani gulma,munafunci hassada sai a dingayi gaban yara,ana daria kaga wasu har tafawa sukeyi da yaransu mata ana cin naman wasu,duk iyaye masu haka su sani suna gurbata tarbiyyar yaransu,da haka zasu taso suma sunayi,kuma uwa ko yaushe batawa yaranta fada,tana wasa da daria ko yaushe da yara baza su taba jin maganarta ba,rainata zasuyi,ba a hana hira wasa da Jan yara a jiki ba amma a dinga sanin kalar Wanda za ayi,kuma wasa ba ko yaushe ba,shi yasa za kaga yara na dakawa uwarsu tsawa,ta sasu abu sukiyi, suma fada mata direct baza suyi ba,sai kaga idan ubane an masa da wuri a na rawar jiki,da yace a bari an bari,ba raini,amma mu iyaye mata mu ke zubar da kimarmu gaban yaranmu,matsala iri iri,Allah sa mu gyara.


    Omar na hango yana tafiyarsa ta takama sanye da wani blue jean pencil da red din Riga me dogon hannu,wandon irin an dan farfasashi daga gwiwa zuwa cinya,amma ba me yaga ba dan ba a ganin jikinsa,driver ne da sauri ya bude masa wata sabuwar arniyar farar mota,yana yin ribas motar sahar ta cinno kai gidan,tsadajjen gogon hannunsa ya kalla yaga almost 5pm,kawayenta ya hango biyu a cikin motar.horn ta masa hade da daga masa hannu,haushi ne ya kamashi, wurin 2days baya ganin sahar sai yau,ko yaushe tace duty dare ne da ita,kwana takeyi a hospital,yanzu kuma da rana yawo da kawaye da shirme a gari aikinta kenan.sai shewa sukeyi da frnds,wurin babban abokinsa sultan ya wuce,sultan doctor ne babba shekarunsu daya tare sukayi schl a london,har secondary,sultan babansa ya rasu daga shi sai mamansa,sun gaji dukiya ta gaske shi da mamansa,sultan baiyi aure ba amma an kai kudin aurensa gidan wata yar beauty dinsa yasmin,a asibitinsa ya sameshi zaune a office,hannu ya mika suka tafa sultan yace shegen kaya ya kk,ka dawo amma sau daya ka nemeni,omar yace bari Frnd kasan office ba Hutu,baffa ya hadani da aiki,oh na zata amarya sahar ce ta boye min kai,kana can kana Jan kaya,tsaki omar yaja kaifa dan iskane sultan,kasan komai tsakanina da ita kana min tsiya,Allah kyauta cewar sultan,kaga malam gobe around 1pm zaka rakani wani company na baffa zan duba aikin da akeyi,kasan da nisa fa sai an bar garin abuja.


    Allah kaimu cewar sultan.wai Frnd har yau baka samu wacce kake so bane,tsaki omar yaja karka dameni malam.daria sultan yayi yana ci gaba da tsokanarsa.


      Washe gari kamar kullum 1pm tana titin kwalta sai bin motoci takeyi a round tana daga apple da kwanta a ledoji ,ga yayyafi anayi ruwa ya jiketa da dangalalliyar rigarta wacce taje gidan kaji da ita,duk ruwan sama ya jikata kayan sun kara dameta a jikinta,sai boobs dinta kana kana duk sunyi caro caro,hips ya fido,gashinta ya kara kwantowa a goshinta sai digar ruwa sukeyi,


     Omar da sultan suna bayan mota a lafke driver na jansu,suka kawo dai dai danjar da iklas take,suna tsayawa ta karaso wurin motar tasu ga iska ta taso haka take daga musu,ido hudu sukayi da Omar wata uwar zabura yayi hade da nunata da yatsa yace you? Bata jin me yace saboda glass din motar a zuge yake,amma ta karanta lips dinsa ta gane me yace,murmushi tayi me kayatarwa ta daga masa hannu,itama tace oga da karfi,yaji abinda tace ai bai San sanda ya saki murmushi ba,yawa driver umarnin zuge glass kasa,kallonta yayi yanda iska ke daukanta,gashi ta falle mata gyalen da ke kanta gashi yaraf har kusan duwawunta,iska na kadashi sai ta kara kyau,driver yawa umarnin karbar apple da egg din hannunta,dubu biyar yawa driver umarnin mika mata,yana bata ta karba ta duba,hangame baki tayi ta dauki dubu daya,dama  shine kudin apple dinta da egg da suka karba,ta mikawa driver sauran,da sauri omar ya kalleta yace karba nakine na baki,daria tayi ta glass ta girgiza kai tace tnx oga amma bazan karba ba.lips dinta ya karanta ya gane me take nufi,hannu ta daga masa ta juya cikin nutsuwa ta dauko dan gyalenta ta wuce,omar kasa dauke idonsa yayi daga kanta,sultan kuwa tuni yayi suman zaune yana kallo da mamakin abokinsa tare da jinjina kyau irin na iklas.


    Danja taba da hannu amma omar sai waiwaye da kallon iklas yake,yanda take kai kawo a tsakiyar titi,yarinya irin wannan amma tana wannan sa'ar.take yaji ransa ya baci tausayinta ya mamaye zuciarsa, yar waye wannan aka barta tana garari a titi,tana da kuruciya haka,musulma.


Asmabaffa

[9:45PM, 3/21/2018] ‪+234 803 592 9495‬: ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR 

         GOMNATI

          ⓂⓂⓂ


                6


By

Asmabaffa




      Tsaki omar yaja,a ransa yana gaskia an cuci yarinyar nan.sultan Wanda mamaki ya kasheshi shi yayi karfin halin taba kafadar omar frnd ,juyowa omar yayi lfy malam karfa ka takuramin,murmushi sultan yayi yace iyye Ashe kayi sabon kamu frnd wannan zukekiyar fa gaskia tana da kyau,amma ka bani mamaki omar duk matan  turai da yawon da kayi a duniya ban taba ganin ka kalli mace da idon rahma ba,amma gashi akan yar yarinya me talla a titi gaba daya ka haukace ka fita a hankalinka,harara omar ya balla masa,kaga halinka ko sultan,me zanyi da wannan yarinyar,tsaya malam nifa ka gama kasheni da mamaki omar kai da baka shiga shirgin wani bare har ka taimaka masa ba tare da ya nema wajenka ba,hasali ko mu maza sai mu Dade bamu ga murmushinka ba sai gashi karamar yarinya tatsitsiya kakewa murmushi haka har hakora su fito,ka bata kyautar kudi bata nema ba,tana kin karba kana tursasa ta kan ta karba,,harda siyan abun titi kai da baka cin abun kan hanya.


    Sultan wai pls mene haka what is ur problem kasan me ya hadani da ita,za kazo kana wani talk na shirme,yarinya karama zanso,me zanyi da wannan me talla a titi,tallan ma mafi muni,tausayinta naji shi yasa.


   Sultan ne ya kwashe da daria mai da wukar amma wlh wannan yarinyar ka fara sonta ko kaki ko kaso.da karfi omar yace God for bit,over my death body.daria sultan yayi ya leka fuskar omar inye anyi budurwa me kyau,gaskia ka iya zabe,dama omar ka iya murmushi haka me kyau,nima naci albarkacin new catch dinka na gani yau,tsaki omar yaja sai kayi ai.


    Driver na jinsu shima ya yarda da zancen sultan,minti kadan za kaga sultan nawa omar daria sai dayaga omar yakai wuya wajen bacin rai ya ja bakinsa ya tsuke,dan yasan halin omar kwai zucia da zafin rai,sultan ne yace idi driver miko mana apple da kwan nan muci girkin amarya,omar ko kallonsu baiyi ba,ana miko kwan da apple omar ya fisge a hannun sultan,baka isa kaci abun nan ba sultan,


    Daria sultan yayi au na manta hannun amarya ya taba abun kana kishi kar mu rigaka ci.shi dai omar shuru ya musu,har sukaje suka gama abinda zasuyi omar na fushi da sultan,a hanyarsu ta dawowa omar sai zare ido yakeyi ko zai hango iklas bai ganta ba.


    Sultan ne ya kalleshi ya kara kwashewa da daria am sorry Frnd ban San dariar zata fito ba,amaryar ta tafi gida ka daina waige waige,tsaki omar yaja ya dauki apple daya cikin Wanda ya siya wurin iklas glass ya sauke ya zura hannunsa ta window ya wanke apple dinsa fes da ruwa ya kama cin apple dinsa ji kake baras,har wani lumshe ido yakeyi,sai daya ci guda biyu,ta karfi sultan ma yaci biyu,aka bawa driver ragowar biyun,


    Can suna tafiya a mota omar ya kwance ledar kwai yaci daya ya mikawa driver duka.sultan harga Allah abin na omar ya shiga bashi tsoro kamar tsafi,omar da baya cin abun hanun yara,gashi bayacin abunda rana ta dakeshi a kan titi,yau gashi hankali kwance har dafaffen kwai na titi yaci hankali kwance lallai wannan yarinya ta masa babban kamu.


    Har gida suka kai sultan suna tsayawa omar yace dalla malam fitar min daga mota,zaka nemeni next time sannan zan rama kuma kasan ramuwata me zafi ce cewar sultan.gidansa ya wuce yau bazai biya ta wurin mama ba,yana shiga ya tadda sahar kwance a doguwar kujera tana chat,sallama ya mata ta amsa kuwa tace sannu ta ci gaba da chat dinta,shima ko kallo bata isheshi ba ya wuce room dinsa,wanka yayi sannan ya dauko take away da ya zo dashi ya dauko yaci a kyankyame sannan yayi sallar la'asar,karatun Quran yayi da sauran abubuwan lada har magriba tayi ya wuce masallaci,inda ya bar sahar haka ya dawo ya sameta ba sallah,har ya gaji da fadan.


      Dakin haj rahina sadiya ce da naja ke hirar samari suna bawa umma labarin yanda suke cin kudinsu,Aisha tace ai ni full tank nake ja,zuka nake da yawa,jane dani,sai na cika tanki na.tana tsakiyarsu suna ta hirarsu,daga nan suka mike sukayi mangaren maman omar,su uku ne suka je kamar abin kirki, yan matan ne yau cewar mama,tsaki sadiya ta ja ta mata kallon baki isa,suma sauran haka sukayi,can naja tace an wani faffake gida matsafa kawai.wlh sai mun kawo karshen makirci cewar sadiya,abdallah ne ya mike ya cakumo naja suka fara kokawa tukuri,suna ganin ya fara naushin naja,suka hadar masa abinka da namiji yana karami amma da kyar suka sha a hannunsa.part din suka bari Aisha tace sai kayi dana sani yaro.


     Mama kuwa danta ta janye tayi shigewar daki dan inda sabo ta saba,Sam bata damua.haka tasa suleim da abdallah gaba ta kira driver dinta ya tafi dasu shopping har mama,suna fita omar na zuwa gidan,yaga part din kulle dama shima yana da spare key din part din mama,room dinsa ya shige a ciki yayi sallar isha,coffee ya hada ya sha yabi lafiyar gado ya kwanta abinsa.


    Tunanin iklas ya addabi zuciyarsa,to shi mene hadinsa da ita har zan na tunata cewar omar a ransa,lallai ya kamata yasan tarihin yarinyar nan,gashi ya rasa dalilin da yasa ya damu ya sake ganin kyakyawar fuskarta, sunanta ya fada a fili GOMNATI.Da kyar ya samu bacci ya daukeshi.


     Mama batasan a gidan ya kwana ba gani tayi ya sauko daga part dinsa cikin shirinsa na office sanye yake da wani cufta me tsadar gaske brown sai kyalli yake da kamshi,mama ce ta bude baki tana kallonsa babana dama nan ka kwana,ina kabar iyalinka anya babana karfa ka shiga hakkin matarka,murmushi yayi hade da rungume ta,haba mama dutyn dare takeyi  fa,ni sai muyi 3days ma ban sata idona ba,ta fifita aikinta kan aure,nayi fadan da nasiha amma mama a banza Bata San cina da Shana ba,bata San matsala ta ba,batasan komai nawa ba bata damu dani ba,


    Zama yayi ya kwanta jikin mama yace mama kin San ba sonta nakeyi ba ko daya,baffa na yiwa biyayya,amma duk da haka nayi kokarin janta jikina ta dole dan na takurawa zuciata kan dole sai na sota,amma mama ita Sam kullum bakin ciki take tura min taya zuciata zata sota,baffa ya jona min bacin rai kullum tana bata min,bazan boye miki ba mama duk da nasan kin San komai akan abubuwan da sahar keyi wlh na tsaneta,bana sonta,bana kaunar na bude ido na ganta a matsayin matata a gidana,amma ina daurewa muna zama dan nayiwa baffa biyayya.

 

    Tausayin danta ne ya lullube mama tace kayi hakuri babana nasan komai,ka dage da addua Allah zai ma canji mafi alkhairi,Allah zai baka wacce kake so take sonka,kaci gaba da biyayya.muje kayi breakfast,bayan yayi break ya wuce office,tunani yakeyi a office ya zai yi ya kara ganin wannan yarinyar me talla.idi driver ya kira ya karbi key din motar so yakeyi yayi driving da kansa yau,bai so asan ina zaije.


    Sadiya da Aisha ne suke hirar samarinsu,Aisha tace anty sadiya ya kamata kiyi aure haka karfa ki tsufa,tsaki sadiya ta ja dalla yanzu kudi da kayan gyaran jiki basa bari ka tsufa,yanzu duk wacce ta bari ta tsufa to ta rako mata duniya,samarin nawa gaskia naga  basu da kudin danake bukata gwara ma wani alhaji Adam shi kuma yana da mata daya,bai taba haihuwa ba,Aisha tace ni  a ganina ki fito dashi guy din akwai kudi,kina aikinki kinga zaki huta,kuma gidanki ke daya zai Gina miki,ga aikin gomnatinki heeeeee suka rangada shewa suka tafa,sadiya tace haka za ayi yar gari,kefa Aisha ?tace aini kin San wa zan tsayar,yaseen zan tsayar a turai yayi rayuwarsa ga kudi ga wayewa.haka sauran matan gidan ma suka shigo sai hira sukeyi.


      Iklas kuwa dawowarta kenan daga schl,sallah tayi taci abinci daga nan ummi har ta dafa mata kwai kawai tallanta ta dauka ta tafi gefen titi.shi kuwa omar 11am yaje wurin da yaga iklas na tsayawa talla amma shuru bai ganta ba,ba jiran da baiyi ba bai ganta ba,motar sa ya parker ya kira wani yaro me talla ya kwatanta masa yanayin iklas yaron yace ohhhh gomnati kake nufi,yeah ita cewar omar,yaron yace ai yanzu tana schl sai 1to1:30 take zuwa nan tallanta,take omar ya tuno time din da suka ganta jiya,


         Kudi ya bawa yaron ya hau mota ya koma office,1pm dai dai ya sake dawowa wajen danjar da iklas ke talla,nan ma bai ganta ba,shi kadai yake Jan tsaki,can ya hangota ta fito daga wani lalataccen lungu,dakyar take daga kafarta sabo da nauyin kayan,botikin kwai a kanta ledar apple a hannun ta,Tausayinta yaji sosai kamar yayi mata hawaye,yana cikin motarsa yana kare mata kallo,yana kallonta har ta fara talla,omar ne ya daga waya ya kira wani ban San me yace ba,ba a kai 10mnt ba wani ya parker a mota dai dai wajen kayan iklas,cewa yayi yana son apples da eggs amma duka zai saye mata,juye zai mata,da murnarta ta siyar masa gaba daya,yana tafiya ta kara irga kudin sai taga ya mata Karin dubu biyar akan kudin,dubu biyar din kai ta cire ta boyesu daban,da niyar in ta kara ganinsa zata bashi abinsa in bata ganshi ba zata yi masa sadaka dasu.


     Tsalle tayi tana dariar farin ciki an siye mata du,baki har kunne tace kai ni me sa'a ce,duk abinda takeyi omar na mota a gefe yana kallonta har ta tafi gida,shima yaja motarsa ya koma office,amma ya rasa dalilin da yasa yake jin nishadi yau.tunda yaga gomnati yaji damuarsa ta gama yayewa.hajiya rahina sun shirya cewar baza su fara makirci ba sai alhaji Baban su omar ya dawo gida Nigeria.Washe gari karfe 1 na rana omar yana gefen titi a wata kalar motar tasa,yana jiran fitowar iklas daga layinsu da yaga ta fito jiya.



Asmahbaffa

[9:45PM, 3/21/2018] ‪+234 803 592 9495‬: ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR

         GOMNATI

          ⓂⓂⓂ


                7


By

Asmahbaffa



       Yana zaune a motarsa yana shan a.c ta fito dauke da botikin kwanta yau yaga ba ledar apple a ransa yace to ko ta kare ne apple din tata?baki ya tabe hade da daga kafada.ta karasa danja tana tallanta,omar ya kunna motarsa ya hau kan titi yana zuwa saitin iklas ya gangare gefe yayi slow da motar,batasan waye ciki ba ta famfaro da Sauri sauri gudu gudu ta kara masa ledar kwai a glass na window side nasa,glass din ya sauke kasa wani kamshi da sanyin raba ya bigeta,ba tare da ta shirya ba ta kalli cikin motar,oga ta gani a mazaunin driver,lekawa tayi da murmushi sannu oga yau ma kazo wucewa?bai amsa mata ba kuma fuskarsa a tamke take,sai ya nuna kamar bai taba ganinta ba,kunya taji na disgata da yayi,a sanyaye ta juya zata wuce,keee cikin kakkausar murya ya kirata,juyowa tayi itama ta tamke fuska,ya akayi cewar iklas,a ransa yace wai ni zata wa tsawa haka hmm.a fili yace wai baki da wata Sana'a sai wannan?kullum kina gudu a titi cikin maza,kuma bakya sa kayan arziki na musulunci,duk maza an gama kalleki.

 

    Kallonsa tayi ta watsa masa harara to ina ruwanka,ina ruwan biri da gada,taso ta watsa masa bakaken maganganu wanda suka take wannan amma kwarjini da cikar zatinsa baza su bari ta fada masa ba oga omar ba kalar raini bane,Sam fuskarsa baya fara'a baka isa ka rainashi ba,in banda ma iklas ta goge da mutane da word daya baza ta iya furtawa gabansa ba,amma gashi har tsiwa take masa,a hankali tayi maganar amma ita wai nan a dole masifa tayi masa,sai ka zata hira me dadi sukeyi,shi omar daria ma ta bashi,a fili yace hey chill yan mata,I don't mean to hurt u,tambayarki nayi fa kuma dole ki fada min,lallai zaka Dade a tasha baka samu mota ba,murmushi yayi jin kalar Karin maganarta to naji next time zan dawo zo ki bani na siyi kwan naki,lallabata yayi don yasan gomnati akwai tsiwa,ya fahimci akwai son a girmamata,yauma duka ya siye mata kwanta tana tafiya ya bita a baya a mota ba tare da ta sani ba,har gidansu yaga gidan da ta shiga,juyawa yayi ya koma office cike da mamakin lalacewar gida irin nasu gomnati,da gani suna wani hali.


     Tun daga wannan rana iklas bata kara ganin omar yazo ba,tayi tunanin ko fushi yayi kan maganar da ta fada masa,ita da kanta ta gano bata kyauta ba,tunani ya hanata sakat kan maganar da ta fadawa oga omar,ta zama butulu ta manta halaccin da yayi mata,tun damuwarta na boyewa har ta fito fili,yau Saturday tayi jugum tana tunani kaka ummi ta leko dakin,ke yar nan ki raba kanki da wannan bakin tunani da kika dorawa kanki kwana nan,na rasa gane miki,alhmdllh muna ci muna sha,ga makaranta kunayi dai dai gwargwado Allah ya hore mana amma sai tunanin banza kikeyi,ummi wlh lailatul qadarin dana fada miki me gidan kaji?ae ina jinki iklas..to ummi shine ya tambayeni kan Sana'a ta amma na manta alkhairin da yayi min da yawa na masa rashin kunya,to har yau ban kara ganinsa ba,fatana ma ace lfy yake.ummi wlh baki ganshi ba me kyau dan gayu,ya fini kyau fa,kuma ga iya wanka ummi,sai ma kinga murmushinsa.


   Kaka ummi ce ta rafka  salati lailahaillallahu ni kam naga ta kaina,iklas karfa aljanu su shigeki,ko dai sonsa kikeyi ne,dama tunda naji kin saurareshi har ya miki kyauta kin karba nasan da wata a kasa,ke da bakya karbar kyautar namiji,kullum kice suna baki ne dan su lalata miki kuruciya, gashi wannan har murna da ihu kika dinga yi,duk ranar da kika ganshi sai kin hanamu bacci da labarinsa.akan wannan har kika damu kanki tab,ai sai ki tayi aiki ya ganki,


  Baki ta cuno kaka ba haka bane bafa,haba ummi ke bakya ganewa,nawa nake kwata kwata da zan San wani so.rankwashi ummi ta zuba mata tashi sha sha sha ki mana girkin dare wlh iklas ki kiyayeni.kara ta saki ochch haba ummi zaki sani ciwon kai.


      Shi kuwa Omar tun bayan da ya siyi kwai a titi ya tsaya ya rabawa almajirai ya dauki daya ciki yaci,tunani yakeyi ta ya zai San tarihin yarinyar nan,har yasan wanne irin taimako zai mata,baya son ya bata kudi sabo da gudun kar ta yi masa mummunar fassara, tausayinta yakeji ya rasa dalili.


      Baffan su Omar ne ya sanarwa iyalansa zai dawo nan da 2wks,su haj rahina sai murna Sukeyi burunsu ya kusa cika,kamar kullum yau omar yana gidansa a Palo yana cike ciken takaddu,sahar ce ta karaso wajensa tana zuba wani matsiyacin kamshi,ga wata Shiga da tayi ta alfarma kamar zata cin gasa.zama tayi kusa dashi,shafa fuskarsa ta Shigayi,yana dagowa ya kwadawa sahar mari lafiyayye,idonsa yayi jajir u r very stupid,me kika daukeni wawa ko me,duk abinda kikeyi ina kallonki kyaleki nakeyi sabo da biyayyar mahaifina.


     Dafe da kunci sahar tace what omar in ka sa hannu a lafiyayyar fuskata ka Mara,wlh sai kayi dana sani,sai kasan ka mari mai girma sahar, kuma bari na fada ma duk dunia babu namijin da ya isa na masa biyayya dan yana mijina,sabo da ina da komai na kudi,babu abinda zan nema wajen wani.


     Dama sallama nazo yima zan tafi kano wata seminar sai nan da 1wk zan dawo fuuuuuuu ta dauki trolley dinta tayi gaba tsaki Omar ya ja,har airport driver ya kaita ta hau jirgi sai kano.


    Omar kuwa wanka ya fesa yau Wednesday bai je office ba sabo da akwai inda yake son zuwa, cikin shigar wata rantsatsiyar farar shadda kal ya fito,dinkin zamani kamar a jikinsa aka dinka,ga sumarsa ta kara yawa luf da ita yana shining, komai fari yasa agogo ma na azurfa ne,


      Yau ma bai gayyaci driver ba,wata shegiyar farar mota ya shiga,su Kansu ma'aikatan gidan omar cewa suke oga yana kashe kala a garin abuja,oga na tsiya a kasar nan.


      Layin 1:40pm ya parker motarsa kofar gidan su iklas,kowa dake layin kallon motar akeyi,ko waye zai wuce sai yabi motar da kallo.yana cikin tunanin yaron da zai aika gidan sai ga suhaila cikin uniform ta dawo daga schl,kallon yarinyar yayi tabbas wannan kanwar gomnati ce,sunyi kama sai dai gomnati ta fita hasken fata duk da itama suhaila farar ce,motar ya bude yace pls young girl?da sauri ta juyo sai kallon dan gayu takeyi,nan ne gidan su gomnati?yeah nan ne cewar suhaila,pls ki min sallama da dadynku,daria tayi ai mu bamu da dady uncle,ok umma fa,kai uncle ba ummanmu bace tare da kakarmu muke zama mu 3.OK good girl yi min sallama da kakar taku to.OK ta shige gida da gudu,Minti kadan sai ga kaka ummi ta leko sanye da wata tsohuwar atamfarta,da wani yankwanannen gyale amma fa kar kar suke ,omar tunda yaga suhaila da kaka ya tabbatar gidan masu tsafta ne.


    Uummi ce tace samari lfy kuwa?har kasa ya duka ya kwashi gaisuwa,lfy ummi yaji sunanta wurin suhaila,ummi magana nazo muyi in ba damuwa.to shigo daga ciki cewar ummi,wani kamshin dadine ya bigi omar,kal kal yaga gidan,komai tas a tsare ga kamshi Wanda bai taba ji ba dukkan gidan nayi,Palo ummi ta kaishi mamakin kayan palon yayi,masu dan tsada  tsada danshi a wajen omar masu dan tsada zai ce, ga kamshi na gaske komai tsab,ga wata fanka ta kasa me iskar niima,ga ta sama ma.


     Numfashi yaja yace ummi dama akan maganar yarinyarku ne me tallan apple,na ganta sai naga sana'ar bata dace da ita ba,kai yaro ko Kaine lailatul qadarin da tace ta gani,me gidan kaji?daria ce ta kwacewa omar ba tare da ya shirya ba,ae ummi nine,Allahu akabar kabira,dan nan ya sunanka? Omar mohd omar Allah sarki umaru,sannu da kokari Allah ya kara budi,ameen ummi,mikewa ummi tayi ta kawo masa zobo me sanyi da dadi,yasha kayan kamshi,da ruwa pure water,shikam kodan su saba da shi zai sha, sosai yaga kalar gidan ba kyankyami,har lumshe ido yakeyi dan dadin zobon,suna zaune kaka ummi sai satar kallonsa take tana jin dadin yanda ya sha abinsu ba tare da ya ji kyankyaminsu,gashi me kudin gaske amma sam bai kyamacesu ba,kaka ummi ce tayi tunani tace kai yaro ko kai dan gidan mohd omar ibrahim ne dattijon kirki,murmushi yayi yace ummi kin sanshi dama?


Ae ai muna jinsa a radio muna ganinsa a labarai,waye bai sanshi ba,ai ya zaga duk fadin nigertia,nan kaka ummi ta karkace ta bawa omar tarihinsu kaf,har halayen iklas da yanda iklas ke tunaninsa sabo da tayi masa rashin kunya tana son bashi hakuri.


  Shuru yayi yana sauraren maganganun kaka ummi,ya tausaya musu matuka gaya,ya sa a zuciarsa zai dinga taimaka musu dan ba karamin tausayinsu yaji ba,can ummi tace ai mutuniyarka na bamu labarinka,yanzu zaka ga ta shigo,ko 5mnt ummi batayi da rufe baki ba iklas ta shigo da sallama tana kwalawa kaka kira?kaji ta ko umaru cewar kaka,shi kam omar guntun murmushi yayi,yagafa kaka ummi akwai surutu,shi kuma ba ma'abocin son surutu bane,fuskarsa tamke take dama ba wata fara'ace da shi ba,sai ka Dade dashi baka ga dariarsa ba,kaka ummi ma ta gano hakan,ga izza da takama.


    Ummi ina suhaila wai tana daki tayi bacci,yau nace baza taje islamiyya ba ta kwanta ta huta,haba ummi so kike naje nasha rana a titi ga kunya da tozarci ruwan sama,iska,sanyi,rana su kare min akai,kema kina naki wahalar mun biya kudin schl din nan duk da ba me tsada bace amma kin San asarar kudin zamuyi ko,alhmdllh ni na samu dai dai gwargwado na addini,amma ummi suhaila fa kin San yarinyace,ni gaskia bazan bari ta taso a jahilci ba.sabo da schl fa nake talla a titi.dole taje schl wlh,bari na shiryata ummi zauna Palo ki dauko min Biro da jotter lissafi za muyi,


     Ke dalla rufemin baki ni cewar ummi tare da shigewa Palo wajen omar dake zaune,duk yaji hirarsu da iklas gaskia ta birgeshi,tasan me takeyi.



     Asmabaffa

[9:46PM, 3/21/2018] ‪+234 803 592 9495‬: ⓂⓂⓂ

     MA'AIKACIYAR 

          GOMNATI

           ⓂⓂⓂ


                  8


By

 Asmabaffa




      In hakane to iklas na da nutsuwa da hankali,yarinya karama,ummi ce ta katse masa tunani sannu umaru kaga shashashar can bata ma kula da bako ba ita kawai ta makaranta takeyi,yarinyar nan da jarabar son makaranta take,rai ba hutu,ummi ai yanzu ilmi shine gaba,Allah kyauta cewar omar,iklas ta yiwa suhaila wanka,ta shiryata a uniform din islamiyyarsu Wanda shi kanshi wandon ya yage ta gwiwa kayan sun tsufa tukuf,amma a wanke a goge kal,sam iklas bata kula da takalmin bako ba,kawai abinda ke ranta take tunani,har Palo taja hannun suhaila wani mahaukacin kamshi ne ya daketa,kallon palon tayi,da sauri ta zabura tana zare ido,ta zata a mafarki ne sai taga tabbas a gaske ne,idonta ta kara murzawa,


     Dan rusunawa tayi kasa sannu ina yini,lfy kawai yace yana shan kamshi,tunda taga bata samu tarba me kyau ba ta mike,ta dauki Biro da jotter tace pls tsohuwa yi sauri muyi lissafin nan ina da aikinyi,iklas ke naga dan ana ce miki gomnati kanki rawa yakeyi ke a dole jinki kike kamar wata ma'aikaciyar gomnati,wlh ki cire wannan haukan ko kunya bakyaji kin fara girma kina cin kasa,baki ta cuno haba ummi dan Allah ni ki daina cewa na girma,dan uwaki ke bakya gani makauniyace jibi fa kirjinki iklas,wata kunya ce ta rufe iklas a gaban omar,kun San tsofaffi akwai baro zance,shi kuwa omar murmushi yayi ya kara wani nutsewa hade da tabe baki,a ransa yace wai wannan ce ta girma,ina abin yake,breast kamar gudan lemon tsami.


     Kasa kallon inda yake tayi sabo da kunya,da kyar ta fara rubuce rubucenta,tana ta faman buga lissafi a paper,kudin ta ebo tana turo baki gashi nan ummi wannan kin San ranar Saturday zanje kasuwa dasu,ungo wannan ki hada Dana wajenki na cefanen gida na fada miki ummi kullum ko naman 100 a dinga girki dashi ko kifi idan bani zan dafa ba dole ki dinga dafawa dashi,bana son muna cin garau garau ina shan wahala a rana a banza,blood dina zai kare a banza,kuma ban son skin din suhailata ya lalace ko babyna ta kalli suhaila,murmushi suhaila tayi tace anty ranar Monday za muyi debate a schl fa,kuma ance mu fadawa mom and dad Wanda sukaci akwai gift,muje da masu karba mana,ok suhaila Allah kaimu zanje ai cewar iklas.


  Ummi kuwa tabe baki tayi kwaji dashi can,daria suhaila tayi,iklas kuwa cewa tayi ummi yau daga islamiyya zan wuce siyowa,a'a iklas wlh baza ki wani gidan kaji da magribaba,ban yarda ba duniya ta lalace.mutane ba tsoron allah ne dasu,suje su lalata minke,a jawo mana masifa,dan yanzu da kike ganinki karama sai samu matsala.ba musu tace to ummi nifa tunda na dan Tara na abinci zanyi hutun 1wk bazanje tallaba.


   Ina ruwana da in na ce ki huta ai kin yarda kikeyi Yanzu gashi ai kin bi shawarata.kwantawa tayi jikin ummi tsohuwa zaki ci girki me dadi na zamani har na 1wk.daria ummi tayi oh ni jikar luba ta kaiwa iklas rankwashi.


      Omar kuwa birgeshi sukeyi,baren ma acting iklas tana abu kamar namiji magidanci,ga iya planning rayuwa,kai Wanda ya aureta yaji dadi,ga yanda take kula da kanwarta.ummi ce ta katse masa tunani da umaru kayi shuru,ba komai ummi ni zan tafi sai wataran,to har zaka tafi mun gode Allah saka da alkhairi,mun gode kwarai da kulawarka,hannun suhaila ya rike zo ki rakani beautyn anty.dadi suhaila taji dan gayu yace mata beautyn anty.


      Har mota sukaje da suhaila kudi ya dauko bundle guda na dubu dubu yace gashi beauty ki bawa ummi kice suyi cefane,ya kara dauko wasu manyan kwalayen sweets masu dadi da tsada da biscuits yan gaske da wasu snacks cikin katuwar Leda gashi wannan duka nakine,har kasa tace tnx uncle tana ta murna,wata ledar ya kara daukowa katuwa wannan suhaila baza ta iya dagawa ba,yace jeki ki kai wa ummi kisha sweets dinki,sannan ki cewar antynki tayi sauri ina kiranta,kafin ya rufe baki ta fada gidan da gudu,ummi murna da dadi ya rufeta,kakarsu ta yanke saka,tsalle sukeyi da murna kaka harda rawa da juyi,Riga damammiya pink bodyhug ce jikin iklas da wani jean skert shima da kadan ya haura gwiwa,


    Kallonta yayi ya tabe baki,mika mata kayan yayi gashi nan kuyi manage kafin na dawo,godiya ta shiga jerowa,juyowa yayi cikin hade rai da kakkausar muryar dake firgitata karki sake na ganki kan titi kina talla wlh,sannan ki daina yawo tsirara ga kaya nan,daure fuska tayi har zatayi magana sai kuma taji tsoro gani tayi yayi mata kwarjini.


 Amma aranta tace kuji min iyayi da shishigi,ina ruwansa da tallana,uba nane shi,shi zai dauki nauyinmu in banje talla ba,wai ina yawo tsirara kut..yayi sa'a shi ya fada min haka ina ganin mutuncinsa da wanine wlh sai ya San wace gomnati.


     Kafin ta gama wannan zancen zucin nata tuni omar ya Dade da figar motarsa ya bar layin, bayan motar ta hango kadan.gida ta wuce itama,


     Nan fa murna sabuwa gidan su iklas, ready made dogayen riguna ne masu tsada da kyau dai dai iklass kamar an aunata kala biyar,Riga da skert kala uku readymade suma,takalma kala uku flat,da yan gyale,brst basu isa sa bra ba panties kawai ya siyo kala 10,vest da tight wando guda uku,rigar bacci na yaran gida kala uku,bai San iklas Nada kanwa ba shi yasa bai siyo da ita ba,sai ya bata sweets da snacks din,atampofi kala biyar masu tsada du iklas tace kaka ummi ta dinka nata ne.  


     Murna wurin kaka ummi ba a magana ita kuwa suhaila ta sweets kawai takeyi,omar  Kuwa wurin sultan ya tafi gaisar da mom din sultan,sannan suka je wajen wasu frnds nasu,sultan yayi yayi omar ya rakashi wurin Yasmin budurwarsa amma omar Sam yaki zuwa,sultan ne yaja tsaki wlh zan rama omar,Yasmin din da zan aurace baza kaje wajenta ba?shuru omar baice uffan ba,sau daya fa ka ganta Frnd shima a hospital office dina kuka hadu.malam karka dameni kafi kowa sanin waye omar bana zuwa rakon zance,so pls excuse me cewar omar,nasan halinka mana maramutunci,miskilanci,da rashin damuwa da matsalar wani sai in matsalar ta me tallan egg ce.headphone omar yasa a kunnensa yana jin wakar Chris brown. 


   Kallonsa sultan yayi dan iska tashi ka tafi gidanku ka bar min daki ba abinda ka iya bakin hali ba annuri a fuska,gaka da mata amma baka da maraba da gwauro,gwauron banza kawai.murmushi omar yayi ya mike tare da shigewa toilet din sultan wanka ya fesa,wani closet din sultan ya duba da yake ajiye sababbin singlet dasu boxers,3quater  dan bangaren new da ba a taba sawa ba daban suke,sultan ma kwai kyau tsabta da daukan wanka,sultan shi ba fari bane chocolate ne,ya danfi omar kiba da kadan,shi yasa size dinsu kusan daya,


       Farar singlet omar yasa da 3quater ya fesa turaruka,sultan na shan kallonsa,kayan jikinsa daya cire ya eba ya zuba a mota,ya dawo room din sultan karar ruwa yaji yasan sultan na toilet,wajen mom din sultan ya wuce yaci abinci suna ta hira a kayataccen kantamemen palonta kamar aljanar dunia,30mnt yawa mom sai da safe ya wuce room din sultan,sultan ya hango jikin mirror ya hade cikin wata arniyar gezna sai turaruka yake fesawa,


    Tabe baki omar yayi daga bisani yace malam kayi sauri ina jiranka,da wata uwar masifa sultan ya juyo ubanwa zaije dakai gidan surukai haka,kamar inyamuri,ga suma duba fa shigarka,tsaki omar yaja ya sake bude layin sababbin jallabiya,wata milk color me mugun tsada ya dauko,siririya me shape dai dai jikinsa ta manyan guys,Turare ya kara fesawa sannan suka fito,mom suka gani a Palo suka mata sallama cike da fara'a hade da jindadi gami da birgewar abotarsu ta musu adduar dawowa lfy,7:30pm suka cinna hancin motarsu cikin gidan su Yasmin,gate man ya wangale musu makeken gate din su yasmin,har katafaren palon baki aka musu iso,kafin wani lokaci an cika gabansu da kayan motsa baki,


      Karaar takalmi sukaji das das,sannan kamshinta ya iso,cikin nutsuwa ta shigo da sallama,sultan ne ya amsa,ba laifi Yasmin kyakyawace fara ba kal ba amma tafi sultan haske,sun gaisa da omar ya dan jira for 15mnt ya fice ya koma mota,karfe 9pm sultan ya kira omar har umma da abbun su Yasmin suka gaisar.omar ranar gidan su sultan ya kwana.


    Asmabaffa

[9:47PM, 3/21/2018] ‪+234 803 592 9495‬: ⓂⓂⓂ

     MA'AIKACIYAR 

          GOMNATI

           ⓂⓂⓂ

  

                  9


By

Asmabaffa



    Wannan page din dominku nayi shi readers masu yabo da jinjina.



       

      Da safe tare sukayi break sultan,omar da mom sultan,sannan omar ya wuce office.bayan kwana biyu da zuwan omar gidan su iklas,wasu ma'aikata suka zo da kayan gini a motoci cewar oga omar ya turosu za suyi musu kitchen a canja toilet da sauran wasu abubuwa,abin har kaka ummi ya daure mata kai amma me zasuyi,nan da nan cikin 3days anyi toilet ta zamani tasha tiles,kitchen ma haka,rooms dinsu ma daga baya ya bada umarnin a sake sababbabi,kai readers gidan dungurugum aka sake ginawa komai sabo na zamani,2room da Palo tsakiya,toilet kitchen duk a tsakar gida yanda suke kawai Palo aka kara musu,ansa kofofi da windows na zamani,gidan tiles da tiles dan dagwas dashi gwanin birgewa,sai murna ake tayasu,su kuwa sai suce dan uwansu ne ya Gina musu,Palo sun maida kayansu na da, sai ya tashi haduwa,daya room din kuwa gani sukayi ankawo bed mirror sip new yan gaske aka shirya,duk rooms din an sa musu labile na zamani,next day suka kara ganin mota guda ta kayan abinci a tsorace suka yarda suka shirya kayan a kitchen komai akwai,dama suna da fridge me kyau da girma da tsada,


      Har gas da kayan kitchen kamar amarya an kawo an shirya musu,shifa omar kawai kudi yake bayarwa da umarni,next day aka kara kawo wasu kayan a Ledoji wai inji oga,dayar kaji,kifi da naman rago,a fridge suka zuba,harda lemuka masu tsada a takaice readers komai yaji a gidan na jin dadi,


      Next day kuwa wasu kayan aka sauke,ai iklas kuka tasa kaka ummi ma haka su dai karfa ace watarana su biya,dadi ya zama wahala,duk Wanda ke musu har anfi 1wk basu ga keyarsa a gidansu ba,sun shiga uku karfa ko ba nasu bane,ko aljanune ma,


    Kayan suka bude bayan sun gama kukan,uniform suka gani na wata schl dake kusa dasu schl din me tsadace,iklas dai dai ita,itama suhaila kamar an gwadata,mamaki sukeyi wai to a ina yasan size dinsu,uniform din har kala 4-4 ya musu,ga books din kowa a schl bag kala 3-3,takalman schl ma kala 3-3,a cikin jakar iklas yasa takadda me dauke da rubutunsa,


     Da sauri ta dauko ta fara karantawa kamar haka.

      ki duba cikin wata Leda akwai envelop in kunje schl din da ita zaku tafi, ki bawa p.c din,7:30 za kuga me kaiku yazo,banda talla a titi,ki gaisar da ummi.

                  Omar


    Ai tsalle suka fara da ihu suka cika gidan,wlh ummi shine yayi mana komai,lailatul Qadari Allah maka albarka,ai duk sallah sai na ma addua cewar iklas,kaka ummi babaLola science sec schl fa ya biya mana kinga receipt har na gama an biya min,suhaila iya js3 ya biya mata,.. 

  

     Daya ledar suka jawo gaba daya kayan suhaila English wears masu kyan gaske kala 10,takalma masu kyau harda kayan baccinta kala biyu,pant itama dasu vest kala 10.kuma nan ma kamar an gwadata.


      Tsalle kawai takeyi tana murna,saura wata ledar atampopi kala biyar dinkakku diff stile,shaddoji kala 4 yan gaske suma sunsha aiki,lace kala 3 sunsha dinkin zamani,da material kala 6,suma gaba daya an dinkasu dai dai jikin iklas,lace2,shadda2 mayafai manya masu tsada kala Biyar, ba a dinka ba takadda manne jikinsu anyi rubutu kamar  haka.


     Na ummi ne ki bata ta dinka,ga kudin dinki nan cikin lace,mayafaima nata natane.karamar ledar karshe suka bude,hijabaine masu hannu kala biyar size din iklas dagwas,kala uku na suhaila,kala uku manya na ummi,mayafai suka Ciro yan madaidaita masu kyau da tsada kala 6 na iklas,sai uniform din islamiyyarsu da ya gani jikin suhaila ya canja musu new kala 2-2.


    Yau har nafila sukayi suka dinga godewa Allah tare da yiwa Omar addua da iyayensa,next day kayan kwalliya iri iri Dana gyaran gashi da turaruka aka kawo musu,3days tsakani ya turo da wasu latest takalman roba na mata da jakankuna cikin Ghana must go babba,da address din company gashi nan suyi business,su dinga siyarwa a cikin gida babu zuwa talla,ai kuwa haka akayi,iklas an kulla alaka da company nasu omar,banda jaka da takalmi har wasu abubuwan take sarowa suna saidawa a cikin gida ake zuwa ana siya,sai schl tana kaiwa.sosai suke samun kudi,ga schl me kyau,sutura me kyau,ci da sha zam zam,ga tsabta da kwalliya suna bugawa,gasu wayayyu sai suka kara kyau haske da kiba.


      Tun zuwan omar na farko bai kara zuwa gidan su iklas ba,komai da yayi musu aike yayi dasu,su kuwa sun matsu su ganshi ko godiya suyi masa,amma shuru,gashi basu da number sa bare su nemeshi dan iklas ta siyawa ummi wata karamar tecno sabuwa,ita kuma ta siyi wata Samsung me kyau touchscreen,haka kawai iklas ta ji ta shiga damuwa na rashin ganin omar,


     Kullum sai ta tunashi,shi kuwa omar a ganinsa har ga Allah ya taimaka musu badan wani abuba,me zaije gidansu yayi,me zaice dasu yayi aikin ladansa suzo suyi zarginsa ko da wata manufa yayi.shi yasa tace Sam bazai kuma lekasu ba,tunda komai yayi dai dai shike nan.amma me zuciyarsa kawai sai yaji yana son yaga lafiyarsu musamman iklas,yana so ya ganewa idonsa ya suka koma,


     Baffan  su omar yayo waya cewar bazai dawo ba sai nan da 2mnths,dan haka ya umarci daya daga cikin matansa ta bishi Russia, ai rahina wuta ta bude dole itace ta tafi Russia wurin baffa Wanda Sam baiso itace zata zo ba amma ya zaiyi.


      A can ta dage tana ta kulla makirci,hade da kiran tsofaffin bokayenta tana danna musu kudi suna sheka aikinsu,sun bata tabbacin maman omar ba abinda zai iya cinta na tsafi dole tana nan daram,kuma baffa bazai daina sonta ba,dan haka tace to danfa a koreshi ya bar gidan,nan ma sukace shi zai iya tafiya amma bazai nisa da gidan ubansa ba,kuma dole zai dawo,cewa tayi koma yane ayi mata ya bar gidan.


       Sahar kuwa tunda ta dawo yanzu tafi da fita gantali,dan yanzu tafiyar kwananki takeyi.tun omar na fada da damua ya gaji ya kyaleta.kowa harkarsa yakeyi.


    Yau watan omar 1 da zuwa gidan su iklas,ya gaji da daurewa,yau dole ne yaje ya ga lafiyansu.saturday ba islamiyya ya sani,sanye yake cikin  pencil wandon jean arsh color da farar Riga me rubutu da baki jiki,ga suma taci kudi,kai ka rantse bature ne 4:30pm ya parker wata jibgegiyar sabuwar motarsa a kofar gidan,da kyar ma ya gane gidan,dan ma ma'aikatan sun nuna masa a waya ne,knocking yayi suhaila ce ta bude sanye take da vest da wandonta iya Rabin cinya,gashinta yasha gyara,tun daga kallon suhaila yasan sunci gaba wlh.


     Baki ta washe ta daka tsalle ta daneshi,oyoyo uncle,muna ta nemanka baka zo ba,to ai gani beauty yana murmushi kadan,sama ya shilla suhaila ya sabata a kafada suka shige gidan da sallama,kaka ummi ce ta fito tana amsa sallama..turus taja birki da mamaki tabbas wannan umaru ne da suke nema ido rufe domin suyi masa godiya,ummi baki har kunne ohhh dan nan yanzu sai yau kazo,muna ta jiran ganinka shuru,abubuwan arziki sai barkowa sukeyi ta hannunka,nanfa kaka tahau zuba godiya harda kukanta,daga nan ta fara yi masa hira,shi omar a bai son labari da yawa amma haka yake amsawa a dole,


     Kuma yana jin dadin labarin da take masa domin masu amfanine sosai a wurin dan Adam,dan ita ummi bata surutun shirme a nutse take,suhaila kuwa tana cinyarsa ta lafe,


      Iklas sanye take da wando 3qutr tight fari kal da riga dark blue,siririn gyale ta daura a kanta fari,tana kitchen ta gama shirya musu abinci ta gyara kitchen,sai surutun ummi take jiyowa dan ita bata ma San anyi wasu bako ba,wanka take so tayiwa suhaila itama tayi domin ita ke yiwa suhaila wanka saboda da wai suhaila jika jika takeyi kawai.fada sukeyi da suhaila sosai kan wanka,dan suhaila tace ta iya wankanta ita.


     Da sauri ta fada  palon da sallamarta....ummi wai surutun me kikeyi hakane?ina suhaila tazo na mata wank......bata karasa ba takai kallonta kan 2seater ai cik ta tsaya ganin Wanda ko a mafarki bata zata ba,ganinsa tayi ya kara kyau da kwarjini,ai da Saudi ta durkusa sannu da zuwa sir,ina yini,ya hanya? Da kyar ya amsa da lfy yana shan kamshi,ga fuskarsa ba rahama tamke,


     Ganin yanda ya amsa mata bata samu karbuwa ba a wulakance,kamar bai Santa ba yasa ta mike tare da fadin taso suhaila na miki wankan,kafada suhaila ta make a jikin omar...ni anty na iya wankana fa zanyi da kaina,no ban yarda ba jika jikar da kikeyi,kinga baby dont waste my time ki taso na miki,ina da wurin zuwa.


      Omar a ransa mamakin iklas yakeyi yanda takeyi acting kamar babbar mace bayan ita kanta iklas din bata wuce a mata wankan ba.


     Ganin suhaila bata da niyar tashi yasa ta karasa wurin omar ta jawo hannun suhaila nan suka fara kokawa,suhaila ta tura hannun iklas da karfi ta hade hannun da kirjin omar sai kiciniya sukeyi iklas na kokarin zaro hannunta wani azabar bala'in shock ne ya shigi omar,bai San sanda yace shishsh a hankali,tana janyo hannun ta fara masa sannu da bada hakuri duk ta dauka bigeshi tayi yaji zafi,...tsawa ya buga mata get lost stupid kin takurawa yarinya,


      Kaka ummi zabura tayi Allah maka albarka Umar yarinyar nan bata da kunya wlh wani halin banza ta dakko na son girma,gashi bata jin maganata na rasa inda zanyi da iklas wlh ka ganta duk wannan haukan da takeyi sauri takeyi zata je party na makwafta.dan ta taba taimakamana shine wai dole sai taje partynta na murnar zagayowar haihuwa,


     Giya fa suke sha a wurin umaru rawa maza da mata a cure ana badala nayi nayi akan Kar taje amma takiji,bata jin maganata sai abinda ta tsarawa rayuwarta kaka ummi ta fashe da kuka wiwi.


     Asmahbaffa

[9:59PM, 3/21/2018] ‪+234 803 592 9495‬: ⓂⓂⓂ

     MA'AIKACIYAR 

          GOMNATI

            ⓂⓂⓂ


                  10


By

Asmahbaffa




Wannan shafin nakine MAMAN WALEEDA ina godiya sweet sis.




           Kiyi shurunki ummi yanzu zan kula da ita duk wani iskanci da take ji dashi zan gyara ta,cuno baki iklas tayi ta bar palon,wanka ta samu tayi ta palon ta wuce sanye da hijab,kwalliya ta tsantsara ta sa daya daga cikin  rigunan da ta siyo rannan a kasuwa wata yar gaunt me dogon hannu ta haura gwiwa da kadan,daga sama ta matse kasa ta bude,orange and black color tayi kyau ba laifi harda yafa siririn gyale orange wai ita a dole zata birge,tayi shiga me kyau,don kaya manya su atamfa nauyi suke mata,bata saba ba sam,batan me yasa take so yau tayi kyau ba.wuce su omar tayi a Palo ta koma kitchen hade da kiran suhaila,abinci suka Jere a gaban omar,kallonta omar yayi tayi kyau amma wai ita bata sa kayan kirki ne?ga bako ai kamata yayi ta suturta jikinta,wato kowa haka yake kalleta tab,ummi ce tayi magana umaru bari inje makwafta zanyi ta'aziyya anjima  kadan zan dawo ba dadewa zanyi ba ka jirani,ba matsala ummi sai kin dawo,kallon iklas ummi tayi tace sai ki zauna wajensa na dawo uwar giggiwa kullum aikinki kenan yawo da watsatsun kaya,zigidir kullum da kayanki ba babu.


     Umaru kaci abincin dan Allah kaji,ko albarka kasa mana,kar ka bari na dawo na tarar baka ci komai ba,bazan ji dadi ba.ok ummi cewar omar.

Fitar ummi keda wuya dakin yayi dif ba Wanda yayi magana ga suhaila tayi bacci,sadda kai kasa iklas tayi bata son kallon omar wani faduwar gaba take ji,


       Kallonta yayi fuskar sa daure,ke a tsawace yayi maganar wato bakyajin magana ko,tun baki tafasa ba za ki kone kamarki har kin isa zuwa wani party kuma partyn na wasu tambadaddun yare,tsohuwa na zaune daku kina bata mata rai,ki kiyayeni wlh,da na kowa ne bar ganin bamu hada dangantaka ba duk lokacin Dana kamaki,ko na ji kin yi abu rubbish sai na hukuntaki.itafa iklas mamaki ya gama kasheta irin karfin  halin omar,ina ruwansa da rayuwarsu wai,sai kace ubansu,ko wani sabawa dajuna basuyi ba amma yake wani fada haka,lallai ma,Nima asmah naga shishigin omar anan.


    Turo baki tayi to birthday din maman ola ne fa sir,kuma....shut up  ba inda zaki .to ai dama na hakura sir cewar iklas a sanyaye,karma ki hakura.shuru dakin ya kara dauka can tace sir?Ina jinki,kaci abincin mana to,jagwalgwalonki zanci an fada miki ina cin girkin irinki,dama ummi ce tayi sai na ci.shuru ta masa dan taji haushin kalamansa,ta rasa why take daga masa kafa,ita da take masifaffiya bata kyalewa amma akan omar ta kasa daukan mataki.ba komai ko dan taimakon da yayi mana zan dinga kyaleshi.bani ruwan nasha kawai s ok ma maganar omar ta katsewa iklas tunani,da sauri ta mike ta fara tsiyaya ruwa a wani glass cup me kyau da tsafta,cikin izza ya karba yasha hade da mikewa tsaye idan ummi ta dawo na wuce ni ki sanar mata


     Pls ka bari ta dawo mana ko ka tsaya na kira  ta yanzu pls,sallamar ummi sukaji ta shigo palon,yawwa ummi zai tafi wai cewar iklas kuma baici komai ba wlh,hangame baki ummi tayi haba umaru ya zaka Mana haka,mu ka taimakamana mun yarda mun karba duk da bamu sanka ba,ba dangin iya ba na baba amma mun yarda da kai,yanzu dan mun baka abinci shine baza ka ci ba,kamar mun baka guba ko wata cuta.


   In dai kana so mu shirya gaskia kaci ko kadan ne idan kuma kyankyami kakeyi bazan ma dole ba.da sauri omar ya koma ya zauna haba ummi ba wani abu kiyi hakuri bari naci.baki ummi ta washe haba ko da kaifa amma ai sai ka sa muji ba dadi ai,iklas zuba masa bari naje na karasa gyara wasu kaya.omar ji yakeyi tsohuwar na birgeshi,kallonta yakeyi kamar mama.


    Tana bude flask wani kamshi ya daki hancinsa me dadi,fried rice lafiyayya tasha hadi da su hanta etc,zuba masa tayi ta kara bude wani bowl me kyau na glass kaji ne soyayyu zuba masa tayi a gefe ga hadadden salat,mika masa tayi ta zuba masa lemon kwakwa.


    Yatsina fuska ya dauki spoon da kyar ya fara ci,wani arnen dadi yaji kamar kunnensa zai fita,sai santi yakeyi a ransa a fili kuwa yatsina fuska kawai yakeyi,iklas na kallonsa kafafunta sunyi sanyi tun a fuskarsa ta gane baiji dadin abincin ba,kamar zatayi kuka bata San ace girkinta baiyi dadi ba.


    Musamman a wajen Omar bata San me yasa take so ya yaba girkinta ba.idonta har ya Tara kwalla kadan,omar yana kallonta ya gama ganota tsab,a ransa sai daria yakeyi,ganin kaka ummi bata kusa yasa yake ta wannan yatsina fuska,tunda yaga yanayin iklas ya kara yatsine fuska dan yanzu har yi yakeyi kamar zaiyi amai,abin mamaki yaci abincin yafi Rabin plate,lemon ma yasha yaji dadi amma harda rike ciki wai a dole yaci guba.can yace kai ummi ta takura naci jagwalgwalo,babu dadi haka akeyin girki,wannan  ai sai ki kashe mutane.


     Hawaye ne ya digo dis  daga idon iklas da sauri ta goge kar sir omar ya gani Wanda ta Riga ta makaro a idonsa tayi komai.kitchen ta shiga sai gata ta fito da wata Leda me kyau a hannunta,mikawa Omar tayi ga wannan ka kaiwa mom dinka,


       Tunaninsa ne ya tsaya cak wannan yarinyar akwai mamaki acikin alamarinta,wai tana 15yrs har tasan ta bawa mamansa kyauta yaji dadi kuma ta kara birgeshi.karba yayi hade da cewa tnx kira ummi,sai gani yayi iklas ta tsaya rubutu a jotter bai San me ta rubuta sai da ta gama ta wuce kiran ummi,ita kuwa iklas ta Riga tayi lissafi wannan week din sunyi dambun naman kaza gashi basu ci ba ta bayar kyauta,shi yasa ta canja lissafinta..sallama omar ya musu ummi ma ta bashi sakonta ya ba mama,


       Gidansa yaje ya duba lafiyar sahar sabo da amanar aure dake kansa,yar aikinta ya tambaya ina sahar ?ranka Dade tayi tafiya yau tace a fada ma ta tafi kasar ghana akwai wani aiki za suyi..ok kawai yace ya koma gidan mamansa,abinda Omar bai sani ba sahar ta kara lalacewa sai matan manyan alhazawa take kulawa Wanda suke da naira,wata kawarta hajiya talatu matar wani gomnace ita ta bawa sahar shawarar tunda kullum a hanya take ga mijinta ba wani shiri sukeyi ba kuma sahar akwai tsananin sha'awa kawai tunda tana da kudi a hannu ga maza nan samari yara sai ta zaba tunda yanzu matasa sun zama kwadayayyu kudi suke nema ta ko wacce hanya komai kudi,to ta mori dukiyarta ta samu wasu suna biya mata bukatarta tana biyan kudi.amma ta daina zubar da ajinta wurin omar mijinta tunda shi baya taba nemanta itama ta daina kai kanta.wa'iyazu billah mai makon muyi kokari mu gyara halinmu sai mu kara dilmiyewa mu jefa kanmu halaka wacce  har ka mutu kana da na sani.Allah shiryamu gaba daya.dan yanzu wannan ya zama ruwan dare wurin wasu matayen musamman masu naira


       Mama na room dinta tana shafa magani a kafafunta da suke mata ciwo omar ya shigo da sallama,da fara'a ta amsa masa babanmu ina ka shiga ne haka ban ganka ba,maganin ya karba ya karasa shafa mata,ina gida mama ga office ba sauki,omar kenan na dauka ma ko suruka ta biyu ka samo min,murmushi yayi mama aure tun yanzu zan kara aure,ina zan kai matan dayar ma da za a yagemin ita so nakeyi,daria mama tayi omar sai hakuri dan kawai ba auren so aka maka bane kuma matar taka ba ayi dace ba shi yasa ka fadi haka,


    Mama kinji yanzu na dawo gida wai ta bawa yan aiki sako a fada min ta wuce Ghana,duk yawon da takeyi kasar nan bai isheta ba mama.mama ma ranta ya baci da jin abinda sahar tayi,ka bari zanwa baffanku magana a waya sai aje gidansu a sanar da iyayenta tunda ta Gagari kowa,ni ma zan kirata a waya,mama ki kyaleta pls kar tazo tana miki rashin kunya kin San bazan kyale ba.ya isa omar dole a fada mata gaskia.to mama ba matsala.ledar da iklas ta bashi ya mikawa mama,ledar kaka ummi ma ya mika mata gashi mama sunce a baki kuma suna gaisheki,murmushi tayi na gode Allah saka,amma banana wannan su waye suka bani bazan bude ba sai ka fada min,ohh mama wannan red din na kaka ummi ne wannan kuma na jikarta iklas,


    Murmushi mama tayi tana jin dadi tana fatan abinda tayi tunani ya zama gaske,a fili tace ban ganesu ba ai...uhm..uhm yana Sosa kai yace aikine ya hadamu gidan gona.kyaleshi mama tayi, tace angode kaga mutanen kirki bari mu gani mene ciki.


     Ledar iklas ta fara budewa wata katuwar farar roba ce  mai murfi shake take tam da dambun naman kaza iklas yinsa tayi musamman sabo da suhaila na sonsa ganin omar yasa ta canja idea ta juye masa duka me uban yawa ta bawa mamansa.mama taji dadi sosai,ta bude ledar ummi kayan kamshi ne da sauran abubuwan miya busassu.mama sai murna takeyi omar har mamakin murnar mama yayii,babana ya kamata ka kawo min su na gansu ko ka kaini gidansu,ba yanzu ba mama to allah kaimu koma yaushene.kasan bana cin maiko sabo da ulcer ta,kadan zan iba ni da su abdullah.dauki wannan kaje dakinka dashi..da kyar ya karbi na robar wai a dole bayacin girkin yara,amma ya dauke ya wuce room dashi yana bata rai da muzurai.


      Sadiya na hango sai masifa take zazzagawa tana dura ashar a compound din gidan,duk wani ma'aikata sunyi luf suna jinta,suleim na hango da uniform jikinta tsugune a gaban sadiya tana faman bata hakuri,anty sadiya kiyi hakuri ban San takadar tana da amfani ba shi yasa Dana gani na yaga na zuba a dustbin,


       Wani lafiyayyan mari sadiya ta kwadawa suleim Allah sarki yar yarinya sai ga shatin hannun sadiya radede a fuskarta,kuka ta tsala hade da dafe kumatunta,gashinta sadiya ta ja da karfi dan uwarki baki San darajar takarda ba,gadon tsiya ba laifinki bane uwarku ba ilmi ne da ita ba jahila ce shi yasa Baku San darajar takarda ba,tsabar masifar da sadiya keyi ko kula da motar omar wacce ta shigo har ya parker bata sani ba,hankada suleim tayi ta tintsira ta bige kanta da bakinta,wani gigitaccen kuka ta fasa,omar Wanda yana kallon abinda ke faruwa ransa ya baci,idonsa yayi jajir,zuciya ta tashi,karasowa yayi wajen ya ware hannu ya dinga zubawa sadiya mari,tun tana tsaye sai da takai kasa,belt din wandonsa ya zare ya fara zabgarta gashi ya riketa ram sai daya zaneta tas jikinta duk ya fashe,a hakan ma dan mama ta fito ta rikeshi ne,duk yan gidan suna wurin suna kallo,kafin kace me su Aisha naja sun kama zage zage suma,sannan suka kira baffa da ummansu dake Russia suka fadi karya da gaskia.


    Nanfa hajiya rahina ta haukacewa baffan su omar,wlh bazan yarda ko a dauki mataki ko na dauka da kaina,an Dade ana zalinta ni da yarana Sam bazan yarda wlh,akan haka sai dai in ka sakeni amma billahillazi bazan yarda ya kashe min yara ba.tsawa baffa ya daka mata ki saurara min shashashar banza,duka kannensa ne yana da damar hukuntasu,nasan dole omar yana da dalilinsa me karfi,yaran naki bansan halinsu bane an fada miki, marasa tarbiya omar ne wakili na yana da daman yanke komai a gidana.kuma wlh tun kafin na koma ki fada musu dukkansu su fito da miji,na gaji da zubar min da mutunci da sukeyi a unguwa..... Wai wai ai rahina kururuwa ta sa da gunjin kuka,baffa kuwa gidan ya bari.



    Asmahbaffa na godiya gareku masoya readers,masu commenting idan nayi posting kunfi kowa birgeni, domin kuna bani kwarin gwiwar typing, na tabbatar kuna jin dadinsa.

ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR

         GOMNATI

          ⓂⓂⓂ

                

             10-15


By

Asmabaffa.




      Pls readers a dinga kula ana amfani da sakon da muke isarwa me kyau,marar kyau ayi watsi dasu, bukatata kenan,kuskuren da mukayi Allah yafe mana kuma readers ayi mana afwa.Allah tsarkake mana zucuyoyinmu,a dinga rula sakonni nake isarwa ko wanne page lol na gode muku yan readers dina ina ji daku.kunyi male male araina.

      

     Tunda baffa ya fita taki daina kuka sosai take sheka kuka an Zane first daughter dinta me irin halinta sadiya,sai da ta koshi da kuka daga bisani ta jawo wayarta,ta kira haj bilki babbar kawarta tas ta kwashe zance ta fada mata,lallai yaron nan kwai tsinane tambadadde cewar haj bilki,rahina tace shi yasa na fada miki kije min wurin babban malaminki na kasar Mali ayita ta kare,na gaji da tsinannun mutanen nan,akan wannan zan iya dawowa Nigeria muje tare bilki ki rakani,duk wanda na sani nawa malaman ba kudin da ban kasheba abu shuru,nasan naki manyan shegu ne,daga bangaren haj.bilki baki ta tabe daga bisani taji dadi a ranta tana adduar insha'allah bazaiyi aiki ba,yar iska wai ke mijinki me kudi har yanga kike mana kin fimu kudi,ga yaranki masu aikin gomnati,ai sai na miki sanadiyar barin gidan alhaji mohd wlh,hauka nake na yarda ki samu daula ke kadai,Baki San yanda nake miki bakin cikin auren alhaji mohd ba,dan yafi mijina kudi...


     Haj rahinace ta katsewa bilki mugun tunanin dake ranta tana ta hello....hello....inajinki network ne wlh rahina,kina jina ki kwantar da hankalinki ni danake babbar kawarki ai dole zanje kasar Mali ko dan ke,ki bar komai hannuna,ammafa sai kin turo isassun kudi,babu matsala wannan cewar rahina,kuma dole sai mun haada da tuggunmu na mata.kin san yanzu sunfi tsafi aiki wajen maza,wasu maganganu haj bilki ta tsarawa haj rahina wanda koni banji me suke cewa ba readers.


       Suna katse wayar haj rahina tace shegiya haj bilki tasan takan duniya....banza marar wayo yar matsiyata kina taimakamin na samu abinda nake buri ko kawa  nafi karfin nayi dake,jahilar banza yaushe ma inba dole ba zan tsaya ko kusa dani ki raba,iyakarki primary schl.nan umma rahina ta kwashe da daria,a karshe tace har a bada bilki sai dai ki zama baiwata ba kawa ba.haj bilki kuwa tsaki taja tace shashasha naci banza,kudinki zan cinye na Gina kaina,ta zata shawarar Dana bata zata bulle,hhhhh lallai alhaji mohd zai saki dattijuwar banza zaki gane wace bilki.


     Kunji fa readers ko wacce cin amanar ko wacce takeyi,kuma wannan cin amanar ya zama ruwan dare tsakanin kawaye musamman mata,kowacce bata son yar uwarta taci gaba hassada,ga mugun nufi wannan ya zama ruwan dare a rayuwarmu ta yanzu,taya zamu ga dai dai wannan ya jefi wannan ,wannan ya jefi wannan.Allah ka tsarkake mana zuciyoyoyinmu.


     Bangaren su oga omar kuwa abin nasa yaci tura,da kyar mama ta janyeshi suka dauki suleim,family doctor mama ta kira yawa suleim dressing,abdallah harda kuka an jiwa kanwarsa ciwo,omar kuwa jikinsa sai rawa yake ran maza ya bacifa readers,dama can ya gaji da halin kannen nasa,sharesu kawai yakeyi amma komai da sukewa mama da kannensa ya sani kyalewa yakeyi dan a zauna lfy,amma tunda haka suka zaba zaiyi maganinsu idan basu nutsu ba.sadiya kuwa sai ihu takeyi jiki ya kumbura,sun hadu a kanta su Aisha suna ta Gasa mata jiki yayinda suke ta zage zagensu iri iri,sadiya kuwa jinsu kawai takeyi dan Allah ne kadai yasan irin matakin da zata dauka kan su omar da uwarsa,dan tayi alkawari ko zata mutu,ko zata karar da salary dinta sai ta kulla musu bala'i,yanzu ta fara ta daina jiran ummansu yanzu itama ta zauna da kafafunta daram sai taga karshen omar da wanda ya rabeshi gaba daya...ruwan zafin da Aisha ta danna mata a gefen wuya shi ya dai daita tunaninta ta saki kara da ihu hade da cewa Aisha zanci uwarki kasheni zakiyi.tana ta ciccijewa sabo da azaba..ni kuwa nace heeee..na fece daga wurin,


     Omar bakin ciki ya cunkushe masa zucia,haushin gidan yakeji gaba daya,mikewa yayi ya bar gidan gaba daya,har ya dauki hanyar office din sultan ya fasa ya canja hanya,dan yasan idan yaje wurin sultan bacin rai zai kara masa,da gudu na bishi readers na tafi gulma....lol.mayenta layin su iklas na ganshi gheto area yana Jan motar a slow yau 6days rabonsa da gidan,a tsakiyar layin gefen titi ya hangota tana magana da wasu maza igbo su biyu,sanye take cikin uniform 1:30 da alama daga schl take,


     Wani bakin ciki ne ya kara mamaye cuciyar oga omar,ya kwaso bakin ciki yaci karo da wani,haka kawai ya tsinci kansa cike da bacin rai ganin iklas da wasu kucakan maza Igbo,tana ta surutunta hankali kwance.omar na karasowa wajen ya danna wani horn da karfi wanda ya janyo hankalin kowa dake wurin suka zubawa shegiyar azababbiyar motarsa na mujiya,cikinsu harda iklas me dafaffen kwai,glass ya sauke sukayi 4 eye da iklas,alama ya mata tazo sallama tayiwa mazan Igbo bye Emma a gwarance suka ce gomnati gomnati murmushi iklas tayi tare da mikawa Emma hannu suka tafa hade da cewa  NO BE SMALL THINGS WOOO,Dayan Dennis yace,ur first salary is my share,nanfa gomnati tace,never mind A NO DEY CARRY LAST MY BRO,daria sukayi dukansu sannan ta daga hannu tana WE GO RUNNERM,U ASEY DEY NOOOOW.ta nufi motar omar kafin ta karasa wani bahaushe saleem yace gomnati sai kinci da biro hannu ta daga masa tare da bude gaban motar ta shiga,ta glass ta leko da kanta tace saleem salary na farko da kasonka ciki,fisgar motar omar yayi ji kake gwaf kan iklas ya bigi gaban motar,birki yaci kyaaaaa....ta koma da baya jagwaf...kafin ta nutsu ya kara fincikar motar ta kuma gwaraf da kanta a jikin glass,kuka ta kece dashi yanda zafi ya hadata ta ko ina.cisgar motar omar ya karayi kamar zasu kifa,ina gefe nace Allah tsare na cikinta Dana kan hanya,kuka iklas takeyi musamman da goshinta wani katon kululu ya fito,parking yayi kofar gidansu,da Sauri iklas ta fita dan ta ga mutuwa with her own koro koro eye,tana fita omar ya sauke glass ji mana....juyowa iklas tayi, u hv to be very careful banda sauki ina gargadinki ki tausayawa lafiyarki kiyi abinda ya dace kunnena yaji da wanda idona zai gani,zan dawo next time hukunci yana nan zaki karba dai dai da ke cewar omar tare da figar motarsa ya bar layin gaba daya cike da jin tsananin haushin iklas,shi kadai ya rasa ma ina zaije ya huta,wani katafaren guest house dinsa ya nufa dake gwagwalada,da ma'aikata da komai a gidan so very neat.


      Iklas kam ta Dade a tsaye tana tunanin to ita wai me tayi masa,mene hadinta dashi da haka kawai zai tsaneta,ya dauki karan tsana ya Dora mata..tsaki taja tana mulmula ciwonta ta wuce gida tana kunkuni za a kasheta a banza.


    Ummi ce ta tsare iklas da tambayar me ya sameta a goshi,fada mukayi a schl ummi Da wata,shine ta buga min kai da chair nima na fasa nata da dutse.kin kyauta iklas Allah taimaka cewar ummi,shashasha matsa ko na makeki wacce bata San ta girma ba,bari Allah ya kawo min yaron albarka umaru na fada masa tunda naga kinfi jin fadan sa.


    To wai ummi ni me nake mikine dazaki dinga hadani da wani azzalumi bare can,bamu hada dangi dashi ba amma har kinfi sonsa akanmu...ummi ce ta maketa da gudu ta mike ta wuce toilet,sallah tayi,wanka da cin abinci,mikewa tayi ta kwanta tana tunani kala kala wanda yafi yawa akan omar.tana tunaninsa kuma sai taji ranta yayi fari,ji tayi gwara tayi tunanin oga fiye Dana schl,ita kadai idan tayi tunanin schl sai tace no sai tayi na omar,sai ta saki murmushi tare da cewa kai ni kwai banza,mene abun tunashi,me ma zanyi dashi,ina Sam mijina yafi wancan ogan kyau ma,


       Maman omar ce ta kira wayar sahar sai da tayi mata 5 missed calls bata daga ba,after 40min sahar ta kira back tasan Maman mijinta ce tana da number amma sai tace hello who is on the line pls?,who am I speaking with? Shuru mama tayi tana jin sahar na turancinta ta gane me take fada amma baza ta iya mayar mata da turanci ba domin abdallah yana koya mata sosai shi yasa tana ji sai dai baza ta iya mayar da magana da turanci da tsayi ba.


    Sahar Maman omar CE...ohh mama ya gida ya aiki,lfy alhmdllh,sahar dama naji tafiyar da kikayi ne shine naga rashin dacewar hakan,bai....din din din mama taji an datse wayar,kira ta karayi ringing daya taji wata ta dauka tana ta watso turanci tabbas tasan sahar ce ta bada wayar dan a ci mata fuska.mama taji zafin abin sosai amma bata fadawa kowa ba,da kanta ta shirya driver ya kaita har gidan su sahar ta sanarwa iyayenta duk abinda ke faruwa,Maman sahar tabe baki tayi to ai sahar yarinya ce hajia,dole Ku dau hakuri,mu yarmu gaskia banga wani abu da takeyi ba,ya kuke abu kamar muna kauye,zamani ya canja balle ma sahar yar boko ce tana aiki babba dole sai tayi tafiye tafiye.


    Baban sahar kuwa gyaran murya yayi am hajiya za a mata fada kar Ku damu,yarinya kuma sai hakuri domin dole tayi aiki,kuma ita yar dangi ce dole sai da ziyarar yan uwa,aikinta kuma gaskia baza tayi wasa dashi ba dan yanzu rayuwa planning akeyi,amma tunda kunce tayi laifi kar Ku damu za a mata fada.haka mama ta dawo tana jimamin halayen iyayen sahar da sahar din kanta.ko omar bata fada masa ba.


     Sadiya tayi shige shige ta samo yan daban ta inda ta basu kwangilaar a sassara mata omar,in ta yiyuwa su hallakashi nan da 3wks,kudinta kaf da ta Tara na albashi shekara da shekaru ta basu.


     Ita kuwa hajiya rahina ta ajiye shawarar da haj. Bilki ta bata sai nan da wani lokaci zata fara hada makircinsu,yanzu wata kawarta hajia magajiya ta hada da wani shahararren malamin bokanta ta sanar masa so takeyi kawai omar ya bar gidan ubansa da kafarsa.yayinda haj bilki ta samu kudin da rahina ta tura mata na bokan kasar Mali ta bude makeken wajen saloon dinta dama ta gama ginawa rashin kudin siyen kayan ciki ya jawo ta kasa budewa,


    1wk da faruwar hakan Omar ya fara jin baya son Sam yaje gidansu,haka gidansa ma bai son zama ciki dole yake zama,mama kanta taga omar ya rage zuwa wajenta,sai ta dauka ko sahar ta gyara halinta ne sun shirya,har tana murna,omar sabo da mama yake daurewa watarana ya shiga gidan,dan in ya dauki hanyar gidan ji yake kamar za a zare masa rai,ga wani mugun bakin ciki da faduwar gaba,haka the same da gidansa,steal guest house nasa ma hakan take,ya canja gidaje da dama nasu amma hakan yakeji,hotel ya koma da zama yafi jin sauki,office kuwa bashi da ikon zuwa.duk wani harkar kula da dukiyar baffa sai wani manager su me amana ya dora akan komai ba wasa


    Kuma salisu manager ya kafa ya tsare kan komai,shi yasa baffa yake ganin komai normal,sadiya yaranta sun bazama Neman Omar.amma Sam sun kasa gane inda yake kwata kwata,yayinda Omar ya hada kayansa ya tare a hotel,hakanma kullum tsoratashi akeyi,ga muggan mafarkai,a firgice yake kullum,ya rame,kullum kwakwalwarsa a tunani take ina zai je yaji dadi,ya samu peace of mind,


    Omar gashi ya kasa fadawa kowa halin dayake ciki,yayi niyyar sanarwa sultan da mama sai yaji bakinsa yayi nauyi,ita kanta mama taga omar kwata kwata baya hayyacinsa,ko sun tambaya sai yace office ne,kuma sai su Dade basu Ganshi da idonsu ba,abin ya dami mama da sultan,mama ta sanarwa baffa yace suyi masa addua kawai ko da wani abun a ransa da yake damunsa wanda bamu sani ba,


     Yaran sadiya sai Neman omar suke su aikashi garin da ba a dawowa,amma abu ya fassakara,sadiya sai masifa takeyi an kasa cika mata burinta,yayin da omar ya kara boye kansa a hotel yana karbar masifu a jikinsa,


     Dan yanzu Sam ya bacewa ganin su mama,ya kashe wayoyinsa,an rasa inda ya shige,yanzu ko bacci baya iyayi da kyar yakeyin sallah ma,amma addua ta gagareshi,ko Quran ya dauka tofa faduwa yake ya sume,idan addua zaiyi sai bakin yaki motsawa,kawai gaba daya ya yanke shawarar barin hotel din ko garin abuja duka,


    Wani tunani yazo masa ransa take ya tattara trolley dinsa ya shiga taxi har kofar gidan su iklas,cike da izza ya tura gate din yana shiga gidan yaji mugun nutsuwa ta shigeshi,hankalinsa ya dawo jikinsa,ga wani ni'ima hade da nishadi a cikin zuciarsa,tofa readers,wani hanin ga Allah baiwa,haj rahina tsafinta yaci Ashe gata Allah yayiwa omar,domin yaran sadiya sun kara nemo wasu manyan yan daba duk Inda suka San wurin kashe naira na yan Hutu,na masu kudi sunje sunje amma Sam ba Omar ba labarinsa,shi yasa komai kaga ya sameka na kaddara Allah yafika sanin dalili,sonka yake.



      Sallama yayi gidan su iklas,kaka ummi ya iske ita kadai  tana kulla citta a Leda,iklas tasha baccin rana ta mike ta fito kenan tana mika hade da yin hamma,vest ce jikinta pink da skert dogo me roba.wuf ta koma daki da sauri,ummi kuwa baki ta washe tana tarbar oga umaru,a tabarmar da ummi take nan ya zauna gefenta.





Ku kara shiri readers yanzu za a fara.




       Asmabaffa

ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR

         GOMNATI

          ⓂⓂⓂ

      

             15-20




By 

Asmahbaffa




      Ina godiya masoyana masu karatu,ban San wanne irin farin ciki ma zan nuna ba yanda kuke kara min karfin gwiwa.tsakanina da Ku sai addua.



       Tunda omar ya zauna gefen kaka ummi suka gaisa bai kara magana ba,Sam ya rasa me zai ce mata,ummi kuwa ta fuskanci umaru matsalace dashi babba,tun daga yanayinsa ta gane gashi ya dan rame ya kara haske,gashi harda trolley dinsa kamar dan gudun hijira,


    Kallonsa ummi tayi a nutse kana tace umaru iceko dai lfy?naga kamar kana da damua,omar kamar zaiyi kuka amma bazai iya fadan matsalar sa ba,uhm...uhm...ummi kawai ina cikin Matsala akan lafiyar jikina,nan ne kadai Dana shigo naji nutsuwa,ban San me ya sameni ba,kawai ki tayani da addua ummi,


   Kallon omar ummi tayi tabbas iyaka gaskiarsa yayi maganar,ta tabbatar akwai Matsala tattare da omar,gashi kowa yasan babansa a kasar nan kuma da alama suma basu San matsalar dan Nasu ba,



   To umaru me kake so ayi?ina

kaje haka?ummi ko ina ya gagareni zama,nan gidan kadai naji na samu nutsuwa,jinjina lamarin ummi tayi amma har yau bata gano matsalar omar ba,dan kar ta takura masa da tambaya ta kyaleshi sai nan gaba idan ya kara samun nutsuwa,


     Umaru zaka zauna damu kafin komai ya daidai tane?cewar ummi cike da murna ya daga mata kai,murmushi ummi tayi ko ba komai gidansu zai kara armashi samun namiji tsayayye cikinsu,duk hirar nan da sukayi iklas tana labe jikin labile ta zuro kanta waje,sai da taji komai,a ranta tace to shi me ya sameshi,sai kuma ta tuno yanzu room din da take kwanciya shi za a bawa wannan ogan,


    Ta gama planning dinta an rusa mata,yanzu wajen ummi da suhaila zata koma da kwana,daki daya zasu ruguntsuma,abin haushi cewar iklas a ranta.


   Omar tunaninsa ya canja state ko ya koma wata kasar amma sabo da baffa ya ce dole ya kula da harkokinsa ba inda zaije,ummi ce ta kwalawa iklas kira,wuf ta yo waje gani ummi jeki kwashe kayanki a dakinki umaru zai zauna zuwa wani lokaci,kallonsa tayi shima kuwa ya dago da kansa sukayi 4eye,Wani sanyi iklas taji a ruhinta,idonta ta janye ta gaisar dashi,yau ya dan sakar mata ba laifi,kayanta ta kwashe tas,ta kara gyara room din sai kamshin ni'ima,daga bisani ta kai masa karamar akwatinsa ciki,alwala yayi yau a nutse yayi sallar azahar da la'asar duk a gidan,


 Suhaila kuwa murna take ta tayi dan gayu zai kwana gidansu,zasu dinga shan sweet,shi yasa ta makale kusa da omar.


     Abinci iklas iklas ta kawo masa ita tayi girkin kasancewar yau ba islamiyya,tuwon danyar shinkafa miyar egusi,da dan namansu na talaka,rabon da omar ya ci abinci a nutse haka har ya manta,iklas wani table da chair dinta ta jawo ta zauna kai ita fa bata yarda ba ma'aikaciyar gomnati ce,shi yasa in tana kai tana lissafinta wani dadi take ji,kanta kara girma yake sai ta dinga hangota kamar a office,


     Tunda omar ya fara cin abinci yake satar kallon shirmen iklas,sai yanga takeyi tana ta faman rubutu,sai da ta gama karatun schl ta jawo jotter lissafinta ta fara,har yi take tana kwankwasa tsinin Biro a dole babbar ma'aikaciyace,


     Ummi na gefe suna kallonta,har gumi ta hada  sabo da lissafi,readers duk lissafin nan da iklas keyi bai wuce kan karuwar omar da suka samu a gidan ba,dole komai yanzu na ci dashi za ayi lissafi,shi yasa take ta tarawa da ebewa,ummi ce tayi murmushi su kuruci dangin hauka,in kin gama sai ki tashi ki hadawa umaru ruwan wanka.


     Ba tare da ta dago kanta ba tace ok,sai da ta dauki lokaci me tsawo sannan ta gama ta kalli agogon dake sakale a hannunta sannan ta mike ta maida littafin palo cikin drower ta dawo,sai da omar yayi wanka sannan ya shiga dakin da aka saukeshi,gaba daya jinsa yake a takure,zafi ya dameshi,ala dole zai danyi kwanaki a gidan nan kafin ya tafiyarsa,ina Sam bazai iya rayuwa haka ba,komai a takure,dan karami kamar yana prison haka yake jinsa,dan ma akwai wuta available, Daren ranaar gaba daya ya kwashi bacci cikin nutsuwa,har makara yayi,sai 9am ya farka,su iklas yau ma Sunday ba schl,tuni har sun gama gyara gidan kawai ummi ce bata karasa musu breakfast ba,fitowa waje yayi dan toilet ma sai iya ta tsakar gida dole,brush ne a hannunsa da wani tsadajjen toothpaste, omar kwai kunyar a kallar masa jiki shi yasa da 3quater da singlet farare ya fito,harda towel dinsa,kallon yan gidan yayi yaga duk sunyi wanka kowa radau dashi,iklas ya kalla wacce ta wani hakimce a farar kujera tana latsa kuturwar wayarta,ummi ta kitchen tace umaru ka makara ni na hana a tasheka saboda naga akwai gajia jikinka,guntin murmushi yayi ya wuce toilet,kalar sabulun omarma daban suke,yana Shiga wanka iklas ta shige room dinsa zuruf ta gyareshi fes fes,aka dame masa bed,roomfreshner da turaren wutar data sa masa yafi na ko ina yawa.


     Palo suka hallara da kayan break ana jiran oga dan kwalisa ya fito,sallah yayi da addua ya shirya cikin wata jallabiyya dark brown yayi kyau,,duk gidan ya dau kamshinsa,yana fitowa ya gaisar da ummi,ta amsa tana tsokanarsa da bakunta,suhaila kuwa tsam ta mike zata je wajensa iklas ta riketa ram,zauna malama zaki je ki kama hawan masa jiki,jikinkine? Ya fada fuska tamke,ummi tace kyale iklas da iyayinta,sharesu tayi ta gaishesa ya amsa tare da jawo suhaila kusa dashi,


    Kunun gyada ne da chips girkin yayiwa omar dadi,kallon ummi yayi yace amma daga ji tsohon hanu ne yayi girkin nan ko? Daria ummi tayi sosai tasan sarai iklas yake tsokana,


     Iklas kuwa haushi taji ta katse maganar da tsohuwa yau zanje wuse market,a dawo lfy saura ki kwaso wannan yan iskan gwanjunan dangalallu da kike kwasowa,


   Baki ta turo ta Mike ta wuce room dinsu,omar kuwa har fadi yake anya kuwa iklas ba aljanu gareta ba lol,ya matsu ta tafi kasuwa ya sace book din nan da yake gani tana lissafi,so yake yaga wai me take rubutawane kullum,


     Yaso ya hanata fita amma wannan kudirin nasa yasa ya rabu da ita,fitowa tayi sanye da atamfar da omar ya dinka mata red da yellow Riga da skert,tayi kyau sosai das da ita,ansha jambaki maroon,bata daura dankwali ba,gyale siriri ta yafa a iya kanta,gata jajir da ita ta haske ko ina tal,duk suna zaune Palo ta fito,idon kaka ummi omar ya faka ya dallawa iklas harara,ya mata nuni da ido kan ta koma ta canja gyale babba,ko tasa hijab,kafada ta make cike da shagwaba ta buga kafa alamar taki din,ido ya zaro ya daure fuska yayi kamar zai mike ya kamota da gudu ta fada daki,ta dauka kamata zaiyi,tasan muguntar omar dan bata manta wahalar da Tasha ba cikin motarsa,


    Hijab tasa yellow me hannu yakai tsayin Rabin cinyarta,ummi ce ta kalleta da mamaki tace yar albarka ko kefa,Ashe kin fara hankali,a lallai shi yasa akace komai da lokacinsa,Allah miki albarka yar nan,sai kin dawo kinji jikalle,tana fita ta leko kanta taci sa'a su ummi surutu suke da suhaila,a hankali ta dan girgiza labile yanda omar zai gani,kallon wurin yayi ai kuwa suna hada ido ta murguda masa baki,shi daria ma ta bashi,a take ya saki murmushi ya nuna kansa irin ni?ido ta karkada far far ta daga kai alamar eh din,kai ya jinjina alamar zaki dawo ne.ummi ce ta juyo wuf iklas ta sake labile ta bar gidan,shi kam ogan naku wani matsewa yayi.ya dauki remote ya kunna TV,


      Kaka ummi ce tace to ni umaru na shiga zan dan matse,bacci nakeji,to ummi a fito lfy.iklas kuwa kayan ta kwashe ta maida kitchen,tana fita Omar ya sadada a dauke jotter iklas ya shige dakinsa,


    Kwancia yayi a bed ya fara dubawa,murmushi ya farayi ganin harda date take sawa,kuma kome ta rubuta sai ta zanashi,Daddawar miya ya fara gani tace ta Dari biyu for 1mnth,sannan yaga ta zana daddawa,su tattasai,da sauran kayan abinci


Yanaa ci gaba yaga irin bashin da take bi su ma gasu nan,ga wani bangaren business dinsu ne,abinda ya bashi daria kwandala in ta shiga ko ta fita sai ta rubuta,wani bangaren ma planning rayuwarsu da budged tayi na 1-2yrs,bai gama shan mamaki ba sai dayaga ko bako in akayi sai ta rubuta tayi lissafi nawa aka kashe a kansa,rufe littafin Omar yayi yana daria ganin an rubuta har dambum naman da ta bashi kwananki,komai na rayuwar gidan na lissafe a cikin littafin,gajia yayi da karantawa dan kato ne littafin,ga lissafi da rubutu kaca kaca mayar mata abinta yayi inda ya dauka,a Palo yaga suhaila na kallon cattoon, kwancia yayi a 3seater yana tunanin rayuwarsa,da mamansa halin da take ciki,


       Yana wannan tunani tare da adduar Neman agajin Allah suka tsikayo sallamar iklas ta dawo,tana shigowa ta durkusa tasan tayi laifi,sannu da hutawa oga sir



Asmabaffa

ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR 

         GOMNATI

          ⓂⓂⓂ


              20-25



By

Asmabaffa





        Tana kifta ido fiki fiki  da gani bata da gaskia,sum sum ta wuce,sannu da zuwa anty cewar suhaila, tsayawa tayi ta dawo wajen suhaila,baby ya gida,kinyi karatu kuwa?anty Sai anjima zanyi, to Allah kaimu..me kikaci after break? Ba komai anty..so kike ulcer ya kamaki ko,juyawa tayi ta shiga kitchen,cake ta ebo da fresh milk ta dawo palo,a gaban suhaila ta ajiye gashi nan maza ki cinye,komawa kitchen tayi ta ebo wasu snacks ta kawowa omar harda juice yasan tabbas iklas sai ta rubuta cikin jotter dinta omar yaci cake da lemo,


     Shi Sam baya son zaki juice kawai ya sha,iklas tana kitchen tana girki Omar ya shiga kitchen din,gwagwa take ta yi wajen yanka wata kaza amma ta kasa dan ta mata tauri,sai huci takeyi tana yarfe hannu,kusa da ita ya matsa hannu yasa ya karbi wukar,tsorata tayi sosai,ido suka hada tace kash wlh har naji tsoro,kazar ya fara yanka mata,tana gefe tana mamaki yanda ya iya aikin mata,sharp sharp ya yanka mata,satar kallonsa takeyi tare da yaba kyau irin na omar,shi wai to baya daria ne,mutum kullum shuru haka,omar kuwa yaji ajikinsa tana kallonsa,yana gamawa ya wanke hanunsa da liquid soap,yana juyowa ya dungure mata kai sai da ta kusa faduwa,kina kallona kamar baki sanni ba wth ur big eye,nuna min kayan abincinku cewar omar,


nuna masa tayi yaga suna da su amma sun kusa karewa,wayarsa ya kunna ya kira wani daga cikin yaransa,kwatancen gidan ya masa ya umarceshi ya kawo kayan abinci gidan,3hrs tsakani aka cika gidan da abinci.amma basu ga omar ba domin yana dakinsa bai son a San Inda yake ma kwata kwata,su kuwa yaransa sun zata yana office ko gidansa,ummi kuwa rasa bakin godiya sukayi a wajen omar,


      Maman omar kullum addua da kuka take zabgawa,harda kannensa su abdallah,su Aisha bangaren haj rahina sai murna sukeyi yayinda labari ya riskesu,Wanda hakan Sam baiwa sadiya dadi ba,an cuceta bata dau fansa ba,ga asarar kudin da tayi,Haj.rahina kuwa sai dadi takeji tana nishadi,baffa kuwa manager ya kira ya tabbatar omar ba a San inda yake ba shi ke kula da komai.gaba daya baffa ya daina walwala da farin ciki,Sam haj rahina ta kasa gane kansa,domin ko sakar mata fuska bayayi,tattarowa yayi suka dawo Nigeria,


    Waje waje gari gari suke bincike,sultan ne a gaba kullum basa zama Neman omar sukeyi,sadiya na hango ta Tara yan dabanta su wajen shida,tace isa a.c da usy a boy ya kuke ganin za ayi,kudina zaku bani ko kuwa yaya za muyi?isa a.c ne ya saki daria yace ke hajiya karki kawo yawa mana,ya kike mana shirme ne,a boy yace dalla malama saurara yasin sai na sokeki da wuka,karki raina mana hankali mana,ji mana ke ai munci kudinmu,taimako daya za muyi miki duk ranar da muka ganshi idonmu idonsa zamu cika miki burinki,idan kuma bamu gani ba sai ki ware kawai ko ya kukace.a boy ya zuki sigari ya fesawa sadiya yace ware kawai hajia kar ki bari na canja mind dina na murde miki wuya


     Tsorata sadiya tayi jiki na rawa tace kuyi hakuri ko me kukayi dai dai ne,hakan ma is OK,motarta ta figa a 100 ta bar wajen,a boy ne ya kalli yaransa suka kwashe da daria kana yace men this girl inaaaa ey na bad girl,she stingy bad.wani ciki ashar ya kunduma yar kut...da wani dry leg nata,ko shape babu komai flat.


      Hajiya rahina tsabar yawan bokayen da tabawa aiki ba a San Wanda aikinsa ya ci omar ba,kowa kawai ta yarda kawai.ciki kuwa har karyar su HAJ bilki kawayenta.


     Dare ya tsala kishirwa ta fito daga room dinsu shan ruwa,tazo Palo ta jiyo nishi dakin omar sosai abin tsoro,lallabawa tayi ta shiga dakin omar a hankali ta murda kofar ta shiga,


     A kudundune ta Ganshi ya hada gumi yana ta karkarwa yana nishi,da gani mafarkin abin tsoro yakeyi,sai ciccijewa yake yana tirje tirje,tausayinsa iklas taji sosai karasawa jikin gadon tayi ta zauna gefen bed din hade da kura masa ido,A hankali tasa hannunta a kafadarsa kamar jira yakeyi ya juyo a sa hannu biyu ya damke hannun hade da kankamesa a kirjinsa,shuru iklas tayi tana matukar tausayawa oga,da gani matsala ce jikinsa babba,ba tare da ta zare hannunba ta Kurawa hadaddiyar sumarsa ido,tasha gyara tana kyalli yalala da ita,kamar TV haka ta kurawa surar Omar ido,ta shagala sosai sai da ta share lokaci me tsawo,farkaawar da Omar yayi ita ta dai daitawa iklas nutsuwarta,


     Zumbur ya mike zaune yana kallonta tare da mamakin rike hannunta da yayi a kirjinsa,mamakin iklas shine yana rike hannunta taga ya daina karkarwar tsoron,sannu oga sir,hannu takai zata taba wuyansa,make hannun Omar yayi ya watsa mata harara mind ur business pls,ruwa kawai zaki kawo min nasha,ni ba irin su Emma bane as u can see musulmi ne ni,so u better get ths in to ur skull, ki daina gigin taba min precious skin dina.


    Baki iklas ta tabe a fili tace sannu muslimu daga taimako,kuma hannuna kai ka kamashi zuwa jikinka anji hannun yarinya me laushi ba a sababa an wani kankameshi,wuf ta fece daga dakin,dan dai kawai ta tausaya masa ne amma da wlh baza ta kaimasa ruwan ba,


      Ruwa ta dauka faro da glass cup ta koma room din,sadaf sadaf ta ajiye can nesa dashi a tsorace take kadan take jira ta zura da gudu,kafafunsa ya daga hade da dafa cinya alamar zai mike,kararaf ta kwasa da gudu ai kuwa ta daki kofa da hancintaa garin gudu ji kake fas,wayyoooo ta furta hade da rike hanci,kara kwasa tayi da gudu zata arce,caraf omar ya riko hannunta ba tare da yayi magana ba ya cire hannun da ta rike hancin,


      Jini kadan ya gani alamar ta fara habo kadan,gashi kan tsinin hancin yayi ja ya kwarzane kadan,tissue ya dauko ya matsa jikinta sosai suna jin numfashin juna,tuni jikin Omar har ya shocking yana rawa a cikin jininsa,


     Ita kuwa iklas wani kasala kasala taji kamar ya danyi hugging dinta haka taji,daurewa kowanne yayi cikinsu,hannu yasa ya dago fuskarta ya goge mata hancin tas,yana karewa pink lips dinta kaallo,kamar ya dan.....lol


      Kije toilet ki wanke cewar omar, mika mata tissue yayi har wacce ya goge mata hancin, jeki nyt.cike da tunanin kyan dirin Omar ta fice,toilet ta shiga sannan ta koma dakinsu,


    Kaka ummi ke kuwa iklas zawo kikeyi ne?kin Dade daga cewa zaki sha ruwa sannan kiyi fitsari,ummi bigewa nayi da kofar toilet kinga habo ma nayi,sallallami kaaka tayi tana ta faman yiwa iklas saannu,harda shafa mata magani a hancin wajen da ta kwarzane,


   Ni kuwa nace su iklas badai iya karya ba.kwanciya sukayi kowannensu cike yake da tunani kala kala,iklas an kalli ceiling anyi kuri da ido ana tuno kasancewarta tare da Omar dazu,duk sonta da aikin gomnati sai taji da tayi tunanin salary ko ta gama schl ta fara aiki,ga mota tana ja,suna zaga kasashe ita da su suhailanta sai taji yanzu kamar tafi jin dadin tunanin oga omar,kawai fuskarsa in ta tuno dadi take ji,a'a juyi ta karayi taja tsaki,yanda omar ke daure fuska ta tuno sai taji sanyi,a ranta tace oh zuciyata yanzu fushin nasa ma birgeki yakeyi tab,da kyar bacci ya sace iklas,bangaren omar kuwa mugun mafarkin da yayi yake tunani,ga tunanin family dinsa musamman mama ko a wanne halin take oho,rayuwar da yake ciki yanzu ya tuno da iklas me kwai sai yaji dan sanyi a ransa,ya yanke shawarar yanda zai sa iklas ta masa wani acting yanda zaiji lafiyar mama da baffansa,hade da kwantar da hankalinsu,yasan iklas tsab zata iya,ko ya wannan abu zai kasance readers oho,za dai muji nan gaba.da wannan shima yayi bacci,


    Da safe su iklas sunyi shirin schl,omar kuwa fitowa yayi so yake yaga ya hancin iklas yayi,uniform ya gani sun mata kyau,bai taba ganin wacce uniform yawa kyau haka ba irin iklas,kallo ya kare mata suka gaisar dashi,ummi ma ya gaisheta,iklas ya kalla ya kara fakar idon ummi ya dagawa iklas gira daya,hade da nuna hancinsa yana murmushi me kayatarwa,tasan tsokanarta yakeyi ba wani dubiya,baki ta turo,ta juya masa baya tana yaba muguntar omar,ummi ta juya tana gyarawa suhaila jaka ya dan ja hijab din iklas kadan,waigowa tayi itama ta dage masa gira daya,alama yake mata da hannu kamar kurame,kaka ummi ta tarfa su,sosai sun bata daria,umaru shirmen iklas kake kulawa ko,so kake ka koyi shiriritarta naga alama,ummi kalli hancin ta fa,hmmm umaru baka da dama ai jiya a bayi ta bige da kofa,ta dade tana habo,da kyar ta samu tayi bacci,daria omar yayi sosai jin karyar da iklas ta tafka,kallonta yayi suna hada ido ta kifta masa wai ya rufa mata asiri,kafada ya rike alamar yaki din,kaka ummi na kallonsu tace ohhh yau kuma umaru kurame kuka zama haka,wlh ka daina saurarar iklas,ummi wannan jikar taki bata ji ne cewar omar. 


wani yaronsa daban Omar ya kara kira ya gwada masa gidan su iklas,dalleliyar wata motar omar ya dakko ya kai su iklas schl,sai kallon su iklas akeyi a schl.


     Shima dai Wanda ya kai su iklas schl bai San daga ina omar ya kirashi ba,gashi ko wanne da new sim yake kiransu,kuma yan amanarsa yake sawa aikin Wanda yasan duk runtsi baza su bashi matsala ba,kowanne sai ya gargadeshi kar ya fadi ya kirashi a waya.


    Iklas kam yau daga schl company ta wuce ta saro kaya,yaron omar ne ya kaisu ko ina ya dawo dasu gidansu sannan ya tafi


     Kafin su iklas su dawo omar ya fadawa ummi zai aiki iklas gidansu ta gano masa lafiyar iyayensa,umaru kai da kanwarka sai ka nemi izinina,dadi yaji sosai su iklas na dawowa ya sata ta shirya cikin doguwar Riga da mayafinta,wajensa taje yana zaune tsakar gida a kan kujera sanye da Riga armless fara,da black jean gashin kansa ya kara yawa,


       Ummi tana Palo suhaila na gefenta suna kallo da cin abinci,envelop ya mika mata nan ya Shiga tsara mata yanda zata yi acting a gidan nasu, hhhhhh iklas ta kama daria yanda taga Omar ya gwada maganar mata, kallonta ya tsaya yi,yanda daria ke matukar yi mata kyau, tsayawa tayi da dariar ganin omar ya kafeta da ido,daga bisani tace action ta fara gwada masa yanda ya koya mata har kara masa idea tayi,sosai sunji dadin moment din,iklas uwar shirme ji tayi inama suyi ta yin wannan film haka me dadi.


     Kudi ya mika mata na taxi tare da address ta tafi kuwa.yau zata ga gidan su oga da family nasa,ya za aga haduwar su cewar iklas.


    Sahar kam sai Allah ita cewa tayi Omar makaryacine yana can London munafiki za a ce ya bata kato dashi,to saceshi za ayi dan haka iyayenta suka ce ta dawo gida tayi zamanta tayi aikinta.haka kuwa akayi ta kwashe komai nata tas ta bar gidan cike da nishadi ta samu yanci.


    Tun daga waje iklas take kallon haduwar gida kamar baza a mutu ba,gate ta buga,masu gadi wajen biyar suka leko ganin tsaleliya iklas suka ce wannan da gani kawar yan gidan nan ce,suma mamakin kyan iklas sukeyi kamar larabiya,gashi da ganin rigarta ta masu kudi ce,dama a rigunan da Omar ya batane tasa daya,


    Da sauri sukace ta shiga suna ciki,tana shiga nan ta rantse a ranta da zata yi bacci ta farka ta ganta a wannan gidan to cewar zatayi ta mutu tana aljanna.


       


  Asmabaffa

ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR 

         GOMNATI

          ⓂⓂⓂ


              25-30


By

Asmabaffa




    Page din nan naki ne DIYAR KATIBI.




    Tunani iklas tayi domin omar ya gwada mata yanda gidan nasu yake ba tare da tasha wahala ba ta gane part din maman omar,shiga tayi dakin part din tare da danna door bell din da omar ya fada mata,abdallah ne ya bude kofar,iklas dauke da hand bag a hannu an wani shanye hannu irin na wayayyun mata,kallon abdallah tayi da ganinsa kasan kanin oga omar ne,


     Kallonsa iklas tayi pls mama nake nema,OK shigo tana ciki cewar abdallah sai bin iklas yakeyi da kallo yanda yaga baby me kyau haka,shiga ciki tayi salati take maimaitawa a ranta yanda taga tsaruwan palon,a kujera ta zauna abdallah kuma ya hau sama domin kiran mama,suleim ce ta fito cikin shirin islamiyya,sannu da zuwa ina yini cewar suleim,lfy zo mana mu gaisa cewar iklas,zama tayi kusa da iklas,can iklas ta kunna video recording a wayarta tana daukan suleim,wani katon pic din omar ta gani a palon,suleim waccen yayankine?ae anty amma ya bace,an nemeshi ba a Ganshi ba,mama kullum sai ta yi kuka tana ta addua,dady ma addua yace mana mu  dinga yi,kinga su anty sadiya kuwa nurma sukeyi sosai,har kida suka kunna a gidan nan,suleim kwai surutu.


    Yanzu in suka ganmu da mama suyi ta mana daria,kuma anty sahar matar yaya omar ta gudu gidansu wai ba za ta zauna gidansa ba,gaban iklas ne ya yanke ya fadi jin an ambaci matar yaya omar,dama yana da mata? Take taji wani bakin ciki a ranta,gabaa daya jikinta yayi sanyi,cikin kankanin lokaci suleim ta bawa iklas labarin gidansu,duk da batasan su waye anty sadiya ba,suna haka mama ta fito ita da abdallah,yi tayi kamar tana latsa waya nan kuwa video take musu,tsugunawa tayi cike da ladabi ta gaisar da mama,mama kuwa me aiki tasa ta kawowa iklas kayan motsa baki,


  Ganin kalar girkin hadadde yasa iklas sauka kasa ta baje kamar gidan ubanta ta kama cin abincin cikin dabara takewa kanta video record tana cika baki da abinci,


    Mama da abdallah har suleim daria sukeyi ita kuwa iklas tana sani tayi haka dan su saba da ita,sai da taci ta koshi sannan ta kalli mama tace mama wlh har na dawo hayyacina bakuga wahalar Dana sha ba kafin na gano gidan nan,kwashe kayan mama tasa akayi,yan mata meke tafe dake ne? inji mama,sultan ne yayi sallama ya shigo palon,iklas taso ta ganeshi amma ta rasa Inda ta sanshi,shima bangaren sultan hakan take sai kare mata kallo yakeyi ya kasa ganeta,domin tun iklas na tallan kwai ya taba ganinta,yanzu kuwa ta kara haske,kiba,kyau da girma.


      Zama yayi suka gaisa da mama,iklas ma ta gaisar dashi,shi dai sultan wannan bai taba ganin me kyau irinta ba sai me tallan kwai da apple ta Frnd dinsa omar,kai har muryarma suna kama,amma wannan da gani yar masu kudi ce,waccen talakace haka Allah ke ikonsa wani ba dangi yayi kama da wani duk a ransa sultan ke wannan tunani.


      Iklas ce taga sultan na kallonta,shima sai da ta masa video record,mama iklas ta kalla tace mama dama wannan na hoton tayi nuni da yatsanta jikin pic din omar dake jikin bango ne,harrrrr su mama sukayi aka zubawa iklas ido a ji bayaninta,naje company dinsu Neman aiki da dan dadewa,shine aka turani office dinsa naje interview,shine yace bazan samu aiki a company dinsu ba,amma nayi hakuri kuma yana Neman alfarmata na kawo wa mamansa sako,


      Shi zaiyi tafiya ne,har naki karba amma ya dage,mama baki gani ba har kuka yayi kan sai nazo gida wajenki na baki sakon,Baku gani ba abin tausayi har kuka ya min cewar bashi da kowa da sukafi mama da baffa,sune farin cikinsa iklas ta karashe tana matsar kwalla,mama tace Allahu akbar da su suleim tuni hawaye na ambaliya a fuskarsu jin labarin omar,tabbas iklas ta tausaya musu amma ta dau alkawarin gano wannan lamarin dake faruwa da omar da family sa ko zata tallafa.


    Sultan ke bawa su mama baki bayan sun nutsu iklas ta zaro envelop daga jakarta ta mikawa mama,wannan yace na kawo miki,Allah bai bani iko ba sai yau,


       Mama batasan karantawa don bata so ta karantowa kanta bacin rai,sabo da wannan ta mikawa sultan takarda,sultan nutsuwa yayi yana karantawa can su mama suka ga yana daria da fara'a wannan ya nuna sakon dadi ne bana bacin rai ba.


    Kwace takar dar mama tayi taga guntun rubutu ne ma,fara karantawa tayi kamar haka:


    SALAM......MAMA NAYI MATUKAR KEWARKI BURINA KI DAGE MIN DA ADDUA INA DA MATSALA A LFYR JIKINA,KI BAWA BAFFA YA KARANTA DA KANNENA SULEIM DA ABDALLAH,NAYI KEWARKU,SULTAN MA ABASHI HAKURI,INA NAN A NIGERIA MAMA CIKIN KOSHIN LFY,BANYI NISA DAKU BA,ZAN DAWO SOON,KUNSAN BAZAN TABA YIN ABU BA KWAKWARAN DALILI BA,A SANARWA BAFFA NASAN SHIMA ZAI FAHIMTA.


    Dadi mama taji dukkansu sai murna da jin dadi sukeyi,iklas kuwa sai video take musu,mama ce ta rungumeta yata yar albarka mun gode kwarai,kowa godiya yakewa iklas,mama tace yaushe ya baki sakon?ya kai week nawa?sati dayafa kenan cewar iklas,,take kowa ya kara cika da murna,suka tabbatar da Omar yana kusa kuma lfy yake,hankalinsu ya kwanta,


       Dakin baffa mama ta nufa yana ciki ta shiga ta labarta masa komai tare da mika masa takardar,yana gamawa ya dago fuska cike da annuri,dama na fada miki ki kwantar da hankalinki yana nan ni nasan son namijin gaske ne, sai mu dage masa da addua,kira min yarinyar na ganta,


     Tare da mama suka Shiga dakin baffa,a kunyace iklas ta durkusa har kasa ta gaida shi,da fara'a ya amsa tare da yaba tarbiyarta,mama hakan take,daga bisani mama tace ki saki jikinki duk lokacin da kiga kina da lokaci ki dinga bullowa muna gaisawa,baffa ya kalli hajia baki fada min sunanta ba,oh kaga murna tasa na kasa tambayarta,yar albarka ya sunanki? UMMI kawai tace,bata San wanne suna zata ce ba.


      Palo suka dawo iklas ta mike rashe rashe kwance kan 3seater tana ta yiwa kanta selfie,taga gida me kyau,


    Suleim ta jawo da uniform tayi musu pic kala kala,abdallah ma haka,mama na gefe amma saida iklas ta dauka da ita,sultan ma kiransa tayi ya manne gefenta ta musu  kala 3.duk tayi ne sabo da ta nunawa oga omar.


       Sai daria take basu iklas ba boye boye waje ya burgeta ta yaba.sai 5pm tawa su mama sallama,an cika iklas da sha tara ta arziki,mama turaruka,atamfa kala biyu,baffa 20k ya bata,sultan ma 10k ya bata,ta fito tsakar gidan kenan iyayin iklas ya kaita ta dinga zagaya compound tana ta daukan selfie,har jikin motoci,tana haka ta kai garden,yaran haj rahina ta hango birjik a garden.


      Lallabawa tayi taji Suna ta gulmar su Omar suna zancen asiri,bata karasa ji ba sukayi karo da Aisha,kallonta Aisha tayi take taji ta tsani iklas,ga bakin cikin kyau da taga iklas ta fisu kaf,tayi imani wannan tafi omar ma kyau,


     Kwalar iklas Aisha taci ke gidan ubanwa zaki,?gidan ubanki cewar iklas,ai tuni su sadiya ma suka karaso wajen,iklas taga tabbas zaneta zasuyi,da sauri tace kuyi hakuri Ku saurareni, wajen sadiya aka aiko ni,sadiya cike da bala'i tace gani lfy,karewa sadiya kallo tayi tana tuno maganganun suleim yanda sadiya ta tsanesu ta tsani yaya Omar.a kan me za a zagi oga wlh ba a isa ba kunji iklas da karfin Halifax.


      Gajiya sadiya tayi ta dakawa iklas tsawa ke karki raina mana hankali fa,duka iklas ta makawa sadiya a kirji,ba tare da  sadiya tayi tsammani ba,,tana juyowa ta dullukawa Aisha dundu ji kake dummmmm ta arce da uban gudu, gateman sunga komai,su kansu dadi suka ji,domin su aisha sun gallabesu,tana zuwa gate cike da murna suka wangale mata kofa tace na gode da karfi ta ci gaba da gudu,saida tayi nisa da gidan sannan ta Shiga taxi sai gida.


      Su sadia kuwa sunyi suman tsaye,Aisha tace billahillazi duk ranar Dana hadu da yarinyar nan....wlh.....hmm...sai na kusa zare mata numfashi. Sadiya kasa magana tayi tsabar bacin rai,yarinya karama ta kwada mata duka haka.


           Taxi na tsayawa ta wuce gida sai daria takeyi hade da haki kamar tayi gasar tsere.oga Omar yana kwance a Palo bacci ya fara daukansa dan ya gaji da jiran dawowar iklas,dariarta ya jiyo ya fito waje sanye da wata dakakkiyar gezna milk color,yasha kyau,


       Fuska tamke kamar kullum ya kalli iklas ke lfy,kusa dashi tazo tana tuntsira daria hannunsa ta kamo,yarrrr omar yaji bai San sanda ya fisge hannunsa ba,kara sakalo hannunsa tayi ta jawoshi tsakar gidan tana murmushi ta shimfida musu tabarma,kaka ummi tana kallonsu domin fitowarta kenan zata je makwafta,murmushin manya tayi tasan iklas bata fiye tsoron maza ba ta saba da gogayya dasu,tayi talla a kwalta,ga unguwarsu hausawa kadan ne,dole mutum ya tashi haka,danma iklas kwai tarbiya,  sallama ta yi musu ta tafi gidan suna makwafta zasuyi aikin abinci sai dare zata dawo,


    Suhaila ce itama tayi sallama ta dawo daga islaamiyya,oyoyo beauty cewar omar dadi suhaila taji tace sannu da gida yaya omar,ta wucewarta dakinsu, 

 

      Iklas kuwa kalonta ta mayar gefen omar,sir dole kasha lbr yau,nan iklas ta kwashe komai ta fada masa,sannan ta nuna masa video da ta musu,omar harda kwalla ganin mama da yan uwansa abin sha'awa, yayinda iklas ta bashi daria sabo da shirmen da ta dinga yi a gidansu,kamar irin yar gida,omarma ji yayi hankalinsa ya kwanta ya kara samun nutsuwa.


      Kinyi kokari yan mata cewar omar,iklas kuwa cinyar omar ta dafa kasan me nake wa daria,zame cinyarsa omar yayi,ita kuwa iklas kallon omar takeyi kaamar jininta,kamar dan uwanta,kuma ita bada wata manufa take taba jikinsa ba,ga kuma unguwarsu sun saba da hakan sabo da yaren da suke unguwarsu,wannan ba komai bane wajensu.


      Wai pls oga sir su waye sadiya ne?kar ki kara ce min wani oga ko sir,sunana omar..sorry to ya omar,ina jinki suna ta zaginka da su mama har zance asiri sukeyi,ban gama ji ba mukayi fada.fada kuma?cewar omar,sisters dinane fa,shekewa da daria iklas tayi ta manta ta sake riko hannun omar daya,kash wannan zata kasheni wlh batasan yanayin Dana ke shiga ba a zuci yayi maganar,daya hannnun yasa ya cire hannun iklas a jikinsa,ji yayi hannunta kamar Auduga dan laushi.


Video ta kunna masa fadansu da su sadiya omar kanshi yasha dariar abin,sau 2 yana kalla,drama queen dama sun zaneki,tab ai wlh basu isa ba,wannan sadiyan me siri siri kafa kamar ta sauro,wasu zagada zagada dasu,tab Allah gidanku ya omar rida ridan tsofaffine ciki hhhh kaga wata me kwalliyar aljanu kuwa,baki ya bige mata sannan tayi shuru,kayan da ta samo ta nuna masa.


     Yana gani yace kinji dadinki,wayarta ya karba ya dinga kallon pics din iklas a cikingidansu,sai daria yakeyi,mikewa tayi zata kwace wayarta ta fara jin haushin dariar da yake mata,hanata yayi tana kokarin kwacewa ta kasa,sai haki takeyi,


   Zuwa tayi da iya karfinta zata makalkaleshi da sauri ya mike tsaye ya matsa kamar irin yaga wuta zata konashi,bai son ta haddasa masa masifar da take jawo masa da zarar ta rabi jikinsa,


    Pics yaci gaba da kalla har yazo kan nata da sultan,gani yayi kafadan sultan tana gogan ta iklas,wani takaicin iklas yakeji,zuciyansa ce yaji ta baci,ga wani kishi daya taso masa,wato ma yanda take taba shi haka takewa kowa,ai kuwa sai yayi maganinta,sai ta daina shashancin taba jikin ko wanne namiji.


     Kara kalla yayi yaga wato pics dinsu da sultan har kala 3.bai San sanda ya kwarankwatsa wayar da kasa ba,sai da tayi warka warka,tayi raga raga.tsaki yaja cike da bacin rai ya ficewarsa daga gidan baki daya.


Abinda Omar bai taba yi ba kenan,tunda ya dawo gidan su iklas bai taba gigin fita ba sabo da tsoron yanayin lafiyarsa.


   Iklas tayi matukar firgita kamar me aljanu,daga yi masa abin arziki ya zama tsiya


    Tsoro taji kar ummi ta dawo ta tadda Omar ya bar gidan,tasan yanda ummi ke kaunar omar,gashi bata San me yasa ya dawo gidansu da zama ba,,duk irin arziki da Allah ya musu,yanke shawara tayi gwara fa tabi bayansa ta dawo dashi.da gudu ta bi bayansa kamar zata tashi sama.


   Titin layinsu ta mike a 80 tunda uwarta ta kawota duniya bata taba yin gudu irin wannan ba,sai tareta matasa keyi suna gomanti gomnati,iklas amma ina Sam bata ji bata gani,


    Wani uban lungu ta shawo kwana,wata majalasa ce guda ta maza,sun hango gomanti na sheka gudu,wani cikinsu tace hey weyting?iklas tana gudu tace ba lfy ta wucesu fuuuuu...suna gani haka suma suka kwasa da gudu suka rufa mata baya.


     Tazo dai dai jikin wani shago taji an riketa caraf da mugun karfi,ido 4 sukayi da omar,da karfi tazo zata rungumeshi tana murmushi hade da Jan numfashi,gocewa yayi da sauri ya matsa ta rungumi iska,


     Kunya taji ganin namiji yafita kamewa da taka tsantsan.




Ayi min afwa idan an samu matsala readers dan Adam ajizine.



Ina ji dake MAMAN SULTAN.

     


Asmabaffa

ⓂⓂⓂ

     MA'AIKACIYAR

          GOMNATI

           ⓂⓂⓂ


               30-35


By

Asmahbaffa



    Masoyana masu karanta wannan novel duk inda kuke a kasar nan ga gaisuwata na sauke muku mota mota,kwando kwando.ina jinjina Allah kara nisan kwana me amfani da karfin ido.ayi min afwa kwana biyu banyi posting ba.




        Me hali baya fasawa fuskar nan kamar Wanda akace mama ta rasu! haka take a daure,tunda omar yabar gidan su iklas gabansa ya kara faduwa,gaba daya tsoro da fargarba ne ya shigeshi Wanda bai San dalili ba,tuni yaji ciwonsa ya fara dawo masa,yayi niyyar kiran driver sa domin ya gwada zuwa gida wajen mama,amma me yana fitowa daga gidan hankalinsa ya tashi,ji yake kamar ana hura masa wuta a jikinsa,gaba daya ya fita a tunaninsa,ji yayi yana neman sumewa shine ya tsaya dai dai jikin shagon da ya hango iklas na famfara gudu,cikin zafin nama ya riketa dan tabbas ya San nemansa ta fito yi,gashi magriba ma tayi,

  

    Iklas kuwa tunda taji kunyar gocewa da omar yayi dan kar ta rungumeshi, ido ta kafa masa,nan ta hango jikin omar na rawa kaf kaf kamar mazari,ga gumi na keto masa duk da cewar ba a Dade da dauke ruwan sama ba,kara kura masa ido tayi nan fa ya fara dafe kirji yana cije lips kamar zai fadi,idonsa sai wani lumshewa sukeyi,tsoro ne ya kamata,sir....ya omar wai lafiyarka kuwa?

 

      Hannu ta kai zata kama hannunsa ya boye hannun,fuska ta daure itama ta fisgo hannun nasa tare da cewa! muje gida ya omar baka da lfy,rike take dashi gam,shi kuwa ba musu ya bita,suka jera abin sha'awa kowannensu na ji da kansa wajen baiwa.

    

   Duk inda suka ratsa sai an kallesu an kara kalla,duk sun haske unguwar,kowa nuna gomnati yakeyi suna ai bro dinta ne yazo,me kudi ne,gashi nan gomnati ta daina talla,ta zama yer gayu,maganganu kala kala.


       Gida suka karaso lokacin Omar ya fara nishi ma zai fadi kasa,da sallama suka shiga,yana zura kafarsa daya cikin gidan yaji wani azababbiyar niima da kwanciyar hankali,take yaji gaba daya ciwonsa ya yaye lokaci daya...a ransa ya furta lallai wannan gidan ni'ima ne,


      Bayan sallar isha kaka ummi ta dawo daga unguwa,yanzu most of d time omar ke wa suhaila assignment, yau ma hakane shi yayi mata homework, 


misalin karfe 1 na dare iklas ta farka,hanklinta ya kasa kwanciya tana tunanin ya omar karfa ko bashi da lfy,


       Mika da hamma tayi ta kama shagwaba tana ummi fitsari ki rakani,farkawar ummi keda wuya ta fara masifa ba inda zani da tsohon Daren nan,ke kenan fitsari da zawo,dama haka iklas ke so,ficewa tayi sadaf sadaf da sanda ta murda dakin omar,a zaune ta ganshi yayi tagumi a gefen bed,dago kansa yayi yasan dama sai ita,


     A tsorace ta karasa kusa dashi sir omar bacci ka kasa yi ne?harara ya watsa mata,ki daina zuwa wajena da dare ko ba komai sabo da gudun zargi,ba kya jin magana,ki daina sani magana fa tam,baki ta turo kai ya omar Allah baka San a ma gwaninta ba,me zanyi ma ina tunanin ko baka da lfy ne that's y na leko ka,OK tnx as u can see am fine sai ki tafi.


    A shagwabe tana buga kafa to kayi bacci mana,dan ta tafi kawai sai omar ya kwanta a bed din,kafin ya mike kafarsa ta karasa ta hada leg nasa wuri daya ta mikar masa dasu,blanket taja ta rufa masa,a.c ta kara karfinta kana ta kashe masa light,ta fice zuwa dakinsu,da rarrafe ta shiga dan kar kaka taji tafiyarta, kwantawa  tayi ta  bar omar da tunaninta, yanda ta iya kula da mutum , wai bata ma auri mutum ba kenan  ina ga ta aureshi.lallai mijinta ya more,sahar dinsa ya tuno wacce ko kallon arziki bata yi masa bare ta gyara masa kwanciya,wai a haka ta waye kuma yar boko,ga me talla nayin abinda ta gagara yi.


    3days later omar yasa an kawowa suhaila sweet da snacks,wayoyinsa duka a flymode suke yana buga game a Palo,yayin da suhaila da ummi suka tafi kasuwa,iklas ta tafi kai kayan siyarwarsu makwafta,Omar bacci ne ya daukeshi a Palo,nan ya shiga mugayen mafarkansa kamar kullum,ya hada zufa,sai nishi yakeyi,iklas ce ta dawo da Sauri ta fada palon,tsugunawa tayi kasan kujerar da omar ke kwance,addua ta shiga tofa masa,falaq da nas,fatiha,ayatulkursiyyu,amanarrasulu,can taga ya daina mafarkin,dadi taji tace kai Ashe zan iya rukiyya ma in na dage,


     Omar ne ya bude idonsa cike da bacci,tashi yayi zaune, a hankali ya bude idonsa tare da aza su kan kyakyawar fuskar iklas jinjina kai yayi,a ransa yana fadin wannan yarinya tana da nacin tsiya,ruwa ta dauko masa da sauri,a ransa yace ikon Allah kaga shishigi.


       A gabansa ta tsugunaa tare da kallonsa cike da tausayawa, Jim kadan tace pls sir ka fada mana abinda ke damunka,inma baza ka fada min ba ka sanarwa ummi,in kuma baka son ummi ta sani ka fada min zan boye ma sirrinka,


   Maybe zamu iya baka shawara,bai dace ka zauna haka ba,in kuma kaki to zan fadawa ummi mafarkan danaga kanayi da kuma time din Dana ganka a bakin shago,


    Ido kawai ya zubamata yana kallonta har ta gama.Hannun iklas ya riko da hannu biyu ya zaunar da ita a kujera,kinyi alkawari in na fada miki baza ki fadawa kowa ba?da sauri  iklas tace ae wlh sai in kai kace na fada,I mean sai da yardarka.Good muje tsakar gida to sai na fada miki,cike da zumudi tayi waje.


    Farar kujera ta mika masa ya zauna itama haka,har sun dauki kusan 20mnt amma omar ya kasa bude baki yace komai,a zuciyarsa har ga Allah yana so ya fadawa wani matsalarsa ko zai bashi shawara amma ya kasa,daga lokacin da yayi niyyar sanarwa wani sai ya kasa furtawa.


     Gajia iklas tayi da zama ta kirashi cike da sanyin murya,ya omar kayi shuru,kallonta ya kara yi ba tare da yace komai ba,sunyi wurin 30mnt amma yaki magana


     Da kyar da sidin goshi ya cije ya furta bani da lfy a jikina,kamar ya?cewar iklas shuru yayi mata,haka ta hakura ta kyaleshi tunda ya kasa cewa komai,ita kuma bata gane me yake nufi ba.


     Har ta mike zata wuce  sai ta fasa ta dawo ta zauna inda ta tashi,tana zama ya zuba mata ido daga bisani yace zan fada miki next time not know,


     Zuciyar omar kuwa ko ya yi niyyar fadi sai yaji a cikin ransa ana gargadinsa,zuciyarsa na tafarfasa,bakinsa yayi nauyi sai ya kasa fada.


    Ya schl yanzu aji nawa kike?cewar omar dan kawai ya canja zance.suna hira su ummi suka dawo,ummi sai Murna takeyi ganin iklas tare da yaron kirki umaru.


     Bangaren sahar kuwa duniya take tsikara da tsinke,babu ta inda bata cokalar duniya,ta manta ma da aure a kanta.

Mama da baffa sun yanke hukuncin zuwa gidan su sahar domin yin bikonta. 


    IKLAS na gidansu yau Sunday haka kawai taji yau ta tashi da masifa,ji tayi duniyar ta mata zafi,kamar ta kunnawa kanta wuta,kowa ta tsaneshi,magana kadan sai ta balbale mutum da masifa,


   Ita kanta ta rasa dalili, mamakin kanta takeyi,omar na kallonta yanda takewa ummi da suhaila,da safe ma sai da ta Zane suhaila akan kallon film.iklas tana kwance ta baje a tabarma tsakar gida,omar na gyarawa suhaila farce yayinda ummi ke kitchen,haka kawai sukaji iklas a ta fashe da kuka wiwi. Kuka take sharba sosai tsakaninta da Allah,Har shidewa takeyi.


    Kallonta omar yayi da sauri ke kumafa?lfy kikewa mutane kuka,da ganinta yasan akwai matsala,ummi kuwa fada ta kamayi me yasa zaka saurareta umaru tunda ta zama shashasha ba sai tayi ba,yarinyar nan tun safe take bala'i! haka kawai ki dauki halayyar banza da wofi,wlh bazan laminci iskanci ba.


Omar bai so fadan kaka ummi ba sai yaji haushi danme zatayiwa iklas fada,ai ruwa baya tsami banza tunda iklas tana da juria haka kawai baza tayi kuka ba


A fili yace ummi ki kyaleta maybe tana da damua ne,pls ya fada da kalar tausayi,hmm ai dama nasan kai umaru baka ganin laifinta biye mata kakeyi shi yasa take kara shagwaba.murmushi yayi ba tare da yace komai ba,sai gomnati da ya kafe da ido wacce take ta sheshekar kuka harma da jingina kanta ki?? Jikin bango tana ta yi.


     Ranar haka ta kwana tana kunci da bakin ciki,washe gari Monday haka ma taje schl kowa cin ubansa takeyi ba mutunci...


     11:30am dai dai suna class taji kamar danshi a kasanta ita kanta ji takeyi kamar acikin ruwa ta zauna,mikewa tayi tsaye ,Ai firgita tayi sosai,tabbas shine! jini ne,wato abinda takejin lbr period, ta fara itama,abin yazo kanta.


   Kunya taji yau kam ba zaman schl dole ta tafi gida,hijab din wata Christian da bata sawa ta ara, ta daura saman rigarta ta rufe wurin daya bata mata uniform.


    Omar zaune a Palo yana danna computer sanye cikin jallabiyya yar ubansu fara sai kamshi yakeyi,sumansa tayi yawa sosai sabo da ya jima baije an rage masa ita ba,sai ya kara kyau musamman da baya fita sai ya kara haske da sheki.


     Ummi na gefensa suna ta labari,iklas ce ta shigo ko sallama babu ta wuce su ummi da omar fuuuuuuuu kamar zata tashi sama,su har sun tsoratama suna tunanin ko lfy.


    Minti 2 tsakani ta kara fitowa daga room dinsu wannan karan har gudu ta hada dashi,waje tayi kofar gida wani shago ta shiga,pad ta siyo ta kara dawowa ta wuce su ummi,sai gata ta fito da Riga,da wasu tarkace a Leda,toilet ta fada karaf...... kararaf ta rufe kofar,suna jinta tana ta kwaramniya da botiki da ruwa.





Asmabaffa

ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR 

         GOMNATI

          ⓂⓂⓂ


             35-40



By

Asmahbaffa




        Ta kai wurin 1hr a toilet sannan ta fito,mikewa omar yayi ya leka ta window ya hango iklas tana shanya kaya,daure take da zani da hijab a jikinta,


 Omar ganin iklas ta wanke uniform dinta ya sashi nazari ko lfy?amma dole sai ya tambayeta yaji meke faruwa da ita, Shanyar ta gama ta shigo palon da sallama, kaka ummi ce ta amsa tare da kallon iklas sama da kasa,ke kuma lfy?me ya sameki?


     Kunya ce ta lullube iklas sai take ganin kamar kowa ya gane halin da take ciki,sai wani matse kafafu takeyi,su ummi fa sun kasa ganewa,wai me ya sameki ne iklas?ni yar nan na shigesu,


    Umaru tayani figa uwar kishiya ta zama kaza,iklas kuwa daki tayi wucewarta ta bar ummi na sallallami,shiryawa tayi cikin dangalalliyar sabuwar doguwar rigarta fara me digon ja,rigar ma da kadan ta wuce gwiwarta,irin kayan da iklas tafi so kenan,


       Turare ta shafa yau sosai a jikinta kamshi kawai takeyi ta ko ina,batayiwa kowa magana ba ta wuce kitchen,tea ta hada me kauri ta dawo Palo kusa da omar ta zauna a 3seater da yake zaune yana danna system.


     Iklas Sam ta kasa zama,sai taji kamar period zai bata mata kayanta,shi yasa minti biyu uku sai ta mike tsaye ta waiga ta kalli bayanta,sai ta wayance kamar za tayi mika,


     Omar ta gefen ido yake kallonta,ya kasa gano matsalar iklas yau,ummi kuwa tun tana masifa har ta kyale iklas.tsakar gida ta koma ta zauna a farar kujera ita kadai,wai nufinta ko da zata baci to ita kadai zata gani,


    Ta kasa sakewa Sam ta takure waje daya yau ko akwalar wayarta ta kasa dauka bare tayi danne danne,Ummi ce ta kalli omar....umaru dan Allah jeka wurin yarinyar can kaji meke damunta,tunda naga ni baza ta fada min ba, watakil in anyi dace kai ta fada maka,


    Sai da omar ya dauki 5mnt sannan ya fito waje ya nufi inda iklas ke zaune,ta hada kai da gwiwa sai hawaye takeyi tare da kallon gabas ta daga kai sama tana addua,fadi takeyi Allah ka yayemin wannan abun daya sameni,


     Idan taji zubowar period zuuuuuu sai tace wayyyoooo Allah na,ta kara daga hannu tana ta zuba addua kan Allah ya yaye mata.tsawa omar ya daka mata! lfy kiki dami mutane,shuru tayi tana kwalla idonta yayi jajir,dake fa nake karki bari raina ya baci..


    Kallonsa tayi amma kunya ta hanata fada masa meke damunta,kujera shima ya jawo ya zauna,suna zaune kowa yayi shuru,omar sai latsa wayarsa yakeyi,sun kai kusan 2hrs iklas ta mike ta shiga daki,fitowa tayi dauke da bakar Leda da abubuwa a ciki ta shige toilet,


    Nan ma ta Dade sannan ta fito,ledace kulle a hannunta zata jefa a dustbin,fisge ledar omar yayi yana kokarin dubawa,ai iklas kukan kura tayi hade da kurma ihu ta makalkale omar,wayoo ledata dan girman Allah kar ka bude min,dan Allah kayi hakuri,gani tayi da gaske budewa zaiyi,kuka ta sa masa sosai tana rokonsa,pls ya omar karka bude min,


      Omar kam ko kulata baiyi ba sai bala'in da ta haddasa masa a cikin jikinsa sanadiyyar Makalkaleshi da iklas tayi,amma ya rantse sai ya gani me take boye musu,ledar ya bude pad din da iklas ta cire ya gani,ai da Sauri ya rufe idonsa ya jefa mata ledar da sauri,


    Iklas kam fashewa tayi da kukan takaici tare da zabgawa omar harara,4eye sukayi yaga yanda iklas ke harararsa,kallonta yayi ya saki shu'umin murmushin sa me rikita yan mata,


    Ki harareni da kyau kazamar banza dama nasan bazai wuce wannan ba,kinbi kin damu mutane da kuka da masifa,wurin da ta shanya panties ya kalla jiba duk kin baza mana wannan a gida salon wasu su shigo sugane size naki.tun dare bai miki ba ki kwashesu daga nan ki kaisu can baya.


       Omar Ya kai kofar Palo zai shiga ya juyo ! ki tabbatar kin wanke mana toilet neat kar na shiga na shaki dirtyn ki.kallon omar iklas tayi hade da sakin kuka da karfin tsiya tana shure shure,


       Kaka ummi ce ta fito da Sauri jin kukan iklas, shima Omar tsayawa yayi ya fasa shiga dakin,umaru lfy?cewar ummi,hmm ummi girma ne fa ya kama jikarki, bata da lfy period ne cewar omar ko kunya bai ji ba.


    Dogon tsaki ummi taja shine kika hanamu jin dadin rayuwa ja'ira tashi kar cikon kunzugun naki ya goce ki baci.


    Daria Omar yayi ya faki idon ummi yawa iklas gwalo,daria da kuka iklas keyi, yanda Omar yayi gwalon shi ya bata daria kamar wani tom.


     Baffa da mama ne suka kama hanyar gidan su sahar domin yin bikonta tunda yanzu sun San dansu yana nan lfy,an musu tarba ta ban girma,maman sahar tunda taji biko sukazo ta daure fuska,cika take tana batsewa,dady Baban sahar kuwa fada da masifa ya fara,ta inda yake shiga bata nan yake fita ba,gaskia alhaji mohd ka raina mana hankali,billahilazim badan kai abokina bane da sai nayi kararka,kuma dan naka ya daawo ya sakar min yata,na gaji da azabtar da ita da kukeyi,ita kadai Allah ya mallakamin sannan Ku dinga min wasa da ita,fafafafaffa maganganu marasa dadi Baban sahar ke yi, haka baffa ya Shiga bada hakuri da Neman sulhu amma Sam maman sahar ta janye mijinta suka shige room suka bar su mama zaune.haka dole suka dawo gida,cike da takaicin wulakancin da iyayen sahar suka yi musu.ba komai duniace cewar mama.



        Haj rahina burinta ya kasa cika,ta kori Omar daga gida domin ta kwashi naira a wajen alhaji mohd amma hakanta ya kasa cimma ruwa,domin baffa ya daina Sakar mata fuska ma,bare ma ta samu dama,ta rasa ta wacce hanya zata bullo masa domin so take ta yashi rabonta tunda wuri.sabo da haka ta kara Neman haj bilki kawarta domin ta bata shawara.


 

    Naja na hango a kitchen ita da wata me aikinsu sai dungurewa yarinya kai takeyi tana zaginta ta uwa ta uba,duk yan uwan na kallo ba Wanda yayi magana har umman tasu haj rahina,yar aikin gajiya tayi tace dan Allah ki daina zagar min iyaye,kafin kace me naja ta ebo soyayyen man gyada akan gas ta watsawa yar aikin,tare da kunduma ashar,


    Ihu sosai takeyi tana kuka tare da Neman agaji,rankwashi sadiya ta zuba mata sannan a wulakance suka dauketa zuwa hospital daga nan suka maidata kauyensu.


      Yau kwanan iklas 1 tana period yau Sam  kasa zuwa schl tayi,omar kuwa wani new sim card yasa ya kira yaronsa hade da bashi umarnin kawo pad ,iklas na zaune taga an shigo da pad da yawan gaske,kamar Zara bude shago.


   Godiya tayiwa omar,ki daina godemin fatana ki wanke mana toilet sosai.Baki ta cuno cike da shagwaba haba sir kasan fa kai yaya nane sai kana bani kunya,ai kasan dama ni ke gyara gidan ko,?


       Kafe iklas da kallo omar yayi,in tana shagwabar nan birgeshi takeyi,shi a kanta ya San shagwaba na yiwa mata kyau sosai,lalacewa yayi wajen kallon iklas na zuba masa shagwaba.da kyar ya jawo nutsuwarsa ya mannata jikinsa tare da cewa hope kin iya wankan musuluncin dai ko?daria iklas tayi ya omar bafa a asarar kudin tara in fadama babu kalar da ban sani ba ehe,


       Lumshe ido yayi wani nishadi da dadi ya tashi a sararin samaniya a dirga a zuciarsa tsabar iya fadan OMAR da iklas tayi,a dunia yana son yaji iklas tace masa omar ji yake kamar sunansa yafi na kowa dadi a dunia,


     Ya omar kazo yau da yamma muje yawo kaga kai baka fita,kai kawai ya daga mata dan ta kara kashe masa jiki,ta tsinka masa jijiyoyin jikinsa jin  ya omar again daga bakin iklas,


     

       Karfe biyar iklas ta fito sanye da wata arniyar super atamfa dinkin riga me coler da dogon hannu Riga da skert,bata daura dankwaki ba gyale ta yada,ta sha kyau pose ta dauka pink kalar atamfar takalmi ma same color,


     Numfashinta ne ya dauke ganin omar sanye da 3quater arsh da riga T-shirt milk color sai rubutu da pink ansa defence da babban baki,yayi kyau sosai ummi sukayiwa sallama,omar na fargaba da tsoron fita sabo da lafiyarsa.


      Iklas kuwa ta nace sai ta kaishi yawo,sun fita iklas ta ga wata sabuwar mota dal arsh color,mota ta alfarma ta fita kunya ta nunawa a gari,zagawa Omar yayi ya shige mazaunin driver,itama ta shiga gaba,suka fasa gari,ko Nisa basuyi ba ciwon omar ya fara motsawa,iklas ma ta kula da hakan,to shi wannan meke damunsa haka cewar iklas a ranta,


     Ciwon karfi yakeyi sosai har driving yana nema ya gagareshi,iklas ta tausaya masa ganin yanda ya fita a hayyacinsa lokaci daya,hannunsa daya ta kamo ta rike gam cikin nata,sabo da haka ya gangare kasa da hannu daya yake driving har yayi parking gefen titi,


    Duk ac dake motar omar gumine ke keto masa,iklas du ta tsorata ta rude tausayin Omar takeji sosai,hannunsa ta kara damkewa tare da goge masa gumi da handkerchief tana tofa masa addua,


       A hankali yaji sauki amma da zarar iklas ta zare hannunta cikin nasa sai ya fara jin ciwon zai dawo,kawai sai yaja hannunta har kan sitiyarin ya hade da nasa ya ci gaba da driving,har sukaje city wani tsadajjen wurin shakatawa ya kaisu,na manyan yara kowa ka gani wajen to karshene wajen rike doller.


     Iklas yar kallo ta zama,hannunta cikin nasa ko ina birge mutane sukeyi sai kallonsu akeyi,da yawa sun zata ango da amarya ne,iklas har wani gadara da yanga takeyi ita a dole babbar yarinya,omar na kallonta ta gefen ido daria yakeyi a ransa kawai,


     Dan zagawa yayi da ita,maza kowa kallon iklas yakeyi sabo da baiwar kyanta,harma da wasu matan amma su omar yafi yi musu kyau,baya son ciwonsa ya tashi that's y kawai ya musu take away,wannan karon iklas hannunta ta gwiwar hannun omar ya sakaloshi, istigifari yayi wai a bisa lalura ya rike hannunta,


    Sunzo jikin mota zasu shiga kenan motar sultan Frnd din omar ta danno kai,omar na Jan motarsa sultan shi kuma ya parker a wurin,tabbas sultan yaga omar amma gani yakeyi kamar shi kamar ba shi ba,kai tabbas wancan omar ne  cewar sultan,amma yayi mamaki da yaga kamar yarinyar nan da taje gidan su Omar takai sakon takarda,kai sultan kansa ya kulle,to omar da mace?aure yayi?to meke faruwa da Omar haka,amma kuma kamar me tallan kwai ce tare da omar.duk sultan ke zancen zuci.


    Yasan idan ma yabi bayansu yanzu sun bace masa,da ganin kalar motar ma da tsadarta gata sabuwa yasan sai omar,shine keyin too match da kayansa da mota most of d time,kuma shi ke yawan order new cars don kawai ya hau yaji dadinsa.


    Bangaren Omar kuwa yaga shigowar sultan,yaso ya masa magana amma sai yaji ya kasa,bazai iya ba,katon shopping mall ya tsaya sukayi siyayya da yawa stl hannunsu na damke da juna,nan ma wani cikin yaran sadiya yan daba yaga omar,amma kwokwanto yakeyi kamar yanda sultan yayi,


     Suna karasawa gida sun kwashe kayan da suka siyo tas,Omar ya kira yaronsa yace ka dauke motar mutumin ya fasa amfani da ita.bazai siya ba,yaro shi ya zata Omar business sukeyi.bai San oganne da kansa ba.ya musu haka ne dan karma su San inda yake.kowanne ya Kira tsarashi yakeyi.


       Omar da iklas mamaki kowannensu keyi tare da tunani to me yasa idan Omar na gidansu su iklas baya ciwon,me yasa da suka fita ciwonsa ya tashi amma tana rikeshi ya warke,idan ya saki hannunta sai ciwo ya dawo,tofa readers koma mene zamu ji nan gaba.


   Omar kullum yana yin mugayen mafarkansa,washe gari iklas ta dawo daga schl suka shigo gidan tare da Frnd dinta dan unguwansu wato saleem,zai kai 32yrs kusan made din Omar ne,


      Ummi ya gaida tare da mikawa omar hannu,da kyar Omar ya mika masa hannun,tsakar gida suka koma shi da iklas suna ta hira suna daria,ummi ta shige room,bakin ciki omar keji a ransa ganin saleem da iklas tare,


     Kujerar dake jikin window ya dawo yana jin me suke cewar dama burinsa kenan,ruwan jarka Omar ya dauka ya bude,ta window ya zuro robar dama iklas da saleem suna saitin window,kwara musu ruwan omar yayi a Kansu,.



  




       Asmabaffa 


  Godiya dubu readers.

ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR 

         GOMNATI

          ⓂⓂⓂ


              40-45


By

Asmabaffa



     

        Ruwa kawai iklas da saleem sukaji a jikinsu,kara shararo ruwan yayi tas ya juyeshi jikin saleem da iklas,da sauri suka mike tsaye,omar na jikin window yana zabga harara,ya omar ka jikamu fa da ruwa cewar iklas,so what ni nace ku zauna jikin window,nazo zan zubar da ruwa ni na kula da akwai mutane nan?


    Amma ya omar jibafa yanda ka jika saleem,sorry saleem hannu ta kai zata karkadewa saleem rigarsa,wata uwar tsawa omar ya bugawa iklas...wlh wlh if u dear touch that guy yau jikinki sai ya fada miki,saleem kallon omar kawai yakeyi yana tunanin to me yayiwa wannan mutumin? Daga zuwa wajen iklas.


   Kallonsa iklas tayi haba ya omar me nayi ma kana daga cikin room kawai ka leko ta window sai fada kake mana,ok bakiyi komai bama ko...ki taba jikinsa ki gani ke na rantse da Allah yau Indai hannunki yakai jikin wannan sai na zaneki tas  a gidan nan.


     Malam pls ka tafiyarka ka daina zuwa wajenta an mata miji a kauye,daga yau ka kiyaye...ni wlh ba wani miji da akamin cewar iklas,omar ne ya fito waje ransa bakikirin,yana fitowa iklas ta fada toilet da gudu ta banko kofar,


    Saleem takaici ya kamashi ya bar gidan yayi ficewarsa,omar kuwa jikin toilet yaje gwara ma ki fito kafi na bude toilet din ta karfi na kamoki,daria iklas tayi naki na bude kuma ka balla kofar mu gani,abinda kai baka da karfi,wani karfine da kai,amma kika gudu me yasa baki tsaya ba,ai ni wanka zanyi shi yasa kaga na shiga toilet.


         Murmushi Omar yayi,na kyaleki yarinya tunda matsoraciya ce ke,ka jira na fito ka gani mana...cewar iklas,sai da ta tabbatar omar ya shiga daki ta fito sadaf sadaf,suhaila ce tace anty kiyi min gugar kayana,ke baki isa ba bani da lokaci unguwa zanje yau.


      Kije ummi ta miki,shiryawa iklas tayi cikin tsadajjiyar shaddarta para kal da dinki light blue kalar zaren,takalmi da jaka da mayafi du light blue,fitowa tayi omar ta gani a Palo wajensa taje ya omar zanje unguwa anjima kadan zan dawo,


     Ke kullum wai in baki fita ba Sam bakya jin dadine?no sir kawai dai wannan fitar me muhimmanci ce,to muje tare mana cewar omar,ni bazani da kai ba ciwonka ya tashi haka kawai,rannan hannuna har zafi ya min tsabar rikewar da ka masa,


       Sallama tayiwa omar tayi tafiyarta,direct gidan su omar naga ta tsayar da me taxi,masu gadi suna ganinta suka su bude mata ta shige,tana shiga sukayi ido 4 da Aisha,ai Aisha tana tabbatarwa ganinta ta koma part dinsu,yau ta fasa fita sai tayiwa yatinyar nan dukan kawo wuka,


    Tana shiga ta sanarwa sauran sis nata,shegiya Allah ya kawota zata ci ubanta yau wlh,sadiya kuwa wata sandar karfe ta dakko.tana Ashe yau za ayi daukan rai,kwanan wata zai kare,naja jeki waje ki jira tana fitowa ki mana flashing.


    Ita kuwa iklas part din maman omar ta wuce,hannu bibiyu suka tarbeta,yau iklas an sami waje har kitchen ita ta taya mama girki,wajen 5:30 tayiwa mama sallama ta fito domin tafiya gida,


    Tazo tsakiyar gidan su sadiya suka zagayeta kafin kace me sun rufe ta da duka,sai da suka farfasawa iklas jiki,da kyar mama da masu gadi suka kwaceta,


   Hhhh Allah sarki iklas da kyar take motsi ko ina jini,fuskarta ce kawai take normal,hospital mama tasa driver ya kaisu ita da iklas,dressing akayi mata,mama tayi tayi iklas ta bari su kaita gida amma taki yarda,dole suka kyaleta ta shiga taxi ta tafi gida,omar da ummi hankalinsu ya tashi ganin ba iklas ba labarinta,har dare shuru,Omar sai tsaki yakeyi ya kasa zaune ya kasa tsaye,sai duba agogo yakeyi,


    Shaddar iklas ta baci da jinin dukan su sadiya,sannan gashi period din da takeyi shima garin fadan pad ta goce,duk ya bata mata jiki,tana dingishi hade da nishi ta rarrafa ta shiga gidan,su ummi ta gani tsaye a tsakar gida hankalinsu tashe,da gani ita suke jira,tana shiga da sauri suka tareta,


     Rushewa da kuka iklas tayi,tana ta kuka me ban tausayi,jikinta suka gani duk rauni,omar ne ya riko hannunta,accident kikayi? cewar omar ,cikin sheshekar kuka iklas tace wash...was...wasu suka dakeni,sai ta kara sakin kuka,


      Su waye?wanne yan iskanne suka Dakar min jikata marainiyar Allah ummi ke fadi,wasu ne ummi,idan kin sansu ki fada min cewar omar,ni ban sansu ba kawai sunce na zagesu wai,omar kuwa Sam bai yarda da zancen iklas ba.ummi kuwa yarda tayi tace Allah zai saka miki,muje kiyi wanka ki gasa jikin.


    Ruwan zafi ummi ta hada mata kana tayi wanka,tana daga cikin toilet ta kwalawa ummi kira,ummi kuwa bata kusa sai omar dake zaune a kujera,me kike so a miki ummi sallah takeyi,pls sir wata Leda zaka dauko min a room kan bed dina,dakin su iklas ya shiga ya dauko ledar wacce ba komai bane ciki face pant da pad,tsaki ya ja karbi kayan kazantarki malama,hannu ta miko ta window ta karba,omar kam hannun nata ya bi da kallo,yanda suke masu matukar kyau ga ruwa jiki sunyi fresh fari tas, shirya kanta tayi, tea omar ya hada mata ta sha,duk abinda sukeyi ummi tana sallah tana kallonsu tare da jin dadi, suhaila harda kukan tausayin iklas.


    Gomnati sai kuka takeyi tana yarfe hannu abin nata harda shagwaba ya koma,omar kuwa tausayi ta bashi har wani lallabata yakeyi duk zatonta zafin ciwo ne,kukan nata jinsa yake har ransa.


     Haka sukayi fama da iklas har ta warke,kamar kullum iklas ta fito daga schl a gefen titi wata mota dalleliya ta parker a saitin iklas,sauke glass kasa akaayi,ba kowa bane face sultan,yazo wucewa ya hango wata kamar ummi da taje wajen maman omar,wacce ya gani da omar yana kokwanto,


    Gaisawa sukayi ummi kike ko?yea ya gida ya aiki?cewar iklas dan ta San sultan,ahmmmm...kamar ke na gani da omar rannan a garden kingdom ko?da mamaki iklas ta nuna Sam bata San waye Omar ba,ta manta ma da wani omar,wanne omarfa?frnd dina mana Wanda ya baki envelop ki kaiwa mamansa.ohhhhh na tuna dama sunansa omar?ai na manta ma,pls ya koma gida kuwa,


      Au dama bake na gani tare dashi ba,gaskia ba ni bace,maybe wata ce,ok pls kin taba yin sana'ar talla?cewar sultan.mene kuma talla ban gane ba.it's OK bari naje na gode fa,sultan yaja motarsa yayi gaba abinsa.


      Da sauri iklas ta sha kwana,ko nisa batayi ba wasu Igbo suka parker sukayi mata lift,har taki shiga motar saboda yan iska ne a unguwar,sabo da kar sultan ya ganota ta shige motar ba tare da tunanin komai ba,


     Joseph ne ya dawo baya kusa da iklas India shi kuma nmandi ya ci gaba da tukinsa,ga hanya kusa amma sai suka canja suka dauki ta nesa wacce za a Dade ba a zo layin su iklas ba,


   Sai shawagi sukeyi da ita a mota,Joseph ne ya matsa jikin iklas,ta kara matsawa,har suka kai karshen bangon murfin motar,


      Iklas sai hakuri take basu tana rokon su sauketa amma ina,tuni Joseph ya fara shafa cinyoyinta,kuka ta saka musu,amma sai daria sukeyi mata tare da kara kwakwumeta,manne jikinta tayi waje daya yayinda shi kuma ya sutale hijab dinta,wow this girl fine woooo,omoh see her hair like arabs girl,


      Kirjinta ya fara kokarin shafawa ta tsala ihu, make bakinta yayi,a take ya fashe yana jini har hancinta,tafiya sukeyi har sukazo gidan su iklas basu gane cewar gidansu bane,omar ya leko kofar gida yana jiran suhaila ta kawo masa recharge card daya aiketa ta siyo masa,


      Iklas ya hango a bayan motar wasu kuma mutumin taba jikinta yakeyi,iklas kuwa tana ganin gidansu ta kwala ihu tana Neman agaji, su Joseph tabbas sun ga alama zata tona musu asiri,gashi ta makale jikinta ko kirjinta ya kasa latsowa,haushi yaji ya fesa mata mari ya taka birki kuuuuu,ta fito kuwa da gudu suka ja motarsu da gudun tsiya.

 

    Suka bar unguwar,Omar kam ya gama tsorata da lamarin iklas, ya rasa ma tantancewa me yakeji a zuciarsa, wanne kalar bakin ciki ne yake ji ya kasa ganewa.


       Hannun suhaila ya ja sukayi cikin gida, kallo daya yayiwa iklas ya dauke kai,baki duk jini da hanci,a waje ta tsaya ta goge jinin sabo da ummi,


     Wanka tayi da sallah taci abinci,sai istigifari iklas keyi a ranta, duk da tasan bata da laifi amma ai ganganci tayi tasan yan iskane amma ta shiga motarsu,


    Ba abinda ya dameta irin kallon da Omar ya mata,haka kawai taji ta shiga damua,gashi ko magana yaki yi bare ta samu damar wanke kanta,yanzu zai mata kallon yar iska.kunyarsa take ji sosai,duk tayi wani sukuku da ita,ummi har tambayarta tayi ko lfy?amma tace normal take gajia ce.


          9:30pm washe gari kowa ya tashi banda Omar, yau ba schl Saturday, ummi ce ta umarci iklas da taje ta Kira Omar suyi break,kwance ta sameshi sai marfakansa yakeyi, tashinsa ta fara yi.a tsorace ya tashi zaune daga shi sai boxers, tsoro ne ya kamashi sosai kan mafarkin da yayi,bai San sanda a rungume iklas ba,yana shakar kamshin wuyanta tare da sakin ajiyar zucia




Asmabaffa

ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR

         GOMNATI

          ⓂⓂⓂ


              45-50


By

Asmabaffa




      Na gode  masoyana Allah karo karfin ido.



  

     Kiciniyar kwace kanta takeyi amma ya mata rungumar karfi,da kyar ta fara zamewa cikin magagin bacci omar yace 2nmt pls.....tsayawa tayi cak tare da lafewa ita dama iklas ta Dade da son ta jita a kirjin omar,bata San me yasa ba kuma ta rasa dalilin da yasa jikin omar ke birgeta.sun dauki minti biyar haka omar ya dawo normal,jinsa yayi manne jikin mace ai bai San sanda fancakalar da iklas daga jikinsa ba,sai da ta fado kasa daga bed din.


       Masifa ya fara IKLAS karo na farko da Omar ya kira sunan iklas,wani zirrrrrrrr taji lokacin da omar ya furta iklas,kallonsa tayi tare da tsilli tsilli da ido tana Sosa gashi,me ya kawoki dakin nan,mikewa yayi idonsa jajir ya damki kunnenta,kara ta saki kadan,ba kyajin magana ko iklas,am I ur mate? Ke bakya banbance tsakanin maza da mata,bayan yan iskan da suka saukeki dazu kinga bance miki komai ba shine zaki sauke iskancinki kaina ko?


     Ina ina ta fara ....to wai...wai ba kaine ka janyoni jikinka ba kuma ka rokeni kan na tsaya,har hawaye kayi fa wai kar na tafi,kuma kace kai dadinka kake ji,kukan karya ta fara yi,kuma ni taimaka maka nayi,daga taimak....shut up tashi ki fita mayyata kar ki kuma zuwa min room kije kiyi raping dina,ki samin kazamin jikinki duk dazu wasu gardawa sun gama goga jikinsu a naki.


    Kuka ta saka masa harda rufe ido da hannu,dama nasan yar iska zaka na kallona,na rantse da Allah billahillazi la'ila ha illahuwa Allah daya ragemin hanya sukayi shine suke kokarin tabani sir.


   Kaga Allah kallo wurin da suka dinga marina akan naki yarda ai kaga jinin ma ko,ni ban wani gani ba ke dai kawai kin lalace jikin maza kike so,in auren kike so ayi miki mana,har kayan daki zan miki, cewar omar


Iklas tsalle tayi ta make kafada  Allah kiyaye na haihu na ragwaje,ai nasan ma yanda kake ji dani baza ka bari amin auren wuri ba,tunda kai kaka tana jin maganarka.


     Igbo za a aura miki tunda su kike biyewa suna lagudaki.hawaye ta fara, wlh sir na fada ma ni ba yar iska bace,Omar yasan gaskia kawai maganinta yake son yi sabo da ta daina ganganci.

 

    rike haba iklas tayi kamar gaske tace ohh sir wai kai wanne mai kake shafawa ne?mene kuma?hmmm jikinka Allah ya Omar kamar flour baka ji ba.daria ce ta kwacewa omar,ga iklas tayi wani zaman cin tuwo a kasa, banza omar ya mata.


    Minti 1 iklas tace yaya?kinga get out,kofa ya bude mata tare da kamo hannunta ya tankada keyarta waje ya rufe kofar,sai da ta kusa faduwa kasa,tunawa tayi bata fadi kiran da ummi tace tawa Omar ba,jikin kofar ta Dora kanta ya Omar kazo inji ummi muyi break,tsaki yaja ke kinfa isheni kije zanzo wanka zanyi...ok.


       Kamshin omar da suka ji shi ya basu tabbacin fitowarsa wani danyen yadi ne sanye jikinsa light blue,har kasa ya gaida ummi,umaru wannan kwalliya haka kamar me zuwa zance?amshe zancen iklas tayi haba ummi ke ba dama mutum yayi kwalliya sai kice zance zai je to shi ya omar wa yake da ita,ina yake fita Da har zaiyi wata budurwa, to uwar shishigi ki bari umaru ya bani amsata mana,


    Murmushi omar ya saki ummi bikon matata zanje,tayi yaji sabo da rashin ganina da batayi.sallallami ummi ta fara yanzu umaru kana da mata amma baka fada min ba,ayi hakuri ummi,yanzu ma so nake iklas ta rakani can.dole kaje ai baka kyauta ba umaru.


    Da karfi iklas tace bazanje ba kaje kai kadai ina ruwana da wata matarka,ni nasa ka aureta,zamana takeyi,kai ta shafa can kaje da wata badai ni ba.cike da masifa ta mike zata shige daki,omar kuwa daria kawai yakeyi kadan kadan wannan masifa ta iklas da takeyi,riko hannunta yayi tunda bazaki ba suhaila jeki shirya ki rakani,


      Tana zaune suhaila ta fito sanye cikin English wears Riga da wando masu kyau,ummi ta gyara mata gashinta,wuce iklas tazo yi iklas kuwa kafa tasa wa suhaila ta shatile kafarta ta fadi kasa,kuka ta fashe dashi me karfin gaske,rufe iklas da masifa ummi tayi.


    Omar da ummi ne suka lallasheta da kyar,gani tayi da gaske tafiya zasuyi,fuuuu tazo ta wuce su tare da bangaje omar,mota ta gani rantsatsiya a waje, omar na danna remote ya bude iklas ta balle murfin gaban motar ta shige,


    Shi kuwa omar murna yayi a ransa dama haka yakeso,a baya ya zaunar da suhaila shima ya shiga.yasan idan ba iklas tafiyar baza ta yiwu ba saboda definitely ciwonsa zai tashi,amma idan iklas na kusa ya riketa sai ya warke


   Tafiya sukeyi sun fara shiga abuja city iklas kawai kumburi takeyi kamar zata ce wayyo na shiga uku na lalace


     Tunda suka fara tafiya omar ciwonsa ya fara tashi kawai zufa yakeyi ya rasa inda zai sa kansa, ba shiri ya sadada hannunsa ya riko hannun iklas,da karfi cike da masifa ta fisge hannunta,naga Wanda zaka rike ai yau.


     Omar ta kansa yakeyi kawai shi yasan me yake ji,suhaila ce dake bayan mota ta mikowa omar hannu gashi ya omar ni ka rike nawa hannun ka kyale na anty.iklas juyawa tayi a fusace ta zubawa suhaila rankwashi ta make hannun wai ni sa'arki ce,ina ruwanki da shi,ba a son hannun naki to.


      Omar na nishi da kyar yake tukin motar kallon iklas yayi idonsa yayi jajir,ki daina dukanta ke iskancin da kikeyi a garin nan wa ke dukanki,kunya iklas taji tace to a kyale maganar kana fama da kanka,hannunta ta miko masa ungo gashi ka rike na taimakamaka.yatsunsu ya sarkafe wuri daya yaci gaba da driving,5mnt omar ya dawo garau dashi,yayinda iklas da shi suka shiga wani hali na shauki kowannensu ji yake jininsa na masa wani yammmm.....yammmm.


     Wani katafaren barbing saloon Wanda yake hade maza da mata omar ya parker,mata maza birjik ciki ana gyaran gashi,matan manya da yaran manya,da manyan masu kudi sune a cikinsa,turawa ne masu aiki a ciki.gurin ya hadu kamar a turai,


    Fitowa yayi sakale da hannun iklas kamar chewgum,tafiya sukeyi cike da izza,iklas ta raina kanta kyaune kadai ya ceceta,dan duk tafi matan ciki kyau nesa ba kusa ba,sai kallonsu akeyi,suhaila na kusa da ya omar.bangaren mata ya fara kaisu yana zaune,iklas ta karbe daya hannun ta mika masa daya hannun gashi rike wannan dayan ya samu ya huta.


      Kujera aka ba omar yana zaune gaban iklas hannunsa rike da nata haka akayi mata gyaran gashi aka gama,suhaila ma an mata,sunyi matukar yin kyau,su Kansu masu saloon din sunyi jinjina.


    Wurin maza suka koma wannan karan iklas aka bawa kujera ta zauna gaban omar rike da hannunsa,masifu kawai take ji a jikinta na kamar sha'awa amma ta rasa gane mene take ji.


      Omar kuwa a cikin jininsa yake jin bala'in sha'awar iklas wacce bai taba ji ba,amma haka ya daure ya cije.tunda aka fara gyarawa Omar suma iklas ta fara turbine fuska,idan ta kalli Omar sai ta tabe baki,wlh ka cuci kanka ko kyau bakayi ba,minti daya ko biyu zata kalleshi tace ko kyau,wai dole za a je bikon mata.


   Gajia Omar yayi yace tunda sahar na son kalarsa ai alhmdlh dama dan ita nayi.mutumin da ba a sonsa anyi yaji an barshi wooooooo....cewar iklas,duk rashin fara'ar Omar iklas daria take sashi.


      Haj rahina ce gaban baffan su omar,pls baffan yara 1million nake rokonka ka bani zan canja motata.hajia rigimarki ta isheni duk motocin gidan nan,omar fa baya bari motoci su shekara yake kawo sabbi,jin baffa ya ambaci omar yasa ummansu sadiya daure fuska,kaga alhaji ni ba zancen tambadadde nazo kamin ba,dan iskan yaro Wanda tsabar bin matane yasa ya bar gida.wa ya sani ma ko a waje tayo cikinsa....bata rufe baki ba taji saukar lafiyayyun mari har uku...kunci ta dafe tare da tsagewa da kuka tana kururuwa ta cukume baffa da kokawa tare da danna masa ashar,ai kuwa baffa ya sa kafa ya harbata gefensa,ta bigi center table,


    Takadda ya dauko ya rubuta mata saki daya,tare da dafe kansa da kyar ya karasa dakinsa.faduwa yayi kasa yayi sharab...mama wacce abin ya faru kan idonta da kuka ta dago baffa,sannan ta kira maza masu aiki da driver suka kwashi baffa zuwa hospital.


       Gaskia kowa ya ga yanda omar ya hadu sai ya kyasa,mata sai kallonsa sukeyi,da yawa suna so su kawo kokon bararsu na love amma yanda suka ganshi kankame da hannun iklas yasa suka ja baya, sai kallo daga nesa,


       Take away ya musu na abinci kala kala sannan ya kamo hanyar gida,dadi ne ya kama iklas sosai ganin baza a je bikon sahar ba.


      Sabo da murna sai labari takewa Omar,suna isa gida iklas ta hango saleem, da Sauri ta bude mota zata fita,Omar yaga saleem sarai,rigar iklas ya rike gam, kallonsa tayi yace muje gida waccen dan iskan zaki je wajensa ko?


  Naji ai na fasa zuwa,to sakeni muje gida mana,kayan suka shigar gida,a cikin motar omar ya bar key din iklas na kusa dashi ta kwace hannunta taje wajen saleem da gudu ta karasa, har sun fara hira akan business da aikin gomnati yanda ake cuwa cuwa kudi na shigowa, wajensu Omar ya taka yaje cike da takama ya zubawa iklas rankwashi muje gida,cike da shagwaba tace ya omar da zafi fa,gani yayi zata bata masa lokaci kawai ya sunkuceta ya sabata a kafada. mutanen layin sai daria sukeyi GOMNATI ta hadu da dai dai ita.




       Asmabaffa

ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR

         GOMNATI

          ⓂⓂⓂ


              45-50


By

Asmabaffa




      Na gode  masoyana Allah karo karfin ido.



  

     Kiciniyar kwace kanta takeyi amma ya mata rungumar karfi,da kyar ta fara zamewa cikin magagin bacci omar yace 2nmt pls.....tsayawa tayi cak tare da lafewa ita dama iklas ta Dade da son ta jita a kirjin omar,bata San me yasa ba kuma ta rasa dalilin da yasa jikin omar ke birgeta.sun dauki minti biyar haka omar ya dawo normal,jinsa yayi manne jikin mace ai bai San sanda fancakalar da iklas daga jikinsa ba,sai da ta fado kasa daga bed din.


       Masifa ya fara IKLAS karo na farko da Omar ya kira sunan iklas,wani zirrrrrrrr taji lokacin da omar ya furta iklas,kallonsa tayi tare da tsilli tsilli da ido tana Sosa gashi,me ya kawoki dakin nan,mikewa yayi idonsa jajir ya damki kunnenta,kara ta saki kadan,ba kyajin magana ko iklas,am I ur mate? Ke bakya banbance tsakanin maza da mata,bayan yan iskan da suka saukeki dazu kinga bance miki komai ba shine zaki sauke iskancinki kaina ko?


     Ina ina ta fara ....to wai...wai ba kaine ka janyoni jikinka ba kuma ka rokeni kan na tsaya,har hawaye kayi fa wai kar na tafi,kuma kace kai dadinka kake ji,kukan karya ta fara yi,kuma ni taimaka maka nayi,daga taimak....shut up tashi ki fita mayyata kar ki kuma zuwa min room kije kiyi raping dina,ki samin kazamin jikinki duk dazu wasu gardawa sun gama goga jikinsu a naki.


    Kuka ta saka masa harda rufe ido da hannu,dama nasan yar iska zaka na kallona,na rantse da Allah billahillazi la'ila ha illahuwa Allah daya ragemin hanya sukayi shine suke kokarin tabani sir.


   Kaga Allah kallo wurin da suka dinga marina akan naki yarda ai kaga jinin ma ko,ni ban wani gani ba ke dai kawai kin lalace jikin maza kike so,in auren kike so ayi miki mana,har kayan daki zan miki, cewar omar


Iklas tsalle tayi ta make kafada  Allah kiyaye na haihu na ragwaje,ai nasan ma yanda kake ji dani baza ka bari amin auren wuri ba,tunda kai kaka tana jin maganarka.


     Igbo za a aura miki tunda su kike biyewa suna lagudaki.hawaye ta fara, wlh sir na fada ma ni ba yar iska bace,Omar yasan gaskia kawai maganinta yake son yi sabo da ta daina ganganci.

 

    rike haba iklas tayi kamar gaske tace ohh sir wai kai wanne mai kake shafawa ne?mene kuma?hmmm jikinka Allah ya Omar kamar flour baka ji ba.daria ce ta kwacewa omar,ga iklas tayi wani zaman cin tuwo a kasa, banza omar ya mata.


    Minti 1 iklas tace yaya?kinga get out,kofa ya bude mata tare da kamo hannunta ya tankada keyarta waje ya rufe kofar,sai da ta kusa faduwa kasa,tunawa tayi bata fadi kiran da ummi tace tawa Omar ba,jikin kofar ta Dora kanta ya Omar kazo inji ummi muyi break,tsaki yaja ke kinfa isheni kije zanzo wanka zanyi...ok.


       Kamshin omar da suka ji shi ya basu tabbacin fitowarsa wani danyen yadi ne sanye jikinsa light blue,har kasa ya gaida ummi,umaru wannan kwalliya haka kamar me zuwa zance?amshe zancen iklas tayi haba ummi ke ba dama mutum yayi kwalliya sai kice zance zai je to shi ya omar wa yake da ita,ina yake fita Da har zaiyi wata budurwa, to uwar shishigi ki bari umaru ya bani amsata mana,


    Murmushi omar ya saki ummi bikon matata zanje,tayi yaji sabo da rashin ganina da batayi.sallallami ummi ta fara yanzu umaru kana da mata amma baka fada min ba,ayi hakuri ummi,yanzu ma so nake iklas ta rakani can.dole kaje ai baka kyauta ba umaru.


    Da karfi iklas tace bazanje ba kaje kai kadai ina ruwana da wata matarka,ni nasa ka aureta,zamana takeyi,kai ta shafa can kaje da wata badai ni ba.cike da masifa ta mike zata shige daki,omar kuwa daria kawai yakeyi kadan kadan wannan masifa ta iklas da takeyi,riko hannunta yayi tunda bazaki ba suhaila jeki shirya ki rakani,


      Tana zaune suhaila ta fito sanye cikin English wears Riga da wando masu kyau,ummi ta gyara mata gashinta,wuce iklas tazo yi iklas kuwa kafa tasa wa suhaila ta shatile kafarta ta fadi kasa,kuka ta fashe dashi me karfin gaske,rufe iklas da masifa ummi tayi.


    Omar da ummi ne suka lallasheta da kyar,gani tayi da gaske tafiya zasuyi,fuuuu tazo ta wuce su tare da bangaje omar,mota ta gani rantsatsiya a waje, omar na danna remote ya bude iklas ta balle murfin gaban motar ta shige,


    Shi kuwa omar murna yayi a ransa dama haka yakeso,a baya ya zaunar da suhaila shima ya shiga.yasan idan ba iklas tafiyar baza ta yiwu ba saboda definitely ciwonsa zai tashi,amma idan iklas na kusa ya riketa sai ya warke


   Tafiya sukeyi sun fara shiga abuja city iklas kawai kumburi takeyi kamar zata ce wayyo na shiga uku na lalace


     Tunda suka fara tafiya omar ciwonsa ya fara tashi kawai zufa yakeyi ya rasa inda zai sa kansa, ba shiri ya sadada hannunsa ya riko hannun iklas,da karfi cike da masifa ta fisge hannunta,naga Wanda zaka rike ai yau.


     Omar ta kansa yakeyi kawai shi yasan me yake ji,suhaila ce dake bayan mota ta mikowa omar hannu gashi ya omar ni ka rike nawa hannun ka kyale na anty.iklas juyawa tayi a fusace ta zubawa suhaila rankwashi ta make hannun wai ni sa'arki ce,ina ruwanki da shi,ba a son hannun naki to.


      Omar na nishi da kyar yake tukin motar kallon iklas yayi idonsa yayi jajir,ki daina dukanta ke iskancin da kikeyi a garin nan wa ke dukanki,kunya iklas taji tace to a kyale maganar kana fama da kanka,hannunta ta miko masa ungo gashi ka rike na taimakamaka.yatsunsu ya sarkafe wuri daya yaci gaba da driving,5mnt omar ya dawo garau dashi,yayinda iklas da shi suka shiga wani hali na shauki kowannensu ji yake jininsa na masa wani yammmm.....yammmm.


     Wani katafaren barbing saloon Wanda yake hade maza da mata omar ya parker,mata maza birjik ciki ana gyaran gashi,matan manya da yaran manya,da manyan masu kudi sune a cikinsa,turawa ne masu aiki a ciki.gurin ya hadu kamar a turai,


    Fitowa yayi sakale da hannun iklas kamar chewgum,tafiya sukeyi cike da izza,iklas ta raina kanta kyaune kadai ya ceceta,dan duk tafi matan ciki kyau nesa ba kusa ba,sai kallonsu akeyi,suhaila na kusa da ya omar.bangaren mata ya fara kaisu yana zaune,iklas ta karbe daya hannun ta mika masa daya hannun gashi rike wannan dayan ya samu ya huta.


      Kujera aka ba omar yana zaune gaban iklas hannunsa rike da nata haka akayi mata gyaran gashi aka gama,suhaila ma an mata,sunyi matukar yin kyau,su Kansu masu saloon din sunyi jinjina.


    Wurin maza suka koma wannan karan iklas aka bawa kujera ta zauna gaban omar rike da hannunsa,masifu kawai take ji a jikinta na kamar sha'awa amma ta rasa gane mene take ji.


      Omar kuwa a cikin jininsa yake jin bala'in sha'awar iklas wacce bai taba ji ba,amma haka ya daure ya cije.tunda aka fara gyarawa Omar suma iklas ta fara turbine fuska,idan ta kalli Omar sai ta tabe baki,wlh ka cuci kanka ko kyau bakayi ba,minti daya ko biyu zata kalleshi tace ko kyau,wai dole za a je bikon mata.


   Gajia Omar yayi yace tunda sahar na son kalarsa ai alhmdlh dama dan ita nayi.mutumin da ba a sonsa anyi yaji an barshi wooooooo....cewar iklas,duk rashin fara'ar Omar iklas daria take sashi.


      Haj rahina ce gaban baffan su omar,pls baffan yara 1million nake rokonka ka bani zan canja motata.hajia rigimarki ta isheni duk motocin gidan nan,omar fa baya bari motoci su shekara yake kawo sabbi,jin baffa ya ambaci omar yasa ummansu sadiya daure fuska,kaga alhaji ni ba zancen tambadadde nazo kamin ba,dan iskan yaro Wanda tsabar bin matane yasa ya bar gida.wa ya sani ma ko a waje tayo cikinsa....bata rufe baki ba taji saukar lafiyayyun mari har uku...kunci ta dafe tare da tsagewa da kuka tana kururuwa ta cukume baffa da kokawa tare da danna masa ashar,ai kuwa baffa ya sa kafa ya harbata gefensa,ta bigi center table,


    Takadda ya dauko ya rubuta mata saki daya,tare da dafe kansa da kyar ya karasa dakinsa.faduwa yayi kasa yayi sharab...mama wacce abin ya faru kan idonta da kuka ta dago baffa,sannan ta kira maza masu aiki da driver suka kwashi baffa zuwa hospital.


       Gaskia kowa ya ga yanda omar ya hadu sai ya kyasa,mata sai kallonsa sukeyi,da yawa suna so su kawo kokon bararsu na love amma yanda suka ganshi kankame da hannun iklas yasa suka ja baya, sai kallo daga nesa,


       Take away ya musu na abinci kala kala sannan ya kamo hanyar gida,dadi ne ya kama iklas sosai ganin baza a je bikon sahar ba.


      Sabo da murna sai labari takewa Omar,suna isa gida iklas ta hango saleem, da Sauri ta bude mota zata fita,Omar yaga saleem sarai,rigar iklas ya rike gam, kallonsa tayi yace muje gida waccen dan iskan zaki je wajensa ko?


  Naji ai na fasa zuwa,to sakeni muje gida mana,kayan suka shigar gida,a cikin motar omar ya bar key din iklas na kusa dashi ta kwace hannunta taje wajen saleem da gudu ta karasa, har sun fara hira akan business da aikin gomnati yanda ake cuwa cuwa kudi na shigowa, wajensu Omar ya taka yaje cike da takama ya zubawa iklas rankwashi muje gida,cike da shagwaba tace ya omar da zafi fa,gani yayi zata bata masa lokaci kawai ya sunkuceta ya sabata a kafada. mutanen layin sai daria sukeyi GOMNATI ta hadu da dai dai ita.




       Asmabaffa

ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR

         GOMNATI

          ⓂⓂⓂ


             50-55


By

AsmaBaffa


          Daukan da Omar ya mata bai direta ko ina ba sai daya kaita har Palo sannan ya jefata a kujera da karfi tare da shigewa room dinsa,

  Sosai Iklas taji zafi yar kara ta saki ohhh tare da dafe hips dinta..ko juyowa baiyi ba bare ya San me take ciki.

     Lokacin da su Omar sukaje saloon daya daga cikin yaran Maman Omar tare da wani abokin Omar tabbas suma sunga Omar sun fito daga saloon hannunsa rike da na wata kyakyawar budurwa.


     Lallai sunyi mamakin Omar ashe tafiyarsa yayi yana sheke ayarsa da mata,amma ake ta nemansa ana cewa ya bata.

     Abokin Omar wato Raj  ya daukin alkawarin zuwa ya fadawa Maman Omar cewar sunga Omar a saloon da mace.


   Haj.Rahina ta dauki akwati da sauran abubuwan amfaninta kadan tare da Tara yaranta tayi musu hudubar banza sannan ta bar gidan ta koma gidan babban yayansu da ke zaune a garin Abuja shima.

     Tasha fada wurin yayanta saboda yayanta Alhaji Magaji mutumin kirki ne sosai ya nunawa Rahina kuskurenta amma Sam ko a jikinta sai ma kara kaimi da tayi wurin son daukan fansa,kuma ta sa a ranta dole sai ta koma gidan Alhaji Mohd.


     Tunda su Maman Omar suka dauki Alhj Mohd wato Baffa suka yi hospital dashi gado aka basu bayan aune aune da bincike ya tabbatar yana dauke da ciwon hawan jini kuma ya masa babban kamu,sosai ake kula dashi a hospital Mama ta tsaya tsayin daka wajen mijinta,ita ke jinyar sa,su sadiya ma suna zuwa dubiya amma kullum idan sunje sai sunci mutuncin Mama tare da habaici da zage zage.

   Mama na mamakin wai ga mahaifinka a gadon asibiti rai a hannun Allah amma su sadiya suna shirme Allah kyauta.


     Sultan ma kullum yana kan hanyar dubiya,kuma shi ke kula da Baffa kasancewarsa likita babba,abokan su Omar ma kungiya kungiya suke zuwa dubiya,kamar yau ma Raj yazo yana dakin da aka kwantar da Baffa tare da wannan yaron me yiwa Maman Omar hidima duk wani aike me nisa da wasu abubuwan wannan yaron wato Nura shi ke wa Mama kusan same age suke da Omar.kuma Nura yana da dangantaka tsakaninsu da Raj.gasu frnds ne shi da Raj,shi yasa suke yawan fita tare duk da cewa Raj me kudi ne,

   

     Raj suna zaune kusa da Mama suna hira sama sama yayin da Sultan ke gyarawa Baffa kwanciya,Raj ya kalli Mama hade da gyaran murya Mama akwai wata magana da nake son fada miki,wato yau kwana uku kenan abin na damuna,gaba daya dakin Raj aka zubawa ido har Baffa da ya samu sauki shima ba a barshi a baya ba,

    Naje kusa da saloon in da Nura mun karbi sako a hannun wani Mama wlh munga Omar ido da ido ga Nura nan ki tambayeshi kiji,har kokonto mukayi sai da muka karasa har kusa dashi amma kafin mu is a wajensa sun shiga mota sunyi mana nisa,kuma Mama abin mamaki Omar da mace budurwa zankadediya muka ganshi rike da hannunta da wata yarinya zasuyi same age da suleim dinki,

 

       Sultan kuwa an zo wajen nan ya karbe zancen da cewa haba Ashe nima ba gizo idona ya min ba don nima rannan tabbas naga Omar a garden kingdom sun fito shi da wata charkwadediyar budurwa yarinya karama,Mama kamar yarinyar da ta kawo miki sakon envelop da tace Omar ya bata,kuma kamar wata me tallan kwai a titi da Omar ke taimakawa,

   Daga Mama har Baffa Kansu ya kulle,to ko dama maganar Haj.Rahina gaskia ce da tace Omar na gari sheke ayarsa yakeyi bin mata yakeyi,yaushe Omar ya zama haka,maybe zaman London ne ya lalatashi ko kuma rashin samun kulawa daga wajen matarsa ne.

     Gaba daya su Mama da Baffa sahar suka daurawa laifi sai kuma Omar da ya biyewa son zuciya tare da zubar musu da tarbiyar gida da mutunci.


    Baffa ransa ya kara baci da jin wannan magana,yasan Raj da Sultan baza suyiwa Omar sharri ba,gaskia suka fada,lallai Omar ya bashi kunya zai kuma hadu da hukuncinsa duk ranar da suka hadu.Mama kuwa harda kukan bakin ciki Omar ya watsa musu kasa a ido,amma ya za tayi dole addua ce mafita,

     Sosai su Sultan suka Shiga kwantarwa da su Baffa hankali tare da yi musu alkawarin nemo Omar,dan sunce zasu sa ido sosai a kansa.zasu Dana masa tarkon da dole sai ya fada tare da damke wannan tsinaniyar karuwar tasa wato Iklas.


    Kwana biyu tsakani Baffan Omar har yau jiki yaki sauki sabida damuwa jinin yaki sauka wahala yake sha wanda sai da su Sultan sukayi Dana sanin fada musu cewar sunga Omar.

     Mama abin ya hade mata ga rashin lafiyar miji ga rashin Omar dinta tare da jin mugun labarin yana neman mata.


     Su Iklas anyi musu hutu daga Ta boko har islamiyya,sabo da haka Iklas ta rikewa business dinta wuta yanzu ma tace sana'ar saida danyen kifi zata fara,kudin da ta samo gidan Maman Omar su ta tattara kaf ta siyo katuwar freezer sabuwa dal ta ajiye a kitchen,saura kawai ta fara saro kifi,duk tsare tsaren Iklas Omar bai sani ba,

     Dukkansu suna zaune a tsakar gida da yamma lis,Iklas na kwance a kan katuwar tabar ma da wata Rigarta doguwa ta atamfa tayi kyau,Suhaila na kan cinyar Ummi kwance tana karanta Arba'una hadith, Omar yana kan carpet gefe tare da laptop sai nunawa Ummi wakar shata me ganga yakeyi,Ummi har gyada kai take tana Allahu akabar oh kaji mazan jiya,Allah sarki jiya ba yau ba,Umaru danno min ta Ali makaho da Dan kwairo naji..daria yakewa Ummi ganin abu ba wani Dandano amma Ummi dadinsa takeji ko dan azamaninsu ne akayi wakar,


     Iklas littafinta ta dakko tana ta buga lissafin sana'ar kifi da zata fara domin gobe take sa ran sarowa,juyowa tayi dan Allah Ummi a canja mana wakar zamani amma wannan mu bama fahimtar me suke cewa,kaka Ummi dalla mata harara tayi aike ba hankali gareki ba amma ai sune sukayi wakoki masu ma'ana,tabe baki Iklas tayi pls ya Omar kai mana wakar Timaya ko ta  Devido,

    Ai kece Timayan  see ur mouth anki a kunna miki manya na maga kina shiga ciki cewar Omar,murmushi Iklas tayi cike da shagwaba ta ajiye littafin dake hannunta kajika ya Omar da nawa ka girmeni,ai ko zaka girmen kadan ne,hmm na San da auren wuri nayi da tuni na haifi kamarki,ummi ma tace fada mata Umaru in banda rashin kuya dudu shekararki nawa saboda kinyi tsayin kafa,dadin abun dai a gaban Umaru kika fara Al'ada,ba wani iyayi da zakiyi masa ,kukan shagwaba Iklas ta fara haba Ummi wai mene haka dan Allah,kunya Iklas taji sosai,Omar kuwa masu rayuwar London ko a kwalar rigarsa,saima kafe Iklas da yayi da kallo,idonta ta dauke daga kallonsa a ranta tana kai Sir din nan dan duniya ne harda kallo na.

  Su dama Maza  munafukaine abinda suke so kenan dama taji frnds dinta suna fada a schl.


  Washe gari da wuri Iklas ta saro kifinta Carton daya  na gwajin kasuwa,Omar yana bacci bai San Iklas ta fitaba,sai fitowa yayi yaga Iklas na shirya kifi a fridge Omar ya shiga kitchen din dauko furarsa dagashi sai jallabiya fara me hula dai dai jikinsa gashi sabo da baya fita baya shiga rana ya kara haske sosai skin dinsa har wani sheki takeyi,

    Kamshinsa ne ya bigi hancin Iklas a take jikinta ya mutu murus,kasala ta sakko mata,ta gefenta ya raba zai wuce jikinsa ne ya gogi nata baisan sanda a hankali yace ushshsh shshi sabo da wani irin yanayi daya tsinci kansa ciki.furar ya ebo a glass cup tare da zuka,ke me kike yi haka,duk wannan kifin da wa zaki cinye?kallonsa Iklas tayi tare da murmushi tace au baka da labari ai kifi zan fara siyarwa danye,da kudin da Baffa ya bani na kafa jarin,kaga sana'a goma maganin me gasa,kaga kala kala nakeyi kenan,

   Jinjina son kudi irin Na Iklas yayi a ransa,idanuwansa kyawawa masu matukar haske ya zubawa Iklas Wanda yasa Iklas dimaucewa hade da jin kunya,sunkuyar da kai tayi ta tsinkayo muryar Omar ba a nan gidan za ayi wannan sana'arba,baki isa ki cika mana gida da karni ba,duk sana'ar da kikeyi bata isheki ba sai kinyi kalar wannan,haba mene aibun wannan sai da kifin,ummi ma fa da kyar ta yarda wai bata so nayi,nidai ina son siyarwa sai nayi,


    Tamke fuska yayi to baki isa ba,ba a gidan nan ba na fada miki idan kuma kinga ina wasa dake kiyi na gani,da shagwaba tace pls Sir nasan in ka fada Ummi bayanka zata bi,ke kika sani ni kam na gama magana ko ki je ki mayarwa Wanda kika siyo wajensu ko a cinye a gida,ko ki bayar kyauta,tab lallai inyi asara ba riba,sai dai ka biyani kudin Dana kashe in kuna so na daina,

   Zare ido Omar yayi ina wasa dake,tsorata tayi ta fara bin bango tana rabewa hade da tafiya kadan Kadan ta fice da gudu daga kitchen din tana ae na fada a biyani kudin Dana kashe tare da kulewa dakinsu.


    Daria Omar yayi sosai ya fita shima,washe gari da safe Omar ya fito da brush da toothpaste zai shiga toilet sai ga Iklas ma ta fito tana kallon Omar ta wuce da sauri ta rigashi shigewa toilet din.Ummi sakin baki tayi yau naga yar banzar yarinya,ke dan bantan ubanki fito Umaru ya shiga,kyaleta Ummi zanyi maganinta,daki Ummi ta koma tana cewa kunfi kusa.


      Iklas kuwa har ta fara brush Omar ya jawo rigarta kiiiiiii ya jefota waje,kafin ya rufe toilet di Iklas ta kara bankawa ciki,murmushi Omar yayi oh..yanzu na gane me kikeso Ashe wanka kike so na miki,damkota yayi kamar zai fara cire mata kaya tuni Iklas ta fara kuka tana Neman agaji,da gudu ta fito daga toilet din,Omar ya rufe kofar tare da Jan tsaki karamar yar iska da kin tsaya kin gani.

    Iklas kuwa a ranta tace kut lallai Sir cikakken dan iskane.yau Iklas shiri tayi tsab domin zuwa gidan su Omar so take ta dubo masa lafiyar su Mama,fito tayi Palo tare da yiwa su Ummi sallama,da sauri Omar yace muje tare unguwar na kaiki,batayi musu ba ya kira a take aka kawo wata new Car din.


      Tofa kunji masu karatu.




ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR 

         GOMNATI

          ⓂⓂⓂ

 

            60-65


By

 Asmahbaffa



      MASOYANA READERS NA GAISHEKU,MASU COMMENT AKAN WANNAN NOVEL ALLAH MUKU ALBARKA GABA DAYA INA GANIN SAKON KOWA.




           Fafur Omar yaki yarda saima room dinsa daya shige ya bar Iklas waje tana tunanin yanda zata bude kofar,hakura kawai tayi ta kyale Saleem a waje yana jira.tunda Saleem yaji Iklas shuru shuru yasan bazai wuce wannan shedanin yayan nasu bane ya hanata fitowa

     Tunda Omar suka bar su Baffa da salati cikinsu ba Wanda ya kara koda tari,Suna a haka Sultan da Raj suka shigo,tambaya suka fara yi Lafiya sunga Mama ta rafka tagumi,da kyar Baffa ya fadawa su Raj halin da ake ciki,suma sosai suka sha mamaki,

    Sultan ne ya fara Baffa da kun sani Baku kori Omar ba,da kun barsu sunyi bayani,Omar nasan baya abu ba reason,me yasa ba a fada min a waya ba nazo wajen,Mama kema kin manta halayen Omar masu kyau,na tabbata zai wahala idan Omar zai iya aikata abinda muke zargi,


    Raj ma haka ya fada Baffa da Mama sai sukaji dama sun tariyo baya sun tsaya sun saurari Omar,sun yanke hukunci cikin bacin rai,ta leko ta koma ga Omar amma sun koreshi,Baffa ne ya dubi su Raj..Sultan yanzu mafita daya kusa ido a garin nan,da sauran abokan Ku da security duk inda aka ga Omar a kawo minshi har gida,in yaki binsu a kawoshi ta karfi ko da igiya Ku dauroshi a kawo min shi,

    Aje a sanarwa mutane,nan take suka fara waya tare da hada connection,shima Baffa haka,kwana 2 tsakani aka sallami Baffa,yana hutawa ya koma gidan su sahar wannan karan sunci sa'a an lallaba iyayen sahar da sahar sun dawo da ita gidan Omar,sahar kuwa dama kudi take so ta karba wajen Omar masu yawa tattalin arzikinta yayi kasa shi yasa ta yarda ta dawo..yayinda da taci gaba da sheke duniyar ta.


     Tana nan tana jiran ganin an dawo da Omar gida,bayan dawowar Sahar Baffa da yan uwansa suka je bikon haj.rahina,sai murna su sadiya sukeyi,gogar kuwa dama ta samu rana ta bude mata sai shanya,dama abinda take nema kenan Baffan su Omar ya lallaba ya dawo da ita.

       Sultan dasu Raj da sauran mutanensu sun fara aikinsu ba ji ba gani,kullum basa zama Neman Omar sukeyi ba dare ba rana,


      Iklas ta gaji ta yanke shawarar sanarwa da Ummi abinda ke faruwa da Ya Omar,tausayinsa takeji sosai gwara ta fada ko Allah zai sa a nemo masa magani,Omar kuwa kullum addua yakeyi sosai akan matsalolinsa,

     Yau Ummi ce ta dauko naman ganda ta jikashi a cikin ruwa a wani bowl,Omar ta mikawa da soson karfe da wuka Umaru gyara wannan yau ganda nake son ci,ragadada zan bararraka mana,Omar kuwa bin naman gandar yayi da kallo Ummi wannan tsohon abin tun na last year ai ki bari a siyo mana fresh mana,yaushe za aci guba a ciki,kaga idan baza ku gyaramun ba to na dauke abina ban son iyayin banza,ke uwar yan lissafin duniya matso kema ki tayashi Ku gyara da sauri,yanzu in aka gyara wannan yaji hadi kamshi ne zai cika unguwar nan,murmushi Omar ya saki Wanda ya janyo hankalin Iklas ta kafe Omar da ido tana kallon kyan da murmushi ke masa,

     Ummi nifa ban iya gyara abin nan ba cewar Omar tare da toshe hanci,sannu gayu mutanen Allah Iklas matso ki koya masa kuyi maza.


       Hand globe Omar ya nemo yasa a hannunsa wai kar hannunsa ya dauki warin naman,Iklas kuwa tuni ta fara gyaran a garin yi ta fallatsowa Omar ruwan a fuskarsa ruwan ya sauka a kumatun Omar,sorry cewar Iklas tare da ci gaba da dirzar gandarta,kyankyami ya kamashi Omar ya fara wanke fuskarsa da ruwa bayan ya gama ya dawo yana wlh kika kara bata min jiki sai na miki wanka da ruwan wanke naman gandar nan,


       Baki Iklas ta tabe ya Omar dama shan ice cream ka kaimu shi nake sha'awa muje pls da dare,harara ya watsa mata kin isa ma na kaiki daga nan ki kaini wajen su Baffa ko?haba dai ni na isa da wanne idon zan kalli Mama cewar Iklas to shike nan zan kaiki ke da Suhaila amma yau sai dare zamu fita,dadi Iklas taji sai washe baki take,kara fallatsawa Omar ruwan naman tayi a farar T-shirt din dake jikinsa,

     Haushi yaji kin kara bata ni da warin abin nan saboda kin rainani fuskarsa a daure ya dan ebo ya shafawa Iklas a fuska sai daria take tana rokonsa ya bari,yatsunsa ne suka sauka kan lips dinta wani taushi yaji tare da shagala wurin shafasu yana yawo da yatsansa kan lips dinta,goce fuskarta tayi gaskia ya Omar baka kyauta min ba ,jiba face dina ta fada cike da shagwaba kamar zatayi kuka,

   

         Sannu yan mata ni da kika min har sau biyu fa,Ummi ce ta fito daga daki tare da kallon bowl din taga ba abinda suka gyara kawai jagwalgwalo sukeyi musamman Omar ma,dauke bowl dinta tayi tace kuje Ku karaci shashancinku,haba Ummi ki kawo mu karasa miki cewar Omar,a'a kuje na yafe.


    Cike da shagwaba Omar yace Ummi kalla rigata yanda jikarki tamini da ita gaskia ta tashi ta wankemin abata,yanda Omar yayi shagwabar abin daria kamar yaron da aka yaye jiya,Sosai ya bawa Ummi daria a ranta tana lallai Omar masu kudin gaskene naira da gata ya gama ratsa jininsu.


      Iklas kuwa bata San sanda ta kyalkyale da daria ba dan shagwabar Omar abun daria gashi tayi mugun yi masa kyau,Omar kuwa ya manta Ummi ba Mama bace ga Iklas kusa zata rainashi dan shi a zahirin gaskia bai San yayi bama don kallon Ummi yake kamar Mama.

   Daure fuska Omar yayi tare da shigewa room dinsa,kayan jikinsa ya cire ya fito ya fada toilet tare da sake feso sabon wanka kaji fa dan gayu readers,

       Wasu kayan ya canja  jean fari da wata tsadajjiyar T-shirt baka me rubutu fari an rubuta I do what I want da many an baki,

      Kallonsa Ummi tayi Umaru sarkin wanka ga iya shiga oh matarka tana shan kallo.murmushi kadan yayi Ummi kenan na gode.


    Kallonsa Iklas tayi da kyar ta iya Jan numfashi sabo da kyan da Omar ya mata,amma a fili tabe baki tayi cike da masifa wai ke Ummi an fada miki ya Omar bafa ya son matarsa kuma fa itama ta tsaneshi kudin sa take so,ita bata son aure tafi son aikin Gomnatinta,kuma yar isk......Omar ne ya cire kafarsa daga hadadden takalminsa ya dora tafin kafar a kan Iklas ya dungura kanta kasa ya danna sabo da Omar a tsaye yake jingine jikin bango yana danna waya.

     Ba shiri Iklas tayi shuru tana nishi,Ummi kuwa ta gama gane Iklas kishin Omar takeyi amma ita kanta Iklas bata gane hakan ba.

        Iklas ta dauka abin na Omar wasa ne,suna hada Ido taga idonsa ya canja yayi jajir kamar dai ciwonsa zai tashi don jikinsa har rawa yakeyi.da kyar Ummi tazo ta janye Omar tana ke in banda shirmenki Iklas me ya kaiki tsara karya kan matar mutum fada Ummi tayi mata sosai,ita kuwa Iklas mamaki  abin na Sir Omar ya bata.


        Maza ni yar banza me Jan fadan tsiya kije kiyi wanka ga magrib zatayi,da sauri Iklas ta shige wanka,Omar kuwa sai daya dauki like 5mnt ya dawo normal daga jin yanda zuciyarsa ke masa zafi.

       Bayan sunyi sallar isha Iklas ta dan Dasa kwalliya tasha Riga da skert English wears tayi matukar daukan kyau,shape sosai ya fito ta dan yi acuci da gashinta tare da yana mayafi karami,kwas kwas tasha choge,tana fitowa Omar ya watsa mata wani kallon koma ki canja shiga,ba shiri ta juya ta sa shadda dark purple duk cikin kayan da  Oga Omar ya mata ne.


       Ummi suka yiwa sallama suhaila na bada sautun chocolate, suna fita already mota sabuwa dal tana waje kamar yanda suka saba,yau Omar ba fara'a fuska daure Iklas tsoronsa takeji kar ya shaketa,a tsorace ta miko masa hannunta gashi ka rike kar a samu matsala cike da bacin rai ya fisgi hannun sai da kashinta yayi kara.


     Da sauri sukayi take away na abinda suke bukata suka shiga mota,suna hanyar fita daga wurin Sultan da security suka shigo wurin Sultan bai gane motar ba saboda Omar bai fiye yawan hawa mota kala kadan ba,kullum cikin sake motoci yake,


     Omar ma bai ga shigowar su Sultan ba yana can ya Lula duniyar tunani,suna dawowa gida  a bakin kofar Omar ya tsayar da Iklas kallon kallo sukeyiwa juna,u hv to be very careful wlh kika sake kika fadawa wani yanda ciwo na yake sai nayi maganinki ya fadi tare da tallafe mata keya tas ya zuba mata rankwashi kwas.


    Kanta ta dafe tare da turo baki tana dire dire da kafafu kallonta Omar yaa tsaya yi sai kuma yaji ta birgeshi tare da bashi tausayi,nan take ya tsinci Kansa cikin farin ciki gaba daya damuwarsa ta yaye,

     Hannu ya mika da niyar rungume ta,ita kuwa Iklas ta zata dukanta zaiyi da gudu ta goce ta zura gida da gudu wayyo Ummi ta fada palon, daria ma ta bawa Omar.

       Yau ko girkin dare ba Wanda yaci abunda Omar ya siyo musu shi aka baje aka ci aka sha akayi dam.


      Wurin 3wks kenan su Sultan suna aikin neman Omar amma shuru Allah baisa sun hadu da Omar ba,

    Ummi kawo mu siyo miki naman miyar cewar Omar,to Umaru kuje da Iklas akwai dan nisa tsakaninmu da wajen da muke siyarwa,yawwa Ummi kinga ma dan wasa kafarmu cewar Iklas tare da zaro hijab dinta iya cinya me hannu,Omar kuwa jallabiya ce fara jikinsa,

    Suna fita ya rike hannun Iklas kamar kullum suna tafiya amma Iklas ce kadai ke bashi labarin babanta da babarta da suka rasu,

      Sai kallonsu akeyi kamar sabon aure kowanne naji da nasa radadin kyan.

    Sunsha tafiya a kafa har baabban titi suka tsallaka sun siyo, sun bar wurin me naman kenan wasu suka parker da motoci wajen guda biyar,kartai ne manya manya wajen su biyar suka fito daga cikin mota daya, basuyi wata wata ba suka fisge hannun Omar daga na Iklas tare da make iklas gefe can har sai da ta fadi kasa,da gudu Omar yayi kanta da niyar dagata,wasu manyan kartin ne suka sake fitowa su hudu,sukayi sama da Omar tare da cusashi a mota,

     A gigice Iklas ta kama ihu da fadin barayi Ku taimakamin jama'a sun sace minji,kajifa Iklas wai miji, help me pls my husband oooo shuru babu Wanda ya jita wurin ba mutane gata abj ne,


    Motocin sun Fara tafiya Iklas na kuka ta zo tsallaka titi mota ta banketa a kan idon Omar domin yana bayan mota sun daureshi tam tam da igiya saboda sunga ya fara fisge fisge kamar me aljanu,Wanda su basu gane ba ciwon omar ne ya tashi sosai ba Iklas kusa.


       Omar na kallon mota ta bige Gomnati ya rushe da kuka a motar kamar yaro,ga zafin ciwo gashi mota ta bige masa iklas Gomnatinsa.

        Tuni kartan nan sun sanarwa Baffa da Sultan cewar sun kamo Omar,murna sosai sukayi baren ma Mama.


        Omar har yau hawaye yakeyi ga zafin ciwo,duk wani masoyin Omar suna nan sun hallara damkam a compound din gidan,ana son tarbarsa bakin kowa a washe.

      Iklas kuwa tuni jama'a sun taru a kanta,labari ya watsu mota ta bige gomnati, kaji fa popular. Wani dan saurayine me dan saukin kyau ya fito daga motar da ta kade Gomnati,baiyi wata wata ba ya sureta sai asibiti.





Asmahbaffa

   Asmabaffa

ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR

         GOMNATI

          ⓂⓂⓂ

            


            65-70

      


By

Asmahbaffa



      

       Wangale gate din su Omar akayi tare da jera Shiga wakeken rangadeden gidan da motocin gaba daya wannan kartan sukayi,Omar Wanda ya gama galabaita gashi an kawoshi har gidan da bazai iya rayuwa ciki ba,ji yake kamar za a zare masa numfashi yayin da motar da yake ciki ta shiga cikin gidan iyayensa,kafin ka bude ido Omar ya fara shuru shure da make make,gashi an daure shi kamar wani huhun goro,mutanen da suka taru za a tarbi Omar jiran fitowarsa kawai sukeyi suna washe Baku,Abdallah da suleim sai zumudi sukeyi,yayin da kungiyar haj.Rahina suka tsaya suna zage zage da masifa,aikin banza akan wannan fasikin suka wani taru aikin banza cewar Aisha,


     Bude motar akayi wasu mutum biyu suka fito da Omar dake cikin mawuyacin hali,Mama salati ta kwada tana hawaye ganin halin da danta yake ciki,da karfi Omar ya fisge kansa tare da girgije kartin nan daga jikinsa sai gasu kasa zube,huci kawai yake yana gurnani,kara ya fasa tare da zubewa kasa a yana ta birgima daga nan ya suma gaba daya numfashinsa ya dauke,mutanen dake wajen ko wanne salati da lahaula yakeyi,Mama kuwa kan Omar ta fada tana kuka haka ma su suleim,da kyar Baffah ya janyesu,su sultan ma har hawaye suka digar tare tausayin Omar,duk wani masoyin Omar sai da ya tausaya masa,su haj.Rahina kadai ke murna tare da shigewa part dinsu suka saki sautin kida.

     Sahar dake wajen itama domin sai da aka shigo da Omar sannan tazo wajen tana ganin abinda yakeyi tabe baki tayi ta kalli Baffa ta yatsina baki a kyaishi psychiatric hospital,

     Harara Baffa ya watsa mata ya wuce wajen Omar,ita kuwa sahar glass dinta baki ta kafta a fuska ta shige dalleliyar motarta ta koma inda ta fito.

      Kwance daurin da akayiwa Omar Sultan yayi,sannan suka taru aka dauki Omar aka kaishi room dinsa Wanda yasha gyara,wasu Allurori Sultan ya masa,gaba daya kowa ya tafi gida Sultan da Raj ne kawai zaune suna jiran tashin Omar suga taya zai farka.

    Mama da Baffah harma da su Abdallah suna palon Omar sunyi jugum jugum suna jiran tsammani,Umma Rahina tana ta yiwa frnds dinta waya cike da Murna tana basu labari,haj Binta tana jin labarin haushi taji taga lallai in tayi sake nan gaba Burin Rahina zai cika,don haka tace Sam wlh bazai yiwu Rahina ta fini kudi ba dole na wargatsa shirinta,sai na karya wannan tsafin da ta yiwa Omar. su sadiya kuwa rawa kawai suke takawa.


     Hospital Iklas kwance tana bacci saurayin da ya bigeta yana kusa da ita yana jiran tsammani tare da karewa surarta kallo,

     Saleem yana jin labari a rude ya fada wajen Ummi,da sauri ta tari saleem yawwa saleem maza ka bimin bayan Iklas daga aikensu amma har dare ya kusa yi,Ummi bafa lfy Iklas wai tana asibiti mota ta bigesu,innalillahi wainnailairrajiun,Ummi sai kuka Suhaila ma hakan dannan in sun mutu Ku fadamin,Ummi ba kuka za kiyi ba zo mu tafi kawai asibitin mu San a wanne hali take,guruf guruf Ummi ta sa takalmi ko mayafima suhaila ce ta mika mata hijab a waje,saleem rike da hannun suhaila suka shiga taxi suna bulayi har Allah yasa wani ya musu kwatancen asibitin da aka kai Gomnati.

  

     Fadawa dakin sukayi sai ganin Gomnati sukayi kwance saurayin na gefe,Ummi da Suhaila sai hawaye suke sharewa,Ummi na oh mun shigesu tsautsayi yasa na aikeku da nasan haka zata faru da ban fara ba sai ta kara fashewa da kuka,saurayi kuwa sai hakuri yake basu,haushinsa ummi taji ta juyo da masifa kwalabar ubanka dan jakar uba zaka dakeni ka hanani kuka ne?


A ransa sai dariar zagin kaka yakeyi,a fili sai hakuri yake bayarwa,kai da Allah ka rufe min baki cewar Ummi.likita ne ya shigo tare da cewar Goggo a daina hayaniya pls ta kusa farkawa,bata da wata matsala Allah ya gajarta wahala.

    Likita ina daya saurayinfa?wanne fa?dama su biyu aka bige?da Sauri saurayin yace no kaka wannan kadai na bige banga namiji ba,kan kakane ya kulle to Ina Umarunsu,dole su jira farfadowar Gomnati suji ina Omar ya tafi.sosai Ummi ta damu rashin sanin inda Umarunta ya Shiga.


       Baccin 6hrs Omar yayi sannan ya farka,ciwon dai yana nan sai dai Omar jikinsa Sam ba karfi dakyar yake daga yatsansa sabida Allurar da Sultan ya masa.

     Hawaye Omar ya fara ga ciwo na cinsa ga tunanin mota ta kade masa Gomnati, Sultan ne ya lura da farkawar Omar,da Sauri shi da Raj suka nufi wajensa,Mama,Baffa dasu Abdallah duk sun banko cikin room din,Omar kuwa ido jajir,ga karkarwar jiki tare da danne saitin zuciyarsa da hannu daya,

    Sultan ya kai hannu da niyyar taba Omar amma duk halin da Omar ke ciki saida ya make hannun sultan wai kar ya tabashi,Mama ce ta matsa kusa dashi ta riko hannunsa tare da dora kan Omar a cinyarta tana hawayen tausayi,Omar na jinsa a jikin Mama yaji ciwon ya karu,kuka ya fara tare da rungume Mama yana ajiyar zuciya,Baffa ma hannu yasa ya dago Omar  jinginashi a jikinsa,


   A hankali Mama tace Babana fada min me ya sameka haka?wacce cuta ce ta sameka haka ka kasa fada mana?wai ni wanne ciwo wannan Banana?

   Baffa ma haka ya dinga lallaba Omar yana tambayarsa meke faruwa,amma Omar yaki magana,kwanciya ma yayi kan bed yana numfarfashi.


     A hankali Omar yayi magana da kyar muryarsa ke fita,Ba..bazan..iy...iya...zama....nan..Gi...dan...dan..ba,Ku fitar.....da...in....Don't...Allah.

    In..kuna... So...na...za...una...Ku can...ja... Min gida...pls

Zuciyarsa ya kara dannewa yana idan....Ku...ka...barni... Nan... Mutu....wa... Zanyi sai hawaye ya ziraro daga idonsa.suma du mutanen dakin sai da suka goge ido.

      Yaci gaba da I....na..da matsala...a....lafiyata...Ku...fahim.....ce....ni.

   Da sauri mutanen dakin suka hada baki da karfi wallahi mun fahimta mun fahimceka Omar.

    Murmushin karfin hali yayi Ku...canja...min...wa...ni gidan....ko.....Ku..nemo...min...Gomnati,

   To fa mene kuma Gomnati?cewar Mama

     Iklas...na...ke ...nu....fi.a...dubo...min...lafiyarta...mo...ta...ta...kad..e..ta....ku memo...mi...n...ita...itace.....maganina.....da karfi ya kara volume cike da zafin ciwo She IS MY MEDICINE MAMA yana fadin haka ya kara sumewa,Sultan wasu alluran ya kara makawa Omar daga suma yaci gaba da bacci,sannan ga drip ya sa masa.kowannensu ya hallara a Palo suna tattauna maganganun Omar ya za a bullowa lamarin,Sultan yace Baffa da farko dole mu koma Neman Iklas a garin nan ina ganin itace Ummi wacce yake rike hannunta,wacce ta kawo sakon envelop gidan nan,kwarai kuwa Sultan cewar Mama.sannan dole fa a canjawa Omar gida a kaishi wani guess house din cikin gidajensa,kafin a nemo wannan yarinyar,sannan ya dace ayi masa maganinsa Hausa cewar Raj.Baffa ma yace dama hakan na fara tunani kawai.haka suka kwana a palon,baccinsu kadan ne.


      Da dare misalin 11 Iklas ta farka da Kuka wiwi kamar ranta zai fita sai shure shure takeyi an sace ya Omar,Ummi wlh wasu ne suka sace oga Omar,yanzu mu yaya zamuyi mun Shiga uku wayyo sir......wayyo Omar dinmu na mutu Ummi...na mutu Ummi....naga ta kaina...mene amfanina a duniya ni kuma Ummi...tawa ta kare...saleem ne ya riketa yana lallashinta da kyar aka samu tayi shuru,taki cin abinci ma wanka kawai tayi ta fara sallah bayan ta wacce ake binta ta koma yin nafeela ba ji ba gani har sai da ta kai 4am sannan Allah ya kawo nurse suka tsira mata Allurar bacci aka shimfideta tare da sa mata drip.


      Washe gari da safe  aka sallami su Iklas,gaba daya Gomnati ta birkice,bata uhm bare uhm uhm,ta daina ma magana wai duk cikin Bacin ran sace Omar take,damuwa ta shiga sosai su Ummi sai lallashi sukeyi tare da kwantar mata da hankali,Ummi tace kin San fa Baban Umaru me kudine yana can babansa ya sa a dauko masa dansa,ke banza ce wa zai iya sace Umaru,ai ba a satar manyan mutane yara ake sacewa idan aka dafa su ance sunfi manya dadi..Iklas kuwa dadi taji wai ba a sace Omar ba,daria ta saki kuma fa hakane Ummi ko a radio cigiyar yara kadai akeyi,can mintuna kadan suna Shiga gida Iklas ta fara kuka tayi missing din Omar sai gidan yayi wani iri,


     Tunowa tayi da cutar Omar yanzu tasan ma yana can ta tashi kukanta ta kara sautinsa sannan ta ruga da gudu jikin Ummi ta jata Palo suka zauna sannan Iklas ta kwashe labarin cutar Omar ta fadawa Ummi


    Ummi ma harda kuka Allah sarki Umaru,Iklas wayon banza ne dake me yasa baki fada min da wuri ba,wannan aikin sihiri da jinnu ne da tuni munyi kokarinmu an karya abin.nan Iklas ta Kara bawa Ummi labarin gidan su Omar kaf,harda dukan da aka mata su sadiya,da sahar matar Omar.sosai Ummi taji haushin Iklas da bata sanar mata ba.

     Ke rabu dani shashashar banza gashi nan ai kin jawo matsala da kin fada tun wuri da tuni haka bata faru ba,Ummi shi yace kar na fadawa kowa,yaushe dama ababen dake jikinsa zasu bari ya fada kar a masa addua.


     Ummi gobe muje gidan su ya Omar mu gani,ban yarda ba Iklas ki bari tukun muga abinda Allah zaiyi...kawai muyi masa addua,jiki sanyaye tana kwalla tace to Ummi sai kuma kuka ya kwace mata ta rufe ido da tafin hannunta biyo tana tunowa da rayuwar da sukayi tare da Omar.

      Yanda ya taimakesu,yake hanata kula kowa,kula dasu,yanda suke fada da kuma wasa da dariya.

    Kara tunowa tayi sanda ya shafa mata ruwan naman ganda a fuska sai kuma ta  fara daria ga kuma kuka da hawaye duk ita kadai.


    Ummi kuwa tausayi Iklas take bata,Suhaila ma damuwa ta shiga babu me siyo mata kayan sawa da sweet.da Sauri Iklas ta shige dakin Omar tana shakar kamshinsa tare da kwancia a bed din tana tunanin lokacin da taga Omar a mota tana talla a kwalta,yanda take kwala masa Kira ta glass din window tana Oga tare da daga hannu,murmushin da Omar ya sakar mata a lokacin shi ta tuna.


    Mikewa tayi ta cire kayan jikinta tare da daukan singlet din omar fara tasa, sannan tasa wandonsa short fari tayi kyau dama gata fara,ga gashi har tsakiyar baya.lekowa dakin Ummi tayi taga shigar Iklas daria Ummi tayi ta koma kitchen.Iklas kuwa mayyar Omar a dakinsa ta kwana tana jin kamshi tasha bacci kuwa ji tayi kamar ta rungume Omar shi yasa tayi bacci sosai.


       Omar washe gari haka ya farka da ciwonsa yana  a nemo min Magani ta,Iklas Mama kuma a fitar dani daga gidan nan,bakwa tausayina Baffa?ba shiri Su Sultan suka sashi Mota tare da kaishi wani rantsatsen gida ga yan aiki da security ko ina.Alhmdllh  kuma Omar ya dan ji sauki sauki,har yayi wanka da kyar tare da cin abinci abincin ma saida Raj yace in bai ci ba baza a memo masa Gomnati ba.

        Wani babban malamin Izala Baffah ya fadawa matsalar Omar,malamin yace Ku nemo yarinyar da yaron naka yace Alhaji sannan nasan wacce addua zan tofa masa a ruwa yasha.dole sai naga yarinyar na mata wasu tambayoyi sannan ayi addua.


         Address din gidan su Iklas Omar ya bawa Su Sultan, gaba daya Mama,Raj,Baffa da Sultan suka rankaya zuwa jin ya lafiyar Iklas da kuma daukota a kawowa Omar maganinsa.



     






Asmabaffa

ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR 

         GOMNATI

          ⓂⓂⓂ


              70-75


By

Asmahbaffa


     

    KUNA BIRGENI MASU COMMENTING KUNE NAWA .KHADY CHAFE  ALBARKA.




        Tsala tsalan motoci har biyu suka dau hanya daya motar Mama da Baffa dayar Sultan da Raj  Yanda suka ga unguwar su Iklas ta talauci basuyi zaton zasu ga gidan su Iklas me kyau haka ba,sallama sukayi Mama ta kutsa kai cikin gidan,Ummi da Suhaila suna Palo suna kallo,Iklas kuwa tana dakin Omar sai kuka da tunaninsa takeyi gaba daya ta rame sabo da bata cin abinci,

      Kamar kullum yauma sanye take da jallabiyar Omar milk color tana kan bed din sai shinshina wata T-shirt dinsa takeyi tana lumshe ido,gaisawa Mama sukayi da Ummi dama nice mahaifiyar Omar da sauri Ummi ta zabura Umaru Dana sani yaron kirki dan mutunci? sai Ummi ta fara kuka yaron da muke ta nema an saceshi,ki kwantar da hankalinki Omar yana wajenmu bari a kira sauran Mazan ma kiji bayanin komai cewar Mama.


    Da sauri Mama ta kira su Baffa su shigo,suna shigowa kowanne ya zauna a kujera,Ummi ce tace ina zuwa bayin Allah,a sukwane cike da murna ta shiga wajen Iklas tashi anga Umaru Ashe yana wajen Mamansa,gasu can yan uwansa sunzo domin yi mana bayani ki fito ayi a gabanki,ki fara kawo musu lemo da sauran kayan dadi,

     Iklas tsalle ta dira tare da murna kamar bakinta zai yage,rawa ta farayi tana Anga ya Omar...duniya sabuwa fil a kwali,ras nake jina wlh yau bacci harda munshari kuma zuwa wajen Omar ko ba tayar mota eh....eh....eh...Omarun mu.tana juyi.daria Ummi tayi tare da komawa wajen baki suna gaisawa.


     Iklas tsabar Murna ta Manta Rigar Omar ce a jikinta ta fito palon Gaba daya bakin suka zubawa Iklas ido,Raj ya zunguri Sultan a lallai dole mutumin ya rude yarinyar ba karya,gaskia dai cewar Sultan kaga ma rigar namijice jikinta kuma wlh kamar size din Omar ce rigar,Raj yace kuma ta mata kyau wlh.

    Baffa ma sosai ya tabbatar wannan Ummi ce me kai sako gidansu me hankalin nan.

     Mama kuwa ita dai tana son ummi bata San me yasa ba.Masu karatu karku manta Iklas da suna Ummi tayi amfani a gidan su Omar lokacin da takai sakon takarda.


      Tsugunawa Iklas tayi har kasa farin cikinta yaki boyuwa haka ta gaishesu baki kamar gonar auduga,kitchen ta wuce ta kawo musu lemuka da snacks,sannan ta nemi wuri gefen Ummi a kasa ta zauna,

     Baffa ne ya fara magana tare da basu labarin gidansa da komai nasa tas har lokacin da Omar ya bar gida,haka Mama ma,sannan Iklas ta basu tun farkon haduwarta da Omar har karshen da aka daukeshi mota ta bigeta,

    Godiya sosai su Baffa suka yiwa su Ummi suma su Suka musu tasu.Mama harda bawa Iklas Hakurin ci mata fuska da sukayi da kazafi,Mama ta kalli Iklas 'Yata Ashe sunanki Iklas ko ?Murmushi Iklas tayi Tare da sunkuyar da kai kasa cike da kunya tace ayi min afwa Mama.'yar kaniya cewar Ummi.


     Baffa ne yayi gyaran Murya ya roki alfarmar Ummi ta bashi Aron Iklas za a yiwa Omar magani,ita kuma Mama shawara ta kawo akan a daura aure tsakanin Omar da Iklas kawai tunda yana rike hannunta haka kuma ba san ranar warkewarsa ba,idan kuwa matarsa ce komai zaizo da sauki,sabo da gudun shedan gwara idan da aurensu ba Wanda zai damu.

     Ummi ce tayi magana duk naji batunku gaskia sai dai na Baku Aron Iklas sabida ko sec schl bata gama ba,kuma Allah gatanmu ita ce gatanmu,sannan Ummi itama ta fara basu tarihinsu Iklas kaf.sun tausayawa su Iklas gaskia.


        Baffa ne yayi magana Kaka gaskia abin a tausaya muku ne,kuma lallai Omar yayi abin kirki, wato ni Ku koma gidana da zama ke da kanwar Iklas, zan dau nauyinku babu matsala,kome kuke so ba matsala ga part din Maman Omar ne a wajenta zaku zauna abinda kuke so shi za ayi,kuma munyi muku Alkawari baza a fadawa Omar wannan auren ba har sai shi da kansa yace yana sonta zai aureta sannan mu bayyana masa,gudun kar mu aura masa ya zalinceta ma tunda babu wanda yasan zuciyarsa itama kuma yarinya haka ya dace ace da aure tsakaninsu amma bai dace ace kamarsu suna taba jikin juna ba kuma da niyyar magani shedan ake gudu.


ummi ma ta yarda da maganar su Mama kuma idan Iklas ta auri Umaru to tayi dacen miji.Ummi tace Alhaji na yarda da zancenku amma rigimar gidanka nake tsoro,karki damu Ummi nan gidan da kuke ciki Ku zuba yan haya Ku koma gidana fatanmu ki amince a daura musu aure.

Kefa 'yata?ya kika gani kin amince cewar Baffa yana kallon Iklas,har Ga Allah Iklas bata son aure yanzu gashi ko schl bata gama ba bare ta fara aikin Gomnati burinta.ita burinta ta fara aikin Gomnati sannan tayi aure ko banza ta huce takaicin da namiji.ga kawarta Fauziya kwanan nan ta samu teaching amma sai wanka take dauka rannan ma ta siyi fili a garin Abuja,ba ruwanta fantamawa take amma ita auren wuri za a mata abin haushi.

     Mata sai ci gaba sukeyi ita kuwa mijin ma da za a bata bai San ya aureta ba,ba sonta yake ba,gashi me mata,wlh badan Omar bane da ko sama da kasa zata hade baza ta taba aurensa ba.


    Amma kunyar Baffa da tuna Alkhairin da Omar ya musu,ya maidasu mutane yasa Iklas tace ta Amince kallonta kaka tayi tana mamaki,la..la...la..kaji yar banza mara kunya shi yasa gata nan kullum kayan Omaru take sawa daria akayi gaba daya tare da zuba mata ido.

     Turo baki Iklas tayi cike da shagwaba kai Ummi komai sai disgani.yo in ba munafunci ba me ya kaiki ko kunya babu wai ae kin amince.dama na Dade da ganoki.cuno baki Iklas tayi tare da shigewa daki.Sultan ne ya kalli Raj sukayi daria yace lallai Omar dan Iskane shi yaga abinda ya gani yarinyar tayi fa.

    

      A wajen Baffa ya kira yan Uwansa 20mnt suka zo su uku,Baffa da dayan dattijon walliyan Iklas,sauran kuma sukayiwa Omar,nan take suka dan taru a masallacin Unguwar harda liman nan aka daura Auren OMAR MOHD DA IKLAS,Iklas haushi ma taji an mata aure tana karama gaskia an dauki hakkinta dan ma tana so taga Omar.


      Baffa kuwa saida ya gargadi yan uwansa na Amana kada su fadawa Omar an daura masa aure.Baffa sun shigo gidan Alhmdllh an daura Ummi yanzu Ku yi shiri kayan sawa kawai zaku dauka Sultan zasu zo a daukeku Gobe insha'Allah,lefenta da sauransu duk zan mata komai idan lokaci yayi,duk da haka yanzu Mama zata hada mata akwatuna set ko 4 ne kafin na lefe suzo. Allah sa Albarka cewar Ummi.

    Sallama sukayiwa Ummi suka tafi cike da Murna.


       Ba Wanda yasan me akayi,saleem yana wajen aiki bai San komai.Ummi da Suhaila Kadai su suka gama shirya kayan tas,Iklas na daki tana kuka an daura mata aure bata fara Aikin Gomnati ba.shike nan miji zai rainata,komai sai ta tambaya.Ummi ce ta sameta a daki ta fara fada ke wato baki San lallashi ba ko,akan an miki aure kike kuka,Gata fa akayimiki,samun miji irin Omar ai sai an tona,Allah ya rufa mana asiri kina hauka,kin fi so mu tagayyara ana kiranku goyon kaka,'yayan mace,in ma zaki daina wlh ki daina taimakonmu sukayi mune abun tausayi idan kince bakya sonsa mata Dari zasu soshi,


     Da Sauri Iklas ta shigo ai wlh ba a isa an aure Omar ba shi din banza ya Isa ma,itama matar tasa na tsaneta.daria Ummi tayi to kince ba kya sonsa kuma...to wai ke Ummi nifa aikin Gomnati nake ji kar ya hanani.


     Yau naji shashasha ke ai Hutu kika samu,to bari kiji mata masu mushen tunani su ke tunanin sai sunyi aiki Gomnati za su sayi sabulu ko Omon wanki,Idan kin cika mace ba abinda miji bazai miki ba.Aikin mace shima yana da amfani,amma ki gane ko bakiyi boko ba indai mijinki na dashi kina kyautata masa ta ko ina baki Gaza ba to ba wani matsayi da baza ki taka ba.


     Mata nawane ko A basu sani ba kuma suka zaga kasashe, sun hau motoci na Alfarma, duk wani jin dadin duniya sun gama ji duk ta silar miji, suci takaucinsu tare kuma yayi kudi ki famtama sai marasa tsoron Allah Wanda nasan Omar baya cikin irinsu.


     Haka Ummi tayi ta yiwa Iklas nasiha da koya mata dabarun aure.

   Iklas kuwa jin Ummi takeyi tasa a ranta dole fa sai tayi aikin Gomnati domin ta tsaya da kafafunta.


     Washe gari da misalin 5pm Sultan da Raj sunzo da dankara dankaran motoci guda biyu daya aka zuba kayan akwatunan su Iklas daya kuma aka kwashe su sai city.Iklas kirmishishi bata kuka ganinsu tare da su Ummi.


    Tun daga gate Ummi da Suhaila suke kallon haduwa,suna fitowa daga Mota Najja kanwar su sadiya ta fito da gudu ta koma part dinsu tare da kiran gaba daya sis dinta har Umma kallon su Iklas sukeyi ta wani window suna kus kus,Sadiya tace Ku kyale munafukai zamu gano kulla kullar da makirar tayi, wlh duk sai munci Ubansu sai sun bar gidan nan.


       Suhaila daki daya aka hadasu da Suleim,Abdallah sai wani likewa Suhaila yakeyi,Iklas kuwa cewa tayi wajen Ummi zata zauna Mama tace ki dai zauna kawai amma Mijinki Marar lfy fa bari dai tukun a kawo Omar anjima mu gani inda yuwuwar zaman zai kasance.


     Sahar kuwa tuni ta kara guduwa gidansu wai Omar yahaukace,iyayenta sukace tayi zamanta dan kar ma a kawo Mahaukaci Omar watarana ya sheke musu yarsu tilo.


       Omar a daddafe yayi Sallar isha su Sultan suka daukoshi a mota sai gida,Raj gani yayi Omar kamar zai mutu tun kafin su Karasa gate ya kira Mama a waya cewar ta turo musu Iklas waje Ita kadai zata iya shigo da Omar gidan.


       Rankatakaf Mama, Iklas, Ummi dasu Abdallah suka fito Baffa shigowarsa kenan daga masallaci shima yaci Birki wajen motar su Sultan.


        Da kyar su Raj suka fito da Omar daga mota,Kamshin Iklas Omar yaji da sauri cikin mawuyacin hali ya dago kasa ai kuwa sukayi 4eye da Iklas wacce tuni ta fara kukan tausayin Omar duk ya rame ya fita a tunaninsa, Da kyar Omar ya wara hannayensa biyu cewar Iklas tazo gareshi.Mutanen dake wurin sai kallon su sukeyi cike da tausayi. Su sadiya ma suna daga cikin gate sun leko ta wata yar kafa.


     Iklas da gudu ta karasa wajen Omar tare da fadawa jikinsa tayi lamo a kirjinsa shi kuwa ya kankameta a jikinsa,hannuwanta tasa tare da tallafo kumatunsa tana Sir sannu ya Omar ciwon nan ya baka wahala,Iklas ina ta Neman ki su Mama basa tausayina,no  ya Omar sunfi kowa tausayinka fa,riko hannunsa tayi zo muje na baka abinci juyowa sukayi sai sannan Iklas ta tuna da mutane a wurin kunya taji zata zame hannunta daga na Omar taji ya kara damkeshi rada ya mata a kunne muje ni wlh yunwa nakeji.


        Su kuwa su Mama Murna da Mamaki sukeyi ganin Omar na Rike Iklas ya warke ya dawo sumul Mutum kamar kowa.Sultan ne yayiwa Iklas Magana ya kika tsaya kuma kuje ciki gamu nan zuwa,ki kaishi part dinsa akwai komai ciki har abinci an kai.


    



Asmabaffa

ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR 

         GIMNATI

         ⓂⓂⓂ


           75-80


By

Asmabaffa




      WANNAN SHAFIN NAKUNE MASOYANA.




      

       Rike yake da hannunta har suka shiga part din Omar.Su sadiya wani uban tsaki suka ja Ashe shegiyar marar kunyar yarinyar nan ce take wannan iyayayin da shishigi, Aisha tace haba no wonder ina ganinta naji na tsaneta Ashe yar bakin gida ce wlh sai tayi dana sanin zuwa gidan nan.

     Part dinsu suka koma kowa na fadin kalar nata muguntar da zasuyiwa Iklas.har palonsa Iklas ta kaishi dole tare suka zauna kamar chewgum haka ta zuba masa abinci ya tsaya yaci sosai da yawa sai da yajishi dam sannan ya Kali Iklas ina Ummi da Suhaila yanzu zasu shigo Good yace.


       Yana son ya saki hannun Iklas Gudun kar Mama ta ganshi yana jin kunya gata ita ba matarsa ba,yana wannan tunani su Mama suka shigo gaba dayansu,suna masa sannu,mamakin Omar yaga Sam su Ummi basu damu ba da suka ganshi rike da Iklas.

    Baffa ne ya shigo tare da malamin nan kowa waje ya samu ya zauna,Malam Usman ya kalli Baffa yace Alhmdllh mun godewa Allah lallai Allah da iko yake,dama Baffa ya sanarwa Malam usman batun auren da sukayiwa Omar yaji dadi shima malamin yace dakyau kar a sanarwa kowa yanzu tukun a bari ya warke. yanzu wannan yarinyar dole ta zauna kusa dashi har ya gama shan ruwan adduarsa Wanda a kalla na 3wks ne,a dakinsa zata dinga kwana dashi har agama komai,Omar kansa ya kulle sabo da cuta za a sabawa Allah su kwana 1room da wata.

 

      Kallon Baffa yayi Baffa kwana 1room da itafa haramunne za a sabawa Allah,karka damu Umaru ba abinda zai faru mun yarda daku,ta lafiyarka mukeyi cewar Ummi.

    Shuru Omar yayi zuciyarsa cike da tsoro,kwalayen ruwan faro aka shigo dasu na addua,dama malamin yanda sukeyi Ku zaku kawo ruwan roba carton din dasu ke addua ciki su Baku abunku a tsaftace ba shan cuta,Omar ma su Baffa kwali biyu suka kai na faro,sai kudin su za a basu masu tsada domin dubu Dari da hamsin malam usman ke yi ba ragi.


      Bayanin maganin ya fara musu a bashi yasha da safe Rabin jarka ragowar Rabin kuma da dare ya zauna a kan towel a shafe masa shi a jiki gaba daya,ga wannan ya mika musu man zaitun shima an Masa addua ciki kullum a shafa masa da dare a jikinsa,yau Ku fara bashi su.kome ake ciki Alh kamin waya..Godiya sukayi Masa ya mike ya tafi.

     Sultan da Raj ma jaddadawa Iklas sukayi kan ta kular musu da abokinsu sannan suka tafi gida,tuni su Suhaila sunyi bacci,Mama yau har hira kadan sukayi da Omar ammafa har yau rike yake da hannun Iklas,hannunta yayi gumi ya gaji.


      Baffa ma jaddawa Iklas yayi cewar ta kula da Omar ta Saki jiki ba kunya.sanna suka wuce part dinsu ita da Baffa,Ummi ma tayi nata sannan ta tafi,shi kam Omar tunani yake wai meke damun su Mama zasu hadashi daki daya da balagaggiya

     Kallon Iklas yayi yaga ita Sam ko a jikinta,harkarta takeyi tana latsa waya.kina jin fa su Mama wai ki kwana Room dina,ba tare da ta kalleshi ba tace to ya na iya?me zan yi ciki lfy fa za a nema maka.muje ciki kayi wanka ,fuska ya daure in sa'ankine zaki dinga sani abu wai?ko na miki kama da yaronki?lallai ka samu lfy sir ,muje pls ni bacci nakeji gwara ma ka taso,ni dai yarinya baki isa kin hau bed dina ba wlh,ba dan iska bane ni.


    Murmushi Iklas tayi to badan tsoro ba ka sakar min hannu mana yanzu a gani,baza a saki ba din,to kaga kuwa ai Kaine babban......sai ta tuna Oga ne fa wannan da sauri ta kulle bakin ta,saukar wasu rankwashi taji kwas masu zafi a kanta Omar ya zuba mata,

     Ouchshsh.....tayi kara tana Sosa kai,shice da shagwaba tace da zafifa zaka kasa kwakwalwata ta hadu da jini.

    Mikewa yayi rike da hannunta suka shiga Room dinsa,sakin hannunta yayi ya shiga toilet da kyar yayi wanka saboda ciwon ya tashi,kafin ya fito ta dauko kayan baccinsa tana ta sauri ya fito kar ciwon yayi karfi,

   Ai kuwa a wahale ya fito da sauri ta matsa kusa dashi ta rike hannunsa sai dayaji ya dawo normal ya kwace hannun ke nifa kina yawan sani aikata sabo kin dameni fuska daure yayi maganar,

      Fushi Iklas tayi ta mike fuuu ta dauko maganinsa da malamin ya kawo,to ko shima wannan din baza ka sha ba,ae bazan sha ba kije kira min Mama, fita tayi direct part din Mama taje kofa ta kwankwasa Mama ta fito Iklas lfy? Wlh Mama Ku fada masa ni matarsa ce yaki yarda ma yasha maganin komai fada yake min wai iskanci ne,kalla inda ya rankwasheni fa Mama,


     Kuma yace kije wai, murmushi mama tayi rigimamme ke kuma in banda abinki hakuri akeyi ai da marar lfy kuma kin San bai San matarsa bace ke,ni bazanje ba babu abinda zan masa kece me yin duk abinda ya dace kuma mun koya miki komai sabo da haka kije kowa yaji da mijinsa,nauyi ne kanki kije ki kula da mijinki.


     Jeki Allah tashe mu lfy,komawa iklas tayi itafa an takura mata an lakaba mata aure.komawa tayi ta sameshi ciwo ya tashi gadon tahau ko kulashi batayi ba ta dauko addua  ruwan faro ta tsiyaya a glass cup ta mikar dashi zaune da yake ciwon na cinsa karba yayi ya sha,ta kara bashi sai da ya sha rabi kamar yanda malam yace sannan ta dauko zaitun nan ma da kyar ya bari ta shafa masa yana ta lumshe ido sabo da dadin yanda take shafa masa kamar kar ta daina,sai mamaki yakeyi yarinya karama da abun mamaki,kato dashi take iya kula dashi haka,rigar ta dakko zata sa masa ya bige hannunta kin ma isa ke wai ni danki ne?mikewa tayi ta koma wata hadaddiyar kujera ta hutu ta kwanta,badai haka zaki kwana ba? kazama kije kiyi wanka,itakam ta gaji mikewa tayi tayi wankanta ta fito sanye da kayan jikinta,kije ki dauko kaya mana,mikewa tayi ga mamakin Omar yaga ta bude sip dinsa ta dauko farar jallabiyarsa ta koma toilet ta fito sanye da ita a jikinta,tayi kyau sosai.shanya waccan kayan tayi a toilet dinsa,fresh milk ta tsiyayo ta bawa Omar a baki ta sha itama suka kora ruwa tayi kwanciyarta,shi kuwa Omar ciwonsa yakeji,sai masifu yake karba

 

    Iklas tuni tayi nisa a bacci bata San me yake ciki ba,karfe daya na dare nishin Omar ya tasheta da gudu ta haura kan bed din yau ciwon na Omar ya banbanta da Wanda yakeyi wannan nishi kawai yake fitarwa da gumi shar shar,

    Iklas sosai take tausayawa Omar halin da yake ciki,tallafoshi tayi jikinta da kyar ta iya daura kansa a cinyarta ta jingina da jikin bed sai addua take tofa masa tare da shafa kansa,Omar bai San halin da yake ciki ba kawai dai yaji ciwon ya warke nan take bacci ya kwasheshi,Iklas tun tana masa addua har itama tayi baccinta a zaune jingine da bango hannunta kan sumar Omar haka suka kusa kwana,wurin 4am ta zameshi Daga cinyarta ta kifa jikinta ana Omar gashinta me matukar tsayi ya rufesu basu ma san a yanda suke ba haka suka dinga kwasar bacci,har rana ta fito basu sani ba,9am Mama da Ummi suka nufi dakin dan ganin ko lfy anjisu shuru,


     Ummi ce ta fara murda handle din tana zura kanta ta juyo ta fito tana mu koma Hajia yaran nan yan zamani ne ,Iklas ba kunya gareta ba ,murmushi Mama tayi tace Allah dai yasa karta fadawa Babana nafiso ya fara furtawaa tukun...to ameen dai cewar Ummi.


     10:30am Omar ne ya fara farkawa ji yayi kamar an danneshi hannu yasa zai ture Iklas daga jikinsa dan shi ya manta ma akwai Iklas,bai sani ba dai dai boobs dinta hannunsa ya sauka wani lutsum yaji kamar ya sa a flour,da sauri ya cire hannuwansa ya janye jikinsa,sai sannan yaga Iklas ce, a ransa yace kan uba dama yarinyar nan a bed dina ta kwana?

      Wannan batajin magana mayyar mazace,amma koma me ya faru su Mama ne suka jawo wlh ni ba ruwana.tunanin irin laushin jikin Iklas da yaji yakeyi,shi kam gaskia yarinyar nan zata tasar masa da sha'awar da zai kasa control.


     Da wannan tunanin ya shige toilet,Iklas kuwa tun farkawar Omar ta farka kunya ce ta hanata bude ido,kai yau sunsha bacci me dadi,Iklas tace yau na shaki kamshinsa da yawa bama na rigarsa ba na jikinsa.


     Mikewa tayi tare da mika ta gantsare tana salati sai murmushi takeyi ta fice daga room din da gudu,tana zuwa Palon Mama taja birki tayi turus ganin,Baffah, Mama, Ummi, Sultan da Raj.suhaila suna room suna buga game,Abdallah na koya mata da suleim.

     Kunyace ta kama Iklas musamman da tasan da jallabiyar Omar sanye jikinta,ganinta za ace mata mayyar miji,tunda Omar bai San da auren ba.

     Komawa tayi Inda ta fito da gudu su Mama kuwa daria ma ta basu,tana shiga dakin Omar ya fito daga wanka idonsa jajir yana jin ciwon amma ba kamar na da ba,da sauki sauki,

     Kallon Iklas yayi wai nikam tare aka haifemu ko mene,kin hanani sakewa sai kallon tsaraicina kikeyi bazan dauki wannan abunba ni,to ka bari nayi wanka nayi tafiyata mana.na fita wurin Mama naga mutane su sultan da Raj,


     Masifa ya fara yanzu a haka kika je maza suka ganki,jikinki fa yayi showing,Su Raj sunganki?ae har muka gaisa haushi Omar yaji da tsananin kishi baisan dalili ba.a tsawace yace Shiga kiyi wanka ki fitar min daga room,kuma ba ruwanki da ciwona na mutu ma mene damuwarki.


     Masifa kai ya Omar wallahi kasha ruwan alwala da cikin zafin nama ya rikota yana nunata da yatsansa kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa tunawa da yayi yanda take matukar kula dashi,damuwa da damuwarsa sakinta yayi kinci sa'a,kuka tuni ya kwacewa Iklas, 

Omar kuwa ji yayi ransa ya baci yasa Iklas kuka.


      Daga shi sai guntun towel iya kugu da wani a wuyansa karami farare jikinsa sai shining yakeyi ruwa dis dis.Matsawa yayi sosai kusa da ita wani shock yakeji itama wani abu taji yana fisgarta kamar ta rungumeshi,gudun kar alwalarsa ta karye kawai sai ya koma baya yana to me namiki kike kuka,kin kula shi tayi tana kukanta,to sorry yi shuru kinji Gomnati,sai kinyi Gomnati Allah dai ya biya Gomnati ba a ja daku.....daria ce ta kama Iklas sai kuwa ta fara kyal..kyal..kyal...Omar kuwa ci gaba yayi kamota nan kamota nan sai daria sukayi gaba dayansu tuni Iklas ta share hawayenta,shi kuwa Omar shagala yayi da kallon Iklas Tana dariar birgewa.Wani kayataccen kallo yake mata da yasa ta kasa jurewa ta shige toilet.da Sauri Omar ya shirya dan kar ciwo yaci karfinsa. Sallah yayi yau har nafeela yayi.inye su Omar an fara farfadowa.

     kayanta na jiya Iklas tasa ta fito itama tayi sallah da addua.

     Kafin ta idar tuni Omar ciwo yayi karfi.


       Zama tayi kusa dashi,kafadar ta tana gugan tasa sai ga Omar ya warke.hannunsa ta kama suka fita sashen Mama. Gaba daya suna palon ana jiransu kuwa.

     Kwace hannunsa Omar yayi ya koma jikin Baffah yana gaishe da kowa tare da musu Godiya.kowa ya jiki sukayi masa,tafawa sukayi da Sultan da Raj suna masa signa da ido suna kallon Iklas.


     Duk yanda yaso dannewa sai da suka bashi daria.Iklas kuwa suna gaisawa ta tafi dakin Ummi,tsantsara kwalliya tayi ta sa wata atamfa super cikin kayan da Omar ya taba dinka mata,bata taba sawa ba sai yau.Riga da skert sun kamata das tayi kyau,tasa red jambaki in ka ganta sai ka rantse yar shugaban kasasun


       Sai kamshi takeyi ta fito kowa kallonta yakeyi ,Omar ji yake kamar ya lasheta duk da cewar ciwo ya fara cinsa,su Baffah ciwon omar daure  musu kai yakeyi.


     Gomnati na zuwa taji kunyar rike Omar gaban su Mama,Gaba daya barin palon sukayi,Sultan da Raj ne kawai  suka zauna ganin kwakwaf.

      Omar sanye da wando 3quatr marar nauyi baki da blue,rigarsa blue itama,Iklas zama tayi kusa dashi wai kunyar Raj taji sai ta sa hannunta kasan cinyarta,ta danne hannun da cinya a hankali ta dinga tura hannun ta kasanta har ta tabo cinyar Omar.bata sani ba su Sultan na kallonta ai kuwa suka kwashe da daria,Raj yace mu ki daina kunyar mu ki kularmana da Frnd.ga breakfast dinku can.

    Harara Omar ya zuba musu ya fara magana.






Asmabaffa

[8:58AM, 4/10/2018] ‪+234 810 468 7075‬: ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR

         GOMNATI

          ⓂⓂⓂ


             80-85



  By

Asmabaffa




    READERS PLS A DINGA HAKURI DANI IDAN ANGA TYPING ERROR.JINJINA GAREKU CIKIN CONTAINER.




      To kome ya faru ai da laifinku kuna gani an hadani zama da baliga waje daya ko muharramata bai dace ba akan wani magani,idan ban warke bafa kunsa ina ta aikata sabon Allah.

       Murmushi sukayi Sultan yace kaji munafiki Raj wai mu zai dinga Rainawa hankali shi a dole Ustaz,kyaleshi mu wuce zanje office ni cewar Raj tare da mikewa,Omar ya fara gaku nan yan iskan gwauraye kullum Ku dami mutum,daria sukayi calm down Frnd da me ka fimu?mene marabar kwado da gaya,gwara mu bamu dandana ba kai fa tunda ka dandana kullum a damuwa kake cewar Sultan, tuni Iklas ta toshe kunnuwanta jin musun da suka fara yafi karfin kunnenta.

    Kun auna arziki da wannan yarinyar wajen da sai kun gane kurenku cewar Omar.su sun manta Iklas na wurin.ficewa sukayi kowanne ya nufi office. 


       Mikewa Omar yayi tare da fincikar Iklas zuwa dining,ina zuwa ta mike tare da komawa room din Omar ta dauko maganinsa ta dawo.


    Kafin aci komai zaka sha wannan fa kar a manta,yatsina fuska yayi Oh my God wlh kina takura min a duniya why kike min haka wai haka kawai zaki dinga bani wahala kina sani yawan magana,tsoro taji yanda taga yana kakkafe ido sabo da fadansa

       Hannunsa ta kara rikewa sosai haba ya Omar kana wahalar da shari'a kasanfa abinda ya kawo ni hidanku in baza ka sha ba zan bar gidan nan kawai ta fada da kalar tausayi,to ki tafi mana wani ya kawoki,gata fa ake maka,lfy ake nema maka,haba sir.karba kasha kaji....bazan sha bafa abunda jiya tsutsa na gani cikin ruwan,kai ya Omar kaji tsoron Allah wannan ruwan da yake neat,to yanzu ma gasu can ina gani a ciki.fafur Omar yaki shan magani wai tsutsotsine da ruwan

     Abincin dining Iklas ta kwashe to wlh baza kaci ba sai ka sha magani.idon Omar yayi jajir ya dago wlh ba Wanda ya isa ya bani magani,ko Mama ce? Eh ko waye na fada muku.

      Matsawa yayi zai damko Iklas wayyyyooooo Mama ta kwashe da gudu,fitowa su Mama sukayi gaba daya har Baffah ana lfy Iklas.tana haki tace wlh bazan iya ba zaneni zaiyi fa akan magani yaki sha wai tsutsa ne ciki.

     Baffa ne ya kira malam a waya ya fada masa komai,daria malamin yayi yace alhmdllh aiki yana kyau,dole ayi masa wayo yasha,karku damu sharrin jinnu ne komai zai warware insha'allah.


       Baffa ne ya lallashi Iklas kan ta jaraba bashi ita kadai zai yarda da ita.komawa sukayi daki akabar Iklas a tsorace.dabara ce ta fado mata

      Dakin Ummi ta shiga kamar gaske ta jawo akwati ta wuce ta gaban Omar Wanda ciwonsa tuni ya tashi,a gigice ya kalleta,gyale ta dauko ta yafa tana fadin tunda mutum yaki shan magani mene amfanin zaman sai na tafi gida ai bazan bari wani ya sake ganina a duniya ba.

    Da Omar ya shareta sai kuma yaga da gaske takeyi domin har ta fita compound na gidan.


    Iklas kuwa na fita suka ci karo da Aisha tana leken munafunci a kofar part din su Mama.zuwa tayi wajen Iklas tana yatsina fuska cike da rashin mutunci,su munafuka kuma nan aka dawo kenan aka tare,yayan matsiyata dangin jaraba yayan tsinaniyar Uwa,kafin ta rufe baki Iklas ta kwada mata mari,Aisha ta daga hannu zata rama taji an rike hannun gam tare da zuba mata wanu Marin sai da ta daina gani na wani few seconds, dagowa tayi taga wanne me tsautsayine haka Omar ta gani tsaye yana huci idonsa jajir,ai mukus tayi taja baya tana kuka sai wajen Ummansu. hannun Iklas ya kama tare da jawota cikin Palo,ita kuwa sai kuka takeyi.harda Karin shagwaba na ganin Omar.

     Kwace hannunta tayi ka kyaleni ni tafiyata zanyi kuma zan dawo na dauke su Ummi,a sanyaye ya matsa jikinta kamar zai janyota jikinsa ya rungume,habarta ya dago da yatsa daya ya sauke mata kyawawan idonsa cikin nata har wani zaiba zaiba Iklas ke hangowa cikin idon Omar,a ranta tace tab kaga aljani wannan kyau haka.

    A sanyaye Omar yace ya isa haka badai akan magani zaki tafi ba?kai ta daga masa wai eh,to bani zansha ko micijine a ciki zan sha.tausayi ya bawa Iklas sosai,murmushi ta saki tare da rungumeshi kadan haba ko kaifa,murmushi yayi ya janye jikinsa haka kawai baliga na rabarsa karfa yaje ya aikata barna,daria take sosai dama ita tsokanarsa takeyi ganin bai San matarsa bace ai kuwa zai sha tsokana cewar Iklas a ranta.kunji fa gulma wajen Iklas tana jin dadinta dai kawai.

     Ganin tana tunani ya dungureta ta kusa faduwa,dawowa hayyacinta tayi ta dakko masa maganinsa.tana dakkowa ya bata fuska to gashi sha kaji pls...kafada ya make kamar yaro.

         Kaifa kayi alkawari zaka sha masifa ya fara Allah karki bari na fara dukanki a gidan nan.me yayi zafi haka ya Omar?yi hakuri kasha kaji yi tayi kamar zata fara kuka sannan yace to bani na sha badan halinki ba.

    Murmushi tayi tace haaaaa bakin kulle bakinsa yayi in danki ne ko sa'anki zaki wani cemin Haa bakin ke nifa baki isa kin juyani ba.da kyar ya yarda zaisha maganin ba karamar wahala Iklas tasha ba.


    Cike da jin dadi ta bashi yasha sai fushi yakeyi,da kanta ta cika masa tumbi da abinci yayi dam.sannan suka zauna suna kallon film har Mama da Ummi suka fito suma, suna mamaki tare da jinjinawa Iklas,

     Ummi tace yar jakar uba Hajiya kinga yarinyar nan na fada miki kokari gareta ko waye sai ta iya ji dashi. Ummi ta dan daki kafadar Iklas Gomnati uwar yan lissafi kenan.daria sukayi dukansu har Omar dake jikin Mama Iklas sai kunya yakeji dan Omar ya riketa gam,

     Omar shugaban yan shagwaba yanda ji yan manne jikin Mama sai lallabashi akeyi cewar Ummi sai tsokanar Omar takeyi.Suleim,Suhaila,da Abdallah su suka fito suma sai wajen Omar suka manne masa,Suhaila ya jawo kusa dashi beauty ya garin,daria yaran sukayi.Mama ce ta gaji ta koresu.

    

       Mama ta saka Suhaila schl both islamiyya da boko class daya da suleim.Abdallah kuwa dama yayi candy tussia zai tafi karatu.

      Sadiya da Aisha sun fito da mazajen aurensu,sadiya wani Alhaji Dan Bala zata aura yana da kudi matansa 2 ita ta uku gidanta daban ya Gina mata.Aisha kuwa Yusuf dinta dan me kudi gaba daya a turai ya taso can ya girma.an kawo kudin aurensu yayin da Baffa yace su canja mazaje wannan Sam basu kwanta masa ba sukace su gaskia in za a musu aure a musu haka,in ba haka ba su hakura gaba daya,su rike aikin Gomnatinsu.shi kuwa Baffa ya karbi kudin aure aka sa biki nan da 3mnths.


      Haj Rahina tinda ta dawo taga Baffa ko harkarta bai wani cika shiga ba.wani bokanta ta sanarwa tace dole in tana son samun nasara sai ta kawar da Iklas nesa da su.cuku cuku ta fara yayin da kawarta Hajia Binta ta hanata aiwatar da hakan,ta yaudareta kan akwai wasu manyan aiki da ta kai ayi musu a kasar arna kudu.

      Hajia Binta kuwa malamanta ta bawa aiki kan a hana Rahina aiwatar da kudirinta kan Omar da Iklas,dan haka da Umma Rahina ta tasarwa aikata sharrinta sai wani abun ya faru Wanda dole sai ta kasa aikatawa,abin ya dameta,ta rasa wai meke damunta,amma tunda hakane zata sa su Sadiya suyi komai,ai tana da jininta.


      Omar bacci yake ji tuni ya fara baccinsa jikin Mama,Ummi kuwa tana can tana gyarewa Iklas kayanta tunda yanzu bata da wani lokaci,Gajia Mama tayi ta dauke kan Omar ta maidashi cinyar Iklas tace idan ya farka Ku koma part dinsa ta wuce Iklas... Tuni Iklas ta fara hawaye ita wai yanzu haka zatayi rayuwa duk ta gaji jikinta ciwo yakeyi,shike nan ita baza ta huta ba,kuma itama baccin takeji fa,ga shi an koma schl wayyo aikin Gomnatinta,


       Omar sai baccinsa yakeyi hankali kwance,Sai daya tashi dan kansa ganinsa yayi kan cinyar Iklas,sai haushi yakeji ansashi aikata sabon Allah.ko kulashi Iklas batayi ba sabo da haushinsa takeji an takurata.

      Kallo ya kare mata ke bakya damuwa wai hada jiki da mazan wasu?haushi ya kara turnuke Iklas bata San sanda ta kwanyawa Omar mintsini a cinya ba har cije baki takeyi dan mugunta,shakota Omar yayi ai kuwa Iklas dole me karfi yau baza ta kyaleshi ba,said suka fara kokawa tukuru suka kaure, shi Omar a hankali yakeyi da tsokana amma Iklas ita da gaske takeyi sai nishi takeyi wlh bazan dinga kyaleka ba na gaji ina ma Abu kana zagina.

     Sosai Omar ke shan dariar Iklas ita dole fada takeyi,Iklas da kanta ta gajiyar da kanta kawai ta fashe da kuka nan take Hankalin Omar ya tashi baya son ganin kukan Iklas,

 

      Bai San sanda ya rungume Iklas ba yana jijjiga ta tare da shafa bayanta,lakwas tayi tana goge idonta,cikin rada ya tambayeta kin gaji ne?kai ta daga masa wai eh,bacci ko?nan ma cike da shagwaba ta daga masa eh.to shine abin kuka kalli yanda kika farfasamin jiki da dukanki dama haka kike da karfi harda naushina fa kikayi ko dai kin taba zama a China ba a sani ba.

      Fashewa da daria Iklas tayi da ta tuno haukar da tayi tana ta kokawa da Omar bayan ita ta wahalar da kanta,hannunta ya kama suka wuce Room dinsa cike da shauki,Iklas tasha mamaki ganin har an gyara ko ina neat yana kamshi,suna shiga Omar ya dauketa kamar baby ya daurata bisa bed maza kema yi baccin tunda naga adawa kike dani kina min bakin ciki nayi bacci ke bakiyi ba,akan Mama ta dorani kan cinyarki kike bakin ciki.murmushi tayi abinta ta juya masa baya sai bacci.


     Shi kuwa a.c ya rage mata ya lullubeta da hadadden bargonsa ya shige toilet domin yin wanka gashi yau so yake Iklas ta rakashi masallacin juma'a sallah,ya Dade bai je ba.

         Sai 1 Iklas ta farka Arba tayi da kyakyawar fuskar yana zaune kasan bed hannunsa kan cikin Iklas kansa bisa bed yana ta bacci shima.minti kadan ya bude idonsa ya dorasu ana Iklas wacce ta shagala wajen karewa halittarsa kallo.

     Kunya taji ta mike tayi hanyar fita daga room din,pls ki shirya za muje masallaci yau.OK tace tare da komawa dakin Ummi.

       Ummi sosai ta kara yiwa Iklas nasiha tare da nuna mata muhimmancin miji.shiryawa Iklas tayi cikin wata rantsatsiyar doguwar Riga baka me adon Golden,cikin akwati set 4 da Mama ta bata kafin a hada mata lefe.

       Yana gyalen tayi a kanta,ta sa takalmi Golden da da jaka Golden masu tsadar gaske,kamar balarabiya haka ta fito.walwali kawai takeyi.

    Ummi ta yiwa sallama ta wuce dakin Mama da fara'a Mama ta tareta ina zuwa haka?Mama ya Omar zan raka masallaci zaiyi sallar juma'a.

       A dawo lfy a kula sosai kinji.to Mama insha'allah cewar Iklas.

  Har room din Omar ta kara komawa sai taku dai dai takeyi,a jikin mudubi ta ganshi da gani kasan karfin hali kawai yakeyi,wata mashahuriyar danyar  shadda ya sa ita ba fara ba ba kuma milk ba,yayi matukar kyau dan dagwas dashi,sumar nan taci kudi luf luf da ita,turaruka masu tsada ya fesa sannan ya kwashi wayoyinsa,Iklas an saki baki ana kallon zasu makara kawai hannunta ya rike suka fito cike da taku me birgewa.


      Yaran Umma suna tsakar gidan sai gulma akeyi.wucesu sukayi Omar wata gangamemiyar mota fara Sol ya nufa driver ya ba key ya tukasu suna Kane bayan mota, har masallacin da Omar ke zuwa.

      Bai fito daga mota ba sai da aka tayar sannan ya saki Iklas yaje yabi sahu,ana idarwa ya dawo cikin mota wajen ta,driver ya jasu ya fada Masa wani park yace can zasu je.shima wajen shakatawar manya ne,da Iklas dinsa ya fito.nama ya siya musu da abubuwan ciye ciye anan suka zauna cikin lafiyayyen wajen inda aka tanada saboda masu zama suci a wurin.


           Kafarsa ya dauka daya tare da zare takalminsa ya dorata kan kafar Iklas gaba dayansu wani yanayi zazzafa suka tsinci Kansu ciki tare da son kasancewa da juna.cike da farin ciki a zukatansu suka dinga baje girki a cikinsu.


         Sun mike zasu tafi sai ga Sultan da Raj suma tafawa sukayi suka fara yiwa Omar cakaki Jan Iklas yayi suka fara tafiya,kafin su karasa mota,dan saurayin da ya taba bige Iklas ya karaso wurinsu har wani kishi yake shifa bai yarda ba Iklas yake so.


        Haba baby Iklas rannan naje gidanku akace kun bar unguwar ina ta nemanki,nasha wahala wlh ko sunana fa Baku sani ba,pls ki bani numberki kinji.ya kalli Omar Wanda ya gama hasala.sannu malam, baby wannan yayanki ne?naga kuna kama dashi.Iklas murmushi tayi ta fara magana,




Asmabaffa

[9:00AM, 4/10/2018] ‪+234 810 468 7075‬: ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR

         GOMNATI

          ⓂⓂⓂ


             85-90



By

Asmabaffa



       

     KUJI DADINKU READERS.



        Sannu ya gida? Yayana ne mana,mun manta an rabu ko sunanka bamu tambaya ba,washe baki yayi Suna na IBRAHIM ZAKARI ana ce min IBZZY BOY.daria ta kusa kwacewa Iklas yanda yace Ibzzy boy har da daga hannu kamar masu wakar raps.shi a dole nigger.

       Omar yaso yayi maganinsa amma ganin kwata kwata ibzzy irin banzayen mazan nan ne sai ya shareshi,Iklas harda jin haushin Omar baya kishinta dan bai San matarsa bace ita.

      

Waya ta dauko da niyyar karbar number Ibzzy sabi da taji haushin Omar ba ko kishinta,fisge wayar Omar yayi tare da sa yatsa daya a dan chakurkurin kirjin Ibzzy ya tunkudashi baya sai da Ibzzy ya kusa faduwa,da masifa Ibzzy ya tasowa Omar dole sai ya ci mutuncin Omar, daukeshi da wani zazzafan mari Omar yayi Wanda yasa Ibzzy dafe kumatu ba shiri,kafin ya dago Omar har ya finciki hannun Iklas kamar tsinke kawai janta yakeyi har mota ya jefata,driver kuwa yaja a kabar Ibzzy da kumatu kumbure,a fili ya furta kai wlh saina ci uwar guy nan sai naga ubansa dan babarsa.


     Gida suka koma a compound suka ci karo da Abdallah zai fita da Sauri yazo wajen Iklas wacce ke kukan masifar da Omar ya zazzaga mata kan Ibzzy.da sauri Abdallah ya kai hannu da niyar sharewa Iklas hawaye Omar ya bige hannunsa,bai gane ba ya kara yunkurowa zai rukota Omar ya shiga tsakani da Sauri ya tsaya a tsakiya,

           Ya kare Abdallah kar ya taba Iklas,gocewa Abdallah yayi ya zame ya nufi Iklas anty wa ya Saki kuka kara kai hannu yayi,Omar ya jawo rigarsa baya kiiiiiiii ya dawo dashi baya,

     Abdallah sarkin naci kara komawa yayi shima Omar cikin zafin nama ya cakuma Abdallah ya turashi baya yana zan mareka wlh,to yaya kuka fa take, cike da masifa Omar yace ina ruwanka ko huruminka ne ban son shishigi...wuce kasan inda dare ya maka.sum sum Abdallah yayi gaba abinsa yana kallon Iklas,an hanashi lallashinta.


        Janta Omar yayi suka wuce wajen Mama... kallon Iklas tayi taga alamar tayi kuka,lfy Iklas me ya sameki?tana shesheka cike da shagwaba tace ba ya Omar bane dan kawai wani ya sanni munyi magana shine ya dinga min bala'i harda murdemin kunne wai zai cire min kunne, dadi Mama taji ganin Omar zai fara son Iklas fa,hmm nace Mama batasan zaman da sukeyi da Iklas ba su kashe su rufe.

     Lallashinta Mama tayi tare da balbale Omar da fada,Omar kuwa kememe yaki karbar laifinsa Mama muna tafiyafa ta kama magana da wani dan ta raina min hankali ni ina sauri zasu tsaya bata min lokaci idan zancen takeso yazo gidan mana zasu shiga rayuwata harda cewa wai ni yayanta ne..to ba hanani karbar number sa kayi ba,kinji ko Mama dan karyane fa wai zata karbi number sa, to koma ki karbo mana yanzu tunda baki da hankali

       Sai da ka bari muka dawo da ka barni mana tun acan cewar Iklas,gajia Mama tayi da cacan bakinsu tace dan Allah Ku je part dinsa kuyi can ni kun cika min kunne na rasa me gaskia cikinku.


   Da sauri Omar yace ni Karta zo min room,tabe baki Iklas tayi to me zanci da room din naka ko kace Nazo bazanzo ba tun yaushe na daina kulaka ma,ae naji cewa Oga Sir, yazo zai wuce amma saida ya matso jikin Iklas ya take mata yatsa daya.ihu ta fasa Mama tace maganinki kenan Babana muguntar tsiya gareshi in kika bashi haushi,ki dinga kyaleshi kishinki yakeyi fa ke baki gane ba.

    Karki yarda ki fada masa ke matarsa ce kinji ko,kai ta daga,idan ya warke kuma zaki koma schl sosai taji dadi wai zata koma schl,wayyo aikin gomnatinta.


        Umma Rahina ce tasa yarta Naja aikin kan tasan yanda za ayi ta shige jikin Iklas sosai har ta jawo musu ita ta dinga shiga part dinsu,kuma ta gargadi su Sadiya su daina nuna mata tsana a fili,ta hakane zasu samu nasara..Sadiya tafi kowa tsanar Omar kawai jiran lokaci take ta kaddamar masa ba tare da kowa ya gane ba.


         Ibzzy Boy ya cika da haushin Omar marinsa da yayi,kuma bazai daina son Iklas ba dole ya nemi gidan da suka koma yaje can,domin so yake ko ma ta halin kaka shi dai ya auri Iklas.wasu manyan kawensa mata da suke masa kawalcin mata JALILA WANKAN TSINKE da FATI GOCEWA ya kira ya shaida musu komai wankan tsinke tace haba Ibzzy kar ka ba damu mana kai da kake kullum matane frnds dinka amma ka kasa da wannan kucakar,


      Fati gocewa tace ka bari kawai zamu je wajen LAWISA ICEN KABARI harda LADI PIJO wlh sai mun shawo kan wannan yarinyar ba gaggawa a nutse zamu wayar da ita dole ka aureta ita din banza dan uwarta ko da ubanta take kwana wace ita ta kara narko wasu manyan zagi.nan suka taru Ibzzy sai barin kudi yake musu.


    Saleem ya kira wayar Ummi ta bashi address din gidan su Omar zai kawo musu ziyara sannan zai ga Iklas dinsa.sai dadi yake ji.har ya matsu Sunday tazo.


      Sahar taji labarin Omar yayi budurwa nan ta fara bala'i wlh bai isa ba yana warkewa zan koma gidansa dole na tara dukiya nayi tafiyata,ko wacece bata isa ta rabi Omar ba,kuma ko ya aureta sai na koreta  kuma sai ya saketa wlh,kai zan iya hallakata nan Sahar take ta bala'i a Office.wannan alkawarin sahar kenan itama.


       Iklas ce tazo sanye da yar wata Riga da kadan ta wuce gwiwa me dogon hannu ce red kanta ba dankwali sai gashi yarab,tunowa tayi bata bawa Omar magani ba tunda sukayi fada ga dare yayi.da tayi fushi dashi amma yanzu ta hakura zata je room dinsa duk da yace karta kara zuwa masa.

      A hankali da sallama ta shiga dakin nishin Omar kawai ta jiyo,kan sofa ta ganshi kwance amma dai tunda aka fara maganin suna ganin sauki,da dane da tuni Omar ya Dade da suma,


      Karasawa tayi ta dakko maganin wajensa taje ta zauna gefensa kadan ta dago kansa sai sannu take masa yau da yake baya cikin hayyacinsa ba gardama yasha maganin,

    Addua ta dinga tofa masa tana sannu kaji ya Omar tare da kara harde yatsunsu waje daya.

     A hankali ya dawo normal yau Iklas tsokanarsa taso yi dan haka zamewa tayi ta kwanta cinyarsa,haushi ya kama Omar yarinya ba kamun kai,ta gama lalacewa a dalilin talla.

      A ransa kuwa ji yake kamar su zauna haka har abada, zuciyarsa ta gayamasa kai bafa muharramakar ba ce kaji tsoron Allah don yana ganinku,ai da sauri Omar ya daga cinyarsa ya hantsilo kan Iklas ya mikar da kafarsa,

     Magagin baccin karya tayi ta wani taho luuuu ta fada jikinsa,zameta yayi daga jikinsa,hannunta daya ta dauka ta wani jefa luuuu kan cinyar Omar,wata zuciya ce tazowa Omar ya dauki hannun Iklas yayi wancakali dashi tare da mikewa ya shige toilet.


      Iklas kuwa daria taitayi amma kuma sai taji dadin hakan ta rasa me takeji haka tare da ita kuma bata ji a wani namiji sai Omar kadai.musamman da ta fada jikinsa sai taji wani ni'ima ta shigeta kamar ta karayi,tunani tayi tace ai kuwa tunda naji dadi saina dinga daneshi wlh,

     Wata zuciyaar tace zai rainaki,can kuma a fili tace to mene ma wai tunda mijinane sai na dinga masa wayo.

   Ai a islamiyya dama malam yace mana idan mace ta taba mijinta ladane,a radio har wanka akace idan kunyi sunna ce.

      Tab bazan iya wanka gaban Sir ba,murmushi tayi tace kai wlh a wandonsa watarana ina hango sandar girmansa tayi katoto da yawa zureriya bazan iya kallonta ba.shuru Iklas tayi ta fara tunani ai kuwa sau da dama nasha tabota by mistake uhmmm maza wlh yan iskane.

      Ya Omar Sam bai taba nunawa ko a fuska yaji wani abuba.Allah shiryeka Sir da gani nasan maita zaiyi.ita Kadai take zancenta har Omar ya fito daga wanka.

 

       Daure da towel yana tsane jikinsa kamshin sabulun wankansa ya cika mata hanci.tunda Omar ya fito Iklas ta kura masa ido wuri daya take ta kallo a jikinsa,kawai joystick din Omar take karewa kallo ta cikin towel a dole sai ta gano adadin girmanta.

     Omar yana kallonta shi kam ya sallamawa Iklas ya kyaleta abin nata yafi karfinsa amma akwai time zaiyi maganin marar kunya.


      Hakawai yaji Iklas ta tuntsire da daria a fili tace yau mun shiga uku mu mata.tsaki Omar yaja tare da maka mata harara.janye idonta tayi ta nutsu ta koma kallon kyan diri da skin na Omar,ciwonsa ya fara tashi yajiyo Iklas sama sama tace Allah me baiwa.

      Da Sauri ya dakko kayan baccinsa har zaisa yaji an karbe kayan a hannusa yasan Iklas ce,bako damuwa ta fara shafa masa man zaitun na magani.


       Mugun sha'awarta ce ta kara taso masa, ga shigar da tayi ta mata kyau ta janye hankalinsa. Har ta gama jikinsa har rawa yake sandar girma ta harba, Iklas kuwa ta samu abin daria sai kare wa joystick kallo takeyi tana murmushi hakan ma a boye takeyi kar ya kamata,Iklas ita kawai abar maza daria take bata,don akwai sanda ta leko daga gidansu taga wani Arne na fitsari a tsaye sai da ta tsaya ta kalle masa sandar girma tsab tana daria.


      Har yan ball idan taga zasu wuce sabo da wandonsu ana ganinta suma saita sa musu ido tayi ta sheka daria.

          Mikewa tayi da niyyar tafiya ji tayi Omar ya jawota tare da dorata saman bed dinsa,ya hau bed din shima cike da sha'awarta,ido ta zaro tana ina ina.....wlh....uhm...uhm tana yarfe hannu Omar Wanda ya mata rumfa tana tsakiyarsa,..nifa....ba...fa...daria nayiwa abakarba...kawai kawata na tuno.

    Kayi hakuri ni indai a gabanka ne nama daina daria gaba daya.ba tare da Omar ya furta komaiba ya fara kokarin cire mata kaya, kuka ta fara da yace abinda kikewa dariar ai zan baki.

     Sosai ta saki kuka na rantse da Allah bazan karaba I promise u,ni ban taba gani ba dan Allah ka yafemin,daria ta ba Omar sai da yayi murmushi sannan ya sauketa kasa.


     Tambayarta yayi kinyi wanka da sauri tace yes.bed chair ya nuna mata to maza kwanta can,a'a dakin Ummi zanje ni, OK to bari na baki abin da sauri ta koma ta kwanta inda yace.


    Hakikanin gaskia Omar baisan me Iklas kewa daria ba,ita ta fallasa kanta da ta kama rantse rantse dama kuma yayi zargin hakan saboda yaga inda idonta ke kallo.

     Wasu rantsatsun kayan baccin maza yasa rigar kalar singlet wandon Short ne guntu farare kal,turare ya fesa kala wurin 4.sannan ya kwanta tare da adduoi.

       Iklas tuni bacci ya dauketa.yau ikon Allah Omar baiyi ciwo ba har suka tashi lfy,sai mugun mafarkin da yake yawan yi.


       Iklas da murna ta fadawa Ummi,kowa yaji dadi.yau kuma Sunday yau saleem zai zo wajen su Iklas. Omar na dakin Mama Iklas ta rude sai shige da fice takeyi a kitchen,Duk abinda takeyi Omar na lura da ita,ya gama Dana mata tarkonsa.








Asmabaffa

[9:01AM, 4/10/2018] ‪+234 810 468 7075‬: ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR 

         GOMNATI

          ⓂⓂⓂ


              90-95


By

Asmabaffa



    

        Iklas sai da tayi girki kala 3 lafiyayyu da kayan  sha ta hadawa saleem,Omar fitowa yayi cike da kasaita ya hango Iklas tana waya,dai dai bayanta ya tsaya kamar zai shige jinkinta mika wuya yayi tare da Dora kansa a dokin wuyanta yana kara kunnensa jikin wayar yaji me suke magana akai,

     Iklas tana jinsa ta shareshi taci gaba da wayarta duk inda ta sa kafa sai Omar yasa dole yaji da wa takewa me take cewa, Saleem ne ya mata waya cewar yana hanya.


     Da gudu ta zille ta shiga dakin Ummi tare da fadawa toilet,wanka da sallar la'asar tayi sannan ta hau shafe shafenta,tasa wani lace red and pink,tasha kyau,kwalli da powder ta shafa sai jambaki shike nan tayi kyau,turare ma iya body spray ta shafa.sabo da tasan yanzu tana da sure,


       Takalmi pink,gyale pink Ummi yazo bari na shigo dashi yana waje,to Iklas ki kula kisanfa da auren wani kanki ban son shashanci,haba Ummi ki daina bata bakinki nasan fa me nakeyi.

    Tana fita taga Omar a compound lallai Omar yaji sauki yaushe da zai iya zama shi kadai haka,

    Shima Omar yasha wani narkakken yadi yayi kyau sai da Iklas ta kalleshi da yawa,shi kuwa Omar ba karamin kyau da girma yaga Iklas tayi ba,sai kallonta yake kamar ya hadiyeta.


      Bayan sun gama kalle juna Iklas ta fara tafiya,tunowa Omar yayi fa wajen Saleem zata je,a hankali cike da isa da takama kamar bazai magana ba ya mata alama da hannu tazo.

     Zuwa tayi ya Omar gani,kallon tsab yayi mata sannan yace je ki kawo min ruwa ,komawa tayi ta kawo masa,ta juya yace saura ki dauko furata a fridge,kai ya Omar bako fa mukayi,haka tana kunkuni taje ta kawo masa, da kyar ya kyaketa ta fita domin shigo da Saleem Wanda ya gaji da tsaiwa a waje tunda taxi ta saukeshi yake jiran Iklas.


      Saleem ya dau wankansa na talakawa ba laifi,Omar bakin ciki kamar ya mutu ganin Iklas ta jera tare da wani,da kyar ya samu ya danne zuciyarsa,a mutunce Saleem suka gaisa da Omar,Iklas cikin palon Mama ta kaishi,sun gaisa da Ummi harda hira haka Mama ma,sun yaba da hankalin Saleem.

Dan haka Mama ta tambayeshi matakin da ya tsaya a schl,yace N.C.E gareshi tace in ya samu time yazo zata bashi manager a gidan gonarta,sai ya samu kudin cin abinci sannan ya biyawa kansa schl.sai godiya da murna yakeyi.


      Bayan ya danci girkin Iklas wajen gidan suka fita shi da Ita suna ta hira,Omar tuni ya koma room dinsa jikinsa yayi sanyi lekensu kawai ya fara yi ta window bazai iya jurewa ba,ruwan da Iklas ta kawo masa ya daga ta saitin kan Iklas ta window ya shararo musu  ruwan,kafin su matsa juice din sa ya dauka ya watso musu,kafin su kalli wajen da aka jikasu Omar ya Dade da barin wajen,sun rasa waye ya musu haka,duk jikinsu ya baci Saleem yace maybe Wanda ya zuba bai San muna wajen ba,

       Hira sukaci gaba Omar sai zirga zirga yakeyi  ya rasa me zai musu ma.palon Mama ya koma ya kama yin abu irin na ciwonsa wai ciwonsa ya tashi,da gudu Suhaila ta fadawa Iklas ba shiri Iklas ta sallami Saleem ya tafi gida cike da jin haushi baiyi wata hira da Iklas ba kuma yau ya shirya fada mata sakon zuciyarsa.


    Iklas na shiga palon Omar ya mike yana wani narkewa ya janye Iklas zuwa part dinsa, suma su Suhaila sunyi Mama ki kwarai ganin Omar na numfarfashi amma lokaci daya ya mike garau.

     Mama basu San me akeyi ba suna daki.Iklas hankali tashe ta bishi har room dinsa sai wani lallabashi takeyi,a sofa suka zauna sai nishin karya yake tare da cewa mutuwa zanyi,da kyar idan zan tashi,wasiyata......sai nushi....a firgice Iklas tace dan Allah ka daina fadin haka Sir,no ni nasan me nakeji Iklas, fashewa da kuka Iklas tayi,ya ci gaba ban San dalili... ba.... sai.... naji bana son ganin.... mace da namiji.... tare.... ko wace Dana gansu sai ciwona ya dawo sabo.

     Yaya to ai kuma gani ni da kai,wasu nace miki ba mu ba,Ashe bakya kauna na warke ban sani ba..... gashi nan kin kula wani ciwona ya tashi,tausayinsa Iklas taji to indai hakane bazan kara kula kowa ba,yawwa ko kefe idan kuma ba kyaso na rayu to....haba ya Omar ka daina fadin haka ai na daina ma baza ka mutu ba da izinin Allah.

      Har Saleem bazan kara tsayawa dashi ba sai dai in dasu Ummi a wajen. dadi Omar yaji yayiwa Iklas wayo wani sanyi yaji a ransa.Ashe kinaso kiyi aikin Gomnati? zabura Iklas tayi tare da yake hakoranta masu matukar kyau da haske Allah Sir da gaske zanyi aikin Gomnati?kai ya daga mata yasan yanda take kaunar aikin Gomnati da wannan zai mata wayo.shi kam sai yanzu ya tuno ma Gomnati ce fa da kanta.


       Ci gaba yayi da indai kin min biyayya duk abinda nace kinyi to aikin Gomnati sai kin zaba,sannan zaki zama cikakkiyar Gomnatin,dadi ya gama cika Iklas kallonsa tayi zuru kamar zata shige masa fuska ya ka ganni a mota ta?ina tukawa fiiiiii, nayi gidana me kyau,habawa ai wlh har Office zan kaika kyauta, Omar murmushi yayi yace har na hangoki ai kin ma zama Queen kawai,

     Daria Iklas tayi me kayatarwa tace kai ai har rancen kudi zan dinga baka,Omar yace lallai zanfi kowa cin kudin kenan, da sauri tace sosai ma Kaine fa Ogana,

    har kudin man mota  du zan baka har ma rance in kana so kazo wajena,daria Omar yake sha kawai ganin shirmen Iklas da kuruciya,na biyawa Ummi makka,nima naje,Suhaila ma har schl zan tsaya mata. Cikin sigar rada Omar ya furta Good girl, mijinki fa? far tayi da ido aishi na daban ne amma bazan bashi ya min kishiya ba.kuma bazan ci dashi ba,dafa kafadar Omar tayi duk cikin labari bari ma kaji dai dai da eyeliner sai ya siya in ba haka ba yaga fuska ba kwalliya,kallonta Omar yake sosai yanda take zaro zance gata yarinya amma tasan wannan.

    

     Uhum ina jinki gyaran jiki kawai zan tai maka na masa da kudina saboda kaina zanwa,Omar ya gane sarai yace mene kuma gyaran jiki bayan wanka da kwalliya? Baki Iklas ta rike yanzu kai duk auren da kayi baka da labari lallai an barka a corner. daria Omar yayi sosai yace to ni me na sani, lallai ka fado wlh,ina fadama zan kashewa jikina kudi alaji sai kowa yasan Gomnati ta kama kasa.


     To ai baki fada min gyaran jikinka ko Wanda ake shafa muku halawa da kurkur indai wannan ne na sani, hmm kawai Iklas tace baza ka gane ba Sir,ana ma zancen gyaran gaske Wanda zai sa na zamo on top kana wani magana,assignment kaje ka tambayi matarka ni kunya zanji gaskia.


      Mikewa yayi tare da yatsina fuska je kiyi sallah magrib tayi maza sarkin surutu ki gaida Ummi.Omar ya samu sauki sosai yanzu baya ciwon da rana sai dare idan yayi mugun mafarkinsa shima mafarkin ba kullum ba.


   Najja ce yau tazo part din mama abin mamaki cike da ladabi ga mutunci sai fara'a takeyi,Mama tayi mamaki kwarai tasan wannan karyane da biyu.ruwa baya tsami banza.


      Bayan sun gaisa da kowa kujera ta nema ta zauna tana baza ido tana so taga ta ina Iklas zata bullo,shuru shuru Iklas bata fito ba,tana zaune tana jira.

      Bangaren su Ibzzy boy ma sun gama shiri tsab domin zuwa gidan su Omar wajen Gomnati domin tuni Ladi Pijo ta nemo address din su Omar, yayinda suka wanke Ibzzy suka karbi kudi me tarin yawa a wajensa suka shirya masa lissafin karya.


      Jalila wankan tsinke da Fati Gocewa su suka dau wankan sukari Ibzzy ya basu radediyar motarsa suka shige sai gidan su Omar.Najja tana ta faman jira su wankan tsinke suka shugo suma,sai yanga sukeyi,Mama dai bata sansu ba,kuma ita tasan bata da yarinya mace babba bare tace kawayenta ne,yan aiki Suna ta kyalkyale gida suka cika musu gabansu da kayan motsa baki.


      Cike da masifaffen ladabi kamar mutanen kirki suka gaishe da Mama,Ummi ma har tsokanarsu tayi da wasa tagansu masu ladabi.Gocewa tace Mama dan Allah Iklas na nan? Oh Allah sarki kawayenta ne ku?ae Mama,,to madallah an gode bari a kira muku ita.


      Kallon juna sukayi suka kashe ido daya. Najja kuwa haushinsu taji zasu bata mata mission. Kafin Suleim ta dawo daga kiran Iklas Sahar ma ta danno cikin palon tana tauna chewgum, so take taga tsinaniyyar da akace tazo gidan su Omar ta manne masa.

       Tunda Sahar ta shigo sukewa juna kallon banza Najja dasu Gocewa.Iklas kuwa tana can tana shirin raka Omar Office zaiyi wani signing da meeting shida wasu manya.

 

     Tana gama shiri ta shiga dakin Omar sun yi kyau,shadda yar gaske dark blue tasa shi kuma wani yard sharara light blue sunyi kyau sosai Iklas sai girma takeyi ga kyau ya karu.


    Kamshin dadi ne ya bigi hancinsu Sahar gaba dayansu,Mama da Ummi kuwa mikewa sukayi ko wacce ta bar palon.su Suleim ma sun tafi garden lilo za suyi.sakkowa sukayi daga sama harrrr idon su Gocewa gaba daya a Kansu.Jalila wankan tsinke bata San sanda ta kalli Sahar ba tace kut balaa'i na koka,wannan guy karshene wajen kyau wlh har na kamu.

    Fati gocewa ta karbe baren ma macen kamar balarabiya wlh ya iya zabe har naji kishi.


     Tsaki Najja ta ja ta gyara zama sai kallonsu takeyi ita kanta sun birgeta.Sahar kuwa Ashe lallai yau za ayi asarar rayuka ta kundumo ashar.Iklas mata ta hango damkam a Palo dan haka tun kafin su sakko ta sagalo hannunta cikin na Omar asanfa da aurensa kar ma wata ta so mijinta. Omar tuni ya hango Sahar shi yasa ya kara shiga jikin Iklas Sosai.

     Har Palo Iklas ta sakko sannunku kawai tace ta juya tana yiwa Omar rada a kunne dan kawai matan su gani taga sun kafe Omar da kallo.Omar kam kallon inda suke ma baiyi ba bare yasan da zamansu.


       Wankan tsinke sai yaba sumar Omar takeyi

Fati gocewa kuwa ji tayi basirarta ta kare kaf,zata sanarwa Ibzzy kawai ya janye wannan ba jagwal bace tafi karfinsa.

     Sahar ba abinda tafi jin haushi irin yanda Omar ya nuna bai Santa ba,kamarma bai San da wasu biladama a wajenba.Iklas ta gama tafiya da nutsuwar Omar sha"awa ta addabeshi tunda Iklas tayi masa rada a kunne, dama kuma kullum cikinta yake,ga so da tunanin Iklas hade da tsatstsan kaunarta sun gama mamaye zuciyarsa,

    

        Gaskia bazai iya ba gwara ya fadawa Mama a daura musu aure da Iklas ko zai samu sauki.

    Naja ce ta kalli su Sahar sai a bar mana gida kuma ai,Itama Sahar wankan tsinke ta fara zagi ai kuwa fada sosai ya kaure a tsakaninsu. Duk sun jiwa Kansu rauni ta hanyar cizo da yakushin juna, da kyar Mama tasa security suka kori su Gocewa, 

      Sahar fuska ta kumbura da cizo haka ta bar gidan, Najja kuwa da kyar take tafiya an barkala mata yatsan kafa da hannu ga tafkeken cizon su Gocewa kwance a kumatunta.


     Sai sannu su sadiya ke mata.Allah kara nace .


     Asmabaffa

[9:02AM, 4/10/2018] ‪+234 810 468 7075‬: ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR

         GOMNATI

          ⓂⓂⓂ

 

            95-100



By

Asmabaffa



    

  MASU COMMENTING MASOYANA DA MAKARANTA WANNAN NOVEL INA MUGUN JIN DADI KUNA BIRGENI TARE DA KARA MIN KARFIN GWIWA.




        Sadiya wacce ke kula da jikin Najja tace ke kika biyewa Umma na fada muku wannan tsinaniyar kodaddiyar yarinyar bata da kunya bata da mutunci,ki kiyayi shiga wajensu,Ku barmin komai a hannuna Ku daina daka ta Umma,

    Da sauri naja ta daga kai tace ai nima na daina biyewa Umma kawai cin uban yarinyar zanyi da kaina ba wani mutunci.

     Ko kefa ai shi ya dace kawai Ku nadawa shegiya duka cewar sadiya.


    Wankan tsinke suna komawa gidan shakatawar Ibzzy suka shiga nan suka fara bawa Ibzzy lbr,Fati gocewa tace wuuuuuu Ibzzy mu hakura shawara tafi karfinka wannan zukekiya haka matar manya ce,kai kaga saurayinta hadadden gaske.

    Wankan tsinke taja tsaki ni haushina ma yanda matan nan suka yakushemun jiki,Ibzzy Boy gaskia bazan koma ba na gama zuwa,Gocewa tace da ya aka barmu ma muka shiga gidan,shi kanshi shiga gidan su Omar duniya ne ko ina matakan tsaro ni kam na zare hannuna.

     Bakin ciki Ibzzy yaji Mara misaltuwa huci kawai yake tare sa furzar da iska, Omar yake kowa dan uwarsa yarinyar Na A.C dey for labs da zai nace mata,Ku dan uwarku ni zaku rainawa hankali in kashe muku kudi kuma Ku dawo kuna raina min hankali.


    Wankan tsinke tace kai dallah saurara ka daina zaginmu baza muyi ba ai munyi kokari ma kasa wasu suyi maka,mari ya kwadawa wankan tsinke Wanda ba shiri tana Allah ya isa ta bar gidan Gocewa ta mike zata tafi ya sa kafa yayi ball da ita saida ta fadi,da sauri ta mike tabi bayan wankan tsinke suka bar unguwar baki daya.an bar Ibzzy kamar zai Ciro zuciyarsa sabo da bacin rai.


    Gida Sahar ta koma ko ina tabon cizo jikinta ga yakushi kala kala a blitching face dinta kuka ta sawa Mum dinsu da Daddy nan suka gigice sai tambayarta sukeyi waye ya mata haka?Mum Omar ne yasa wasu mata suka yimin kuma wai aure zaiyi ni a fada masa ya sakeni,salati Mum ta saki wa yace kije gidansu to kema?kuka kawai Sahar keyi na shagwaba,Mum tace billahillazi Alhaji tun wuri ka kira Alhj Mohd yasa dansa ya sakar min yata,bazan yarda ba ehe,ka fada musu tun wuri ko naje gidan da kaina.su din banza matsiyata su dinga ganawa yata azaba.

     Alhaji yaja numfashi yi shirunki hajia dole ya bawa yata takardarta, kaita yanzu ta gasa jikinta,kiyi hakuri Sahar yana sakinki zaki tafi Canada ki huta doctor ya dubaki, cewar Daddy Sahar sai Murna takeyi zata hole a can.tafi sakewa a turai harka saida turawa.sai taji ma har ta matsu Omar ya saketa ta tafi Canada ta huta,dama can tayi karatu.


     Haj Rahina da Haj Binta sai hira sukeyi suna tafawa Binta sai tsara Rahina takeyi tana mata manakisa,ita kuwa bata gane ba sai kulla sharri sukeyi,Binta na hada mata gadar zare,

    Binta tace ai Rahina wannan yarinyar da ta dawo gidan nan wacce kikace ta manne masa to ita zaku hadawa sharri kawo kunnenki kiji rada tayiwa Rahina wanda ni kaina ban ganeba


     Bayan sun rabu da Haj Binta su sadiya ta kirawo ta fada musu shawarar da Haj binta ta bata,suma murna sukayi tare da jin dadi shikenan karshen zaman Iklas a gidan yazo Omar ma sai Baffa ya fatattakeshi.

    Aisha ce ta nemo wasu guys su biyu AUDU KALATA da SULE TAKWABE ta shirya musu komai ta sa suka dawo part din Umma aka ware musu daki daban su biyu sun gama shiryawa tsab.Umma ta sanarwa Baffa yan uwanta sunxo fa.


       Har part din Mama sukaje gaisheta tare da sa Ido su karewa bangaren Mama kallo dana Omar.

     Omar na dakin Mama yana bacci a gadonta Ikla itama tana wajen Ummi a room dinsu sai rubuce rubuce  takeyi a jotter ta haka itama baccin ya kwasheta ba tare da ta shirya ba.

      4pm Omar ya farka toilet din Mama ya shiga yayi alwala tare fa sallah,har karatun Quran yau yayi amma kadan sabo da ciwonsa da yaji ya fara motsawa.


      Addua ya shafa ya tako cike da kasaita har dakin Ummi,kara ruwa yaji ya gane Ummi ce keyin wanka,kallonsa ya kai wajen Iklas wacce ta kwanta amma gaba daya Rabin albarkatun kirjinta suna waje farare kar dasu yan madai daita masu matukar kyau,luwai luwai dasu,Omar ne ya kurawa kirjinta ido kamar yaje ya dan shafa amma sai ya danne sabida tunawa da yayi cewar ba matarsa bace,a take tsoron Allah ya shigeshi,

     Sai yace bazan kara kalla ba sai wata zuciyar tace dan kallo kawai mene ciki,sai ya kara kalla sai ya gani sosai sai kuma yayi istigifari ya dauke kansa,yana haka har Iklas ta farka bude idon tayi a hankali tare da saukesu kan Ahmad Wanda tuni ya shagala da kallon kirjinsa fir gigit ya dawi hayyacinsa.


       Mikewa zaune tayi ya Omar yaushe ka shigo ne?Harara ya watsa mata,kin wani baje kina bacci yaushe zaki sani,kin kwanta da wata karamar Riga jikinki du a waje yanzu in wani ya shigo fa?

     Mene to naga ba Wanda ke shigowa ne,Ashe zaki fasa yin aikin Gomnati a gidan nan,ke ko su Abdallah ba kya tunanin su shigo..haba dai ya Omar pls kar kace bazanyi aikin Gomnati ba,indai bakya kiyayewa bazan barki ba,ai ina kula sosai gani nayi Abdallah yaro ne,

    hmm Abdallah ne yaro ?almost 20 yrs fa cewar Omar,to me Abdallah ya sani ya Omar,ke kike ganin haka ni dai ki gyara ko bake ba aikin Gomnati shike nan baza ki sayi car ba,ba kai Ummi makka so u better change.ba musu tace I will,never mind Sir.

    Kallonta yayi cike da sha'awa a hankali yace Good for u.


     Ummi ce ta fito Umaru barka da shigowa ka shigo ina wanka,ba komai Ummi cewar Omar har kasa ya duka ya gaishe da Ummi.

      Yawwa Umaru gata nan ciwon Mara tajeyi anyi anyi tasha magani takiya sai bacci.

    kawo Maganin Ummi dole tasha,dukawa yayi hade da fakar idon Ummi yace maza kisha ko aikin Gomnati yafi karfinki kina gani mata zasuci gaba babu ke ciki.


      Sai shagwaba takeyi tana hawayen shagwaba  da kyar ta yarda tasha,shima sabo da aikin Gombati tasha kar Omar ya hanata yi.

        Har yau Iklas ke taya Omar kwana saboda da dare yana muggan mafarkai sannan ciwonsa kan tashi kadan.amma Omar baya hada shimfida daya da Iklas a kasa take sa katon bargo me laushi kamar katifa. 

     Kamar kullum suna kwance Audu kalata da Sule ta kwabe suka sadado part din mama cikin dare tare da yar rakiyarsu Aisha.

    Sai sanda sukeyi kamar barayi har dakin Omar ta kaisu.


     A hankali suka murda handle su Iklas ana ta bacci lallabawa sukayi tare da dakko wani farin handkerchief suka sadada suka shakawa Omar,nan take jikinsa yayi weak ba karfi ko kadan,idonsa lumshewa kawai yayi Sam yaki wani budewa bare ya San suwaye,


      itama Iklas haka suka mata, daukan Iklas sukayi tare da dorata kan bed din Omar,suka kifata a kan kirjinsa,Sadiya ce ta musu umarni da su fita suyi Sauri zata karasa aikin da kanta.ai a kuwa cikin sanda suka bar side din Mama suna masu jinjina baiwa da kyau irin na Iklas da Omar.

    Allah ya taimaki sadiya ba kayan kirki jikin su Iklas,Omar short ne kawai while Iklas guntuwar Riga,bata sha wahala ba ta zarewa Iklas Riga ta barta daga ita sai pant,Hannun Omar ta dakko ta Dora kan gadon bayan Iklas yayinda Iklas ke kwance male male kan kirjin Omar,tabbas su Omar suna hayyacinsu,suna jin Komai amma baza su iya tashi ba bare ma su bude ido su San waye ke aikata wannan aika aikar.

 

    Daria sadiya keyi kasa kasa cike da mugunta ta shiga daukansu pics kyas kyas kyas tayi sun fi kala goma a digital camera ta harda kunna hasken dakin Omar saboda pics din suyi kyau su fito radau.

     Tana gamawa ta kashe musu light tayi waje abinta.

 

     Omar duk ya gane kuma yaji pics aka daukesu za a kulla musu sharri sosai ya shiga damuwa,Iklas tuni ta koma baccinta a kirjin Omar wani dadin bacci taji ta kara gyara kwanciyarta tare da zura hannunta ta wuyansa ta kara rungumeshi hade da manna kirjinta a nasa,

    Abinda Iklas tayi shi ya gigita lissafin Omar,ya lalata tunaninsa nan take muguwar sha'awar Iklas ta dirar masa,mantawa yayi da ba matarsa bace,a hankali cike da kasala shaukin so na ibansa a nutse ya yi kasa  da kansa tare da hade bakinsu wuri daya,hannunsa ya fara Murzawa a lallausar fatarta tare da koma ya tallafo mazaunan Iklas ya shiga murzasu a hankali yana shidewa,

     Tuni Iklas ta farka tana jin komai itama dadin abin da Omar ke mata taji sai mutsu mutsu takeyi yayinda da Omar ya kara rikicewa hannayensa biyu ya daura bisa boobs dinta,Iklas wani likimo tayi ita tasan me takeji kawai,

       Boobs dinta ya fara sucking Iklas kara gyara masa tayi ta kara yi lamo kamar munafuka,rikicewa iya rikicewa Omar yayi ,Iklas harda tallafin kiss tayiwa Omar,sosai yaji dadinsa ta hanyar Romancing kadai yaji ya samu nutsuwa nishadi da farin ciki,


     Godiya yayiwa Allah da bai sa ya aikatawa Iklas komai ba sai dan Mirza,sai lokacin ya tuno Allah na nan fa,Istigifari ya dingayi tare da ture Iklas daga jikinsa cike da kasala dan har yau maganin da su Sadiya suka shaka musu yana aiki jikinsu,a haka bacci ya kara kwashesu .


      Karfe 8am Iklas ta farka Omar ta hango a kasa kan Sallaya yana azkhar,itama toilet ta fada cike da kunya da far in ciki tayi wanka,brush da alwala itama sallah tayi da azkhar,ta hau gyara room din,saida ta gyareshi tsab yana kamshi..sannan ta bawa Omar magani ta fice.Omar ba kunyar Iklas yake ji ba face Allah kadai.Iklas kuwa ta kasa manta Daren jiya sai dadi da kunya takeji tasan Omar mijinta ne ita.har mamakin dadin da taji takeyi,sai tariyo jiya takeyi,ya kasa barin kwakwalwarta.

    Omar ma haka sai dai kawai yana ganin ya sabawa Allah kuma Iklas zata rainashi.


       Sadiya kuwa sai murna suna ta kallon pics,Rahina ta sallami su Audu kalata da makudan kudade suka cika rigarsu da iska cike da jin dadi.tuni suka wanko pics jumbo guda biyar Iklas da Omar tsirara kwance makale da juna bed daya.wajen Baffa Rahina ta dauko pics tazo domin hada munafunci.





Asmabaffa

[9:03AM, 4/10/2018] ‪+234 810 468 7075‬: ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR

        GOMNATI

         ⓂⓂⓂ

 

            100-105



By

Asmabaffa




        Kasancewar Baffa yau a part din Haj.Rahina yake Yana side dinsa ta fada dakin ko sallama babu,Baffa na kan gado kwance ta zube masa pics ko envelop ba a sa ba,gashi nan ka gani danka da fasikar da kuka kawo gidan nan,

 

    Kuji tsoron Allah ku sallami yarinyar in ba so kuke gidan nan ya kama da wuta ba dan bala'i suka jawo mana

     Kukan karya ta fara yanzu Alhaji kamar Omar shi zai dinga wannan abu kuma a zuba masa ido,ba dole bala'i ya samemu ba.wlh ka guji fushin Allah.


    Sai da ta gama tsab sannan Baffa ya ja tsaki ya mike tare da barin part dinta gaba daya,dan yasan shirme za tayi masa da gulma batasan Iklas matar Omar bace shashasha cewar Baffa. baki  ta saki cike da mamaki Baffa ko ajikinsa to lallai su Omar sun gama asirce Baffa kamar tayi kuka sabo da takaici.


   Kyale Baffa tayi saida ta bari yana part din Maman Omar suna Palo gaba dayan yan part din Mama sun hallara ana ta hira ana ciye ciye,Haj Rahina ce ta kara fadowa palon tare da watso pics din jikin Omar tana wallahi baza ku jawo mana bala'i a gidaba,kallon Iklas tayi annamimiya karuwa,kafin kace me su sadiya sun cika palon Mama,

     Suna jiran suga hukuncin da Baffa zai yanke,Mama ce ta kwashi pics din ta kalla daria ma abin ya bata,zama tayi tana murmushi,Ummi ma tana ganin pics ta ja tsaki ta ci gaba da kwasar girkinta,

    Iklas kuwa daria take sosai ta kalli su Umma da su Aisha shekeke  gwalo ta musu tare da furta  kun makaro mission failed..Ku sake new.

     Gaba daya su Sadiya baki suka saki ganin ba wanda yayi mamaki ko bakin cikin ganin pics din bare ace har an yankewa Iklas da Omar hukunci.

  

   Omar ne kadai ya shiga matsananciyar damuwa da tsoron abinda Baffa da ma

Mama zasuyi masa sai gumi yake hadawa Abdallah ma hannu yasa zai karbi pics Omar ya bige hannun tare da kwace hotunan,kishin Omar kar Abdallah ya kalli jikin Iklas.

     Rahina tace algungumi in kana da gaskia ka bashi ya kalla mana,kasan bakayi dai dai ba,kallon Iklas tayi ke kuma muje zuwa sai kin bar gidan nan.

Ran Baffah ya baci ganin yanda Rahina take wa su Omar sharri,tsawa ya daka mata sai me to me sukayi a nan? Ke kullum bakya son zaman lfy,kinfa isheni ki guji ranar da zan yanke babban hukunci kanki.

    Alhaji kasan me kake fada kuwa cewar Rahina,kalli irin iskancin da yaran nan keyi amma ko a jikinka,sai ma Goya musu baya da kakeyi wato an gama dakai.

     korarsu baffa yayi daga part din Mama gaba daya.suka fice da borin kunya


    Shi kam Omar mamaki yakeyi sunyi laifi babba amma ko damuwa su Baffah basuyi ba sai ma ci gaba da sukayi da hirarsu cike da nishadi,kunya ce ta lullube Omar gani yake ya aikata babban laifi a ransa yace lallai iyayensa ba karamin sonsa sukeyi ba sabo da son da suke masa sun kasa masa fada kan mummunan laifin da suka aikata.


     Gashi har sonsa da suke ya shafi Iklas itama sun ki yimata fada.kunya ta cika Omar har ya kasa zaman Palo ya dauki key din mota ya fita,

       Shopping mall yaje ya dankarowa Iklas siyayya ta kayan sawa Dana kwalliya,sai kayan zaki da ya siyowa Suhaila da Suleim.

      Mama da Ummi suna ganin yanda Omar keta faman jin kunyarsu kayan ma daya siyo yar aiki ya bawa ta kai musu.har waya ya siyowa Iklas sabuwa dal Infinix ta dubu Dari da hamsim,Iklas sai murna takeyi tana godewa ya Omar.


     Mama da suke kitchen ta kaiwa kayan ta nuna musu,sosai suka ji dadi,Suleim da Suhaila da gudu suka ruga room din ya Omar suna ta masa godiya nan suka zauna palonsa suna ta surutu Omar na jinsu yana latsa waya,

     Ya matsu yaga Iklas,Sam baya jin dadi in bata kusa dashi,jiranta yake tayi ta Shigo don ya matsu dare yayi yasan dole zata zo bashi maganinsa,

    Tunanin daren jiya kawai yakeyi ba karamin dadi da Ni'ima yaji ba a jikin Iklas.

Ji yake dama tun farko itace matarsa,shi burinsa bai son auren mata biyu burinsa ya zauna da mace daya irin su Iklas ta isheshi.


      Masifa Ummi ta farayiwa Iklas. Da tsohon Daren nan kike tsara kwalliya haka,wlh ki dai kiyaye namiji baya jira ciki zai miki a banza,kuma kin San duk da kuna da aure shi fa bai sani ba,kuma baice yana sonki ba,ki kiyaye kanki har ya furta.

    Baki Iklas ta zumburo daga mutum yayi wanka nasa turare da powder sai lipglow fa kawai,so kike naje furkai furkai wajensa,tana shagwaba kamar zatayi kuka taci gaba bayan ke kikace duk son da mutum ke maka in baya tsabta wanka da kwalliya komai fes cikin kamshi in bakayi sai yaji baka birgeshi ka fara sire masa,kuma zanyi kince wani waye waye,me kike so nayi to mutum da mijinsa ke a zamaninki wa yasan me kikayi.


     Salati da sallami Ummi ta fara yau mun shigesu,ga marar kunya a fili karara,yanzu daga cewa ki kula sai kinmin gori,ke ga me miji ko?Iklas yanzu tun baki tafasa ba zaki kone,akan namiji ke a dole dadi miji, Allah yasa dai muma mun taba auren nan...ae naji din cewar Iklas....marakunya yar banza wuce ki tafi ki barmin daki,hijab Iklas ta dauka zata fita Ummi tace dauki wayarki kuje Ku Karachi rashin kunyarku,naga umaru ma da bai San ke matarsa bace ya fiki rashin kunya.


         Tuni Iklas tayi hanyar dakin Omar tabar Ummi da babatu,tana zuwa Palo taci karo da Mama da Baffa zaune kunya taji sosai sadaf sadaf ta wuce tare da cewa sannu da hutawa tabar Palon cikin sauri

     Murmushi Baffah da Mama sukayi na manya cike da jin farin ciki.

     Tana danna sabuwar wayarta ta shiga Palon Omar yau a Palo ta sameshi yana aiki a system dinsa dagashi sai singlet fara da short, dagowa yayi ya sauke kyawawan idanuwansa a fuskar Iklas,wani kallo ya mata tare da dan guntun murmushi,itama haka sannu da aiki ya Omar harda wani rusunawa ita a dole biyayyar miji,kujera ya dan buga da tafin hannunsa yana mata nuni kenan ta zauna ba tare da yayi magana ba,shi kuwa yana kasan kujerar data zauna,sosai yake shakar kamshinta,gajiya tayi ta cire hijab dinta ta lunke taajiyeshi gefe,wasu kayan bacci ne a jikinta Riga me gajeren hannu iya gwiwa da wandonta dogo masu laushi pink color.

    Sun mata kyau,wata hula tasa me Kyan gaske pink itama gashinta kuwa ya kwanta a gadon bayanta Omar har satar kallonta yakeyi.


     Mikewa tayi ta dakko masa juice ta tsiyaya masa yana danna laptop dinsa yana zukar lemo me sanyi,a ransa sai yabon Iklas yakeyi,wasu takaddu dake gefe sunfi Dari ya kwaso ya mikawa Iklas Biro sakko ki min signing a papers din nan ma'aikaciyar Gomnati,cike da jin dadi ta sakko kasa itafa yau duniya sabuwa tana taya aiki yau gata ga papers wai yau itace zatayi signing a papers,

     Shi kuwa Omar dan kawai yasa Iklas farin ciki ya bata tayi masa,sai dariya yakeyi a ransa yanda yaga Iklas ta kuke sai signing takeyi cike da nishadi har zancen zuci takeyi.

    Kasa yin aikinsa Omar yayi ya tsaya kallon Iklas kamar tana Office,babu bata lokaci ta gama du tana mika masa tace a kwai wasu,murmushi yayi sai next time,OK Oga Sir,biro ya kwala mata a kai,na hanaki fadamin Oga da Sir bakyajin magana.


        Wajen ta Sosa mantawa nayi fa ya Omar to ki kiyaye gaba if not a bakin aikin ki.ko ki fasa komawa schl,hakuri ta dinga bashi,

        Aikin ya gama ya shige bedroom zaiyi wanka har yayi shirin bacci Iklas tana palo,kayan wuta a kashe ya koma room Iklas na biye dashi,magani tabashi yasha ta mika masa na shafawa gashi ka shafa ai kaji sauki,

      Omar harga Allah yafi so ta shafa masa ko zai rage zafin radadin sha'awarta.kallonta yayi je ki kira min Mama ko Ummi su shafamin tunda me zaman jiyyar bata da amfani.

    

       Turo baki tayi taci gaba da yin shinfidarta a kasa ta kwanta abinta,haushi Omar yaji taki shafa masa a jiye maganin yayi a kasa yayi kwanciyarsa,Iklas tana kallonsa da ido daya.


       Saida ta tabbatar yayi bacci kana ta lallaba ta cire masa Riga ta shafa masa a hankali dan kar ta tasheshi tana gamawa ta koma wajenta ta kwanta duk abinda tayi Omar na jinta don idonsa 2 baiyi bacci ba.

Sai dadi da murmushi da ya dinga ji ba tare da Iklas ta sani ba.

   

       Bikin su sadiya sai karatowa yakeyi,suna ta shirye shirye,saura 3wks bikin.su Umma ba zama sai karbewa Baffan su Omar kudi takeyi komai suce hidimar biki ce.

     Ibzzy Boy ya hana kansa sakat akan Iklas shifa dole su wankan tsinke su rakashi gidan zaije da kansa. 


     Baban Sahar da Mum dinta ne sukayi sallama giidan su Omar ba kalar zagi da cin mutuncin da basuyiwa Baffa da Mama ba,duk abinda sukayi a kunnen Omar dan haka yace su je zai aiko da takardar Sakin Sahar.

  Dadi sosai sukaji sun rabu da kaya.


         Iklas na kitchen tana shirya dinner food Kiririn karar text taji a wayarta da ke gefe,number Omar ta gani,da Sauri ta bude text din 

      KINA INA?kawai ta gani,reply ta tura masa

     INA KITCHEN GIRKI NAKEYI. Minti daya wani sakon ya fado

     JAGWALGWALO DAI,KIYI SAURI NI KI TAHO KI BANI MAGANINA, reply tayi 

    KASAN INDA YAKE KASHA MANA PLS

    kirrrrr sai ga kiransa tana dagawa  cike da fada banson shirme kiyi sauri ki zo,kuma ki kawo min girkin naki na dan Dana naji yayi ko baiyiba ok dit ya datse wayar.


    Kallon wayar tayi ta saki murmushi sannan ta gyara kitchen ta ebi na Omar ta shirya a lafiyayyen tire na yan gayu,

     Wanka tayi tayi shirinta na kayan baccinta masu kyau,abicin ta dauka ta shiga part din Omar.

 





    Asmabaffa

[9:09AM, 4/10/2018] ‪+234 810 468 7075‬: ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR

         GOMNATI

         ⓂⓂⓂ


          105-110



By

Asmabaffa




    JANNAT AND ZULAIHAT  NA GODE DA COMMENTING READERS GABA DAYA.👍👍



       

      Kwance yake  headphone makale a kunnensa yana saurarar karatun Alqurani ta shigo palon bakinta dauke da sallama,a hankali ya amsa mata yana mata kallon kurilla 

      Sanyi yaji ya mamaye zuciyarsa,farin ciki yake tsintar kansa da zarar yayi tozali da Iklas,itama Iklas ta rasa dalili kullum idan basa tare da Omar bata jin dadin rayuwarta,


     Tiren hannunta ta ajiye gaban Omar cike da yanga,last maganin Omar ta dauko daga yau an gama shan magani ya kare kaf,Omar bai so hakan ba ko don Iklas dake jinyarsa yana jin dadinsa musamman Wanda take shafa masa a jiki

      Abincin ta bude kamshi ya cika wajen yabi iska ya daki hancin Omar nan take ya lumshe ido sai lokacin yasan lallai yana jin yunwa,carbage soup tasha kifi da pounded yam,sai kunun aya me dadin gaske da ta hada yayi sanyi,

      Serving dinsa tayi nan ya hau ci yana kora kunun aya me sanyi,sai da ya koshi ta dauke ragowar a flask din itama ta fara ci tana rufe ido sai Sosa kunne takeyi na iya girki wlh,ya kaji girkin nan? 

      Sai yau nasan lallai na iya girki,kai lallai mijina ya gama jin dadi dan zai kwashi gara,kallonta kawai Omar yakeyi yanda take yabon kanta,yatsina fuska ya yatsina ai idan yayi mutane zaki bari su yaba ba ke ba,kai ta girgiza ni ba ruwana bana jiran mutane,idan yayi na sani.murmushi Omar yayi tare da daukan maganinsa ya shanye.


         Already yayi wanka jallabiya ce a jikinsa toilet ya shiga yayi brush ya fito Iklas kuwa kwanika ta kwashe ta kara gyara wajen,dakin Ummi ta koma toilet ta wuce ta kara yin brush,ta fito ko kula Ummi batayi ba ta wuce tabar dakin,


    Hango Omar tayi zaune gefen bed yana jiranta,maganin shafawa ta dakko gadon ta hau tana a bayanshi bata son a bata mata lokaci tana da wani plan da zata rubuta a jotter dinta,

       Handsup tacewa Omar ba musu ya dage hannayensa sama rigar ta tattaro kamar wani yaron goye ta dagota sama hannunta ya gogi kirjinsa nokewa yayi yana shan yaji shshshsh,fasa cire masa rigar tayi tana ta diro daga kan bed din ta dawo gabansa ta tsaya tana kallonsa,shi kuwa kasa yake kallo,

    Iklas tazata ciwonsa ne zai dawo hannu biyu tasa a fuskarsa zata dago kansa,kin yarda yayi ya daga kan dan kar taga kalar yanda idonsa yayi jajir,dakire kan yayi tayi tayi ta iya daga amma ta kasa,

     Kyaleshi tayi ta koma bayansa zama tayi tare da mike kafafu ta sashi a tsakiya ta cire masa Riga  tik daga shi sai boxers,habawa Omar kawai vibrating ya fara dan dauriyarsa ta gama karewa, yana so ya kwace jikinsa gudun aikata haramci amma ina zuciyarsa baza ta bari ba yana ji yana gani Iklas ta rungumoshi jikinta ya kwanta rashe rashe a jikinta,duk ta zata ciwonsa ne zai tashi,

   

     Sumarsa me matukar laushi santsi ga yawa ta dinga shafawa a hankali Omar kara gyara kwanciyarsa yayi a jikinta yana narkewa tare da sa hannayensa ya rungumo hips dinta me fadi da laushi,a nutse ta dauki zaitun din guntun Wanda ya rage ta fara rubbing a sassan jikin Omar.


    Omar wani ajiyar zuciya yakeyi kawai a ransa yana Allah sa malamin ya bashi wani maganin na shafawa sabo da Iklas ta dinga Mirza masa a jiki,

    Itama Iklas a jininta take jin yama yama ga laushi da santsin fatar Omar Wanda Hutu ya ratsata,dadin shafa skin dinsa takeyi shi yasa take shafawa a hankali tana kara lallabawa sabo da kar dadi ya kare,

     Tsintar Kansu sukayi cike da shaukin dadi har ta gama shafa masa a gaban kirjinsa ya juya ya kifa kansa duk a jikinta yana shakar kamshinta me dadi, kafin ta karasa shafawa Omar ta gama kure masa maleginsa,

     Yanda kansa ke a jikin Iklas dagowa yayi a hankali ya fara kissing din wuyanta bite masa tayi tana ci gaba da shafa jikinsa,da zafi zafi ya hade bakinsu wuri daya tsotsa kawai yakeyi cike da salon kwarewa itama Iklas haka take shanye wa Omar lips masu tsananin birgeta,


        Idonta a lumshe yake tana amsar sako Omar ya zare mata yar rigar baccinta daga ita sai wata vest,nan ya birkice gaba daya ya ga palace tamjam da albarkatu sosai ya fara shafasu tare da sucking dinsu,tsorata Iklas tayi ta kwace jikinta ta mayar da rigarta zata sauka daga bed din,Kamar dan maye ya rikota tare da kwantar da ita a gadon a hankali murya dashe ya furta calm down bazan take dokar Allah ba,ba abinda zan miki.


      Hawaye Iklas takeyi itafa za ayi mata ciki bata fara aikin Gomnati ba,Omar ganin tana kuka ya fara lallashinta yana shafa gadon bayanta tare da mannata a kirjinsa,a nutse yace mene kika kuka?

    

   Narkewa ta karayi tana shesheka haka kawai... zaka.... min... ciki ban....fara....aikin... Gomnati ba,subhanallah Iklas kefa ba matata bace taya zan miki ciki,hannunki ma da na ke rikewa ba a son raina bane kema kin sani,

    Da Sahar kika ce ma zanwa ciki sai na yarda tunda ita matatace,kishi da bacin rai mai yawa Iklas ta tsinci kanta ciki kwace jikinta tayi cike da masifa fuuuu ta sauka kasa kan shimfidarta tana kunkuni sai kaje wajen Sahar din ai.


      Maganar duniya Omar yayiwa Iklas amma taki amsawa,wayarsa ya dauka ya tura mata text,  

        lallai zaki rasa aikin Gomnati yarinya,da Saudi ta masa reply cike da 

       masifa tace na rasa mana aikin Gomnatin me,basai nayi business ba,

    Wa zai baki jari to?

        me sona Wanda nake so 

waye shi? Bazan fada ba nima,ni kadai basan kayana

  ,tsaki Omar yaja.


      Sannan ya gyara kwanciyarsa ya ajiye wayar ko me ya tuna oho kiran Iklas yayi a waya duk da cewar dakinsu daya suna tare tunda taki magana a fili.

     Da sauri ta dauki wayar kamar ba room daya suke ba,

    Hlo? Mene kuma cewar Iklas,kiyi magana that's what want dit ya kaashe wayar,tare da leko da Kansa ta kasan bed din,kamar an mintsineta tace ya Omar a saitin fuskarsa,na'am ya akayi kaje dani Office dinka na dinga tayaka aiki sai ka koya min,bazanje dake ba kefa kikace baza kiyi aikin ba,wasa nake ma Allah ko dan danani kayi na hau kujerarka me jujjuyawar nan,


     Ko signing sai namaka pls,komawa yayi ya kwanta yace sleep joo kin dameni,da kyar Omar ya samu yin bacci sabo da sha'awar Iklas, Iklas kuwa kusan kwana tayi tana tuna kiss din da sukayi da Omar,da yanda ya mirzata.


      Sultan da Raj tare da sauran wasu frnds. Din Omar ne suka zo da yamma,sai hira sukesha na bikin sultan da za ayi nan da 1wk,

Karar Iklas suka jiyo daga compound wurin garden,Omar ya Riga kowa fita waje,su najja da Aisha ya gani sunwa Iklas taron dangi suna dukanta,daga nan suka dauketa suka jefa cikin swimming pool dake wajen ji kake tamjam.


     Cikinsu babu Wanda yasan Omar ya zo wajen,Iklas da yake jaruma ce tuni ta fito da kanta daga ruwan,hannun najja ya cafke Dana Aisha ya had a wuri daya,igiya ya samu ya hadesu a jikin bishiya ya dauresu tam ya zare belt ya fara laftarsu ba ji ba gani sai da ya farfasa musu jiki,dakyar su Sultan suka rike Omar,Iklas kuwa gwalo take musu tana kwalawa da karfi wlh sai ya Omar,kara musu,yawwa a kara musu,idan taga sun Sosa wajen sai ta fara Ce musu asosa mata asosa,

     Su Sultan har daria Iklas ta basu,Umma Rahina ce tazo kamar zata cire bakinta sabo da masifa zagin Omar da frnds dinsa take ta uwa ta uba, tare da shako wuyan Iklas Omar ne ya fincike Iklas daga hannun Umma gaba daya suka bar wajen,

     Kwance yaranta tayi ta jasu suna ta kuka ba ji ba gani.


       Wajen Baffa ta wuce ta tarar bayanan,waya ta maka masa yana dagawa ta dinga zazzaga bala'i,ki bari na dawo sai nasan abinda zanyi ya kashe wayar,gaba daya Rahina ta hana gidansa zaman lfy.


    Baffa yana dawowa ya kira Omar ya sanar masa komai Baffah nan ya watsar da zance bai kara saurarar Haj Rahina ba.haushi kamar su mutu Mama kuwa kallonsu kawai takeyi


     Omar ya warke sosai ko munanan mafarkanma  ya daina yau bikin Sultan Saura  2days gashi  Baban Yasmin budurwar Sultan ya hana party da sauran shagali,walima da daurin aure kawai sai kai Amarya, Omar ba zama 

  Iklas duk ta shiga damuwa bata ganin Omar ,gashi 2days ita kadai take kwana a room din,duk sai taji kewarsa,shima Omar dan kawai Sultan ne ya zame masa dole.da bazai iya zama ba tare da Iklas na kusa dashi ba.


    Anje daurin aure sun dawo angama walima da komai yan mata da samari cike taf a side din Sultan wasu da matansu suka zo ga wasu dangin su Sultan yan mata birjik,sai shishigi sukewa Omar Wanda a wajen Omar ko kallo basu isheshi ba tunanin Iklas yakeyi.

     Iklas tana zaune tayi tagumi da waya a hannunta,tunaninta daya kar Omar yaga wata budurwar ya kyasa,ko abinci ta kasa ci su Ummi sunyi sunyi har sun kyaleta.


      Kara wayarta tayi alamar kira ya shigo, Sweet Omar ya bayyana akan screen dinta,da sauri ta daga kafin tayi magana yace ki shirya kisa driver kice ya kawoki gidan su Sultan kiyi sauri fa...OK tace tare da fadawa toilet wanka tayi tasan gidan biki ne dan haka ta zauna ta tsantsara kwalliya wata doguwar rigar lace tasa light blue da baki rigar daga sama ta dame kasa kuma tayi tirgija kamar amarya bata daura dankwali ba siririn gyale baki da jaka da takalmi bakake tasa takalmin me dan tudu tayi kyau sosai abinka ga farar fata.

    Mama da Ummi tayiwa sallama ta fita kanta tayi acuci maza tayi kyau,kowa ya ganta sai ya kyasa,driver har gidan su Sultan ya kaita ya juya,cike da cat walking dinta ta taka har ciki,kowa sai kallonta akeyi wasu ma kamshinta ne ya jawo hankalinsu Omar yana saman bene yana kallonta,nan take yaji kishi dama bai ce tazo ba daurewa yayi ya danne zuciyarsa,


       Raj ne ya mata iso har wajen Maman Sultan ta mata Allah sanya alkhairi,sannan ya kawota Palon da Omar yake,maza ta gani damkam wasu da matansu,ido aka zuba mata kunya ta kamata,kafin tayi magana Omar ya dallawa Raj harara an kawo Iklas wajen maza za a kalleta, daria Raj yayi yace a to mu mene namu ciki.


    Tsaki Omar yayi ya riko hannun Iklas suka shige wani bed room.sai daria mazan keyi sunawa Omar tsiya,kowa da abinda yake cewa.

     


     Asmabaffa

[9:10AM, 4/10/2018] ‪+234 810 468 7075‬: ⓂⓂⓂ

   MA'AIKACIYAR

        GOMNATI

         ⓂⓂⓂ

 

         110-115



By

Asmabaffa


    


     MASOYANA MASOYA WANNAN NOVEL ALLAH DAI YA SAKA



      Kallonta Omar yake sosai yanda tayi kyau komai nata cas tsayinta dai dai,kibarta normal,hips,brst ma komai dai abin birgewa gashi kwance a gaban goshinta sak na larabawa,ba wata kwalliya takeyi ba amma mugun kyau takeyi,kunya taji yanda Omar ya kafeta da mayun idanunsa masu rikita mata tunani,

       A nutse ya kara kallonta kinyi kyau yan mata amma rigar ta matseki da yawa ga mayafin kin dakko karami an gama kalleki a waje ko?

     Hmmm ni fa ba Wanda suka kalleni har wani kyau nayi da za a kalleni wanne kallo ya rage da za amin ni da nayi talla a titi kasan ai kallo an gama yimin shi.


    Pls daina tuna min baya maganar yanzu mukeyi cewar Omar,farr Iklas tayi da ido Wanda yasa ba shiri Omar ya lumshe idonsa,kaji ya Omar kai kamar wani saurayina ko Wanda suka ce suna sona basa min haka,saleem kaganshi yanda yake so na amma baya min wannan tamnayar. wai Iklas fa a dole wayo zata  yiwa Omar wai taji ko yana sonta?

     Ki daina min zancen dan iskan yaron nan marar tarbiya cewar Omar, yayi ta sonki mana mene nawa ciki,abunda ina da matata,takaici Iklas taji wani kishi da tarin bakin ciki taji ya shigeta nan take idonta ya canja kwalla ta taru a idonta.


     Da Sauri ta saita kanta ta hanyar murmushin yake, ahaf gayawa Wanda bai da labari,dadin abun dai  matar taka da bata sonka bata damu da kai ba ta murguda baki,

    Mene hadin ki da matata to naga alama kin tsaneta da yawa,tabe baki tayi,me zan maka ka kirani nan gidan?abinci zaki min naci sannan muje ki rakani daukan amaryar Sultan, cike da shagwaba ta turo baki tana dire dire da kafafu ni...gaskia....uhmmm...Sir saida ka bari nayi kwalliyata zaka ce na shiga kitchen pls kayi order abinci ko mu fita kaci,

      Kuma kai amarya ni me zanje nayi tunda ni ba kawarta bace,to naji sarki surutu  muje na rakaki kitchen din Maman Sultan ba musu tace to,hannunta ya rike suka fito,suna fitowa frnds din Omar suka saki tafi kana wuta fa man ko wanne da kalar tsiyar da yakewa Omar,Sultan yace Ku kyaleshi shi ai da nuna mana yake shi na Allah ne,mune yan iska.

      Tsaki Omar yayi ,yaja baby Iklas dinsa har cikin gida, part din Mama ko ina kallonsu akeyi.Maman Sultan ta fara sallallami oh Omar Baku da kunya kai da Sultan  sai dai Allah ya shiryeku,duk mutanan amma tsallakesu kukeyi kuzo Ku dameni,mene ne kuma,mama ga kanwata Zata min girki a kitchen dinki,kun iya gulma Ku dai baza kuci abincin biki ba kun dorawa kanku aiki.


     Shigo muje Iklas ko?ae mama cewar Iklas.mama na juyawa Omar ya yiwa Iklas rada ko indomie kawai ki dafa min ki kirani a waya idan kin gama.

    Mama ce ta bawa Iklas wasu kayanta tace 'yata sa kayan nan kar na jikinki yayi dirty,karba tayi ta cire nata kayan a dakin Maman Sultan.ta sa zanin atamfa da wata T-shirt ta fada kitchen.

      Bata jima ba ta shirya masa egg source da couscous Tasha Koren wake da hanta a flask masu kyau ta zuba masa,Apple ta wanke ta markada ta juye a jug ba tare da tasa komai ciki ba tasa a fridge kafin ta sa kayanta ya dau sanyi,

    Dakin Mum Sultan ta koma ta sake yin wanka a toilet dinta.Mum Sultan tana jin Iklas tana birgeta bata da duhun kai wayayya da ita.kayan kwalliyar Jakarta ta dauko ta kara shirya kwalliya ta mayar da kayan da tazo dashi babu Wanda zai ce ta shiga kitchen,a wani basket me kyau ta shirya abincin sannan ta kira Omar,minti 3 sai gashi har kitchen ya kalli basket din har ruwa Eva ta sa ciki,inye lallai kina ji dani harda basket daria Iklas tayi ba irin matarka ba Aljana me suffar kunkuru,sai na fada mata ta zaneki ni ina jin dadin abata,fuska ta yatsina wannan ce zatayi sweet in and out nothing dey thr malam,murmushi Omar yayi yana mamakin Iklas da bata da kunyar fadar magana,ko dayake a cikin tsatsan arna ta zauna dole tarbiyarta ta zama haka,tayi kokari ma da ta tsaya iya haka,

     Dafe kirjinsa Omar yayi wash har kin tuna min da my Sahar I do love her so much,she is so very sweet,baya Iklas ta juya masa ta danne zuciyarta sannan ta juyo let's go na Sahar ikon Allah,Ganin batayi kishinsa ba yaji haushi ya juya suka tafi Iklas dauke da basket,sunzo shiga Palon waishi Omar dole sai ya cusawa Iklas takaici


      Wuce mana shi yasa nake missing My Sahar wayayya da ita ba sai nace tayi abuba,Iklas takai bango suna shiga palon ta ajiye basket tace sai ka kira Sahar ta karasa ganin zata kunyatashi a mutane ya kama hannunta kwace hannunta tayi, dungure mata kai yayi masifaffiya  jeki , zuciya ta kama Iklas ga mari ga tsinka jaka.


    U better watch ur tongue cewar Omar,fushi tayi ta wuce bed room din yana bayanta frnds dinsa cewa suke shegen kaya kana harka,

      Kwanciyarta tayi a bed din ta shareshi yana kallonta har ya gama yayi wanka cikin tsadajjiyar shadda ya fito sai da ya duba kalar lace din Iklas sai yasa light blue tunda lace dinta da blue jiki,

       Yasha kyau sai kamshi ke tashi cike da kasaita suka fito yan daukan amarya har sunwa Omar nisa,Omar da rigima shi da zai dakko amarya sai ya tafi da mota biyu shi da Iklas a daya motar driver kuma ya dauki wata motar shi zai dauki amarya.

      Motoci Jere aka fara iban kawaye da Dangi,wasu yan mata su Uku suka zo wajen motar da Iklas da Omar ke ciki,budewa sukayi dan Allah zamu shiga wannan kafin Omar yayi magana Iklas tace


     Wannan motar iyayan amarya zamu dauka Ku fita harda murguda baki,wata a cikin yan matan tace kaji yarinya Da iyayin banxa bakifi sa'ar kanwata ba motar ki ce?

     Oho dai ko ma me zaku ce baza a daukeku a motar nan ba,Omar kuwa yaki cewa komai,Raj ne yayiwa Omar horn pls ka kwaso su su kadai suka rage ni zan maidasu gida,Ku shiga badan halinku ba cewar Iklas, shiga sukayi daya daga cikinsu tace karfa ki kaimu bango duka zakici.


       Omar ne yaja mota yana jinsu Iklas sai tsige musu takeyi akan sun shiga motar su kar wata tayi mata snatching. Omar zaiyi magana Iklas ta rufe masa baki da tafin hannunta wai kar aji muryarsa,kiss yawa hannun a Jere sun  kai 8 ji kake dadas dadadas....yan mata Suma sai kallon kallo sukeyi,duniya tazo karshe yau ga budurwa da saurayi sun daina yin kiss a boyen ma sai a idon mutane,

      Iklas sabo da yan matan nan su gane matsayinta ta kama yiwa Omar kiss a saman lips,yan Mata sai gulmarsu sukeyi,daya tace bayin Allah kar kusa Allah ya tarwatsamu sai fada suke kar fa ayi hatsari dasu a banza.

       9pm aka raka ango,ko ina Iklas na gaban mota,har Omar ya tattara kayansa suka koma gida,


    Ummi da Mama suka samu a Palo,omar part dinsa ya wuce Iklas ta zauna wajen su Ummi kunsha biki cewar Mama sannu,yawwa Mama Iklas ta amsa.

    Mama ta kalli Iklas to dama so nake na fada miki daga yau baza ki kwana dakin Omar ba tunda ya warke,an gama komai na schl dinki Baffanku ya gama komai uniform ma duk komai an kawo,ranar Monday zaki koma schl ss3 za a saki dama.

   Taji dadin schl sai godiya takewa Mama, amma taji haushin hanata kwana dakin Omar, gaskia da Matsala,jiki a sanyaye ta koma dakin Ummi,tana Shiga ta kama hawaye an rabata da mijinta.


     Har Ummi ta shigo ta risketa tana kuka,lfy Iklas me ya sameki,kara volume tayi na kukan har kukan yara ta koma yi ayiye....yiye....me ya sameki ne wai yanzu muka rabu lfy fa,cikin kuka Iklas ta fara

    Ni nayi kewarsa...I miss him so much........,dan salon a rabani da mijina za a ce na daina zuwa...shan majina tayi idan an San hakane baza a bawa bawon Allah ni ba dan me zaku daura mana aure,Ummi ce ta bige mata baki,da karfi tana kuka tace shike nan bazan fadi gaskia ba,bawan Allah sai ja masa rai kukeyi baza a fada masa shi mijina bane,yanzu kuma an kuma cewa na daina zuwa wajensa akan wani kudirinku,

    Yanci ake nema miki c shashar banza, akan namiji Iklas kike sharban kuka haka Ummi ta fadi,make kafada Iklas tayi ni ba wani yanci,ya Omar fa me hankaline,kuma dan nayi kuka akan namiji haram ne?ai dai naga mijina nane, Ummi cike da takaici tace kije ki fadawa Uwarsa tunda ita tace ki daina zuwa kuma gata tayi miki sokuwa,wannan so ake nuna miki baki gane ba yar bantan Uba kin sani a gaba .


        Ciwonsa idan ya dawo ALLAH karma a kirani ai da dare ciwon sa dawowa yakeyi zamuga me kula dashi,kawai kun tsufa sai dai kuce wancen kuce wannan,haka Iklas tai tayiwa Ummi masifa akan Omar, cikin tsakiyar dare ta farka magana ta fara Allah sarki yanzu wani yana can ciwo ya dawo.

   Ummi Ce ta farka tana jin Iklas na surutu ta mata banza,kuka iklas ta sa ni wlh a barni naje na kula dashi.

     Da kyar da nasiha Ummi ta shawo kan Iklas ta kyalesu sukayi bacci.


     Omar kuwa juyi da tsaki kawai yakeyi Iklas taki tazo suyi hirarsu dan tana sashi nishadi,Mama ce ta shigo dakin,Babana tunda Allah yasa ka warke Na hana Iklas zuwa kwana room dinka shike nan sai ka daina jin haushi an hadaka da ba muharammarka ba,to Mama wa zai kula dani banfa warke ba,kaje ka dawo da matarka ta kula da kai,kamar yaron goye ya riko Mama pls ba abinda zan mata Allah zan kiyaye kiyi hakuri Mama, a'a bada ni ba cewar Mama,banfa gama warkewa ba kinga wuyana duk  kashi,murmushi Mama tayi Naji in zaka kwanta ka kwanta kaje ka dawo da matarka ko ka auri wata,amma Iklas baza ta dawoba,rokon Mama ya dinga yi amma ta ficewarta ta barshi da kyar ya samu yayi bacci.


     Ibzzy Boy ne ya koma wajen wankan tsinke ta rakashi har gidan su Omar sun Dade bakin gate security sun hanasu shiga ba dabarar da Basuyi ba amma security suka hanasu shiga gidan.

      Haushi ne ya turnuke Ibzzy boy amma dole ya hakura sai wani time din,ko a hanya yaga Omar sai ya ci uwarsa sannan dole ya auri Iklas,


      Sahar ma ta matsu Omar ya aiko da takardar sakinta amma shuru,ta matsu ta tafi Canada ta huta,tana ta jiransa har ta gaji ta yanke hukuncin da kanta zata je ya saketa ta dole,

      Washe gari da safe Iklas da wuri ta shirya kwalliyarta cikin wata gaunt iya gwiwa da wando pencil tight legins gashinta ta saki,Ummi na kallonta ta tabe baki,sai shegen chusa kai ba kwarjini.Allah yasa dai mijina na yiwa kwalliyar cewar Iklas tana fesa turare, da Sauri tayi waje so take taga  Omar jiya sun kwana basu ga juna ba,palon ta sakko da sauri  da Omar taci karo shima ya fesa gayu ya taho ganin Iklas dakin Ummi sukaci karo a hanya,

       Murmushi suka saki a tare Iklas kamar an mata bushara da aljanna tace morning Sir,how was ur night Gomnati cewar Omar yana kare mata kallo,Great tace,su Mama sun korar minke ko? Ae wai mu ba miji da mata bane shine sukace tunda ka warke shike nan,

     Ke kuma sai kika yarda ai sai kice ban warke ba,kai ka fada musu mana,Mama ce ta fada fa dole ayi mata biyayya,Iklas ta birgeshi a maganganunta,

       Ya Omar kalla botin din rigarka ya ciro matsawa tayi jikinsa tayi dage da kafafunta ta shiga gyarawa Omar rigarsa har Colar  rigarsa,sai daga gashin kanta yakeyi yana wasa dashi,Mama ce tayi gyaran murya da gudu Iklas ta shige wani lungu tasha conner ta tsere,


     Omar kadai Mama ta murdewa kunne sai kara yakeyi yana bata hakuri,na fada ma ka kawo min matar aure Mama ki sakar min kunne muyi magana pls,bazan saki ba, Mama to ki aura min Iklas mana  to ni banda wata, dadi Mama taji ta sakar masa kunne,amma kasan Iklas yarinyace bata isa aure ba,Mama ba abinda zan mata sai dai na koya mata karatu duka Mama ta danawa Omar a baya,marasa kunya tashi kaje ga break can,ita ai da tasan bata da gaskia guduwa tayi.


    Lekowa Iklas tayi suna hada ido da Omar suka fara magana da ido,Mama juyawa tayi da niyyar kallon me Omar yake wa signa da ido tana juyowa bul iklas ta bace ta kara shan conner   kar Mama ta ganta kunya takeji,

       Mama na barin palon Iklas ta sakko sai daria sukeyi kasa kasa kunnenka ya Omar yasha murda jifa yayi ja,ke ai wayo kikayi min,wlh ina ganinta na arce.ta window Iklas ta hango sahar taci ado tasha glass baki no respect.

     Laaaaa Sir ga matarka nan ka ganta yanzu zata shigo jibarta ko kyau.


    Aljana me suffar kunkuru gaskia an cuceka ya Omar an aura maka jagwal. Door bell sukaji,Iklas an tamke fuska ana jiran ko ta kwana karasawa wajen tayi ta bude kofar.







  Asmabaffa

[9:10AM, 4/10/2018] ‪+234 810 468 7075‬: ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR 

         GOMNATI

          ⓂⓂⓂ


           115-120



 By

Asmabaffa





    MAMAN SHUREIM jinjina gareki.




      Kamshin Sahar ne ya bigi hancinta yayinda ta bude kofar,atishawa Iklas tayi ta karya tana toshe hanci,Omar ne ya matso tare da kamo kafadar Iklas yana mata sannu, Sahar kallonsu tayi ta ja wawan tsaki,ya Omar wari ba dadi naji,sannu to cewar Omar, mari Sahara ta kaiwa Iklas,kaucewa Iklas tayi marin bai sameta ba,dan uwar ubanki wa yake wari?dama Tara ki nakeyi ke har kin isa ni sa'ar ubanki ce,yar matsiyata,

    Dagowa Iklas tayi an zaki iyayenta tace ubanki dai na gida me gemun dan akuya ba nawa ba,cakumo Iklas tayi suka fara kokawa Iklas ta dafalfale Sahar ta hanata yin komai,

     Omar har wajensu ya tako ya janye Iklas da kyar tana haki tace shegiya me bakin dorunar ruwa, murmushin yake Sahar tayi duk nasan akan wannan kike haukar nan zaki saukene idan akan wannan holokon ne,ubanki ne Holoko ba ya Omar ba,haihuwar kwarin kunya,wacce aka haifeta a titi,

   Omar ne ya rufewa Iklas baki ta kwace bakinta tana haki sakar min bakina ni,Sahar ce ta faki idonsu ta zabgawa Iklas mari kafin ta dauke hannunta Omar yayiwa Sahar mari biyu a jere,daria Iklas tayi woolu anji kunya mijinta ya tarewa budurwarsa ya mari matarsa a kan budurwa,kinga ko tanan na gama dake ke ko kula da miji baki iya bafa sai aiki,

       Baki omar ya makewa Iklas rufe min baki,Iklas kina sani Surutu fa,Sorry Sir cewar Iklas wai agani ita me ladabi zama sukayi a kujera suka share Sahar tsaye,yau Sahar a ranta ta fasa zuwa Canada ta kudurce sai ta koma gidan Omar so take ya auri Iklas suyi kishi sai ta koyawa Iklas hankali daga ita har Omar,juyawa tayi da wannan kudirin ta bar gidan,


      Omar kuwa Iklas ya kama yiwa fada ki daina tsokana Iklas zan daina tare miki,murmushi tayi Allah sai ka taremin yaushe zaka bari a daki Yar marainiyar Allah kana ji kana gani ai shi yasa nake yin tsokanar tunda nasan ina da kai.

     To zaki gani ki kara tsokana zaneki zanyi da kaina,baki ta turo a tsokani mutum ace bazan rama ba,shagwaba ta dinga zubawa Omar sai ya Sosa mata kumatunta yana zafi da kaikayi na Marin da Sahar ta mata

 

        Mama ce ta fito Omar meke faruwa ne naji hayaniya?daria Iklas tayi Mama kin zama yan sanda sai an gama fada,ko fashi duk wani tarzoma sai an gama kura ta lafa sai suzo da jiniya,daria sukayi gaba daya Mama tace ja'ira kin mai dani ma kamar kaka Ummi.


       Da safe Iklas ta fito tsakar gida tana bawa yan aiki shara tana kara sasu sunata kalkale kalkale suna hira sai son Iklas sukeyi maza da mata bata da girman kai, ya Omar ta hango ya dau wanka sai kyalli yakeyi wani me aiki ta tambaya Inusa wai kuwa dan Allah kuma maza kuna ganin ya Omar me kyaune?mukut Inusa ya sharbe yawun bakinsa yace eh....eh....hajia ai Alhaji Omar yafi kowa kyau ke ni  wlh ban taba ganin me Kyansa ba sai da na ganki.

     Dadi Iklas taji ai kawana ne  frnd dina ka gane ko cewar Iklas,daria Inusa yayi yace ai nan gaba hajia Oga Omar daga ganin Alama sonki zaiyi har aure,murmushin jin dadi Iklas tayi,ta kalli Omar da alama bai hangota ba,sanye da doguwar Riga wata siririya English wear da dan gyale ta fara tafiya tana kwalawa Omar kira ya Omar dan tsaya,har ya bude murfin mota yaji kiran Iklas, tsayawa yayi yana kare mata kallo rigar ta fito da shape dinta,tana karasowa Sir ina kwana,lfy me kikeyi a waje da safen nan?

   Wani waje naga yayi dirty fa shine na sasu su gyara, good to kar ki sake na kara ganin ki tare da mazan nan,jibi shigarki fa,so kike su rainaki?girgiza kai tayi alamar a'a.to ki kiyaye mene kike kirana tun daga nesa?

       Ya Omar kudi zaka bani nawa sun kare,me zakiyi dasu? Kyauta zanyi murmushi yayi to nawa kike so Hajia Gomnati cewar Omar, cike da shagwaba tace ko nawa ka bani ya isa,

    Wajen da yake ajiye kudi a mota ya bude mata ebi yanda zai miki,ni bazan iya iba ba ka bani da hannunka,Iban kudi yayi da yawa ba tare da yasan nawa bane ya bata.

     Ya Shiga mota kenan ya fara janta,Iklas ta kara tsaidashi da hannu,birki ya taka tare da sauke glass.


      Sir na manta zanje siyo alawar madara makwafta,sai kin dawo kiyi dai shigar kamala saura naji kin fita da Riga iya gwiwa,insha'Allah hijab ma zan sa,Allah dawo da kai lfy,ameen take care.

    Iklas harda daga masa hannu ita ga me miji.duk abinda Iklas sukayi a idon Haj Rahina dasu Sadiya,Iklas kuwa komawa tayi wajen aiki kowa sai da ta bashi 3k ta rike ragowar a hannunta ta fara tafiya domin komawa part dinsu taji an jawota baya,tana jiyowa taji Saukar mari tako ina,zafi ya hada ta ko ina,Haj Rahina ta makawa Iklas sanda a kafa, da karfi Iklas ta cakumi Sadiya ta cijeta a wuya saida ta daye mata fatar jiki.


    Da gudu Iklas ta bar wajen tana shegu Allah ya isa tsinannu ta shige part dinsu tabar su sadiya na sake saken yanda zasu kamata watarana.Umma tace idan kun kamata Ku sumar da annamimiya babanku yana ghana ba yanzu zai dawo ba sai bikinku gwara aci ubanta da wuri,Aisha tace Umma ya Omar ko kulamu bayayi dan yaga Baffa yafi sonsa,

       Kamar ba ubanmu daya ba,zanyi maganinsu gaba daya cewar Umma


     Iklas na dingishi ga fuska tayi jajir sawun yatsu rada rada a kumatu Allah yasa su Suhaila ta samu a Palo,su Mama basa nan.

      Bata so su ganta haka zasu shiga damuwa lallabawa tayi ta shige dakin Omar 

  Gyara dakin tayi fes duk ta canja bed sheet,su towel ta kai wa me wanki Wanda sukayi dirty,


       Tunda ta fara ba ita ta gama gyaran ba sai 3pm,Sallah da wanka tayi a side din Omar,daga ita sai towel ta lallaba ta zube kayan data cire,ta dauko Wanda zata sa,tana dingishi ta koma dakin Omar ta bar Ummi na baccin rana,


    Shiryawa tayi cikin Jan lace Riga da skert tayi kyau komawa tayi ta kai kayan data cire cikin dakinsu Ummi sai bacci takeyi,tashinta Iklas tayi Ummi zanje siyo alawar madara,kedai kawai son yawo irin naki,sai ki fadawa mijinki da babarsa kuma kar ki Dade,to Ummi,me ya sameki a fuska bata boye ba ta fadawa Ummi, Allah saka miki,ki kyalesu Allah na nan,karki fadawa Babar Umaru kinji,to kawai Iklas tace ta sa hajab dinta Iya gwiwa ta je wajen Mama ta mata Sallama,koda mama ta tambayeta gameda fuskarta gaskia ta fada mata bata boye mata komai ba,

Hakuri Mama ta bata sosai,Iklas ta siyo Alawar madara ta dawo sukayi 4eye da Ibzzy ya ciko mota dasu wankan tsinke,da gudu ta fada cikin gida tare da cewa securities kar Ku barsu su shigo,dakin Mama ta shiga Ummi da Mama ta gani ciki suna hira,


       Gadon Mama ta hau ta fara shan alawar madararta,ta basu tasu dasu Suhaila,tana sha ta rike wata a hannunta bacci ya kwasheta,to 5 Omar ya dawo dakin Mama ya nufa suka gaisa, sai hira sukeyi da Ummi yana satar kallon Iklas kafarta daya ta kumbura a kwauri wurin yayi ja,


     Fuskarta ya kalla nan ma shatin yatsu,gashi tayi ja,a jikin mudubi yake da,amma kamar an mintsineshi ya koma bakin gado ya zauna yana karewa Iklas kallo,Ummi tace kazo yin rashin kunyar taku tashi ka tafi,Mama tace abinci na kitchen jeka dan Allah zaka damemu.Mama kinga taji rauni fa,ga hijab jikinta tana bacci zai takurata,hannu yasa zai cire mata Mama ta bige hannun jeka zamu gyara mata,


      Omar shi kam an takura musu Ummi zai samu ya fadawa ta bashi auren Iklas kawai.

     Ficewa yayi room dinsa yayi wanka zai fito yaga pant da bra shanye a ciki,dubawa yayi sosai size din Iklas ne, ga alama ta gyara masa part dinsa,

    A ransa yaji dadi kowa ya auri Iklas ya huta,sai kallon bra da pant din yake pink color pant da bra din sunyi kyau.sai daya dauka ya jujjuyasu a hannunsa sannan ya kara shanya mata, harda bude window tare da kunna ac cikin toilet din saboda su bushe da wuri


      short da yar karamar Riga Mara nauyi me gajeren hannu omar yasa,dinning ya nufa ya ci abinci ya koma dakin Mama, hamdala Omar yayi ganin Mama da Ummi sunyi shiri zasu gidan suna,sallama suka masa suka hau mota driver ya jasu,

       Omar bed din ya hau a hankali ya cirewa Iklas hijab,ya gyara mata kwanciya,magani ya dakko ya shafa mata a kafarta,yana gadon Yana latsa waya shima haka bacci ya sace shi,kwance ko wannensu rashe rashe gadon Mama,

      Farkawa Iklas tayi sarai ta San Omar ne,tunawa tayi mijinta ne gangarowa tayi ta kanannade jikin Omar kanta bisa kirjinsa tana shakar kamshinsa suka ci gaba da bacci wurin magrib Omar ya farka janye Iklas ya fara kokarin yi

    Sam Iklas taki yarda saima kara makaleshi da tayi tashinta yayi a hankali ganin zata jawo masa aikata babban sabon Allah.

      Magrib fa ta kusa anfi son ayi baccin rana daga azahar zuwa la'arsar, oya tashi ki fada min me ya samu fuskarki?kalli ma kafarki,da gani kinci duka,kukan shagwaba Iklas ta fara gashi taki sauka daga jikin Omar,


        Lallashinta ya fara yi, yi shuru to ya isa haka nasan tsokana kikayi ko?kara narkewa tayi Allah sai ka ramamin dan kawai sunga baka nan suka dinga marina, ummansu ta kwala min sanda a kafa,

     Ran Omar ne yayi mugun baci, shi da baya shiga harkarsu dan kawai azauna Lfy shine zasu Dakar masa Iklas.


     Lallashinta ya dingayi sannan yace ta shirya zasu je gidan Sultan yau,Stl Iklas na jikinshi Mama ce ta shigo dakin sun dawo,kafin kiftawar ido Iklas ta dira a kasa, baram ta bude kofa a gigice, garam ji kake ta rufe kofar ta dauki hanya sai ta jiyo karar omar mama ta murde masa kunne tana buga masa pose dinta a bayansa,dawowa tayi ta kara kanta jikin kofar kiyi hakuri Mama nice fa na kirawoshi,da ya zo ma wani hadith yazo koya min a cikin wayarsa,da ga nan nace ko fiqhu ya ganar dani wani waje,


       Omar kuma a hannun Mama yana kinji gaskiya ko Mama,Iklas ita tasan gaskia,murmushi mama tayi eh dama dole tasan gaskia. Bari  Ummi tazo ta fada ma gaskiar magana,na gaji da halinku,Omar bai gane me Mama ke nufi ba

     Iklas daga waje tace  mun gode Mama Allah sanya Alkhairi. Daria Iklas ta ba Mama tana ganin tarin kuruciyarta.


       Juyawa Iklas tayi ta wuce wurin Ummi tare da fadawa kan Ummi tana murna, Ummi  kiyi Sauri kije Mama na kiranki, wani lamari ne me tsananin girma ya taso mana kaji karyar Iklas,


     Da sauri Ummi ta figa sai dakin Mama, da Omar taci karo Mama ta bankoshi waje.



      


Tnx all masu comment.





Asmabaffa.

[9:10AM, 4/10/2018] ‪+234 810 468 7075‬: ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR 

         GOMNATI

         ⓂⓂⓂ 

 

          120-125



By

Asmabaffa





     Dakin Ummi ta shiga da sauri,Hajiya lafiya kuwa gani nazo.

  Da mamaki Mama ta bambaya wa yace ina kiranki? Iklas ce ta shigo ta sanar dani babban al'amarine,daria Mama tayi oh yayan zamani nan ta labartawa Ummi yanda kan maganar take,

    Wannan ko shashar yarinya cewar Ummi, Mama tace naga yaran nan son junansu sukeyi sosai Babana ma yace a aura masa ita,idan yazo wajenki kice ya nemi soyayya wajen Iklas,idan muka ga ko mai ya dai daita sai a bashi matarsa.na sanarwa Baffansu ma komai shima ya yarda da shawarata,

   An godefa Allah saka ya tabbatar mana da Alkhairi cewar Ummi,Mama tace ameen ameen.

   Haka kuwa akayi Omar takanas ya samu Ummi ya sanar mata yana son Iklas ta bashi ita,ce masa tayi ya nemi soyayya wajen Iklas in tana sonsa ta bashi ita sai biki.godiya Omar yayi,yana ta tunanin ya zai yi ya fadawa Iklas yana sonta 

       Kar taki karbarsa yaji kunya amma bari dai zuwa nan gaba zaiyi shahada ya furta.


      Bikin su sadiya saura 3days Mama ma takanas take sa driver yana kai Iklas wajen me gyaran jiki daga nan har ranar da za a bawa Omar ita,tana zuwa schl idan ta dawo driver ke kaita,tayi kyau ta kara mirjewa da cikowa,skin dinta sai kyalli takeyi,

    Omar mamaki yakeyi yanda Iklas ke ta canjawa,in ya tambaya ina ake kaita sai suce Islamiyya take zuwa.


    Kayan gyara kala kala Mama da Ummi ke ba Iklas tana amfani dasu,da yake Iklas tasan kan gari shanyewa takeyi,har nata take hadawa kanta da fruits.

    Mama tayiwa Ummi da Iklas dinkunan ankon gidan kaf,har wasu ta dinkawa Ummi,Omar kuwa duk dinkin da yayi iri daya Dana Iklas,wasu kuma color ne iri daya,idan ya dinka mata material golden color to shima yadinsa ko shaddar ko suit etc irin same color da nata,

     Akwati guda ya kawo dakin Ummi kayan bikin su Sadiya na Iklas,takalma jaka da gyale duk ya hada,har jelweries ma.Ummi ma ya dinka mata wasu kalar masu tsada kala Uku.


    Iklas sai murna zata nuna wa su Sadiya ba a ja da ita,dan haka ta dage sai shirye shirye takeyi,tace duk sai ta kere su a daukan wanka kuma dole ne ma tana motar Omar zata kame a gaba taga me kallonsa.

     Bangaren su Sadiya kuwa suna ta shirya karya,sai sunyi bikin da yafi na yar shugaban kasa,Umma ta sakar musu kudin salary dinta da Wanda tayiwa Baffa cuwa cuwa,suma yaran nata haka,sai tatse angwaye sukeyi,

      Sai da suka shirya event sunfi 8,ko wanne a tsantsararren waje me tsada.anko kuwa yawansu ya baci,Baffa ya musu kayan daki na bugawa a jarida,duk abinda ya kamata an gamashi na biki,omar gudunmuwar 5million ya bawa amare suyi amfani dashi,tabe baki sukayi suka dinga zage zage an kwashi kudin Ubansu an musu kyauta dashi dan ace shi me kudi ne,yana sace musu gadon ubansu baza su yafe ba.


       Omar yaji komai amma ya toshe kunnensa ya sharesu,dan kawai a zauna lfy, saboda suyi was kawayensu karya su nuna yayansu me kyau ne hadadde na nunawa sa'a zasu nunawa frnds dinsu yayansu dan gayu me kyau ne,wannan dalilin yasa suka kawowa su Mama nasu pass card dinsu,kuma Haj Rahina tana tsoro kar fa bata yashi dukiyar Baffa ba ya saketa akan tambadadde Omar.amma da badan wannan dalilin ba bikinma sai dai su Mama suji anayi.

     Amare ba Hutu shi yasa Iklas ta samu sakewa,ba duka ba zagi bare bakar magana,amma da badan haka ba ita kanta tasan da tuni taci wani dukan.

     Omar yana zuwa office sosai shi yasa bai cika samun time ba,Iklas kuwa sai schl da kuma gyaran jiki,haka kullum HAJ MERO LALLAUSA me gyaran jiki ta gama tangarar da Iklas wajen koya mata dabarun zaman aure da kula da miji ba kunya.

    Iklas har tambayoyi takeyi wai duk dan ta kwacewa Sahar miji.burinta taga Omar bai son kowa,baya kula kowa sai Ita babbar fadar Gomnati take son kafawa a zuciyar Omar.

     Omar kuwa son Iklas da kaunarta sun hana masa sakat,kullum cikin kallon pics dinta yake,idan kaga Omar yasa headphone yana jin kida to za kaga yana latsa waya Wanda ba komai yake ba face kallon pics din Iklas yana tuna shirmenta da abin dariarta da sexy body shape dinta,yana jin shauki da nishadi.shi kadai zaka ga yana murmushi kamar Wanda yazo daga zazzau zaria. Lol.


        Iklas Gomnati kuwa yanzu akan ta dauki jotter tana rubuta plan gwara tasa kida me dadi tana tunanin gata ga ya Omar suna ta zuba love,watarana in tanajin kidan har hangosu takeyi a wata arniyar mota sun fito ga kida na tashi ana ta kallonsu,ko ta gansu a shegen restaurant sun gama cin abinci yana ta kissing dinta a gaban mutane,saboda tsabar sonta da yakeyi baya iya boyewa a gaban uban kowa.ko ta hangota taci kwalliya ta gama hadewa Omar na ta kallonta da mugun so da sha'awa amma tana masa yanga.

     Watarana kuma in tana jin kidan sai ta gansu a gidansu na aure, suna girki,ko tana shiryashi ta masa wanka etc.


      Kai watarana kuma da cikin Omar take hangota yana lallabata,shi yasa take kasa tsinana komai sai tunanin Omar,yanzu gani take ma ganin Omar kawai ma yafiye mata Aikin Gomnatinta kai schl dinma gaba daya gani takeyi an cuceta an hanata ganin Omar akan lokaci,gwara ma ta dunga rakashi Office yana kusa da ita.


      Ana gobe za a fara shagalin bikinsu Aisha,Gomnati tana dawowa daga schl ko abinci kin ci tayi kamar bikin kanin ubanta ta dauki hanyar fita ita da driver karo sukayi da Omar ya dawo dauke da ledar oasis a hannunsa,

    Labewa tayi a bayan labile,jawota yayi gabansa baki da gaskia tunda naga haka kikewa su Mama in kinyi laifi,na ganki da hijab ina zakije,tsadajjen agogon hannunsa ya kalla yanzu kika dawo daga schl fa,

   Har zaki kara fita,kuma time din Islamiyyar taki baiyi ba ai,da Sauri tace na dauki Hutu sai an gama biki zan koma.


      Kallonta Omar yayi lalai zakici duka,a gida ma sun zaneki inaga kinje musu biki,kiyi zamanki yafiye miki, naga ma ko abinci baki ci ba, na koshi ni lallen biki zanje ayi min da gyaran gashi, hmm duk wannan zumudin da wa zakije?da saleem mana aikin da Mama ta bashi har yayi kudi ya siyi mota fa.

     Lallai to ki fada masa kar ya sake yaje bikin kannena bama nemansa.look at u wai kannenka bayan tsine ma sukeyi,rannan ma akanka suka murdemin yatsu,

     To amma zakije bikinsu?ae ai hannunka baya rubewa ka yanke ka yar,ya zanyi na hadu da jininsu ai danginane nima.ban gane ba cewar Omar, saurayi nayi dan uwan ummansu fa.

     Kaga sun zama dangina,jikin Omar yayi sanyi gani yayi kamar da gaskene zancen Iklas,in kuwa hakane to lallai watan mutuwarsa ya kama.


       Ita kam Iklas a kan Omar tayi magana tunda su Sadiya wai sun zama dangin mijinta, kuma so takeyi kishin Omar yayi tsanani har yace mata shi yake sonta don har yau tana tuna maganar Inusa me wanki yace Omar sonta yake.

    Damuwa dankare a zuciyar Omar a fili kuwa snacks da yazo dasu ya dauki daya ya budewa Iklas a tsaye bakin kofa ya dinga bata a baki tana ci aranta tana wlh maganar Inusa me wanki gaskia ce,in ba me Sonka ba wa zai kula da kaci ko baka ci ba,a gaskia zanji dadina a gidan Omar.

   Sai lumshe ido takeyi tana lamushe snack,

    Shi kuwa Omar yanda take lumshe idon ne ke birgeshi sai kalle mata fuska yakeyi da pink lips dinta,

     

     A haka ya dinga bata har ta koshi ya bata lemo da ruwa a hannunta tare da zaro kudi ya mika mata kiyi me kyau kuma idan naga batayi kyau ba sai sun goge miki ita.

     Daria Gomnati tayi ta wuce tana masa bye bye,wajen Mama Omar ya koma shi asan yanda za ayi dashi a aura masa Iklas,Mama tace sai ta yarda kaje wajen Iklas.haushi yaji ya ficewarsa zasu karasa rabawa frnds IV na biki shi da Sultan,


     Baffa ma yana gari ya gama kawai ranar Sunday yake jira tazo a daura aure,tuni an masa waya kan ya koma Russia ana nemansa a office aiki yayi yawa.


      Baban Sahar har gida ya samu baffa kan Omar ya maida Sahar dakinta tayi nadama zata koma,Baffa yasan karya ne ba wani hali da zata canja Indai Sahar ce,amma idan an gama biki zai shawarci Omar yaji,idan yanaa so ta koma sai a kai masa Iklas itama gidan su zauna gaba daya.


      Iklas bata dawo gida ba sai wurin 11 na dare suka dawo da driver, tasha gyaran gashi da lalle.

     Ummi tace ke kuwa yar nan kamar kin tafi lallen Shiga Aljanna wannan dadewa,Ummi bafa ni kadai bace wajen,kingani tayi kyau?masha Allah ta Umaru tayi kyau,nasan sai ya bada tukuci daria Iklas ta kyalkyale da ita na jin dadi ta shige wanka.


      Saida ta fito daga wanka ta duba wayarta missed calls din Omar ta gani da yawa,ga text birjik yayo mata kan ta dawo gida dare yayi.

    Reply tayi so sorry na sata a silent banji kiranka ba,na dawo tuni.Omar yana bacci sai da safe ya gani,Iklas har makarantar boko ta dauki Hutu sai an gama biki.


     Gida yayi gida,bangaren su Umma a cika sosai da yan uwa da abokan arziki masu kwana,kawayen amare makil sashensu daban,bangaren su Mama ta gayyato yan uwanta suma na nesa sunzo da yawa zasu kwana,har a gama biki,Iklas hayaniya ta dameta ta gaji dan haka gani su Ummi na hada hadar biki basu San me takeyi ba kusan gaba daya a part din Omar takeyin komai ko yana nan ko baya nan wucewa takeyi ta dinga uzurinta ba ruwanta,akwatin kayan bikinta ta janyesu ta mayar dakinsa,

     Iklas tsabar kadifiri har kawayenta hadaddu ta gayyato guda biyu wata yar gayu yar gidan wani kusar Gomnati suna ce mata ANGEL,sai wata yar wanka kyakyawa itama yar wani babban soja ce wato PRINCESS, unguwarsu taje ta fadawa kawarta arniya DAMI DAMZEL itama za aje da ita dan tana aiki a company tana kashe wanka duk cikinsu babu wacce za ace bata hadu ba.kuma iya dinner Iklas ta gayayyacesu suzo.

      Ummi ma ta gayyaci mata tsofaffi irinta na tsohuwar unguwarsu mutum uku,Sa'ade,Hasiya da Maman saleem Haj kyauta.


      Komai dai share.

 Saleem duniya ta samu har sun canja unguwa ya siya musu gida shida mamansa sun koma cikin Abuja city,har yayi motar kansa, 

         Mamansa ta uzura masa ta gaji da zaman kadaici ya nemo matar aure,shi kuma Iklas ya fada mata yana so,sai tace ya bari idan taje musu biki zata sanarwa Ummi,sai murna yakeyi.

      Umma Rahina yaranta ta Tara,kan kar su nunawa yan bangaren su Omar komai,idan ana bikinma su nuna komai daya, ana zaman lfy,kuma suja Iklas a jiki ayi komai dasu,yanda idan sunyi wata kulla kullar jama'a ba Wanda zai yarda cewar su suka aikata,dan tace ana gama biki zata fara harba makami me linzami na bama baman tsiyarta bangaren Mama,zasu sha wutar bala'oinsu.


        An tashi yaune za ayi event har biyu daya 3pm-6pm za a dawo a koma na 9pm-3am ko wanne wajensa daban za ayi, Iklas ce ta wuce Omar a palonsa fiiii zata shige cikin bedroom,jawota yayi baya ina zakije haka,kinfa takurawa room dina, na gaji da wankemin bra da panties naki ke ba matata ba ko kunya bakyaji na gani,

   

       To mene abin kunya a pant da bra amma a t.v settelite ai nagani rannan kana kallon american film da bra da pant jikinta kana kalla me yasa nan banga kaji kunya ba,sai idonka ma da naga ka kara warewa,

    Ni ai na saba gani,ke nake nufi,baki ta murguda to Nima bana jin kunya agaban kowa zan iya shanyawa,da masifa Omar yace hey mind ur tongue,kar ki jawo na huce fushina kanki. 

    Ita Iklas duk haushin Omar takeji  yaki cewa yana sonta, ta gaji da jiran sa.


    Me zakiyi cikin Room din to, wankan party,no ki bari sai na 9pm zamuje.batayi musu ba tace to Allah kaimu.

      Da hannu ya yafitota come come muga lallen da akiyi miki jiya,na mantama ban gani ba,a nutse ta wara masa hannayenta,kalla yayi sosai har na kafa dama gata fara kar, lallen ya gama tafiya da Omar, harda shafa hannun,gashin ma ba a magana, har mamaki yakeji yaushe Iklas tasan wurin gyara a Abuja haka.

    Omar bai San aikin Mero Lallausa bane me gyaran jiki.

   Zame hannuta Iklas tayi,tabe baki Omar yayi mutum ya biya kudi an hanashi ganin na kudinsa.

     Je ki dafa min indomie da kwai,ki hada min coffee. Tafiya tayi cika umarnin Omar,Hips dinta yabi da mayen kallo.


        8pm sai shirin dinner party akeyi, su Abdallah shi ke yawo dasu Suleim 8:30 sunyi shirunsu kajifa yara, bangaren Amare mafa nan ake cakarewa.

    Iklas zata shiga wanka Omar ya sa key a toilet din wai baza suje da wuri ba,haka ta koma na Mama duk shirye shirye akeyi,ita kuma baza ta shiga toilet din da wasu yan biki suke shiga ba,sauran rooms du Mama tasa musu key.

    Dolenta ta jira Omar sai abinda yace.9pm sannan Omar yace tayi wanka,10pm sun gama shiri tuni frnds din Iklas sunje can,sai waya suke mata,Sultan da amaryarsa Yasmin, Raj ma yaje.


      Kwaalliyar su Iklas fa 



  INA TARE DAKU MUTANENA





Asmabaffa

[9:10AM, 4/10/2018] ‪+234 810 468 7075‬: ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR

         GOMNATI

          ⓂⓂⓂ

  

           125-130



By

Asmabaffa



     

  

        Iklas ce tayi shiri idan ba mugun saninta kayi ba baza ka gane ta ba,wani tsadajjen material tasa na nunawa a gari,Red ne da zanen Arsh color jiki, yayi mugun kyau,duk yafi na amare kyau da tsada,dan Omar ba karamin kudi ya zuba ya siya ba,Riga da skert ne,tasha kyau kamar Ku saceta dan tsayawa ma fadar yanda shape dinta ya fito bata baki ne,  Omar yasan size dinta mayene.takalmi me tsini arsh da wata shegiyar pose yar gaske same color da shoe,Omar ya fito daga wanka sai da kyar ya tabbatar wannan Iklas ce,

        Iklas fa har gwagwaro itama ta kai aka Nada mata na kece raini,gashin nan ta gyara  jelar na reto a tsakiyar baya murtukekiya,ta fito da ita ta tsakiyar goggoro,dama ga jiki yasha gyara ko ina kyalli takeyi,turaruka kuwa sai da Omar ya koreta,zama tayi tana jiransa yana shiryawq tana ta guntse dariarta wai ganin sandar girman Omar a short wando,yana kalonta ta gefen ido,kin San Allah zanyi maganinki ki koma Palo ki jirani kan me zaki sani gaba ki dinga kallona kina daria,baki ta rufe da tafin hannu nayi shuru to.


    Harara ya watsa mata yana ta shirinsa tana satar kallon jiki da kira me kyau irin na Omar, Allah ya bashi diri da kyau ga skin dinsa kalarta ta kwashewa Iklas Imani,

     Wani rantsatsen yadi me taushi Omar ya sa,shara shara sosai arsh color kalar material din Iklas komai Arsh yasa,dinkin zamani dai dai jikinsa wandonma,Omar uban yan wanka suma taci wani gyara me kyau,tayi luf,turaruka ya fesa sosai,ya fito kwas rike da waya,Iklas ma wayarta fankaceceiya a hannunta,mikewa tayi daram ta isa wajensa yaya Omar kalli fa kayanka shara shara har singlet ana gani,wandonka ma dan an masa landing daga samane amma ai sai adinga hango uhmmm.....uhmm....da ka canja shadda ma ,ke jikinki ko nawa ina ruwanki cewar Omar.kowa ance miki irinki ne me kurawa mazan wasu ido,let's go idan zakije if not na tafi,

      Ita Iklas kar a kallar mata kyallin fatar miji,gashi tasan dole Sahar tana can.


        Hannunta ya rike suka fito duk gidan Shuru sai yan aiki da suke aikin gyara gida kafin a dawo.

    Wata sabuwar mota fil arsh color itama  Omar ya bawa driver key a baya suka kame kamar sune amarya da angon,kajifa yan fassion 

      Har wajen driver ya kaisu,tun daga waje zaka San wajen ya girmi me karamin karfi.

     Sahar da frnds dinta an kwafe a kujera tana baza idon ganin Omar,dama su gulma ce ta kawosu da niyar wulakanta Iklas gaban mutane,

     Amare da Angwaye ana kujera an fara shagali suna kallon masu rawa da liki,su Kansu Omar suke son gani saboda frnds dinsu su kalli haduwa,najja da sauran kannensu sai iyayi akeyi a fili ana kada hips,kaji kannen Amarya fa.Iklas ce ta masa rada pls ka fita munzo fa idan ka fita ka bude min kofa na fito a Gomnati ta.

   Driver ne ya budewa Omar kofa.

     Murmushi Omar yayi tare da fita cike da kasaita,omar kuwa zagayawa yayi ya budewa Gomnati itama ta fito,tana fitowa zuruf ta sakalo hannunta Dana  Omar ta kara shigewa jikinsa kamar zata shige jikinsa gaba daya ba space da ko tsinke zai iya shiga.wani kar kar kawai Omar ke ji a cikin jininsa kawai Iklas yake bukata, kara manneta yayi suka tafi domin shiga hole din,

     

     Duk Wanda yayi tozali dasu sai ya saki baki da ido dan kallon kyau irin nasu,ga iya wanka,ga shiga me tsada da ka gani ba sai ance ba,gasu sun birge masoya da gani wannan real love ne,dama Iklas tace bikine daga mota sai hole shi yasa taki daukan gyale,

    

       Sultan da Raj suka fara gani cikin wurin,daria suka dinga yi sun San Iklas sarai, wuyan Sahar da frnds dinta kamar zai tsinke dan kallon su Omar,suma su Najja sai nunawa frnds Omar sukeyi ga yayansu babba,wajen da aka tanadar masa najja ta nuna masa suka zauna,Mama da Ummi suna can baya sunga su Omar har murmushi sukayi,Iklas ba dama cewar Ummi.


         Duk Iklas ta kasa sakewa yanda taga yan mata na kallon Omar,kamar tayi kuka,shi kam Omar ta kansa yakeyi ganin Saleem a wajen su Angel kawayen Iklas,

       Yayan amare aka kira kan ana so ya chashe a fili dama Iklas ta matsu su shiga fili rawar Igbo zatayi yau tace, ai kuwa kafin Omar ya juyo sai gani yayi Iklas har ta danyi doro kamar zatayi ruku'u tana ta kada hips,tafi da ihu fili ya dauka kafin kace me an rufeta da liki maza da mata,su Kansu su Sadiya ta birgesu rawar,

       Maman waleeda ma sai liki takeyi sai da ta karar da yan kudin cefanen da Baban waleeda ya bayar na 1mnths,kinga ta kanki da me zasuyi girki,Jamila sule,Haj jamila duk sai balle bakin jaka sukeyi,Zulaihat da su Juwairiya duk an Hallara a fili,sai Diyar katibi me gyara fili ce tazo ta koresu kasa tukunna.

 

     Omar sannan ya fara likiwa Iklas yan dubu dubu,itama mikewa tayi ta gama rawar ta fara barin kudi musamman Omar ya bata dama,masu DJ sun washe da Naira, Omar ne ya janye Iklas suka koma mazauninsu sai radar masifa yake mata kan tayi rawa,

      Angwaye da Amare na fitowa suma sai da su Iklas suka yi ruwan kudi.su Aisha ransu ya fara baci fa anzo gidansu ana satar musu dukiyar Uba ana bawa wata banza,

     Sahar takaici ya kamata ganin inda Iklas ke barin kudi Omar ne kuma yake bata,a gabansu ma ta karbi wasu,ita kuwa sahar taga ko time din da take matarsa baya bata haka.


        Da kyar ya bar Iklas taje wajensu frnds dinta da saleem suka gaisa sai kiranta yake a waya ta dawo wajensu,komawa tayi ta barsu suma suna kallon ,tana zama Sahar ta karaso wajen,hararar Iklas Sahar tayi,Iklas ma ta rama harda karin Jan tsaki,

    

      Sahar dauke idonta tayi ta kalli Omar how far kwana 2,ko da yake nasan wasu sun manne maka yayan matsiyata,sun hanaku sakewa a gid....saukar ruwan lemo me sanyi Sahar taji a fuska da kirjinta,wacce ba kowa bace tayi sai Iklas,Omar kuwa yaga sanda Iklas zata aikata kyaleta yayi ta rama.

       Kawayen Sahar ne suka zo da niyar dukan Iklas Sahar ce ta hanasu Ku bari a gama party tukun,komawa wajensu sukayi suna jiran a gama party su karya Iklas,

      Iklas kuwa hankalinta kwance tasan gata ga Omar.


      Frnds din Iklas ma sun zo sun gaisa da Omar,dinner party yayi dadi gaskia,haka har aka fara tafiya gida,su Mama ma sun tafi,Saleem da frnds din Omar Dana Iklas duk sun tafi,Iklas ta rakasu ta dawo wajen Omar wani Frnd dinsa ya tareshi yana ta jansa da surutu kuma wannan duk plan din Sahar ne,

      

     Radawa Iklas yayi je ki jirani a  motar mu,tana fitowa ta ci karo da su Sahar sunyi  da'ira,ta tsure ganin ba Omar gashi mutane sun tafi,ta tsorata sosai, amma bata nuna ba,sai ma murguda musu baki da takeyi tana ja baya,

    Sahar kukan kura tayi ta damko hannun Iklas daya, tana danna mata ashar iri iri,


      Kawaye na zuga Sahar,da dabara Iklas ta dago kafarta ta Ciro takalmi daya me tsini ai kuwa ta kwalawa Sahar a kanta wajen ya fashe sai jini,arcewa Iklas tayi tare da banke wata kawar Sahar dake kan hanya,da gudu ta fada motarsu tacewa driver sa lock.haka driver jiki na mazari ya danna lock,

      Sahar sabo da bacin rai ji tayi kamar ta kashe kanta ta huta,jikin Motar tazo da niyar shako Iklas amma ina a kulle gam,Iklas lekowa tayi tana ta yiwa Sahar gwalo iri iri, ta murguda baki,tayi fari da ido,ta kebe baki,ta tale mata baki,ga gwalo.iya kuluwa Sahar ta kai karshe,juyawa tayi suka shiga motarsu da frnds dinta suka wuce da niyar irin hukuncin da zasu yankewa Iklas idan Sahar ta koma gidan Omar.


      Gaba daya Sahar tace sai ma ta kashe Iklas du.

     Queen mermu ma kungiyarsu duk sun tafi dama kallon bikin yan gayu suka zo, 2:30am Omar ne ya fito tare da bude mota ya shiga,shigarsa ke da Wuya ya ga Iklas sai gyangyadi takeyi,

     Mikar da ita baki isa kinmin bacci ba a mota wa yace kizo sai da na hanaki zuwa amma kika ce ke sai kinzo Ashe burinki kiyi rawa ki kadawa maza jiki,kinci sa'a daya muna wajen mutane da na nuna miki yanda ake ball da mutum.


      Cike da jin bacci ta kwanta a cinyarsa pls ka barni nayi bacci,kyaketa yayi tare da Dora hannunsa kan cikinta,dayan hannun kuma yana cire mata goggoro kanta,wai taji dadin bacci,

     Munafuka Iklas idonta ras baccin karya takeyi wai dan kawai taga yanda Ya Omar zai lallabata,sai dariya takeyi a boye,


       Kara juyi tayi tace wash na gaji kafafuna,takalmi ya zare mata ya Shiga dannan mata kafafun.

   Iklas aranta tace inye ni din ba,naji dadina tun ban shiga ciki ba kenan,kai Allah ya Omar so na yakeyi, duk a ranta take zancen ta


      Kukan shagwaba ta fara uhm..uhm...uhum..bakinsa ya kara saitin kunnenta yana matsa mata kafafu a hankali yace ya akayi wai?yunwa nakeji ni,tuni Omar ya bawa driver umarni ya kaisu wani tsantsararen eatery suyi take away.

     Anzo wajen Iklas ta hana Omar tashi Sam wai ni....ka aiki driver ya shiga ya siyo,haka driver ya je ya kawo gashashiyar kazar hausa,da h-bugger sai chips da kayan sha na sanyi.

      Sunzo gida tace Sam baza ta iya takawa ba,abin na Iklas da iskanci cewar Omar kayan ya kwasa yayi gaba abinsa,dole ta fito takalminta a hannu ta shiga part dinsu,kowa yayi baccin gajiya gidan shuru,

    Wajen Ummi taje ta ganta tana sallar dare,sallamewa Ummi tayi Iklas ki dawo ki kwanta nan nafa gaji da halinki,kinbi kin nacewa mutum ki ja ajinki namiji ya biyoki amma ke kamar ba mace ba.


      Turo baki Iklas tayi in kun San hakane me yasa aka bashi ni,kuka aura masa ni,in hakane Ku kyaleni yazo ya nemi auren da kansa mana sannan Ku bashi ni.


     Amma kun masa aure kun hana bawan Allah matarsa,Ku fada masa ma ni matarsa Ce kun kasa, kun hana mu fada,ni wlh in na gaji fada zanyi,kune kuke ganin abinda nakeyi a rashin class mu zamanin mu irinmu ake nema,

   Baki Ummi ta saki tana kallon Iklas,carbi ta Zara ta zabga mata a baya yar banza wacce bata da kunya ko daya wajen ubanki kikayi gado bazanga laifinki ba,haka shima yake akan matar sa bashi da kunya.tafi ki bani waje kije kiyi ta kwana dakinsa.

     Idan ya miki ciki ke kika jiyo,daria Iklas tayi wlh ni kuwa na haifo Dana kece zaki min wankan jego amma sai ya Omar ya yarda,kuma Allah ki gasa masa cibi ta gasu.

     

       Banda mugunta ki sa yaronmu kuka ki shaka masa sabulu wajen wanka,Ummi ji tayi Iklas ta bata kunya ma,ba shiri taci gaba da sallarta.

    Wanka Iklas tayi tana fitowa taga Omar ya kawo Mata take away,Ummi tana ta Sallarta taga Omar ya wuce wajen Iklas sai rada sukewa juna bata San me suke cewa ba.


     Iklas ta koyawa Omar rashin kunya cewar Ummi, yaro nutsatse ya susuce kan mace ni na gaji ana gama bikin nan a bawa yaro matarsa su karata can,zan sanarwa mahaifiyarsa.

            Abincin da suka siyo ya mika mata yace karba,ki tabbatar kinci da da yawa,zan kiraki anjima na tabbatar kinci,

    

    Ummi ya juya ya kalla Ummi sallah kike yi dan Allah ga amana nan kisa taci da yawa tayi bacci ta huta gobe daurin aure da safe baza ta samu damar yi ba,

     Sallamewa Ummi tayi ba shiri tace kaci gidanku Umaru,dan iyayenka kaima ka zama fitsararre ko,Ku kiyayeni,murmushi yayi ya kalli Ummi zanzo Ummi idan na samu time zamuyi wata magana.Allah kawoka fitar min a daki,ke kuma kin tsaya min a kai wuce ki bani waje.a bed dinsu ta zauna ta fara cin abinci ta ragewa Ummi nata.

      Omar fa shi ya hadu bazai cewa Iklas  yana sonta ba direct  kawai zata gani in action, idan tafiya tai tafiya,ya tabbatar ta gane sai kawai a zarce da I love u. Fadar wance sonki nake,ko ina sonki da farkon farawa to kauyancine kajifa Omar. Iklas lallai in hakane jira ya ganki.

 






    Asmabaffa tana jinjina ga masoya novel din nan a duk inda suke. Allah ya saka muku da Alkairi.


ⓂⓂⓂ

     MA'AIKACIYAR 

          GOMNATI

           ⓂⓂⓂ

 

            130-135




By

Asmabaffa





       Misalin 10am kowa ya gama shirin daurin aure maza da mata cikin kwalliya suke kowa yana ji da kansa,

      Iklas tasan Ya Omar farar shadda zai sa tunda sanda ta kai masa breakfast yana shiri,yasha kyau tsayawa fadar kyan Omar bata baki ne

      Iklas ma wanka tayi ta shirya cikin farar shaddarta kwal,sai kyalli takeyi taci dauri da dankwalin shaddar,Ummi ce tace haba Iklas kefa matar aure ce karki manta ki dauki mayafi,fafur Iklas taki yarda ita ba fita zatayi ba baza ta sa mayafi ba,

     Part din su amare ta wuce,basu mata komai ba sabo da gargadin Umma,kallon yan mata taje yi,itama ana binta da kallo tasha shadda me tsada,wasu cewa sukeyi ko yar Gonna ce,

     Sadiya amarya Iklas tasa ta fara linke mata kayan da ta sa,kafin daurin aure,ai kuwa ba musu Iklas ta shirya mata komai,Aisha ma sai da ta aiketa wajen Umma Rahina ta kai mata wasu plates,

     Tana tsakiyar yan mata ana hira da ita tana tofa albarkacin bakinta cikin manyan mata,


       Sadiya ce tayi magana pls Iklas a fesa roomfreshner a waccen part din an daura aure yanzu angwaye zasu zo mana.

    Nan ma da sauri Iklas taje tayi yanda tace,ta dawo kamar yanda yan mata ke kara goga powder da gyara kwalliya haka Iklas tayi amfani da kayan kwalliyar Sadiya tayi kwalliya,

     Duk mutanen wajen kallon Iklas sukeyi duk Inda ta juya,tayi kyau ga iyayin tsiya gareta kamar babba,shi yasa suke kara mamakinta.musamman in tana tsara zance da kawo shawarar dabarun zaman aure,

 

      Aisha ce tace Iklas jeki ki bude palon gasunan sun zo,sosai suke mamakin Iklas dama haka take da saukin kai da ladabi,Iklas kuwa komawa tayi ta bude,ta fito zata dawo ta hango Omar da Sultan sai Raj da sauran frnds din Omar da yawa,

       Ido suka hada,da ido ya mata alama ta koma ciki,wajen su sadiya ta koma,bayan Omar ya raka frnds nasa sunyiwa mutan gida Allah sanya alkhairi rakasu yayi suka tafi,

      Iklas ya kara gani this time around da gyale fari jikinta maza damkam angwaye biyu ko wanne da abokansa sun zo,komawa tayi da nufin shiga palon da angwaye suke,ji tayi an fisgota sai da ta fada jikinsa,kamshin turarensa ne ya sa ta gane Omar ne,har part din Mama ya jata,

Warning ya mata kar ya kara ganinta a waje,hakura tayi ta koma cikin dakin Ummi tayi kwanciyarta ta dinga bacci abinta.

     Sai da su Sadiya suka kwashe kusan 1wk suna biki,ana gama shagali aka kai ko wacce hadadden gidanta,aka barsu daga su sai halinsu.


      Koda Babar saleem tayiwa Ummi maganar saleem yana son Iklas hakuri Ummi ta basu ta sheda musu anyiwa Iklas miji,har auren Iklas ta fada mata, saleem ya shiga damuwa sosai jin labarin Ashe an Dade ma da yiwa Iklas aure, amma daga karshe ya fawwalawa Allah.

      Baffa ne ya kira Omar  ya bashi Umarnin lallai ya maida Sahar dakinta,sabo da baban Sahar yana ta bashi hakuri saboda Sahar ta dami Daddynta da naci,su kuma suna son yarsu,farin cikinta suke so,shi yasa Sahar ta lalace da yawa, Omar kamar zai mutu har zazzabi yayi,yace wlh bazai je  gidansu ba sai dai a fada mata ta koma,Sahar murna tayi tace ko dan naci uban yarinyar nan bari na koma,tattara kayanta tayi ta koma gidan Omar,gani tayi komai na gidan an canja new kamar ma ba gidan ba,tasha mamaki a ranta tace Ashe dai ya damu dani.

      Iklas kuka takeyi kullum an maida Sahar ta zama kishiyarta,shike nan zasu dinga kwana da Omar.

 

     Ummi da Mama ke lallashinta amma kullum bata da sukuni danma tana zuwa schl da damuwarta sai tafi haka,

     Tunda Sahar ta koma Omar bai koma gidanba ko sau daya,har ta kwashe 2wks amma mijin nata shuru,Mama ta sa Omar a gaba kullum fada takeyi ya koma gidansa kar ya shiga hakkin Sahar amma yaki,ko ta koreshi wani gidan yake komawa cikin jerin gidajensa.

     Satin Sahar 3 da tarewa Baffa ya umarci mama kan ta kira Iklas Ummi da Omar,kafin ta kirasu sai ga yan uwan Baffa Da aka daura auren Omar da Iklas sukayi sheda da kuma Wanda sukayi wakilcin iyaye du sun hallara a falon Baffa


     Omar baya gida yana Office sai a waya aka kirashi,minti kadan Omar ya Iso,Iklas sanye da  hijab anyi lukui a gaban Baffa,Haj Rahina ma an kirata,Sahar tazo don tunaninta tunda taji Baffa ya nemeta to kudi zai bata,Sultan da Raj an cika harda sauran yaran gidan.

       Duk kowa yana wajen,Omar sai mamaki yakeyi ko lfy,

   

      Taro aka bude da addua,sannan Baffa ya fara magana,nasan wasunku basu San me yasa na taraku ba wasu kuma sun sani musamman yan uwana da Mama,Ummi,Iklas, sai Sultan da Raji,ga limamin masallacin da akayi a idonsa shima shaida ne cewar a masallacinsa muka daurawa Iklas aure ita da Dana Wanda kowa ya sani wato Omar,

 

     Omar bamu sanar maka ba sakamakon kana hali na cuta,mukace a bari sai ka warke,nan wajen Baffa ya bada labarin kimai,shedu ma suka tabbatar da hakan,har pics da video Sultan da Raj suka nunawa kowa.

     Omar ne ya fara gani ya rasa ma me yakeji a ransa ga dadin Iklas ta zama mallakinsa sannan ga haushin anki fada masa da wuri an ja masa rai,an barshi da damuwa.


      Yana so ya danyi koda romancing Iklas ne amma ya dinga tunanin babu kyau,an barshi a duhu maza sun tsaya masa da matarsa sunyi hira,tayi rawa a gaban maza, sai yanzu yaji ya kara jin haushin saleem da yayi hira da matarsa,Ibzzy ma haka tab wannan duk laifin Iklas ne,sai yanzu ya tuno yanda Iklas ba ruwanta take taba jikinsa anyhow Ashe tasan komai ita ba rashin kunya ce tayi mata yawa ba,

     Tunani ya shiga yanda zai sawa Iklas sonsa a ranta sannan asha love,tunowa yayi yanda Iklas ta dinga raina masa hankali,a ransa yace dole na rama.Iklas kuwa dake gaban Baffa kanta ta cusa tsakanin cinyoyinta ta dunkule wai kunya,


     Sultan sai daria sukewa Omar kasa kasa.yaran Mama harda Suhaila sai jin dadi sukeyi,Haj Rahina ce ta mike tsaye akan wannan aka bata mana lokaci,dan sunyi aure sai me,fasikan banza fuuuu ta ja su najja suka bar dakin cike da takaici,nan take tayiwa Aisha da Sadia waya ta shaida musu komai.Haj binta ma ta bugo waya suna ta gulmarsu ta kulla tsiyarsu idan Iklas ta tare.

     Sahar kuwa wani wawan tsaki taja hade da shewa tace ta shigo gidan indai miji ne Mara amfani holoko to gashi nan,kizo kiji dadi mugani.ficewa tayi ta shiga motarta ta bata wuta.


     Baffa kuwa kai ya girgiza yace Allah shiryeku sauran mutane sukace ameen,nan taro ya tashi saura Mama,Ummi ,Baffa sai Iklas da Omar ba bata lokaci Baffa yayi musu Nasiha sosai,haka Mama da Ummi ma sunyi tasu Nasihar,an yanke nan da 3days za a kaiwa Omar matarsa,godiya Omar yayi wa Ummi da iyayensa da suka bashi Iklas amma fuskarsa a daure.an kasa gane yanayinsa.



       Iklas dadi taji kamar me zasu tafi gidansu ita da Omar dinta,shike nan itama tayi gida,sai kaji ana cewa mun tafi gidan Iklas, ga Omar Allah dole ne ta dinga baccinta a jikinsa me kamshi laushi da santsi,inyi girkina,inyiwa Ya Omar abinci,muyi wasanmu etc

       A ranta take zancenta ta

     A hankali ta dago da kanta Omar ma a lokacin ya dago caraf suka hada ido,gani tayi fuskar Omar ba alamar Rahma,gabanta ne ya yanke ya fadi wato ma dole akayi masa baya sonta,Inusa me wanki ta tuno zancensa sai kuma taga kamar Omar baiyi farin ciki ba it means ma karya ne baya sonta,

   Lallai dole na fara addua da Sallar dare zata fara Allah sawa mijinta Omar sonta ya basu zaman lfy,yasa ta zame masa Alkhairi shima ya zamar mata alkhairi.


      Sallamarsu Baffa yayi tare da sanar musu gobe jirgin karfe 6 na safe zai bi ya koma kasar Russia wajen aikinsa,addua sukayi masa sosai kowa ya tafi aka bar Baffah da Mama.


     Iklas na bayan Ummi,Omar na binsu a baya hijab din Iklas ya dan ja juyowa tayi amma har yau gani tayi fuskarsa a daure,jawota yayi kiiii kamar zai doketa,ihu Iklas tayi wayyyo.....ta tsorata ta dauka dukanta zaiyi,da sauri Ummi ta juyo ai da sauri Omar ya saki hijab din Iklas,

      Ummi ta riga ta ganshi,kara juyawa Ummi tayi taci gaba da tafiya,Omar ya kara fusgo hannun Iklas,da gudu Iklas ta kwace ta sha gaban Ummi,ke wai wacce shashasha ce,cewar Ummi,waigowa Iklas tayi tana kallon Omar tace wlh Ummi wani abu zai min,Allah ki masa magana zaneni zaiyi.


    Ke rufe min baki marar wayo wuce muje ciki,an kusa kaiki gidansa ai kuje Ku cinye juna ma,karki sake ko a waya ki kirani komai raunin da yaji miki,Iklas bata gane maganar Ummi ba,ta zata zancen duka da tace shi Ummi take nufi za a ji mata ciwo.


       Sun shiga room Iklas zata rufe kofa Omar ya mata irin abu da kafa ya buga kafar a kasa kamar zai kwasa da gudu ya damkota,ai kuwa ta saki kofar ta fada dakin da gudu.


     Daria Omar yayi ya wuce part dinsa,misalin karfe 1 na dare,Omar ya kasa bacci,sai yanzu ma yake tsananin son jin dumin jikin Iklas, fitowa yayi yaci Sa'a kofar su Iklas ya ganta a bude yanda Iklas ta barta dazu.


    Lallabawa yayi ya leka dakin,Iklas da Ummi kwance gado daya suna ta baccinsu,karfin hali Omar yayi ya matsa kusa da Iklas,a hankali ya kama tashinta ta hanyar Sosa mata kunne,

    Firgigit ta bude idonta,alama yayi mata da tayi shuru,saboda Kar ta tonawa Kansu asiri tayi luf tana kallon Omar,tasan idan Ummi ta gansu fadan har Ita.


     a hankali yayi rada ki taso muje dakina,kafada ta noke tana masa nuni da Ummi, kara rada mata yayi ni zakiji tsoro,nine mijinki,itama rada masa tayi ummi zata kamamu.

   

     Tsaki yaja a hankali ki taso kawai malama na fada miki,ni lokacin da kike zuwa kina taba min jiki hanaki nayi?lokacin ma fa ban San ke matata bace amma na kyaleki,murmushi Iklas tayi,harara Omar ya watsa mata,ki taso ki biyani jikina da kika dinga taba min,mijinki ne ni Allah ya konaki kinki bin umarnina kinji dai nasihar Ummi ko,

     Tsorata Iklas tayi kar Allah ya konata fa,Omar ya kara da kizo ko na kwanta anan Ummi ta kamamu.


   Da sauri Iklas tace a'a dan Allah zanzo muje ni,kar ka jawo min masifar Ummi dan laifina zata gani,muje kawai,mikewa tayi a hankali kamar barayi sadaf sadaf suka fara tafiya,Ummi kuwa dake bacci motsi taji kusa da ita ta farka, mikewar da Iklas tayi shine ya tashi Ummi da ga bacci,

 

     Innalillahi wa inna ilaihi raji'un Iklas yanzu iya shegen da kika dauka kenan,nasan Umaru bazai aikata ba ke kika  kirashj a waya,dawo ki kwanta ko wlh na saba miki,mu zaku mayar yan Iska, tuni Omar ya bawa Ummi hakuri yace Ummi cewa tayi nazo na dauketa tafi son dakina.


    Salati Ummi ta kara saki jeka Umaru Allah maka Albarka ai nasan halinta,ficewa Omar yayi da sauri cike da kunya.wlh Ummi bani nace yazo ba cewa yayi.....rufe min baki Ummi ta kai mata duka dan ubanki kwanta ki rufe min baki,Iklas kija mutunci ki ina fada miki namiji ba dan goyo bane.


    Rushewa da kuka Iklas tayi wiwi take kuka haushi takeji Omar ya kala mata sharri ya zame kansa gashi ya barta Ummi tana jin haushinta,shi kuwa ya wanke kansa tas wurin Ummi.


      Gajia tayi da kukan ta shige toilet tayi Alwala ta fara nafila da adduarta Allah sawa Omar sonta,ya sota ita kadai a duniya,Allah bata ikon yi masa biyayya yasa su zamewa junansu Alkhairi.

    Tana idarwa harda karantawa Omar suratul Yaseen Allah sa masa sonta,ita gani takeyi Omar baya sonta shi yasa yanzu yasa Ummi tayi mata fada.da yana sonta ai bazai zame Kansa ya kyaleta ba.

   A ranta tace Allah kaimu gobe lfy Allah sai na rama zai San nice Gomnati.

       Washe gari Iklas da fushi ta tashi cike da shirin ramuwa kan Omar shima sai tasa an masa fada yaji kunya.





   Pls kuyi hakuri da wannan bazan iya forcing kaina nayi muku 2 pages ba,typing akwai wahala ga shi akwai schl ba time,Ku danci wannan tuwon Ku kora da ruwa kuyi bacci.

      Tnx alot readers ..





Asmabaffa


ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR 

         GOMNATI

          ⓂⓂⓂ

  

           135-140




By

Asmabaffa





    Jira kawai Iklas takeyi taga ta inda Omar zai bullo amma shuru,Mama ce ta fito cikin shiri,tashi maza dauko mayafi zamu fita,ba shiri Iklas ta fito dauke da mayafi,driver ne ya kai su Iklas wurin wani saloon,Mama ta biya kudin komai yanda za a tsantsare Iklas,

       Komai da ya dace iyaye suyiwa yarsu Baffa da Mama sunyiwa Iklas kayanta babu banbanci da na su sadiya sai dai color daban,na Iklas Dark brown ne komai,haka kayan kitchen Mama tayiwa Iklas Wanda ya take nasu sadiya,kayan gyara Dana kamshi babu abinda ba a siya mata ba wadatacce,kayan yaji da sauransu du an shirya mata part dinta,


     Allah ya taimaki frnds din Iklas da wasu dangin Mama har aka gama shirya kayan Sahar bata nan,kayan sawar Iklas du an kai gidanta an shirya mata lefe kuwa Baffa ya bada kudi Mama ta hada mata akwati 8 ba abinda babu masu tsadar gaske da kyau domin English wears kaf da wasu tarkace a Russia Mama ta hado su murna Iklas keyi za a sha wanka,Omar kuwa gagarumar walima ya hadawa frnds dinsa maza a wani katafaren waje,ranar kai Iklas ranar za ayi walima.

     

      Omar kafin ayi jeren Iklas har ma'aikata yasa suka kara yin adon golden jikin ginin Wanda yafi na da iri iri,ko ina sai ka rantse adon zinari akaiwa ginin wajen Iklas, komai dark brown da Golden ne,har labile idon gari.tsayawa fada muku yanda part din Iklas ya hadu iya haduwa karshe ya zarta tunanin me tunani,sai na gama novel din nan kaf ban gama ba,

     Iklas koda suka dawo ma Omar na busy bata Ganshi ba,Iklas manya tsabar gyara duk inda ta zauna kamshinta sai yayi kusan 1wk bai bar wajen ba,ko gidan mutane taje to sai tabar musu tsarabar kamshinta.


       Washe gari dangin su Mama mutum biyar sunzo raka amarya gobe,haka dangin Baffa,ga frnds din Iklas zuga guda,Rana ta Uku ranar kai amarya,da wuri Iklas taje wurin Saloon da lalle,masu mata lallen mutum uku ne ,sai mai gyara gashi,Karfe 4pm Iklas driver ya dawo da ita,kunga Iklas kuwa yanda ta koma?tab zankadaziyya kenan,dama gata fara kwal,ga lalle yayi kyau over,

     Tana shiga room dinsu mero lallausa tana jiranta,nan itama ta hau nata gyaran,gashi sai bata abubuwa akeyi ta shanye wannan ta cinye wancen,Lallausa da Mama sun koya Iklas harkoki sosai na mata da ake amfani dasu,Mama da Ummi sun hada mata wasu da yawa an kai gidan,store kuwa both na Iklas Dana Sahar an dankareshi da kayan abinci haka kitchen ma.


       Karfe biyar su Omar suna can suna Walima,amarya an shiryata tsab jiran angwaye kawai akeyi,Ummi da Maman saleem sun sa Iklas gaba da nasihar bin miji,idon Iklas Kamas ko kuka babu tunda wajen Omar ne bata da Matsala.

    Ummi tace to kinji dai abinda muka fada miki kishiya gareki wlh kija mutuncinki,ban son tsokana nasan halinki,kuma ba a dambe da kishiya jahilci ne,ki kiyaye,zaman aure ne ba jin dadi kikaje ba ibada ce,dole sai da hakuri da juriya,ki farantawa mijinki,komai ba musu,sannan kinji na rantse Iklas kikaje kika tashi hankalin Omar da fadace fadace da kishiya Allah sai na saba miki, 

    Ki rike mijinki nasan dole kin San dai dai da rashin dai dai abinda ya shige miki duhu ga Mama ga ni ki bugo mana waya,haka dai suka dinga yiwa Iklas fada,kawayenta ma sai nasihar iya shege suke mata,

        Amarya banda rowa a wangalewa oga cinya etc.

    5:30 yan daukan Amarya suka zo,motoci Jere na alfarma aka dauki amarya da yan rakiyarta zuwa gidanta,Iklas fa har yau idonta tarwai har hira takewa angel kawarta,,

     Gida ya hadu kowacce sai kallon tsaruwar gidan sukeyi,gidan Omar dan gayu gidane na alfarmar gaske,upstairs kadai part uku ne,haka downstairs ma karshen haduwa ce,bare compound ba a magana,kayan da akayi ginin Omar wasu da yawa basu zo kasar mu Nigeria ba,domin turawa ne sukayi masa ginin gidan.


     Sahar da kawayenta yan magaa tantiran yan banaline da codine ne suna Palo sai shewa sukeyi hade da habaici kala kala,idan suka ga wata cikin yan kawo amarya sai kaji zagi da ashar na tashi.


      Kowa tausayawa Iklas yakeyi sabo da Sahar da suka ga abinda takeyi,ita kanta Iklas ta shiga damua sai taji duk ta tsorata,gwiwowinta sunyi sanyi,gashi bata San ya Omar zai karbeta ba tunda ba sonta yakeyi ba,

      Ummi na kusa da Sahar sunyi jugum jiyo muryar Sahar da sukayi tana ta zunduma Ashar.Iklas ji tayi dama bata yarda an daura aurenba,tasan Sahar watarana maybe kasheta ma zatayi.tsoro ne ya kama Iklas,amma har yau zuciyarta bata yi raunin da zatayi kuka ba,

  

     Yan kawo amarya duk sun mata sallama sun tafi har Ummi amma still Iklas ko kuka babu.

     Tana zaune tana tunani 9pm Omar, sultan,Raj sai Usy suka shigo dakin amarya Iklas,tana ganin Omar taji wani sanyin dadi,idon amarya kiri kiri mayafinta a kai amma bata rufe ido ba,haka aka bude da addua,sukayi musu nasiha da barkwanci,suka ajiye mata kudi Omar yaje ya Rakasu sannan ya dawo wajen Iklas fuskarsa a sake,ita kuwar gogar ji takeyi kamar ba aurenta akayi ba,normal tunda ta saba da Omar dama


      Gyalen kanta ya cire mata yanmata Amarya,ya kk,a hankali tace lfy,yau najiye miki dadi abar da kika Dade kina kallon shape dinta a boxers ko a towel gata yau har gida,sai kin gaji,yau zan baki ita,tunowa Iklas tayi da kallo tabi Omar kamar zatayi kuka,

     Cike da shagwaba tace ban taba kallar maka abu ba,kawai bangon dakin nake kalla amma kake ganin kamar idona a kanka yake, murmushi Omar yayi ganin yanda Iklas ta tsorata,bai taba sanin tana da tsoro haka ba sai yau,dama tsokanarta yayi.

      Tausayinta yaji ganin bata San kowa ba sai shi,bata saba da kowa ba sai shi,kwantar da hankalinki amaryas tsokanarki nakeyi,da Sauri ta rufe idonta tana daria,tare da furta ai nasan Sir dama tsokanata kakeyi,


     Omar a ransa yace zakiga tsokana yarinya nan da wasu kwanaki bazan iya jure kallonki ba ga sonki da ke ragargaza min zuciya,a fili yace dama ni salihi ne uztazu kece kike Neman lalatawa Mama ni,

    Je kiyi wanka muyi Sallah,ko na miki?murmushi tayi ba yanzu ba sai watarana,zaro ido Omar yayi yau ga amarya Mara kunya wai Iklas yar yarinya amma tasan zasuyi wanka ma wato nan gaba,inda take birgeshi ba boye boye irin na mata dan a kallesu a nutsatsu, abinda ke ranta zata fada koma wanne kallo kayi mata kai ka sani.


     Iklas ta saba da Omar bare ace zata ji kunyarsa,dama kuma ita bata cutar kanta da kunya a cikin arna ta taso shi yasa ba komai ke bata kunya ba,gogayya da mutane bata tsoro da Shakkar mutane bare ta bari a cuceta tayi fa talla a kwalta readers kar a manta.Iklas kwai wayo sai ta siyar da mutum a gabansa bai san anyi cinikinsa ba...

     Mikewa tayi ta tube gaban Omar daga ita sai towel ta Shiga wanka,ta dan jima ta fito,Omar ya fita yana Room dinsa ko takan Sahar bai bi ba,tunda ya shigo shi da frnds dinsa ta kama zage zage,shi Sam bai dauki Sahar a me hankali ba,baya sata cikin jerin mataye,duk yasan irin bin mazan da Sahar ke yi,yana da labarin komai,shi yasa yanzu bazai iya hada makwanci da ita ba koda sau daya,


     Shuru kawai yakeyi sabo da Baffa kar yayi laifi,kuma yana so lallai ya koyawa Sahar hankali ta gane aikin Gomnati ba shine gatan mace ba.

     Sahar kuwa frnds dinta ta Sallama,ta shige dakinta tana hucin kishi,sai yau tasan lallai tana son mijinta,ga kudi ga kyau ya hada komai da ake bukata,


    Tunowa tayi sanda Omar ya taba saduwa da ita,duk da ita keyin komai tayi enjoying fiye da mazan da take harka dasu,akan tayiwa namiji biyayya ya biya mata bukatarta gwara ta rike aikin Gomnatinta ta nemi maza ta biyasu kudi suyi mata abinda take so.cewar Sahar.

      Haushin Iklas ne ya tasowa Sahar,har akwai wacce ta isa tayi kishi da ita ta kwana lfy,wlh yau babu Wanda ya isa yayi bacci a gidan.

     Omar wanka yayi ya shirya cikin rantsatsun fararen kayan bacci na maza marasa nauyi sannan ya dawo Room din Iklas, a gaban mudubi ya ganta tana tufke gashinta,sanye da da wata rigar bacci kadan ta wuce pant dinta me siririn hannu tasha kyau,sai cinyoyi santala santala lumi lumi dasu farare tas,Omar da kyar ya danne zuciyarsa a ransa yana yabawa Iklas wurin kula da kanta,tasan kanta basai an koya mata ba,


      Jikin mudubin Omar ya taka har bayan Iklas, tallafota yayi ya kwantar da ita a jikinsa,cikinta ya shiga shafawa tare da warware jelar gashinta data tufke,sai shinshinata yakeyi tayi mukui da ita tana zukar kamshinsa tare da yaba taushin fatar omar.


       Bakin gadon ya jata suka zauna da kyar ya fisgo tunaninsa murya a dishe,idonsa yayi wani ja,tashi muyi nafeela,skert tasa tare da hijab sukayi Salla raka'a biyu da addua,

   Suna idarwa tace ya Omar yunwa nakeji ina kazar tawa?daria yayi sosai wlh ban taba ganin amarya irinki ba.

     Baki ta cokalo ni ka bani abinci naci Dama ina jin haushinka ka daura min laifi wurin Ummi rannan ka tafi,murmushi yayi tare da kallonta yana mamakin wai bata manta ba,shi ya Dade da mantawa,


      Leda ya jawo mata gashi kici ki ture,Indai kazace akwai ranar da sai kin biya ni bashi kika ci,daria Iklas tayi Ai Allah bazan Biyaba Sam bata gane nufin Omar ba,bude mata yayi ledar kaji dakwa dakwa,yogourt da juice sai sauran kayan ciye ciye,kafada ta make haka ake bawa amarya kazar? To ya akeyi cewar Omar nifa kin San komai sai kin koya min,haka kakewa Sahar din?kai ya gyada mata wai ae,tabe baki tayi tab haka ake love din?shi yasa ta gama rainaka in zaka mike ka mike kayi maganinta ka nuna mata namijine kai,ka zauna lalaci,jifa sunanka wurin Sahar wai Holoko.hmm maganar nan tana kona min rai,amma kai ko ajikinka,ka tabbatar kayi maganinta ato rai bace Iklas tayi maganar kamar itace Mama.

     

      Omar yasan maganar Iklas gaskia ce fa,dama tun farko ya samu Sahar yayi maganinta yayi mata kaca kaca,amma yanxu bazai iya hada jiki da ita ba tunda ta koma Neman maza.baya sonta,tana masa rashin mutunci amma yana iya kokarinsa ya biya mata bukatarta da abinda takeso shi ba wani karuwa yakeyi da ita ba amma kullim burinta ta yanka masa rashin mutunci.


     Iklas ce ta katse masa tunani ta hanyar riko yatsun Omar tana wasa dasu,never mind idan tafi karfinka ni zan gyarata.kajifa karfin halin Iklas,murmushi me tsada Omar ya saki yace ko ta gyaraki ba,ki dai kiyaye dan zaneki zatayi idan bana nan,ban son abu ya sameki,a ransa yana jin dadin yanda Iklas ke damuwa da damuwarsa, jawota jikinsa yayi ya dinga bata naman a baki,yanko naman yayi shima zai sa a bakinsa hannunsa ta rike,ta sa bakinta ta kwace a hannunsa ta cinye,daria yayi sosai,da hannunta itama ta fara bashi yana ci itama yana bata,abin shar  fa,

       Sunci sun koshi sosai,lemo Omar ya kurba a bakinsa ya tallafo fuskar Iklas da hannayensa biyu  bakinta ya nufa da nasa bakin,ya dan dago da kanta a hankali sannan a nutse cike da nishadi da shaukin so ya hade bakinsu wuri daya da harshensa ya bude bakinta ya juye mata juice din daya kurba a bakinta,ji kake makwat Iklas ta shanye tare da lumshe ido,

     Kallon juna sukayi kowanne dauke da murmushi a fuskarsa,a sigar rada Iklas tace ya Omar kafa hadu ai ka fi kowa iyawa ma,ko novel ban taba karantawa ba,ai a karatuna na theory banzo nan ba.


      Daria Omar yayi tare da yi mata wani arnen kallo na nuna mata zallar son da yake mata,idonta ta janye dan taji kunya yanzu,a ranta tace tab yafi karfina wannan uhm mutumin da yake rayuwar turai dama,

     Do u need more?Omar ya tambayeta,da sauri ta dage kai sama yeah,Allah ya Omar lips dinka laushine dasu har da zaki zaki naji,a kara min.yau Omar har ya gaji da dariar Iklas,shiko Omar dama abinda yakeso kenan da haka ya dinga tsotsewa Iklas lips amma bata gane ba.


         Wurin Iklas ta gyara ta kai komai kitchen,brush suka karayi  Iklas harda kuskura ruwan zafi na kaninfari da citta,ta jefa wata sweet ta ginger a bakinta,Omar yana kallon iyayi wajenta.


      Omar ya Riga Iklas kwancia a bed din,ya matsu tazo su kwanta ko zai samu saukin abinda yakeji yana masa yawo a jiki,hannu ya miko daga bed din ya jawota,karasa hawa bed din tayi da kanta,yau za a mori skin din Omar a ranta sai dadi takeji zata kwanta a kafi katifa.


       Mahaukacin bugun kofa sukaji kamar za a balleta,tare suka karasa jikin kofar Iklas na bayansa,waye pls Omar ya furta cike da jin haushi zai murje jikin Iklas an zo kawai an cuceshi,Iklas kuwa ita ta samu kafi katifa an mata bakin ciki ko waye zai ci ubansa hhh cewar Iklas a ranta.


    A bude Sahar ce  tayi magana,kamar Mara lafiya wai don a tausaya mata,wani wawan tsaki Iklas taja, kafin omar ya bude kofa Iklas ta rungumeshi ta baya,jikin Omar ba Riga sai boxers Iklas daga ita sai fingilar  rigarta,


     Bude kofar Omar yayi tare da cewa mene zaki dinga buga kofa haka,Sahar juwa taji na Neman kwasheta ganin Iklas manne jikin Omar, ta daflafaleshi,wato ita yake rainawa hankali,ko dakinta baya shiga,

     Nan take Sahar ta fara mintsina ido cike da bala'i kamar zata tashi garin,kut billahillazi Baku isa ba,wato ni ka raina min hankali kai ga me sabuwar amarya,aikin banza aikin wofi ke yar matsiyata,dama naji labarin ke yar tallace,wlh ki shirya karban hukunci me tsanani a gidan tunda kika yarda kika shigo kwadayayyu,Iklas ta tunzura amma sai ta danne zuciyarta batayi magana ba,sai mika da tayi a jikin Omar tare da yin hamma,pls horney muje bed am so tired ko tausa kamin,juyo da Iklas gabansa Omar yayi kafin ma tayi motsi nan Omar ya fara kissing din Iklas kamar zai cinye mata baki,Iklas tana sani take kara bashi hadin kai kai,cike da shagwaba Iklas tace babyna ka barni haka karka cinyeni danya sabo da zakuwa,Sahar tama rasa inda kanta yake,Omar shi ya manta ma da wata Sahar na wajen kawai shagalinsa yakeyi,iklas kallon sahar tayi ta aika mata da gwalo kanta a kafadar Omar,hannu ta dago ta sakalo wuyan omar ta kara aikawa da sahar dakuwa da hannunta ta mata ambola,a hankali yanda Sahar zata ji tace da aikin Gomnatinki kika tafi ya fiye miki,baza ki iya ja da yar talla ba,tare da sa kafa ta harba kofarta ta danna key,


      Kuruwar kuka Sahar tasa ita bakin cikinta bata ci Uwar Iklas ba ta kara cusa mata takaici,mikewa tayi ta dauki wata zureriyar wayar caja,ta gyarata ta boye ta,ta kuma dauko almakashi ta ajiye gefe, tace gobe zaki ci ubanki yarinya,Wallahi gobe sai na yanke miki gashin kanki da kike yanga dashi sannan na zaneki tas,ranki kadan zan rage miki shi,Allah kaimu ai gobe zai fita Omar din.

     Jikinki zai fada miki.ita Sahar ta rasa dalili da ta kalli Iklas sai basirarta ta kwace,mugun kwarji ni take mata,sai ta shirya zafafan maganganunta da taga Iklas sai ta kasa komai.


       Ibzzy Boy kullum Neman Iklas yakeyi inda zai ganta dole sai ya saceta in ya ganta,idan kuwa hakan bata faru ba to Acid kawai zai watsa 

ata a fuska ko ya nakasata ta hanyar cire mata kafa daya uban kowa ya huta.





Asmabaffa

hⓂⓂⓂ

     MA'AIKACIYAR 

          GOMNATI

           ⓂⓂⓂ

   

            140-145




By

Asmabaffa






       Iklas na rufe kofarsu,Omar ya haukace mata saura kadan ta saka kuka,taga abin nasa shi da gaske yakeyi ba wasa ko maganar wani wuru wuru       marairaicewa tayi ya Omar pls ka bari haka nifa da wasa nakeyi ma,dan Allah kayi hakuri,ko saurararta baiyi ba dan bai San me take cewa ba Sam,

      Tunawa tayi Omar baya son yaga tana kuka,kukan karya ta fara masa,tana yarfe hannu ganin Omar zai cire mata kayan jikinta,taga alama idan ya cire mata to ba lfy,

     Cak ya tsaya yana sauraron kukan karyarta,dagota yayi tare da janta kan bed suka zauna,da kyar ya iya furta menene?ni bana son abun nan da kake min ka bari pls,ba shiri Omar ya dawo hayyacinsa,cikin sigar lallashi yace aure fa mukayi,nufinki in zauna ina kallonki,cike da lallashi Iklas ta wayance  bafa haka nake nufi ba,I....I....mean ka dan barni na kara girma,Allah tsoro nakeji,ance da zafi ne,if not ma da tun muna gida zan fada ma ni matarka ce, da tuni ma sai dai kaka na kwanta nace Sir I need u,ko na kwanta flat nace ma horney gashi ci ka rufe abinka,Omar bai San sanda ya fashe da daria ba,sai da ya gama,yace to karkada kunnenki kiji da kyau,ina jinka cewar Iklas,


ya fara ni da kika ganni ba dan ci ka rufe bane kamar wani abinci a kwano,dole ki San nayi dani ki zage sosai kimin aiki,dan inda zakiji zam zam nima dole naji haka,

       To ai na San da haka,Dan Allah ka bari na kara girma ji be ni fa dudu nawa nake,har yau ban cika 17yrs ba,yanda ta marairace sai Omar yaji tausayinta,daga bisani yace banyi alkawari ba amma dai duk sanda na ji bazan iya jurewa ba to dole nayi,ba wani time Dana tsayar dan haka anytime ki zama cikin shiri,


     Kai ya Omar kai da kake Uztazu amma kakeyin haka,kaji tausayina mana,ke ce za Ji tausayi Iklas?yanda kike haka,mene baki San labarinsa na aure ba,duk wannan zancen da sukeyi Iklas na jikin Omar a kwance male male kamar ta samu katifa,

 

      Yana shafa bayanta tare da gashinta me santsi da kamshi,haka bacci ya kwashesu,sunyi Sallar asubah sun koma bacci,9am suka ji ana ta buga kofarsu,Omar zai mike ya bude Iklas cike da tabara tace pls ka kyaleta,

      Muyi baccinmu ya omar sleep sleep tana dan shafa masa suma kamar jaririnta,Iklas sai shagwaba take tsulawa Omar bai son takurata ko ya mata dole shi yasa da sigar yana lallashinta yake lagutse mata kirjinta da sauran sassan jikinta,kawai shagalinsa yakeyi,


    Munafuka Iklas ta gane shi kawai kyaleshi takeyi dama itama enjoying abunda yake mata takeyi,shi yasa take ta kusur kusur a bed din sai biye mata yakeyi sabo da shi yake karuwa da wannan shagwabar ta Iklas.


       Tun 9am sai 12 suka tashi daga aikin sunna.lol

     Omar ne ya fara rigima dole sai sunyi wanka tare,da kyar Iklas ta bashi hakuri ya kyaleta, sai da ta fito daga wanka sannan shima yayi,kafin ya fito Iklas har ta shirya cikin wata atamfa super green,riga da skert, dinkin ya mata kyau,kwalliya takeyi omar ya fito da sauri ta bar kwalliyar ta shiga tsane masa jiki,

    

      Mai ta fara shafa masa,tana kaifa dan gatane,shi yasa kake yanda kake so,mai ta koma tana Mirza masa a bayansa a hankali kamar tana shafa kwai,ke kika sani bayan kin sa na zama maraya,ba a kula dani,kin hanani komai,murmushi tayi ka dinga kwantar da hankalinka pls,kaifa nawa ne ni taka ce du,sai yanda kace Alaji ta kashe masa ido daya,murmushi yayi tare da mikewa tsaye yayi hugging dinta sabo da jin dadin kalamanta ya kura mata ido,har sai da ta sunkuyar da kanta kasa,dago kan nata yayi,yana mata kallon so,kunnenta ya kama ya ciji kadan,sosa wurin tayi tana shagwaba ya Omar da zafi fa,k.....bata karasa ba ya kamo lips dinta da nasa ya shiga lashe lashe da tsotse bakinta,

      Iklas ta rufe ido sai amsar sakonni takeyi,hura mata kunne yayi a hankali da bakinsa,sakin cream din dake hannunta tayi tare da shidewa taja yaji shiiiiiii,

  

        Matsawa yayi da sauri ya zata ko wani abunne ya sameta,me ya sameki?nunashi tayi da yatsa kaine,danayi me Allah wani dadi naji ziiirrrrrrrr,ban gane ba?abinda kamin a kunne yanzu sai naji wani luuuuuuu na tafi kamar na sume,

    Dan kara yimin kaji?murmushi ya saki,ya ya kara yi mata kamar yanda ta bukata sai da suka shafe wurin 15 mnt tana daukan darasi,tallafo hips dinta yayi let's go yunwa kike ji na sani,shiryawa yayi cikin shiga ta alfarma,kallonsa Iklas tayi tace kayi kyau sosai,tnx yace ai ke kinfini kyau kalleki fa kamar balarabiya,dama itace ai,murmushi Iklas tayi tana jin dadi an yabeta tace na gode.


Rike hannunta yayi sosai suka fita main palon gidan,

     Abinci suka gani Mama ta aiko dashi amma an kifar da su a kasa da gani takeshi akayi da kafa,gaba daya palon an lalatashi da abinci har jikin kujera an gama shafe abincin.


    Daya daga cikin yan aikin gidan ya tambaya ransa a bace,waye yayi wannan aikin? Alhaji Mama ce ta aiko driver ya kawowa Iklas, Sahar ce tayi hakan kuma tace kar mu gyara wajen,tana ina Sahar din cewar Omar?tana dakinta,Good to ku tabbatar kun gyara palon nan da sauri suka fara aikin gyarawa,

    Iklas ya kalla bari naje na miki take away,kar ka damu ya Omar, store na akwai komai,kitchen komai akwai,da raina da lafiyata ai sai girki,muje kawai karma ka damu kanka, wata cutar tazo ta shigar min kai a banza,

    Murmushin jin dadi Omar yayi tare da rungumo Iklas jikinsa,a hankali ya furta I love u so much my wife,tsaye Iklas tayi sororo sabo da tsabar jin dadi ance ana sonta,


        Ba kiji me nace bane?Omar ya tambaya,kamar zai cinyeta sabo da kallo,bakin Iklas yaki rufuwa sabo da jin dadi,dan ya kara fada taji tace banji ba,volume ya kara na murya yace I do love u,am in luv with u,I really love u Iklas, I wanna be with u forever.kunneta ta kawo dai dai kunnen Omar tace banji ba,I love u,I love u I realy love u.banji ba dai cewar Iklas again,da karfin gaske yace Iklas I love u.

      Juyawa tayi ta rungumeshi kam bakinta yaki rufuwa,tafin hannunta ta kama yiwa kiss a jere kamar tana tsosan wani abu bakinta na das das das haka ta dinga yiwa hannun Omar,tnx ya Omar,wanne irin tnx kuma cewar Omar,jira yake yaji Iklas tace I luv u too sai yaji wai tnx,kyaleta yayi sanda taji tana sonsa ta fada,ba takura,muje palona ka zauna nayi abincin,


       Kitchen ya bita,ya zauna ciki sai aikinta takeyi yana binta da kallo ji yakeyi kamar ya hadiyeta,Iklas na aikinta minti kadan zata juyo ta sakarwa Omar murmushin da tasan yana shiga wani hali idan tayi masa shi.


       Sharp sharp ta soya doya da kwai,tayi warming kazar jiya,tayi strawberry tea,ta shirya komai a dining,Omar ganin Iklas yakeyi gata yarinya amma tafi manyan wasu matan hankali,

     Tunda Omar yace yana sonta ta kara jin kwarin gwiwar kula dashi,kwashe abincin yayi daga dining ya dawo dashi palon Iklas,jikinsa ya jawota,ya zauna kasan center carpet ya mike kafafu tare da warasu ya sa Iklas a tsakanin cinyoyinsa tare da kwantar da bayanta a kirjinsa,abincin ya dinga bata a baki shima yaci,sai yaba dadin girkin yakeyi,

    Suna gamawa ta fara gyara part din,Omar yana mamakinta da jinjina mata har ta gama gyare ko ina na part dinta,sai kamshi da kyalli ke tashi ga sanyin ac.

     Wanka ta karayi ta canja shiga wata doguwar Riga me siririn hannu,amma tsayinta har kasa,an mata tsaga biyu a gefe gefe har iya Rabin cinya,ko ya ka juya cinyoyi waje masu kyau,

      Gashin nan ta kara sharchewa ta sakeshi,kamshinta shi ya jawo hankalin Omar dake aiki a laptop yaana latsa system.


      Kallonta yakeyi kamar maye,tana karasowa wajensa ya jawota a hankali jinkinsa,kinyi kyau wifey. Zama ta gyara sosai a cinyarsa suna facing juna,cikin salo ya fara kissing dinta ba kama hannun yaro,Iklas sai jin dadinta takeyi,wuyansa take shafawa a hankali,jikin Omar rawa kawai yakeyi,


     Mutsutsun da takeyi da mazaunanta kan cinyarsa shi ke sashi kara birkicewa.

      Sahar tana ta jira Omar ya bar gidan ta samu ta chasa Iklas,amma Omar bulun bukwi yaki ma fitowa koda Palo ne,tayi jiran har ta gaji,kuka ta fara yi  sabo da takaici,


      Bayan ta gama kukan nata, wayar Frnd dinta ta kira Deeja ta shaida mata komai,shawara Deeja ta bata na iya shegensu.tana kashe wayar ta nufi bangaren Iklas, baram ta daki kofar Palon da kafa tare da murda handle ta fada palon,Iklas da Omar ta hango kan kujera kamar zasu cinye junansu,Iklas tana saman Omar,Suna lashe juna, taga Sahar a Kansu amma tunda da kaya a jikinsu ba Matsala ta shekara tana kallonsu,


       Ganin Sahar yasa Iklas ta kara volume wai kukan dadi takeyi,sai kiran honey takeyi ba adadi,shi kuwa Omar yaga abinda Sahar tayi amma abinda Iklas ke masa yasa ya manta da komai a duniya,bai ma San inda Kansa yake ba.  Musamman da yaji Iklas ta kara sautin kukan dadinta.


      Sahar ta gama fusata hannu tasa ta mako Iklas kasa ta fadi Tim daga saman Omar dake kwance a 3seater.

      Mikewa Omar yayi da Sauri,iklas  fashewa da kukan shagwaba tayi tana nuna Sahar da yatsa,kwashe Sahar yayi da wani matsiyacin maruka lafiyayyu guda biyu, wayar charger ta computer dinsa ya dauka.


      Ya hau jibgar Sahar ba ji ba gani ya kulle kofar gam, saida ya farfasa mata jiki,tun tana neman agaji da kuka har ta daina,Iklas ta tsorata tare da tausayin Sahar,amma Sahar cewa takeyi shegiya matsiyaciya karuwa,in ba karuwa ba wacce amarya ce farkon aure zata likewa namiji haka,tambadaddiya me bin maza.


     Kwace wayar iklas tayi daga hannun Omar ka kyaleta haka mana za ka mata illa fa,muje ciki pls,handkerchief yasa ya goge fuskarsa, kansa ne ya Sara masa sosai Kansa ya fara ciwo,dafe kansa yayi da sauri tare da nuna Sahar da yatsa,kar kiga ina shuru ina kyaleki kice zaki dinga takurawa rayuwa ta,kinyi kadan,tausayinki nakeji a matsayinki na ya mace that's y in kikayi min abu nake kyaleki,duk ranar da kika kuma Shiga gonata za kiga matakin da zan dauka kanji, shiga bedroom yayi da sauri.


       Wajen Sahar dake tsugunne Iklas ta karasa,durkusawa ta yi gabanta,sannu kiyi hakuri wlh ban San zai miki haka ba.bari na gasa miki jikin,Sahar na dagowa ta fallawa Iklas mari,tana dauke hannu ji kake tassssss Iklas ta rama itama tare da kwashewa da gudu ta fada bedroom, tana haka kawai daga yin sannu,nan gaba ko yankaki za ayi ko kulaki bazanyi ba.Sahar ta tsorata da Omar,dama haka yake bashi da mutunci.Allah ya isa tayi ta mike ta bar dakin.waya ta bugawa daya daga cikin kwaratanta,tace su hadu hotel ya gasa mata jiki sannan ya sanyata nishadi.tab kajifa Sahar baza ta shiryu ba maybe.


   Omar ta gani bisa bed sai murkususu yakeyi, idonsa ya kakkafe sai nishi yakeyi kamar zai mutu.Kwala Ihu Iklas tayi wayyo Allah za a kashemin mijina,  sai da ta jawo cuta ta shigar min miji.a gigece ta haura saman gadon tana jijjigashi.sai kuka takeyi kamar ranta zai fice.


      Sadiya zaune kan kujera dake palonta tayi tagumi sai tunani takeyi tare da Dana sanin auren Alhaji balarabe da tayi,ko mene dalili oho,amma duk ta rame tayi baki.kafar nan ta kara yin siri siri,mazaunanta sun kara chokalewa.




Asmabaffa

 

      Tnx fa Readers kuna birgeni.

[9:17AM, 4/21/2018] ‪+234 903 944 2971‬: ⓂⓂⓂ

   MA'AIKACIYAR 

        GOMNATI

         ⓂⓂⓂ


          145-150



By

AsmaBaffa






       Mikewa Sadiya tayi tana tafiya kamar wacce kwai ya fashewa a ciki sakalo sakalo,sallamar Alhaji Balarabe taji gabanta ne ya fadi ras da sauri ta juyo ta karaso wajensa cankal cankal,hannu ta mika da niyyar karbar jakar Alhajinta da karfin tuwo ya hankada ta gefe,sai da ta fadi,tirgija tirgija Alhaji ya wuce bedroom da katon cikinsa,abincin da ya shigo dashi ya zauna yacinye abinsa yayi gyatsa ji kake kwaaaaaa...tare da zarar tsinken sakace ya fara sakace hakoransa,yana gamawa,alwala yayi tare da sallah,fitowa yayi ya kai kallonsa wurin da Sadiya ta rakube tana jiran ko ta kwana


      Wurinta ya nufa rumbuda rumbudaaa..ja da baya ta fara kamar taga wani kasurgumin tsohon zaki,damkota yayi da hannu daya ya dagata kamar kaza ya wuce da ita bed ya makata bisa bed ya fara aikin sunnarsa ba ji ba gani,Sadiya kuka kawai takeyi,bakinta ya matse da hannu daya yaci gaba da harkokinsa na aure ba wani romance da love yana dan ubanki wallahi sai kin dauki ciki,bazai yiwu a cinyen kudi a banza ba,tunda nake aure aure na ban taba kashe kudi me yawa haka ba sai a kanki duk saboda Neman haihuwa.


     Uban me zanyi dake dama dan ki haifarmin yara na auroki,gashi ko girki baki iya ba kullum in rayuwata a restaurant, duk wani muamular aure baki San komai na aure ba

      Sai Aikin Gomnati makaryatan banza da ace kina sani nishadi ko baki haihu ba zamu zauna lafiya ki samu soyayyata,amma tunda ba yar arziki bace ke dole sai na mori kudina wlh,shashasha uwarku bata koya muku tarbiyar arziki ba sai neman kudi.

    Zaki San kin tabo Alhaji Dan Balarabe tasssss ya Dana mata duka a yar yangwadaddiyar cinyarta kamar ta sauro yaci gaba da sex dinsa,kuka take tana bashi hakuri kayi hakuri...kayi min rai. ...inshaAllah zan dauki cikin dama....dama.....zabura Alhaji yayi daman ubanki.ba shiri ta fasa fadan abinda tayi niyya.


     Wayar Omar Iklas ta raruma a gigice ta kama scrolling numbers suuuuuuuuu sai ta tsaya a Sultan ta danna kira,bugu daya ya dauka.ango ango cik ya tsaya jin sautin kuka,dan Allah kazo......kazo Ya Omar zai mutu,dit ya katse wayar sai gidan Omar a sukwane.

    Minti kadan sai ga Sultan,a guje Iklas ta fito har da bigewa a jikin jujera garin sauri,shigo kawai pls,da sauri suka shiga dakin Omar suka tarar yanzu ya daina kukan ciwon kan yayi lamo kamar gawa,


     Dubawa Sultan yayi yaga yana numfashi komawa yayi motarsa ya dauko kayan Aikinsu na likitoci,ya fara aune aunensa,jinin Omar ya hau kadan sai malaria da ta masa kamun kazar Kuku,

      Wasu Allurai ya hada a drip ya sa masa,fita yayi yace ina zuwa,mota ya Kara ja ya hado masa magunguna ya kawo,Iklas ya kalla tayi tagumi ta tasa Omar gaba tare da damke hannunsa a wuyanta,

     Daria ta bawa Sultan shi yanda take abun manyan mutane ne ke bashi da daria,ita gata ba saurin girma tayi ba ba me garin jiki bace,yar dai dai da ita ga kyau.


       Ga magani nan amarya ki tabbatar yasha kullum,Omar baya son magani sai kinyi da gaske,malaria ce sai dan jininsa daya hau,Ku kula Omar baison hayaniya da bacin rai,in dai hakan ta faru to jininsa yana hawa kadan.

    Pls ki kula dashi makiya sun sashi gabane shi yasa har ciwon ya shigeshi.


         Omar kwai taurin zuciya ki kula da shan maganinsa,a hankali Iklas tace insha'Allah zai sha ai ko kinsha yayi dure zanyi masa,da yafi dai cewar Sultan to sai anjima idan ya tashi kice ya kirani,OK I wl cewar Iklas ta kara da ka gaishe min da matarka,zata ji.to mungode Allah bar zumunci,sultan  a ransa yace inye lallai yanzu muka San Omar yayi aure,sabanin Sahar idan ta gansu daga zagi sai kallon banza.


       Yusouf mijin Aisha ne ya shigo kwance ya Tarar da ita, tana ta garzar kasar calaba,kallonta yayi shekeke ke yanzu daga aure har kinyi ciki,?

   Da masifa tace to ni na bawa kaina?ko ni nayiwa kaina?aikin banza ka takura min,ni bance ka taimakamin da sisinka ba,gidanmu ba matsiyata bane,kudin aikina kadai ya isa ya rikeni,

       A fusace Yousuf ya mike kin sanni kuwa tare da narka mata wata katuwar Ashar.baki ta murguda ba dai ni ba, belt din wandonsa ya zaro daga dan tsukakken kugunsa kamar kullin omo dan ashirin,

    Fyadarta ya shigayi da kyar ta gudu room ta kulle kofar.

       Kwafa yayi tare da karasawa wajen daya tanaja sabo da ajiye barasa, vodka ya dauka kwalaba daya, ya dinga korawa, ya fice a cakee,sai gidan da suke kai mata Suna masha'a.


         Omar ne ya farka yaga drip a hannunsa har ya kusa karewa ma,Iklas na zaune gefensa ta zura masa ido,kallonta yayi suka hada ido,a hankali yace I love u tare sakar mata  murmushi,ajiyar zuciya ta saki,hannunsa me laushi daya ta dauka ta tallafo furkar,tana kallonsa itama a nutse tace I love u more,I missed u,murmushi sukayi a tare, sannu Sir Allah baka lfy,kai ya gyada mata ba tare da yayi magana ba,


    Sir?kafada ya make kamar yaro wai bai son ta kirashi Sir,murmushi tayi bari na cire ma canula ruwan ya kare,dannewa yayi ta zare masa Allurar a hankali,saida ya huta tace me zaka iya ci?anything wanka zanyifa  first,

      A'a ka bari kaci abinci sai kasha maganin,sallah ma ana binka bashi,shi yasa nace miki wanka zan fara, kafin ki gama girkin na gama komai,kinga magrib ta kusa,OK to mikewa tayi tsaye zaka iya tashi?murmushi yayi no zo ki dagani,tahowa tayi ta fara cikiniyar dagashi ta kasa,a hankali ya dungure mata kai,matsa raguwa kawai,daria tayi ae naji muje na hada ma ruwan wankan,

      Har toilet suka shiga tare ,ta hada masa ruwan wanka,ta fito saida taji ya fara wankan sannan ta zabo masa kayan sawa,short kawai ta da wata Riga armless Mara nauyi duka farare kal,

      Kitchen ta fada tasan Omar akwai son tuwon danyar shinkafa miyar egusi shi yasa ta shirya masa shi miyar tasha naman kaza da kifi.

       Coconut juice ta had a yayi sanyi sosai,gefe daya kuma farfesun naman rago tayi masa lafiyayye,a dining din dake sashenta ta shirya masa komai,fitowa yayi sanye da kayan da ta zabo masa,wifey zo nan,cike da yanga tazo wajensa tana shakar kamshinsa,gira daya ta dage masa alamar me zanyi,jallabiyya doguwa zaki zabo min zanje masallaci an kusa sallar magrib,daga nan zan biya wajen Mama, daki ta shiga ta fito dauke da rigarsa,zo na sa maka sunkuya,ai kuwa ya duka dai dai tsayinta ta sa masa rigar harda cewa inye dan gatan Maman ba,murmushi yayi da badan zan karya Alwala ta ba da kinsan dan gatan Mama,

        Cike da kissa tace Kai da baka da lfy pls kana yin sallar isha ka dawo kaji,


       Ya zanyi na wuce Isha a waje bayan na ajiye kamarki a gida,rungumota yayi tare da manna mata kiss a goshi,har yaje jikin kofa Iklas ta kamo hannunsa ta manna masa kiss a kumatu kamar zatayi kuka pls horney ka dawo da wuri ina jiranka


      Fuskarta ya shafa karki damu dear yanzu zaki ganni, tana diren diren kafafu hade da kukan shagwaba. Uhmm.....uhum....uhm...ni dai kar kaje kaci abinci a waje ko wajen Mama,murmushin jin dadi ya saki yanda Iklas ke ji dashi,ni na isa in bar wannan girkin me dadi.....kiss ya kara manna mata a saman lips take care of ur self for me, u too horney Sir,ki sa key a kofarki kar Sahar ta shigo ta zaneki,

    Daria Iklas tayi ai kana fita zan datse ko ina,ka gaishe min da Ummi da Mama, ka cewa Abdallah ya kawo min su Suleim,karma kisa rai za a kawosu yanzu,haka kawai su takura mana.


     Hannu ta daga masa tare da bude masa kofa bye my love,yana fita ta kulle ko ina nata,Sallar magriba tayi tare da karatun Quran,tayi addua sosai kana ta hau gyaran gidan,ko ina kyalli yakeyi kawai,room freshener ta fesa kala kala sannan tayi turaren hayaki ko ina,tare da kunna ac ko ina kamshi da Sanyin dadi ke tashi,


 Toilet ta fada ta shiga gurje jikinta lungu da sako,haka bakinta ma,ga toothpaste, gawayi,gishiri sai lalle dasu take kalkale bakinta,bayan tayi wanka da Alwala kara wanke toilet dinta tayi,ta fito Sallar isha tayi  tare da shafa'i da wuturi,


     Jikin mudubi ta isa ta fara shafa body lotion dinta me tsada da dadin kamshi,8:30 taga har yau bai dawo ba,wasu turarukan jiki tsadaddu ta shafa,jikinta sannan ta dauko wata rigar bacci me hannun bra dark pupple iyakarta cinya me sulbi da tsadar gaske,powder kawai ta shafa,sai lipglow gashinta ta karasa busarwa da hand drier,sannan ta gyarashi da lafiyayyun mayuka,da hairspray,wayarta ta dauka ganin 9pm ta kusa kiran Omar tayi,yana dagawa yace kin ganni na dawo ina compound ma yanzu zan shigo,

     OK tace ta kara goga powder ta kara kyau,sannan ta shiga fesa perfume kala kala.

      Knocking taji da Sauri ta bude kofar tare  da sakar masa murmushi me tsadar gaske Wanda ko shi Omar bai San Iklas ta iya shi ba sai yau,

     Wata wawar runguma ya kai mata ta zille ya rungume iska daria sukeyi gaba dayansu,zuwa yayi ya rungumo waist dinta tare da mannata jikinsa yana me kafeta da ido yana aika mata da wasu wasiku cikin jinin jikinta,wow wifey kinyi kyau,u look like take away, cikinsa ta shafa tare da kallonsa ido cikin ido dear yunwa ko?

     Sosai ma cewar Omar, muje  ur food s ready,kujera ta zaunar dashi ta cire masa rigar daya Dora saman kayan da ta zabo masa dazu,

      Fuskarta ya bi da tasa fuskar da niyyar kissing dinta janyewa tayi abinci shine damuwata nafiso naga kaci ka koshi,na baka magani,fuska ya yatsina nifa na warke ban son magani,


     Hmmm dole kasha kana nufin zan tsaya ina kallonka cuta ta illatamin kai,Sultan yace idan ka tashi u should call him on his phone,Omar bai damu dacin abinci dole a dining ba,duba ga wannan Iklas ta kwaso komai na abincin ta shirya masa a palo,sakkowa yayi kasan center carpet me laushin gaske ya zauna.


     Serving dinsa tayi ta zauna a gabansa dirshan tana bashi a baki,idan ta gutsuro tuwon taji da zafi har har juya hannunta takeyi a Iska wai ya huce sannan ta bashi kamar jariri,Omar a ransa wani son Iklas ne ke sukansa,tare da wani kara narke mata,jinsa yake kamar karamin yaro, to Iklas tana ta shagwaba shi,abinda yake so kafin yace anyi masa, sai dai yaga tayi,


     Kuma dama haka yake bukatar matarsa ta kasance,Saida ta tabbatar ya koshi sannan ta bashi lemon yasha,mouthfreshner liquid ta bashi ya kuskure bakinsa,sannan itama taci ta koshi tayi yanda tawa Omar,


     Kwashe komai tayi ta kai kitchen ta wanke plate din da aka bata etc,Ta gyara wurin,Omar sai binta yake da kallo kamar ya lasheta yakeji,shi kam gaskia bazai iya jira ta wani kara girma ba,wanne girma ake nema da ya wuce wannan cewar Omar a ransa,


     Maganinsa ta dako da ruwa,daure fuska tayi irin ba wasa ta balli magani, tayi lallashin duniya kan ya sha yaki sha,maganin tasa a bakinta kusa da lips dinta yanda bazai shiga mata ta hadiye ba,da hakoran gaba ta tauna shi,kan cinyar Omar ta Dane tayi zamanta ta hardo kafafunta a kugunsa,kansa ta tallafo ta dura masa maganin a bakinsa kamar tattabaru,ruwa ta kora masa tana shafa bayansa,dukiyar fulaninta yake murzawa cike da salo,am sorry kaji,haka suka dinga yi tana masa durar magani har ta gama bashi maganin,

     Tashi zatayi Omar Wanda ya gama shagalta bai ma San ya sha wani magani ba,cikin zafin nama ya damko Iklas mikewa yayi ya dauketa cak har bedroom


        Kan saman bed ya daurata bikinta ya shiga tsotsa yana murza dukiyar fulaninta gaba daya ya zauce,Iklas wacce zafi zafi takeji a dukiyar fulaninta,saboda da bata fara breast da wuri ba,duk da cewar sun girma har yau idan aka matsasu tana dan jin ragowar zafi kadan.


          Ibzzy ne ya samu labarin auren Iklas da Omar,address din Gidan auren Iklas ya samo sannan yasa ranar zuwa ya kaddamarwa Iklas,sabo da shifa yana sonta kawai sai wani ya aureta a banza,dama ya sani tun farkon da ya bigeta a mota ya danne mata hanci da pillow a hospital ya karasa shegiya,bakin cikinsa daya wani ya sha zumar Iklas ba shi ba.


     Sosai Omar ke laguda Iklas,yana mata sambatu, tun bata hassala komai har ta shiga taimaka masa,sucking ta fara masa, domin tasha ji wajen abokan tallarta da kabilar Arnan dake unguwarsu,cewar sucking wa maza ko mata yafi dadi,mutum zai samu nutsuwa ta hanyarsa,shi yasa yau duk zatayi amfani da labarin da takeji kala kala.


         Dagewa Iklas tayi sosai tayi maganin  Omar tsab,ba irin dadin da baiji ba,saida ta sama masa nutsuwa, ba tare da sunyi sex ba,Omar  shi yasan me yaji,kallon kawai yakeyi ba wata kunya ta bashi farin ciki,wani yanayi na nishadi ya tsinci kansa,sai so da kaunar Iklas dake karuwa a ransa,ayyanawa yakey i a ransa yanda zaiji duk ranar da ya sadu da Iklas,

 

     Jin kansa yakeyi akan ya sadu da Sahar gwara Iklas tayi masa ko kiss ne irin Wanda tayi masa yanzu,gaskia iklas matar so ce.karuwace a wajen mijinta .

    

      Haj rahina sadiya da Aisha sun fara kai mata karar mazajensu,saboda  kar suji kunya ko Baffa bata sanar masa ba,lallashinsu  tayi ta maidasu gidan mazajensu.


     Iklas ranar da kyar Omar ya barta suka samu bacci,washe gari 5pm Iklas na kitchen tana soye soye kamshi na tashi,sanye take dawando legins baki me adon fari,rigarta me dogon hannu da coller, tasha adon flower da fararen duwatsu,

       Mazaunanta kamar su fado dan fadi da tudu,waka take rerawa tana rawa sosai take jijjiga iya mazaunanta kawai kai yanda take rawar ka rantse kida takeji a manyan speakers.Omar Wanda tunda ta fara yana jingine jikin bangon kitchen ya harde hannayensa a a kirji kawai

     Yana shan kallo a ransa yace lallai yarinyar nan tana ji da tashen balaga, ya zama dole na sauke mata ita.


Iklas taga shigowar Omar tuni,kara jijjigawa takeyi tana..


   Ku samu kudinku ku damu damu.


  Duk wata harka ayita damu,


   Jalla ilahu ya yarda damu


    Ku leka kasar makka tare damu.


    Maza Naira zo mu gamu


   Ya Allahu ka bamu kudiiiii


    Kai.. kasa..sama.. ehhhh


   Ku matso ku matso ku matso,


     Maza baby shaky body,maza shaky body


    Duk Zaria babu barawo in kaji ihu kwartone.


    Masallacin kura ba a sa kare yayi limanci,


    Sisi baby maza shaky body,


    See that bad guy gety money


    Plenty motors belong to him


     I wl snatch him go buy henecy


    Kasa.. sama


  Uhmmmm shake oya shaky body.

  

      Dariar wakar tata Omar yakeyi sosai gaskia yau ya tabbatar Iklas tayi zaman geto area da talla.nishadinta takeyi kawai.sai ta birgeshi sosai yafi son kullum a kasance cikin jin dadi ace dai nishadi yafi kuncin rayuwa yawa.

     Gaba daya sai ta birkita masa tunani yanda take sarrafa mazaunanta kadai kuma a hankali cikin nutsuwa, shii kadai take kadawa abin sha'awa da birgewa.


       Takowa yayi har inda take hugging dinta yayi ta baya,tare da shafa kirjinta dake matukar birgeshi,tana jin yanda yake goga mataSandar girmansa a mazaunanta, hannayenta tasa biyu ta sakalosu ta bayan wuyansa tana shafawa a hankali,

     Omar ji yake hakurinsa ya kare bazai iya jira ba,bazai iya zama ba tare da ya jishi cikin headquarter Iklas ba,


     Iklas gani tayi gaba daya Omar ya shiga wani yanayin da bata taba gani ba.

   So takeyi ta zille amma Omar ya kanannadeta ya hanata ko da kwakwaran motsi,


     Iklas na birgeshi sosai  yanda take sashi farin Ciki da nishadi ko yaushe  Iklas ce farin cikinsa da nishadinsa yanzu.

    Kullum kara sonta yakeyi.



AsmaBaffa



    Readers 👍👍👍👍

[9:17AM, 4/21/2018] ‪+234 903 944 2971‬: ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR 

        GOMNATI

         ⓂⓂⓂ


          150-155



By

AsmaBaffa





         A hankali Iklas tace na gama fa muje kaci kasha magani yau dole da wuri zakayi bacci sabo da maganin yabi jikinka,daria ce ta kusa kwacewa Omar saboda Yanda yaji kiri kiri Iklas zata raina masa hankali wai a dole shi zatayiwa wayo,

      Murmushi ya saki ba tare da ya saketa ba yace yau ni bana bukatar abinci kuma maganin ai babu na bacci cikinsu balle  kice zai sani bacci,

   To ai shi magani ko wanne kasha ko paracetamol ne yana bukatar mutum yayi bacci sosai,jiya ma da kyar fa kayi bacci,gaskia bazan bari yau ka kai 8 na dare ba tare da kayi bacci ba,


     Munayin Sallar Isha zakayi bacci,dama akwai wani film da zan kalla sai na kalli abina kana baccinka,tun Omar na danne dariarsa sai da ya saketa ta fito,dagata sama yayi kamar jaririya,ya sa hannu ya kashe gas din,tunda ta gama girkin dama,Iklas ta gama tsurewa,bedroom tagafa da gaske indai suka shiga me kwatarta sai Allah.


       Zillewa tayi tare da kwace kanta damkota zaiyi ta fada kujera,tana ta zare ido kamar hawaye zai zubo tace pls kayi hakuri ya Omar dan Allah idan ko nayi candy kaga na kara girma

   Daria ta bashi Ashe kina da tsoro haka?kalar tausayi tayi tace dama ni matsoraciya ce karfin hali nakeyi kawai,bani da wata juriya ko ta kwayar zarra,


        To nikam zan koya miki juriya yau,bazan koyaba kwakwalwata bata ganewa,ae amma tana gane jijjiga hips ko,da sauri tace a'a karambani ne kawai,a ina ki koyi rawa haka,murmushi tayi tare da rufe idonta a wajen Igbo da yarabawan unguwarmu mukeyi tare dasu amma fa tun muna yan yara

    Nidai dan Allah ka bar zancen nan ga abinci kazo na baka maganinka,hmmm duk ranar da kika shiga hannuna zaki gane kurenki, kuka ta saka na gaske to....kaji...ko...ka fada....da bakinka,kuma dama wasu frnds dina Ngozi da Dami sun fadamin zafin da akeji,.

 Su  frnd din naki har sun San komai kenan,kallonsa tayi tab sosai ma kasan ba musulmi bane,wasu musulman ma a wurin talla da na unguwarmu duk sun bari kabilar nan su lalatasu,in ka zauna a unguwarmu ai sai wanda Allah ya shirya kawai,

    Allah kyauta shi yasa suka koyawa matata rashin kunya.


     Ai ni Allah ya shirya ni ya Omar amma da tuni an Dade da tsallaka min boarder.

      Dan Allah ka bari na gama candy,kin daukarwa kanki yan mata bazan iya ba wannan shirmen bada ni  ba in zaki saki saki jiki ma ki saki.ganinda yayi ta tsorata dashi yasa yayi mata wayo kar ki damu wifey wasa fa nake miki gobe ma zaki koma schl,ke baki San wasa ba garin gudu zaki balla kafarki a kujera ki jawo min asara..

     Dadi taji sosai a ranta nan take ta daina kuka,kallonta yayi bani maganin ma na sha abuna bacci zan kwasa yau,murmushin dake kara mata kyau tayi,


      Bayan sallar Isha wanka sukayi kowanne cikin shirin bacci,kamar yanda ta bashi magani jiya haka ma yau,Omar ne ya kalleta da shanyayyun idanunsa muje bacci nakeji yau da wuri,


      A bayansa ya Goya ta har bedroom,kwanciya sukayi nan iklas ido ya fara raina fata,Omar kamar zai cinyeta haka yake sarrafata,so take ta gudu ba hanya,wata gigitacciyar kara sukaji kamar harbi,ajere kamar guda Goma jikin sashen Iklas,

    Omar tsayawa yayi cike da takaici ya kusa cimma burinsa amma komai ya katse sakamakon karar da sukeji,kara tashi karar takeyi kamar saukar aradu,


       Haj Rahina ce zaune ta rasa madafa,bacin rai dankare a zuciyarta na halin da yaranta suke ciki a gidan mazajensu abun yanzu yafi na da,kullum kara gaba abin yake,ba irin yanda Yousuf mijin Aisha jiya yayi mata dukan kawo wuka saida ta kwanta a asibiti,ga shaye shaye ga Neman mata,

     Sadiya kuwa abin nata sai du'ai,ta gama kwarjalewa,ita yanzu ta daina yin Allurar tsaida haihuwa,so takeyi ta samu ciki ko ta huta da masifar Alhaji Balarabe,amma har yau shuru kakeji ba cikin ba labarinsa. Na Aisha kuwa  shi haihuwarce bai so,yafi so a zubar da cikin,


     Mama da Ummi zaune Palo suna hira,Ummi tace Haj kinji yaran nan shuru,Iklas ko waya bata kirani ba ta samu Umaru ta manta damu,gwara ma Umaru jiya yazo, hmm ke kike kare wani Babana,tunda akabashi Iklas sai jiya yazo gidan nan kina gani dai yaron nan ko zama baiyi ba,muna gaisawa ya mike wai ya bar Iklas ita kadai.

    Sahar kuwa in kinga irin fada da faman da nadinga sha kan Omar 

    Allah ne abin Godiya cewar Ummi.ai mu sai San barka inji Mama, yanzu hankalina kwance, har Baffansu nake bawa lbr.

     Ummi tace kinga masifar da Umaru ya dinga surfawa Su Abdallah kuwa daga sunce zasu je su kwana.

     Ohhh Mama ta rike baki yaran zamani sai a barsu ni bazan bar yarana suje kwana gidansu ba,sai dai yini.


      Omar ne ya mike da niyyar bude kofa,Iklas ta rikeshi ina zakaje haka aje ayi maka Illa kuma ma jikinka ba komai fa,Rigarta ta saka wacce ya cire mata tare da zura hijab kato har kasa,Boxers dinsa ta mika masa yasa sannan ta bashi jallabiyya fara yasa,hannunta cikin nasa  suka bude kofar a hankali,knockout ne ke ta tsalle kala kala suna tashi fafafas fas,

     Yasan wannan aikin Sahar ne,amma bazai mata komai ba tukun sai time yayi inda zatafi jin ciwon abin.

      Sahar yanzu bata kwana a waje saboda wanted take Neman su hadu da Iklas, tana dakinta karfe 8na dare ta dawo,knockout me remote ta siyo ta zubasu a kofar room din Iklas tana daga room dinta tana tashinsu da remote din hannunta.ran Omar ne ya baci yanda Sahar ke rainashi,

      zaiyi maganinta.suna tsaye har knockout suka gama tashi.


     Iklas kuwa dadi taji ma an hana Omar aiwatar da aikinsa kanta,a fili kuwa lallashin Omar ta farayi ganin ya shiga wani hali na bacin rai,mood din Omar ya canja kwanciya sukayi makale da juna bacci ya kwashesu,

    Washe gari Iklas shirin makaranta tayi Omar dake kwance kan bed kallonta yayi yace daga aure zaki tafi schl?


     Kaifa kace naje jiya, na fasa to haka kawai kina amarya ko 1wk baki ba baza kije ba,

   Baki ta tabe dama ai kai kace zanje,uniform ta cire ta ta canja kaya ta hau gadon itama,a dungure tayi ta fada kan Omar, tana daria ta dane ruwan cikinsa,turota kan bed yayi,ta kara darewa cikinsa,kara turota yayi ta kwanta rigingine itama ,tsaya nayi miki kiji idan da dadi,kan cikinta shima ya hau bai sakar mata nauyinsa ba amma sai nishi takeyi tana rokon ya daga ta.

     Komawa yayi ya kwanta ba karfi sai tsokanar tsiya ya lakace mata hanci, daria sukayi gaba daya,komawa tayi ruwan cikinsa tana masa chanese a hankali na wasa, lips dinsa na kasa Omar ya cije,yace nasan me kike so wifey,tana kan ruwan cikinsa ya kwantota fuskarta na gugan tasa kamshinsu ne ya hadu wuri daya kowanne na shakar na dan uwansa.


        Karan hancinsa na gugan nata,cike da salon kwarewar basira ya kamo harshenta suka shiga tsotsar juna,biye masa takeyi sosai wai duk dan kar ya nemi babbar harka,

    Zama tayi sosai a cikinsa cire mata rigarta yayi ya shiga lailaya dukiyar fulaninta son ransa ya rigada ya susuce tun tana biye masa taga ya wuce saninta abin,

     Kwantar da ita yayi a hankali sucking ya mata sosai ya sa ta jike ,dama ga abubuwan da take sha na gyara,rada mata yayi a kunne kiyi hakuri wifey bazan iya jiranki ba,kuka ta kece dashi zata gudu amma ina ya riga da ya makalkaleta ta ko ina,dama yasan haka zata yi masa,bai son ya mata dole,yafi so sai da yardarta amma Iklas bata San kara ba,sai ta dinga tsokanoshi tana guduwa,

     Hakuri kawai yakeyi amma yaga taki ganewa,Iklas taga ba sarki sai Allah tasan dole ne,dan Allah ka bari to sai dare ko sallah raka'a biyu  bamuyi bafa?bazan iya hakura ba cewar Omar ya furta kamar zaiyi kuka,na gaji da hakuri wlh zan cutu ne ko tausayina bakyayi,ko bakya sona?


    Tana shesheka tace ina Sonka...ma..na....tso...ro..nakeji..wai da zafi...kuma ni ..yarinyace.is ok to ki nutsu kiji idan mutum baiyi a hankali bane akejin zafi,amma ni kinga ina sonki sosai kuma ina tausayinki dole zan miki a hankali.


       Gashi ni dan gatanki ne fa,komai kina min abinda nakeso shi kike min,wannan ma da ace kin san yanda ake jin dadinsa da tuni kin yarda,amma yanda kike ji dani haka kike shagwabani ace kin kasa barmu mu samu jin dadi,

      Dadi Iklas taji Omar dinta ya yabeta,gaskia dole ta bashi wannan ma ko dan ta birgeshi,gashi yace ana jin dadi,tunowa tayi da maganar su Damilola a ranta tace shegu Ashe dadine dashi sukace da zafi.

     Iklas tagama yarda da tsarin da Omar yayi mata,hawayenta ta goge tas,ta kalli Omar da still wasa yake da dukiyar fulaninta,yanzu horney duk abinda akeji a romance din nan haka za a ji in kayi wannan ma?Omar yace Kai...kai...charkwai ai ya ninka wannan sau dubu dubu ke sau million ma,daria Iklas tayi tace Allah ya Omar?da sauri ya gyada mata kai,

      Kunya ce ta kama Iklas sai murmushi takeyi tana shagwaba,har wani kukan shagwaba takeyi ta dan bigi kirjinsa Allah ka cuceni da baka fada min tun da wuri ba,

    Ai da tuni an wuce wajen,daria Omar yayi sosai yanajin shirmen Iklas,

 

       Honey?naam Omar ya amsa yana ta jagwalgwala Iklas, shi yasa Ashe ko wacce in tanayin abun nan sai ajita tayi luf,baka gani ba duk wuyar haihuwa amma mata sai suyi ta girgizo 'ya'ya....Omar yace ai mantawa sukeyi sabo da irin wannan dadin,


   Shi yasa nakeso kema kiji dadinki kullum da kanki zaki dinga nema,bakiga Sahar ta tsaneki ba? Iklas tace ai bata kaunata Sam, ai duk akan wannan ne cewar omar,langabewa Iklas ta karayi tana jin zancen Omar,

     Na shirya kawai ya Omar amma muyi nafeelar kaji,dadi Omar yaji ya gama tsara Iklas ta yarda, a daddafe Omar yayi sallah shida Iklas da Adduo'i


       Iklas a ranta tace tunda da dadi na daina kunya da tsoro,basirarta ta nunawa Omar fagen romance, ta gama rikirkita Omar ya haukace mata abubuwa take masa na fitar hankali,masu wuyar fadi. readers kunyarku nakeji bazan iya fada ba.lol


     Shima haka,lokacin daya buda cinyoyinta ta zata wani salon zai mata har kara gyarawa tayi,wani bala'in radadin zafi taji zirrrrr tun daga kanta har kafafunta,duhu duhu take gani,nan take ta dinga tsandara ihu da kururuwar kuka,gashi ya gama riketa kam aiki yake mata kawai a headquarter, tunda ta cije lips dinta sai da ta fasashi ba tare da ta sani ba saboda masifar da takeji a kasanta,kuka takeyi kamar ana yankata,tana kiran Ummi zai kasheni,ka yaudareni bazan yafe ba,na shiga uku ka kyaleni haka,

      Amma ina Omar harkarsa yakeyi kawai yana sambatun dadi,bakinsu ya hade wuri daya,abin na omar naga ba tausayi waje na fice ina jiyo Iklas na uhmmm.......uhum....uhummmmm saboda Omar ya toshe mata baki da nasa.so take tayi kuka amma ba hakin jin muryar sai su uhmmm..hakan kara tunzura omar keyi,

     

      Tunda ya fara saida ya sauke abunda ya Dade yana damunsa kaf,tun 7:30am yake abu har 11am,shi ji yake ma kamar ya kara yi idan ta huta saboda yanayin da ya jishi ciki,a ransa yana jin haushin kansa da har ya kyale Iklas tayi 3days gidansa bai sha zumarta ba,dama haka take tab lallai yanzu yasan ya auri mace.


  .  Sai yanzu yakewa Sultan da Raj Allah ya isa da basu fada masa cewar Iklas matarsa ce ba tun da wuri.

     Iklas tsoron Omar ne ya kamata,matsowa yayi wajenta da niyyar bata hakuri kar kar jikinta ya fara rawa kamar mazari,dan Allah ka bari....wayyo ni mutuwata tazo..hannunsa ya kai zai daura saman kanta, ihu ta kwala tana gunjin kuka Wanda yayi sanadiyyar  tashin Sahar daga baccin safen da takeyi.


     Da rarrafe Iklas ta sauka kasa,da rarrafenta ta bar dakin a gigice ta bude kofar palonta wai Omar take gudu yau.

     Ya zata dayan room dinta zata shiga Ashe gaba daya ta rude main Palon gidan ta nufa


    Shi kuwa Omar ganin tana tsoronsa sai ya kyaleta yace bari yayi wanka first sai yaje ya lallaso Iklas dinsa,cike da nishadi marar misaltuwa ya fara wanka.


      Iklas karo taci da Sahar, dariar mugunta  Sahar tayi,wayar wuta ta fisgo a jikin TV,tsorata Iklas tayi gashi baza ta iya tashi ba bare ta ceci kanta,


       kafa Sahar tasa ta hankadata baya ta fadi kwance wanwar  daga ita sai yar fingilar  rigarta, ihun ma Iklas ta kasayi nan Sahar ta dinga tsulawa Iklas wayar nan tana taka cikinta da kafa,Sahar ta gane yaune first day din Iklas, bayan ta gama Zane Iklas tayiwa jikinta rudu rudu,kafa tasa ta Mirza saitin gaban Sahar, ai Iklas saida ta suma yafi sau uku tana farfadowa.

 

     Da gudu Sahar ta dauko Almakashi zata fara aske gashin Iklas kenan Omar ya bude kofa daga shi sai wandon shaddar daya sa,ya duba ko ina sashen Iklas bai ganta ba shine ya bude kofar da sauri yana son ya lallaso kayarsa,


    Ai da gudu Sahar ta jefar da Almakashin da wayar TV ta zura da gudu ta garkame part dinta

     Omar ya mike zai bita ganin yanda ta kumburawa iklas jiki da shatin bulala,

   Riko hannunsa Iklas tayi ta masa alama ya sunkuyo da kansa,kunnensa ya kara a bakinta kar kayi mata komai,kar ma kayi mata maganar abinda ta min


    Haba wifey jifa yadda ta miki yau zata bar gidan nan, wallahi baza ta tafi a banza ba sai na rama idan Allah yasa na warke,murmushi yayi ya gano me Iklas ke nufi,in dai kana sona kaji dadin zumata Dana baka dazu to ka kyalemin Sahar har na warke idan na rama kuma ka saketa wlh ko na tafiyata wajen Ummi....kuka ta barke dashi irin azabar da takeji,


    Omar yace ur wish is my command Gomnatina abinda kika ce shi za ayi, ya sureta sai Toilet.





   AsmaBaffa

[9:18AM, 4/21/2018] ‪+234 903 944 2971‬: ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR

         GONNATI

          ⓂⓂⓂ


           155-160


By

AsmaBaffa




     

       Tana kuka yana mata wanka,Haka ya gasata sosai sai sannu yake mata,fitowa yayi tayi wankan tsarki da kanta da sauransu,bedsheet kuwa blood din Iklas ya gama batashi,cirewa Omar yayi har katifar sai da ya dan shafota,liquid soap ya sawa katifar wurin daya baci yasa dan ruwa kadan da towel karami ya dirje wajen tas,

     Hand dried ya dauko ya busar da wajen sannan ya shimfida wani bedsheet din,a washig machine ya wanke bedsheet din ya baza shi,room din ya gyara kamshi ke tashi kawai,Iklas na rike bango ta fito hawaye wani na bin wani,idonta jajir ya kumbura,

   

      Da sauri Omar ya karasa gareta zai riketa tana kuka tace ni....bana sonka...ka daina....ku...lani.ba so...kake... Na mutu...ba...ka...kyaleni....na mutu...ma sai sabon kuka

    Omar ya rasa yanda zai lallashi Iklas,kusa da ita ya zauna bakin gadon,zai fara magana tace ni...ka...kyaleni...dama abinda akeyi a auren kenan ni kam Ummi ta cuceni an bawa shugaban mugaye na Nigeria ni.

    Daria Omar keyi a ransa,haba Gomnatina dadifa muka je nema,hannunsa daya ya daura a bisa cinyarta, daukewa tayi ta jefar da karfi,

    Am so sorry ai kin huta yanzu an bude hanyar next time kece da garabasar,da sauri tace Allah kiyaye,so nake ma ki warke na kunna mana kida ki min rawar nan taki,harara ta balla masa tana ci gaba da kukanta,da kyar ya lallasheta yace, shafa mai mana kimin kwalliya,kuka ne ya taho mata tace ni yanzu ba duniya bace a gabana ba ka daina takura min,kuma ka kiramin Ummita da Suhailata Allah sarki yan uwana


     Sultan Omar ya kira a waya, ya na dagawa yace kai munafuki wlh duk sai na muku rashin mutunci yanda ace kun San Iklas matata Ce amma kuka ki fada min,tun da wuri,dariya sultan yakeyi sosai kai kuma sai yanzu kaji haushin?


     Malam magani zaka kawo ma Iklas bata jin dadi,nan ya labartawa Sultan yanda Sahar tayiwa Iklas,daga nan yace kuma damafa bata da lfy Sultan sai daria yakeyi


    A lallai mutumina Ashe angwancewa kayi dole kaji haushinmu,gaskia Frnd baka da hakuri yarinya ce fa,to malam ina ruwanka in zaka kawo min kazo ko na kira wani,Allah huci zuciyarka gani nan zuwa

    Iklas dai kukanta takeyi a hankali tana goge ido,Omar sai aikin lallabata yakeyi yana bata hakuri,

      Kukanta ta karawa karfi ga abinda kukayi min kai da matarka yanzu kaje ka kara fadawa Frnd dinka sai sun San me ya faru,sorry baby magani zai kawo kin San kuma dole yasan matsalarki.


       Kitchen ya Shiga ya hado mata tea da dambun naman da ta soya jiya,da kyar ta yarda ta ci,tana gamawa Sultan ya kawo magani a compound suka suka hadu ya karbo,wata Riga ya bata tasa marar nauyi,kana ya bata magani ta sha ya shafa mata a shatin bulalar da ta sha wurin Sahar,tare da kwantar da ita,

Kallon Omar tayi tare da turo baki tace kiramin Ummi a waya,to zan kirata amma sai kin daina kuka,hawayenta ta goge  na daina to.


     Ummi ya kira bugu daya ta dauka a ladafce suka gaisa da Omar,yace Iklas ke son magana dake mika mata wayar yayi,cike da rauni tace Ummi ina kwana gaisawa sukayi,Ummi tace ya najiki haka,lfy kuwa?kukan da ya taho mata ta hadiye tace lfy Ummi kaina ke dan ciwon gobe ko jibi zanzo

     Wanne irin zaki zo daga aure wlh kar na soma ganin kafarki gidan mu,duk iskancin da kika dingayi a gidan nan a bar miki mijinki daga kai ki zaki zo yawo,

     Kuje kuji dadinku Iklas ke da Omar dinki,a sanyaye tace dan Allah Ummi to ki turo min dasu suhaila kinji,babu daya da zan miki,ki fita idona wlh na fada miki,tunda muka dawo gidan su Omar kina kula su Suhaila ne?ke ga me miji ko?to baza su zo ba,


      Um...datse wayar Ummi tayi a ranta tana yar cin uwa taji jiki wa ya fada mata.

  

   Kuka zatayi Omar ya girgiza mata kai amma sai da ta saki kukanta,gajia Omar yayi ya tamke fuska Ko ki min shuru Iklas ko na kara yin second rou...kafin yarufe baki tayi shuru tana zare idanu.

     Jinyarta Omar ya dingayi har tayi 3days ta warke sosai har shatin dukan Sahar ya fara bajewa,kula da ita Omar yakeyi kamar kwai babu inda yake fita tunda akayi bikin su sau daya yaje wajen su Mama sai waya.


    Iklas kullum sai tayi waya da Ummi tana roko a kawo mata su suleim,amma Ummi taki yarda da kyar Mama tace Abdallah zai kawosu yau suyi mata yini,Tunda Iklas tasha wahala hannun Omar tsoron sa takeyi ko bed din sai yayi mata Jan ido take hawa,yanzu bata shishigin manne masa sai dai shi da ya zame mata manniru

     Ko yaushe yana jikinta kitchen bedroom etc sha'awarta ce take damunsa kullum da ita yake kwana yana tashi kamar karota akeyi kullum,gashi ko romancing Iklas bata barinsa,

     Da ya kai hannu zata fashe masa da kuka,da kyar ma zata yarda ta kwana dakin,idan kiranta yayi ko wani abun zai karba daga nesa take mika masa ta fece da gudu,ko ta dinga lallabowa kamar barauniya.

     Shi yasa gaba daya Omar ya shiga damuwa,baya jin dadi kwata kwata sai dayayi Dana sanin ma bai kusanci Iklas ba,saboda sha'awarsa ta karu,gashi gudunsa takeyi,Sahar kuwa bakin cikinta yake kunsa yanda take bin maza ya ninka na da,so yake ya rabu da ita kar wani laifinta ya shafeshi amma yayiwa Iklas Alkawarin kyale mata ita.


      Kafin ya cika mata aiki,yau Iklas murna takeyi su Abdallah zasu zo da sassafe ta tashi Omar na bacci ta zame ta hau gyaran gida,kafin kace me ta gama komai,dakin da Omar ke ciki ne kawai ya rage mata jira takeyi ya tashi,


     Tana shiga kuwa taga ya tashi ya shiga toilet,kafin ya fito ta gyara room din sai kamshi,kayan da zai sa ta Ciro masa,yana fitowa yau sabo da murnar su Suhaila zasu zo gashi taga Omar yana fushi da ita yana shareta,shi yasa taje wajensa da niyyar tsane masa jiki,hanata yayi fuskarsa ba walwala,juya mata baya ma yayi, ya gaji da abinda Iklas ke masa da shi yace ta masa guduwa zatayi tana tsoronsa kamar a kanta aka fara,

  

       Abinda yafi bashi haushi gudunsa da takeyi tana nuna tsoronsa take ji kamar wani zaki ko aljani,yanzu dan gulma saboda tasan baki zasu zo tazo wani goge masa jiki,

     Hannu ta mika a sanyaye ka kawo nayi ma,cike da masifa Omar ya kalleta bana so da ke kike min? Shuru Iklas tayi tana mamakin Omar dinta fa biye mata yakeyi,sai abinda take so yake mata,yau kuwa harda yi mata tsawa daga kawai tana tsoron kar ya kara mata irin abun nan,


      Wata zuciyar tace mata ke Iklas kinfa chanja masa irin tsiyar da kika dingayi kullum,baccin kirki bakya bari yayi saboda masifa,bawan Allah ai yayi hakuri,in wani ne fa ta karfi zai miki,amma ko magana bakyaso ya miki ba irin lallashinki da baiyi ba,idan ma baza ki yarda ki kara bashi kanki ba to ki bari mana ya samu nutsuwa, ki kula da mijinki,Omar bai son hayaniya,dama kuma yaya sarai kin San Omar bai daukan raini,ke kadai yakewa haka,yake miki daria saboda yana sonki,idan kikayi sake wata ta kwaceshi da wuri,kuma kinsan ba ke kadai gareshi ba gobe gobe kwananki zai kare ya koma dakin kishiyarki.


       Omar har ya gama shiryawa Iklas na tsaye kamar gunki tana zancen zuci sai ji yayi tace KUTMAR AI WLH BA A ISA BA.shuru ta karayi yana daura agogo yaji da karfi tace KARYANE BAZAN BARI BA,kallonta yayi da sauri yaga dai waje daya take kallon har yanzu,kafin ya ce komai yaji ta kuma cewa MIJINA NA NE NI KADAI harda kwalla zatayi kuka,

     Tsawar da Omar yayi mata ita ta dawo da ita daga tunaninta keee lfy kike kuwa?Omar ya tambaya, kyararrabewa tayi zatayi kuka,omar ya wuceta yana aikine bai isheki ba.

    Na wuce Office ni idan su Abdallah sunzo su jirani kar su tafi,kallonsa Iklas tayi taga yanda omar ya zuka uban kyau kamar zatayi kuka dan Allah ya Omar ka canja kaya kaji?

     Akan me?kallonka fa za a dinga yi..mene damuwarki to?


     To baka ci komai bafa? in na dawo zanci,shagwaba zata fara masa yagafa lallai zata jawo masa jangwangwama, bude kofa yayi zai fita da sauri tasha gabansa, to ko kiss baza kayi min ba?cuno masa bakin tayi gaba,taso bashi daria amma ya fuske tare da tureta ya wuce,

     Sai daria yake a ransa gwara ya daidaita mata sahu.


            Kamar zatayi kuka Haka ta dinga zaga dakin,toilet ta gyara ta karasa komai,duk hankalinta Na kan Omar kar ayi mata snatching, fresh milk kawai tasha da farfesun da tayi,

        Wanka tayi ta cakare cikin wata doguwar rigar material,cike da kasaita ta fito main palon gidan,bata ga kowa ba sai yan aikin gidan,tsakar gidan ta fita tana zagawa tare da yaba tsaruwarsa,

     Sahar fitowa tayi zata wuce wurin aiki ido hudu sukayi da Iklas kallon kallo akayi ko wacce na Harar yar uwarta, sai da Iklas taje jikin kofa tace sai nayiwa ubanki kaciya da kwalaba,ta gudu cikin palon,sashenta ta koma 10mnt latr sai ga su Suhaila sun fado Palon Iklas da gudu.


      Anty Iklas salamualkm munzo, nanfa suka dinga hira Abdallah yace anty nan da 3wks zan tafi Russia karatu,inye cewar Iklas ta shiga yi masa adduar samun nasara.

      Suleim tace anty yau da girkinki zamuyi lunch,

     Suhaila tace ya Abdallah ance fa mu koma da wuri,harara Iklas ta makawa Suhaila look at u kamar ba wajen antynki kikazo ba,ba inda  zaku je sai Honey ya dawo,

  Daria suka sheke da ita baran ma Abdallah yace kai anty ko kunya babu.murmushi Iklas tayi tace yara mu yayyen zamani ne.wata Leda suka mika mata gashi inji Mama. Lallai Ummi bata Baku komai Ku kawo min ba?suka ce ae ya Omar kawai tace mu gaisar banda ke,murmushi Iklas tayi Ku kyale tsohuwa zamu hadu ne.


     Girki ta shirya lafiyayye kala uku sukaci suka sha,Suna ta hira nan sukayi Sallar azahar da la'asar sukace zasu tafi gida,Iklas ta datse kofar dole sai ya Omar ya dawo Baku isa ba,


    Dolensu suka zauna,wanka Iklas ta sakeyi tayi wankan dakakkiyar shadda maroon tasha aiki da farin zare,kafa dauri tayi tayi matukar kyau,sarka da earing duk farare,kamshinta ya cika gidan,

     Omar ne ya shigo da sallama da gudu su Suleim suka rungumeshi,sai bin Iklas da kallo yakeyi tayi tayi kyau ga iya kwalliya,Suhaila tace Anty ga Horney din naki fa,daria sukayi Iklas harda sunkuyar da kai wai kunya,


        Takaddun dake hannun Omar da ya shigo dasu ta karba hade da magazine, ledar hannunsa ma karba tayi ya mata magana a hankali daya tsarabar su Suhaila ce daya taki ce,ya wuce room,dubawa tayi taga wani tsandareriyar sabuwar laptop ta Apple,dayar ledar kuma kayan zaki ne da gani sune nasu Suhaila.Abdallah ta mikawa gashi tsarabarku su Suleim sai murna sukeyi,daya bedroom din ta shiga ta Adana komai ta bishi daya bedroom din hannunta dauke da takaddunsa,karar ruwa taji alamar yana wanka,a drower ta ajiye takaddun,ta karasa jikin kofar toilet din tare da Dora kanta jikin kofar tace honey na shigo na tayaka,daga ciki yake Allah kiyaye min,pls ya Omar bazan wa abarka daria ba,sai dai in zaki bari muji dadi shuru tayi ta dawo wajen su suleim tayi kus, ba a Dade ba ya fito sanye da jallabiya, mikewa sukayi yaya zamu tafi mu,to Ku Mun gode Ku gaida kowa da kowa,sai munzo har mota suka rakasu,


         Kara shirin fita omar yayi Iklas na gefen gado tana kallonsa yafi dazu kyau,wani takaici ne ya tasowa Iklas tasan ma fita zaiyi,maybe zance zaije,kukanta yaji yana tashi kadan kadan,banza yayi da ita yasan me takewa kuka,kofa ya nufa kafin ya karasa ta rigashi ta sa key wlh baza ka fita ba,

   Haka kawai me na maka da zaka dinga azabtar dani,ko abinci kinci kakeyi bayan ka bani wahala rannan matarka ta dakeni wanne mataki ka dauka?shine yanzu zaka dinga min haka.


       A nutse yace me kike so na miki Iklas,tunda akayi abin nan wanne hakuri ne bana baki,ba lallashin da ban miki ba,koda baki bari na sakeyi ba amma ai bai dace ki dinga guduwa ba kamar wani dodo,dan kinga ina sonki ina damuwa,nasan kinyi min kokari amma ke a tunaninki abinda kikeyi ya dace?girgiza kai tayi tace gaskia nasan dai to banyi dai dai ba, Good amma ai sai ki koma normal ko kamar da,mene baki da labari a harkar nan?to ai ni ban San da zafi ba kuma ai Kaine ka yaudareni kace da dadi,

    To ba hakki na bane?nakane mana kuma sai akace kamin mugunta?first ne wajenki dole kiji amma kullum rigimar ki daban a zauna lfy kinki daga kuka sai masifa dare da rana abinda zakice daban.


    A hankali tana cuno baki to ba sai kayi hakuri ba kayi min uzuri amma da wuri har ka dau mataki.wanne mataki?gashi zaka fita da dare,dazu da kiga na fita a office aka kirani,yanzu kuma Sultan ke nema na zamuje gaishe da iyayen budurwar Raj.


        Da Daren nan shi Raj din bai San kuna da mata ba to baza kaje ba gaskia ya canja time ko suje su kadai,me zaki bani idan na zauna? kajika sai zan baka abu ma zaka zauna kawai nace mijina bazai je ba she, gwara ka kirasu a waya ka sanar musu malam matarka ta hanaka fita,daria Omar yayi lallai sannu Mama, nifa ba wasa nakeyi ba cewar Iklas.


      Haka suka dingayi da Iklas ta hana Omar fita,saboda ya Sata farin ciki ya kira Sultan kai nifa wifey ta hana zuwa kuje kawai next time aje dani,Raj ne ya kundumo Ashar dan Kut...uba  mayen mace,sumi sumi kamar Salihi yana maganganun banza sai muzuren banza a waje yarinya karama tana zare masa ido,zamu hadu dakai ne,Sultan nayi Raj nayi,gajia Omar yayi ya yanke wayar,Iklas kanta taji ya kara girma,gaskia ta kai mace,ta hana kuma an hanu sai abinda tace da mijinta,bata San wayo Omar ya mata ba,ba wai zata iya hanashi bane kawai dan ra'ayinsa ne.


      Abinci ta kawo suka ci suka sha,shirin bacci sukayi ta dauko abinda Mama ta aiko dashi ta sha Omar ya jata jikinsa tayi lamo a kirjinsa, yana shafa bayanta yace babyna kin San me? A'a cewar Iklas wacce ke jinta kamar Sarauniya abinda tace shi mijinta keyi


      Ci gaba yayi wifey na Allah ya jarabceni da sonki,har watarana sai inji idan ba Umarni kika bani nabi ba ban jin dadi,ni nafiso a kirani da kan tace in dai a kanki ne,dadi Ya gama kashe Iklas har doro takeyi, ni yanzu a duniya babu abinda zakice nayi banyi ba,

     Shidewa ya farayi wai zaiyi kuka, amma ke abin mamaki akan a bu kalilan jinina saida ya hau,bayan kin San ance a iya first night kadai akejin zafi, ba komai bazan bari na halaka ba, yana maganar ya gama cire mata kaya tik,tana so ta hana tana jin nauyin hakan yanda shi ke bin umarninta ace ita ta kasa yi masa biyayya tir da halinta.


      Bazan miki dole ba tunda gobe kwananki zai kare Sahar ta sama min Nutsuwa, tunda wacce nakeso ta kasa, da Sauri Iklas ta toshe masa baki ta hanyar zura bakinta cikin nasa, tace haba dan Allah honey nafa warke dama tuni, kawai dama nunawa nakeyi ban warke ba saboda irin zafin Dana ji rannan.


      Karki takura kanki baby Sahar na nan gobe, kuka ta fara masa tana ta tirje bedsheet din, ni dai dan Allah ka daina zancen waccen kazo gashi sai yanda kayi dashi,mene bazan ma a duniya ba, kasan kuwa yanda nake ji da kai?





Asmabaffa 


    Ayi hakuri readers nasan kun jira busy nake yaune that's y na barku da yunwa ba dinner da wuri lol.

[9:18AM, 4/21/2018] ‪+234 903 944 2971‬: ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR 

         GOMNATI

          ⓂⓂⓂ   


           160-165

              



By

AsmaBaffa





        Dadi Omar ke ji aransa ya gama gane Iklas cikin sauki yake mata wayo, dan Allah kar ka min da zafi irin wancan cewar Iklas, cike da zumudi Omar ya fara sarrafa ta,hawaye kawai takeyi tana tsoro,yana lallashinta da dadan kalamai ya samu ya shigeta,yau ma taji zafi sosai sai dai bai kai na farko ba,Albarka kuwa ta shata wajen Omar.

       Shi ya mata wanka da komai,sai farin ciki yakeyi,suna kwance saman gadonsu Omar ya kara kankameta wifey me kike so na baki fadi ko mene ne? Tana kukan shagwaba tace ba komai kawai kayi ta sona,sai kuma waccen matar taka ni bazan zauna da ita ba


      Murmushi yayi yace gashi gobe dakinta zan kwana ya kenan,ina Alkawarin da kamin? Cewar Iklas? Tsokanarta yayi nifa bazan iya cika miki ba,nufinka da gaske gobe can wurinta zakaje?sosai ma kuwa kin San ba ke kadai ce matata ba,shuru Iklas tayi sabo da bakin ciki


    Washe gari da sassafe ta rubutawa wani me aiki magani ya siyo mata,lallabawa tayi har kitchen din Sahar ta zuba  maganin a ko wanne ruwa dake a fridge din,da lemuka,


    Tabar kitchen din,Omar ta shirya tsab ta rakashi mota ya wuce Office,Sahar ce ta Fito tana mika ta dauki ruwa a fridge ta kwankwada ta zauna jigib a palonta dan danan kasala ta rufeta ko yatsa bata iya dagawa,


   Gata da ranta da lfy amma kasala ta hanata motsi,Iklas na labe tana kallonta,ruwan ta kwashe du Wanda tasan ta sawa magani ta juye a toilet ta kai robobin dustbin ta zuba sababbin ruwa a fridge din,


  Wayar wuta ta dauka me makon Iklas ta dauki irin wayar da Sahar ta daketa da ita sai ta nemo zallar waya ta karfe murtikekiya lafiyayya,ta dakko almakashinta da sabuwar Reza,

      Sahar ta Samu a palonta tana zaune ragwab,tunda Sahar taga  Iklas da waya tasan yau sai buzunta,ta kula yarinyar nan muguwa ce bata yafiya,

      Gashi ta rasa wacce kasala ce ta sameta haka,nannade hannu Iklas tayi tana sheka wa Sahar Dariya tace yau zaki ci ubanki da mai da yaji,ba a min a zauna Lfy,juyi tayi gaban Sahar tace kalleni da kyau Gomnati tafi karfinki,ke nafiki fa wayeya na fiki gogewa a duniya,na San rayuwa kala kala,ke wlh baki isa kin iya kishi Da Gomnati ba,


      Har kisa hannu ki iya dukana to yau zakiga yanda akeyin duka,tintsuro Sahar tayi daga kujera ta fado Tim kasa,zama Iklas tayi dirshan tayiwa Sahar tsirara tana kyakyata daria daga ita sai bra da pant,a hakanma Iklas tunowa tayi ba kyau kallon tsaraici amma da tsirara zatayi mata 

     Jibi dan nononki kamar kwai gaskia ya Omar yayi hakuri haka yake taba su,


      Hawayene ke tsiyaya idon Sahar saboda bakin ciki gashi ba ta iya ko daga yatsa,wayar karfen nan Iklas ta fara tabkawa Sahar iya karfinta,duk inda ta zuba mata bulalar sai Fatar Sahar ta dauke,ihu Sahar keyi amma Iklas ta garkame kofar yan aiki suna ta so su bude amma sun kasa,Iklas taki dainawa dukan Sahar takeyi iyaka karfinta,babu inda bai farfashe ba a jikinta,ita kanta Iklas  tasha wahala ta hada gumi hannunta sai ciwo yakeyi

    Amma taki bari,tun Sahar na Kuka har tayi Shuru karfin kukanma babu,


       Bayan Iklas ta tabbatar ta rama dukan da yafi Wanda Sahar tayi mata,juyata tayi ta dauki almakashinta ta yanke gashin Sahar kusan gaba daya,Kadan ta bar mata,

      Pant dinta ta janye kasa ta fara tsaga mazaunan Sahar, sai da ta tsaga ko ina a mazaunan,sannan ta kyale Sahar hakan ma wai tausayinta ta ji,tana tsoron Allah,kwashe kayan tayi ta zubar ta kira Omar a waya,a gaban Sahar ta zauna tare da daura kafa daya kan daya.

    Yana dagawa yace wifey yanzu nake cewa zan kiraki ya kike?ina ta missing dinki,me too honey,ko nazo gida ki bani zuma?shagwaba ta farayi sai watarana kullum sai ka dinga yi min way, daria Omar ya saki haba wayo ai kin fini wayo,ni din me honey ai ni yanzu na raina wayona.hirar soyayyarsu sukeyi Iklas tace honey yanzu yau a dakin Sahar zaka kwana? Yeah mene?to ni da wa zan kwana?ke kadai mana,to wai ina alkawarinmu ba nace ka kori waccen shegiyar matar taka ba,ni bana sonta, gwara ka auri wata akan nayi kishi da ita.


    Haushi Omar yaji wato ma bata damu dashi ba,har cewa takeyi ya auri wata.yanzu me kike so nayi miki kawai kazo ka cika min Alkawarina ni,yau nake so a cika min,sabo dame?kuka ta fara Wanda ke Sa Omar zaucewa,ya isa wifey zan dawo an jima kadan sai na cika miki Alkawarin naki.


      Bayan sun dauki lokaci me tsawo suka gama wayar,Iklas bude kofar tayi ta bawa yan aiki damar Suje su gyara palon Sahar,Su gasa mata jiki suyi mata wanka,hakan kuwa akayi Sahar da kyar take takawa,abinci suka bata taci,su Kansu dadi sukaji gwara da ta samu dai dai ita,sai daria sukeyi a boye.

     Baccin wahala Sahar ta dinga yi har 5pm.


       Omar ne ya kwankwasawa Iklas kofa ya dawo da gudu ta dira tsalle ya cafeta har shillata yayi suna daria,sannu da dawowa babyna,bakinta ya shiga tsotsa nan suka dauki lokaci me tsawo sai murza mazaunanta yakeyi masu matukar laushi,


        Wanka sukayi tare suna wasanninsu,saida suka gama komai sannan ta ja Omar har part din Sahar tace cika min alkawarina.

   A kwance Omar yaga Sahar tana murkususun azaba,lfy cewar Omar, da Sauri Iklas tace dukana na rama kar kaji komai cika mata aiki,daria Omar keyi yanda yaga Sahar ta turo duwawu baya,bodo bodo,kallonta yayi maganinki kenan Sahar yanzu kika fara gani,

    Wifey dan bamu waje zamuyi sirri turo baki tayi Allah ni ban yarda ba sai dai ayi a gabana,hade rai Omar yayi ba wasa yace get out da sauri Iklas tayi waje tana buga kafafu

 

Kallonta Omar yayi yana jinjina muguntar Iklas, ya ce Sahar    

Bazan iya rayuwar

 aure dake ba am so sorry gudun daukan zunubi Wanda kike dauko wa kanki kullum kina hanyar bin maza,chance na baki da dama ko zaki shiryu ganin ke me kudice kina aiki salary na shigo miki shine kike take dokar Allah,da aurenki,duk yawon bin mazan da kikeyi ina sane dake, kiwa kanki fada ki tuba,shi yasa maza ke gudun auren ma'aikata saboda da yawan mata basa iya yiwa mazajensu biyayya,ganin Suna kama kudi,kamar yanda kikeyi

        Kina shigar banza ba kamun kai,zantuka barkatai da maza abokan aiki,kawayen banza,kune shaye shaye bin malamai etc,wasu mazan kwadayi ke jawo musu mace ke raina su,shi yasa a zaman aure musamman namu na hausawa ake samun Matsala,wasu matsalar mazance saboda sawa mace ido kan kudinta etc.wasu kuma mafi yawanci matanmu na hausawa su keyin wannan shirmen,negative thinking kikeyi Sahar,sanin kanki bana zalintarki,ba abinda na Gaza miki,ke ga me kudi ko?nafi karfin dukiyarki wlh har nawa take,da ace normal kike lafiya lau zan zauna dake ko da bana sonki, karma kice ko dan mace ko wani zai juyani nayi miki wani abu no,ni kinfi kowa Sanin namijin gaske ne tsayayye,baza ki jefa ni cikin wuta ba Allah ya konani a kan abubuwan da kikeyi,bazan iya hada jiki dake ba,bani da niyyar wulakantaki ko ci miki mutunci,

    takarda da Biro ya dauko ya rubuta mata saki daya, kafin ya mika Iklas ta banko dakin da sauri ta kwace ta jefa mata,ki dauka ki barmin gidan mijina tunda bana uban......Omar ne ya toshe mata baki da tafin hannunsa.


    Shewa da guda sukaji Sahar ta rangada Ayyiriri nanaye banza a banza kai a tunaninka dan na zauna dakai na dawo gidanka?to kayi mushen tunani me kataba yimin?me ka tsinana min,dama dan waccen yar tashar matar taka na dawo kuma ko banza naci uwarta,

     Kai har me kake dashi,dan kana ganinka me kyau,kyau dinka din banza shegu yan bariki,shegiya yar talla a titi duk Mazan tasha sun gama kwakwuleki,

    Iklas ce ta maka mata kallon banza tace Allah kawo sauki honey da alama ta zare fa,ayi maza a sallameta kar ta fara duka da yage yage,


     Duk da ciwon dake damun Sahar sai da tayi kukan kura ta shako Iklas, Omar ya kwace Iklas dinsa tare da dorawa Sahar sabon mari,ya nunata da yatsa ki kiyayi taba jikin mamata,

     Tabe baki Iklas tayi muje me zubin zuma na baka zuma,yau sai ka suma sau 30,tun a first round zaka suma sau 20 daria suka yi gaba dayansu banda Sahar dake huci,Iklas ta nuna Omar da yatsa ta kalli Sahar tace kinga wannan  babban goro sai magogin karfe yafi karfin ya tsoma ya zare yazo nima ya tsoma min,no...no..no kofar dan shi kadai akayita dai dai package dinsa ce.


      Janta Omar yayi muje kyaleta haka wifey,Sahar ce tayi magana,wlh wlh wlh ni Sahar naci Alwashin sai kin bar gidan nan,kuma sai na batar dake kamanninki ma sai su shafe a doron kasa,idan uwata ta haifeni da jini sai na tozartaki a idon duniya,mu zuba ni dake.


     Iklas tace idan kin fasa bakya kaunar Uwarki da tsohon banza,idan kin fasa Allah tsinewa uwarki,naci uwarki a iskanci kawai tsoron Allah mukeyi saboda lahira,na Fiki daba jahilar banza,Iklas duk kurin da takeyi na ganin Omar na kusa ne wai ita shegiya.

     Janta Omar yayi harda kwacewar ka barni da matsiyaciya wai baka bata labarin wace Gomnati ba,ke bafa da iya common hausawa nayi gogayya ba,ki taimakawa kanki ki wuce gidan Ubanki tun kafin na sako wandon ya Omar da  rigarsa na fede miki yan hanji,yanzu na yo waje da kwakwalwarki,

     Iklas harda matsawa jikin Sahar dan taga Omar na kusa tace honey kawo min aska na cirewa shegiya belin gaba.


    Daria Omar keyi sosai ganin yanda Iklas ke kuri Wanda da taga Omar zai yi waje zata rikoshi tana wayancewa,yanzu ma taka kafarsa yayi zai fita carab ta rikoshi dole a gabanka za ayi ita din banza a hankali ba tare da Sahar ta kula ba ta radawa Omar karfa ka tafi Kasan zata iya zaneni.



    Sai da Iklas ta gama kurinta sannan suka kyale Sahar na sake saken yanda zatayi maganin Iklas. Kayanta ta hada kaf ta bar gidan Omar, Sahar na zuwa gida ta shirya karya da gaskia,dukan da Iklas tayi mata cewa tayi Omar ne yayi mata shi.

     Iyayenta sukace baza su yadda ba,nan take suka kira Baffa suka zazzaga masa masifa tare da sanar masa abinda Omar yayiwa Sahar. da kyar ya basu hakuri yace su jirashi next wk zai taso daga Russia.


     Iklas murna kamar ta kashe kanta,daga ita sai Omar dinta,Saida tayi nafeela raka'a biyu tayi musu adduar zaman lfy da karesu daga mahassada etc.

     Omar sai dadi yake ji yanda yaga Iklas na kishinsa da kaunarsa, shi kam yayi dace.

    Wanka Iklas ta sakeyi kamar yar agwagwa tasa dangalgalar rigarta me dogon hannu da Kadan ta haura mazaunanta,ta baza gashin nan malam,

     Yau ba takura main Palo ta rungumo Omar har can,tace zauna oga Honey yau sai ka koshi da rawa, shi dai Omar sai daria Iklas ke bashi,


      Manyan speakers Iklas ta jona da phone dinta zafafan wakokin nja sababbi ta kunna kamar zata fasa gidan, su Kansu ma'aikatan gidan tunani sukeyi yau wanne abin farin ciki ne ya faru a gidan oga haka.


      Baya Iklas ta juyawa Omar Wanda ke hakimce akan akan daya daga kinkima kinman kujerun dake girke a Palon,Iklas rantsatsiyar rawa take takawa Omar ta birgewa me sa nishadi idan kana kallo, rawar kabilun nan take masa iri iri cikin nutsuwa,


      Hip pop dance ta koma yi yanda take karairaya jiki tuni ta kara sacewa Omar tunaninsa gaba daya, kashe kidan yayi ba tare da yace komai ba ya sunkuce abarsa sai bedroom.





AsmaBaffa



  Masoyana duk inda kuke wannan shafin nakune. Ga Iklas dinku fa in action.

    

    Readers ayi min afwa idan nayi mistake ko typing error bani da time ne.

[9:18AM, 4/21/2018] ‪+234 903 944 2971‬: ⓂⓂⓂ

   MA'AIKACIYAR 

       GOMNATI

        ⓂⓂⓂ


        165-170



  

 By

AsmaBaffa




Gaskia kuna birgeni masu commenting masoya wannan novel jinjinata gareku da godiya ba adadi





        

         Bedroom ya direta saman bed yana mata chakulkuli sai daria sukeyi,wani mayen kallon Omar ya mata Wanda Iklas da taga irin wannan kallon tasan me yake nufi,Omar yace wifey tallan nan ya lalataki da yawa ko kunyata ba kya ji,murmushinta me kyau ta saki ka godewa Allah ma Da Allah ya kare maka ni iya haka.

    Ni da ka ganni ba komai ke bani kunya da yawa ba,kuma ma ai watarana ina jin kunyarka,kasan na saba da kai shi yasa bana boye ma komai,tunda kai nayiwa rashin kunyar ai duk daya,zamu ce ta tadda mujemu kai wacce kunyace da kai?


      Ai ban kaika ba ko kafarka ban kamaba,to naji fada min ni wacce rashin kunyar nayi miki ?cewar Omar, kallonsa tayi tare da yin wani fari tana juya idanunta masu rikita Omar,see u kana danne yar mitsilar yarinya a bed kana sambatunka,rannan ma ina jinkafa kyaleka nayi dan kawai naji zafi ne amma wacce kyauta ce baka min ba,gwada masa ta farayi ohhh Baby,my life ahhh na baki garin Abuja ke da kano state ma impact Nigeria du,zan siya miki jirgi,motocina da gidajena,ni darling du nakine sai abinda kika ce.


Dariya Omar keyi sosai karyar da Iklas ta sambado masa yasan yayi sambatu amma bai irgo da cities ba,kiji Tsoron Allah wifey yaushe nace haka?oh to ai lokacin ka bar kasar nan ka Lula dadi world,amma wai

 kana zancen wai a kiraka me kunya,

     Wanne tabo ne ban sani ba a jikinka? Zaka dinga min pretending, ka fito min a Mutum sak ba wani kwane kwane,


     To naji amma ban yarda ba in kin isa  zo a karayi aji idan zanyi sambatu wannan lokacin,ai na daina sambatu,ni kuma nace dole sai kayi,musu ne ya kaure tsakaninsu shi yana a karayi bazai Sambatu ba yayiwa Iklas wayo bata gane ba tace duk da ba dadi nake ji ba azaba nake sha a kara yi yau sai an kure Wanda baida gaskia,kasan kuwa irin sambatun da kakemin har kuka kayi a last da kayi,to yau kace baza kayi ba,

    Habawa malam dole sai kayi Sambatu,yarinya ai waccen dan ban shirya bane amma wannan ba wani sambatu,a haka ya rinjayi Iklas ta yarda ita dole sai ta kure karya,da suka fara ma jajurcewa tayi iya fasaharta ta nunawa Omar wai duk dan yayi sambatu ta kureshi,sambatu Omar Ke mata sosai tana ta Kara jajircewa,ai kuwa Omar bai San kadan ba sai wajen asuba ya kyaleta,baya gajia da Iklas Sam,iklas kam yau sai murna takeyi tana na kureka Allah sai sambatu kakeyi wooooo,ai dama na fada ma nice fa Gomnati Ikon Allah


     Omar murmushi yayi to naji kin kureni ai zan rama ne kema zakiyi fin nawa watarana,suna samun nutsuwa rungume take jikin Omar yana wasa da dukiyar fulaninta,tace honey Kasan me?sai kin fada cewar Omar,

     Hmm Allah kaga na yau da kayi min baka ji ba kamar dadi dadi kuma zafi zafi,sai naji kamar kwakwalwata zata buga,daria ta bawa Omar sosai,Iklas ba ayin 1mnt bata bashi daria ba shi yasa yake matukar kaunarta,tana birgeshi ko yaushe nishadi take sashi,shi yasa ko yaje office baya iya aikin sai tunanin matarsa.shi kadai zakaga yana murmushi.


      To next idan munyi dadin zaki ji gaba daya na fada miki,tab ai kuwa za ajini a makwafta kai na yau ma fa jurewa kawai nayi,murmushi Omar yayi yana bubbuga mazaunanta kamar jaririya yace bacci kinji maza muyi bacci.

    Haka suka kasance cikin jin dadi da kwanciyar hankali har Iklas ta sha fe 2wks gidan Omar.


     Baffa ne ya sauka a gida Nigeria kwanan sa daya yace Omar yazo yana son ganinsa,wankan sukari suka dauka shida Iklas tasa atamfa blue riga da skert, yasa shadda light blue,sai kamshi sukeyi kamar ka sace su ka gudu.wata dalleliyar mota ya zaba cikin jerin sababbin motocin da ya sake dal dal dasu bayan mota suka shiga driver na tukasu,hannunsu sakale dana juna Iklas na kwance a kafadar Omar tana lumshe ido Sanyin A.c na ratsasu,

   Minti kadan Omar zai juyo ya hade bakinsu wuri daya yana tsotsa,haka har sukaje gida,

     Tun daga nesa Iklas ke kwala sallama sai murna takeyi,su Suhaila suka gani Abdallah zai kaisu Islamiyya,da gudu suka rungume Iklas da Omar,Abdallah kuwa a zuciyarsa Yace bari na tsokani ya Omar Iklas ya mikawa hannu wai su gaisa,Omar bige hannun Abdallah yayi yana zazzaga masa bala'i,Mama ce ta fito kai kuma lfy?daga zuwa zaka cika mana gida da fada,Abdallah yana daria kyaleshi Mama wai daga na tsokaneshi,shinefa yake wannan fadan,Dalla malam get lost naga alama baka San me kakeyi ba cewar Omar,

    Da sauri cike da ladabi da kunya Iklas ta duka har kasa ta gaishe da Mama, Mama sai dadi takeji tayi suraka yar mutunci me kula da danta,just 2wks amma Omar har yayi kiba ya kara wani fresh da kyau,


     Da gudu Suleim ta kira Ummi ta fito tana a'a amarsu ce da angon nawa,Ummi ai munyi fushi cewar Omar,haba dai kai ka isa  har kasa Omar ya gaisar da Ummi tana tsokanarsa ango wannan kiba haka kayi wani ja,me Iklas ke baka ne,tsugunawa yayi kusa da Iklas ya rada mata ki fadawa Ummi irin zumar danake sha,hararar wasa Iklas ta yi masa itama a hankali tace Zafa kasa muji kunya,so what?cewar Omar,

    Ummi ce tace halina da yaran nan kenan sai ana abin arziki su fara na tsiya ba kunya ba komai,Mama tace zasu koma inda suka fito yanzu ai idan suka sake.


Iklas harda sunkuyar da kai kasa wai kunyar Mama, Omar zama yayi kusa da Iklas ya dan bigi kafarta da tasa kafar jibarki kamar gaske wai kunya sai gulmar tsiya murmushi tayi ta kalleshi da gefen ido tayi masa signa irin a bari sai mun kebe mu biyu.

     Wurin Ummi Iklas ta matsa yar tsohuwa ya kk,shine kika manta dani ko? Ke rufe min baki ja'ira kin samu miji kin manta da kowa sai mu zamu biki,hira sukeyi sai ga Baffa ya fito daga sashensa, shima yaji matukar dadi ganin Omar dinsa ya samu nutsuwa,zama yayi a daya Daga cikin kujerun palon, cike da ladabi suka gaidashi yana ta samusu Albarka.


      Babana sabo dakai na dawo kasar nan kayi laifi,cewar Baffa yanzu idan banda abinka Babana da hankalinka kayiwa yar mutane duka haka?wannan wacce mugunta ce,ai gwara da saketa ka kyaleta baka daketa ba,ba girmanka bane, iyayanta sun fada min komai nan Baffa ya basu labarin yanda sukayi da iyayen Sahar.

     Ummi da Mama tabe baki sukayi sunji dadin sakin da Omar yayiwa Sahar gwara haka.


      Omar a hankali yace Baffa kasan duka ba halina bane, ba ni na daketa ba,abubuwan da takemin ne sunyi yawa shi yasa na saketa,Ku kanku kuna da labarin abinda takeyi,

     To Omar wa zai daketa idan ba kai ba?ni dan ka saketa bai dameni ba kayi dai dai,babu me iya zama da Sahar tana wannan lalatar.

      Iklas cike da ladabi tace Baffa nicefa na zaneta, salati su Ummi suka saki suna mamaki,Iklas tace Allah Baffa ni bazan iya kishi da wata ba musamman Sahar,Kasan inda ta kamani tayi min duka ta farfasa min jikina ta kalli Omar ko ya Omar?kai ya daga yace ae Baffa Iklas ce ta rama dukanta,

     Murmushi Baffa yayi to taya kika iya dukan Sahar haka,daria Iklas tayi tace Allah dan Baffa bakusan muguntata bane,a ruwa na sa mata kwaya tasha jikinta ya koma weak ko yatsa bata iya motsawa na cika mata aiki da wayar wuta ta karfe,nan Iklas ta bada labari kowa dariya yakeyi yanda Iklas har gwadawa tayi yanda tayiwa Sahar.amma bata ce ta yanka mata mazaunai ba.

     Ci gaba tayi Dama kuma ya Omar yace zai koreta, Baffa ni kuwa na kara zugashi ya saketa, kowanne na dakin mamakin Iklas sukeyi har Omar dan bai San ta sawa Sahar kwaya ba,dama yayi mamakin ya akayi Iklas ta iya yiwa Sahar duka haka,

   Ummi ce ta zubawa Iklas rankwashi rufe mana baki shasha sha marar kunya,wato kai Umaru ina ganinka me hankali shine ka biye wata Iklas ka saki Uwar gidanka,murmushi Baffa yayi a'a Ummi ki kyale min 'yata ni tayi min dai dai,gashi mijinta ya samu kwanciyar hankali.


  A shagwabe Iklas ta ce Baffa ita Ummi fa ta daina so na amma fa baka ga abinda wannan Sahar din ke wa ya Omar ba,Mama ce tayi dariyar jin dadi Omar fa yayi dacen me sonsa tace kai kulemin 'yata tayi dai dai,ni bana fatan hada zuria dasu Sahar Allah raka taki Gona.

    Dadi Iklas taji tana farin ciki tace Allah barmana Mamanmu.

Baffa yace yana daria wato mu a kashemu ko?kanta kasa tace haba dai Baffa ai bamu isa muce haka ba kai gayya ne ai.kai na daban ne.


      Ummi ce ta shige room kyaji dashi ja'irar yarinya,hira sukayi sosai da Baffa sannan ya mike yana na fita ni idan na dawo da wuri shikenan idan kuma ban dawo ba Ku gaida gida,Iklas tace zamu iya jiranka ma Baffa ko kwana zamuyi,da sauri Omar yace kwana fa kikace bada ni ba,to ni sai na kwana cewar Iklas, haba yarinya kafata kafarki da gidanmu zamu kwana gidan wasu,Mama ce ta make Omar rufemin baki marar kunya,ni ban San yaushe ka dawo haka ba wlh,nan gidan ne gidan wasu sabo da kai kayi aure ga me gida ko,ka manta yanda ka dawo ka tare mana anan.

    Allah kyauta cewar Baffa Babana ka fitsare kafarka ya fice suna masa a dawo lfy.


     Saleem Arziki ya bunkasa yayi wata uwar kiba da kyau,sai fantamawa yakeji ya hadu da wata zukekiya chocolate ce me suna JANNAT har an tsai da ranar bikinsu.Ummi sune kan gaba,

    Sahar ta warke sosai inda taci gaba da duniyancinta,kamar kullum wani sabon Alhaji ta samu me kudin gaske Hon.Saminu a wani katafaren hotel dake abuja ta je tayashi kwana,suna room dinsu suna aikata masha'a Hon  ya faki idon Sahar ya zuba mata wani grain magani a gabanta sannan yaci gaba da shagalinsa,

     Bayan ya nutsu wanka yayi yace mata zaije ya dawo,Ashe guduwa yayi,abinda Sahar bata sani ba Hon Saminu hamshakin matsafine,ta hanyar saduwa da mata yake kudin tsafi,

   Bai Dade da tafiya ba ta mike itama tayi wanka ta shirya fes ta kwashi kudin daya bata ta sauka ta hau motarta harda bar masa short note kan bed,na wuce wurin aiki ka kirani a waya.

   Tun da Sahar ta fara tuki wani kaikayi ya fara damunta a gabanta tun tana Susa a hankali ta koma yi da karfi,da kyar ta kai kanta gida,da gudu ta fada palonsu tana ihu da Susa.

   

       Dakin Ummi Iklas ta shiga suna ta hirarsu Ummi na kara Jan hankalinta kan ladabi da biyayya,da kula da miji Iklas tace tab Ummi kina bata bakinki wlh,ai duk na wuce nan wajen a karatuna,ina sonfa mijina taya bazan kula da abina ba na bashi jin dadi,nifa ko yanzu ji nakeyi nafi karfin nayi Aikin Gomnati indai Allah ya horewa mijinka kuma shi mijin yasan me yakeyi yana sauke hakkokinsa yana ma komai na rayuwa dai dai iya karfinsa me zanyi da wani aikin Gomnati

     Kinga Ummi komai tsadar abu yaya Omar yi min yakeyi jin dadin duniya na sameshi shi yasa na sa masa honey zuma zaki Ummi, salati da sallallami Ummi keyi,Iklas ko ajikinta tanawa Ummi daria tace Ummi ni dama sabo daku nake son aikin Gomnati na taimaka mu samu rufin Asiri sai gashi Allah ya rufa mana asiri,komai mun samu,ga karatun Suhaila jibi irin schl din da suhaila ke zuwa me tsada ji sutura ai mu sai godiyar Allah,Ummi tace aikin ma na mata yana da muhimmanci kwarai ta wani bangaren sai dai kawai na wasu bashi da amfani yanda wasu matan ke kauce hanya sabo da Neman kudi.


    Iklas tace kuma Ummi abin haushi wasu idan miji yace su zaba ko aiki ko aure sai suce sun zabi aiki,idan suka kashe auren su fada hanyar banza,wasu mazan kuma suna cikin talauci mace tayi karatunta tana aiki suna rufawa juna asiri sai kiga ya sa mata ido a kudin,ba zaman lfy sai in zata bashi kudi,bayan baya iya sauke mata hakkokinta da Allah yace, matsaloli dai gasu nan Sai Allah kyauta.


      Omar ne ya bar wajen Mama ya dawo wajen Iklas dake dakin Ummi, kwanciya Omar yayi kan cinyar Iklas rashe rashe Iklas harda sukuyawa tana shafa sumarsa honey ya akayi ne,me kake so,Yunwa cewar Omar,da wuri haka bari to na tashi kaji dan babyna iklas ta furta,Ummi sakin baki tayi ta ciro dankwalinta ta makawa Iklas ta kara makawa Omar dake kwance jikin Iklas sai daria sukewa Ummi.


       Marasa kunyar karshen zamani Ku bar min dakina,Iklas tace ba inda zamu bari ma ki gani,mikewa Iklas tayi bari na kawo mana abinci,sai kuyi ai cewar Ummi,abinci Iklas ta kawo musu ita da Omar,sai lallabashi takeyi tana bashi a baki,shi kuwa sai shagwaba yake mata,Ummi na kallonsu tana mamakin rashin kunyar su Omar.


      Mamace ta shigo taga abinda su Iklas keyi Ku kuma meye haka,kema Ummi ki korasu waje mana kika kyalesu,Ummi tace kyalesu wannan yar banzarce Mara kunya fitsararriya tace ba Inda zasu.nazo kiransu ne cin abinci shi ma kamar gidansu har sun ebo suna cin abinsu Mama ta furta,Ummi nuna Iklas tayi da dankwalin hannunta kinga wannan tantiriyarce ta je ta zubo masa jibi abinda Umaru keyi kamar shine macen.

    Ficewa Mama tayi dan ita kunya suke bata.


      Sunayin Sallar azahar Iklas ta koma dakin Mama time din Omar bai dawo daga masallaciba,Mama na ganinta tace wlh fitar min daga daki yanzu zaku zo Ku addabeni,kai Mama bacci fa nazo yi,Ummi ce ta koro ni,zo ki kwanta to ni dama makwafta zan shiga barka yanzu zan dawo,Mama tayi waje tana saka hijab dinta,

     Omar na dawowa dakin Mama ya nufa,Iklas ya gani har tayi nisa a bacci,hawa gadon yayi tare da buga jikin bed firgit ta tashi idonta cike da bacci a shagwabe tace ka dauki hakkina gaskia,bafa zakiyi bacci ba nima haka kike zuwa kina min,mika Iklas tayi me Jan hankali da dare fa baka bari muyi bacci ka barni nayi yanzu dan Allah,

    Ni kin manta har ruwa kike zubamin dan kawai kar nayi bacci.murmushi tayi ta wulkita kafafunta ta daurasu gadon bayan Omar,kai bayanka zaiyi dadin duka,cikin sigar wasa a hankali ta dinga yin chanese da bayan Omar da kafafunta,Omar sai kallonta yakeyi kamar ya cinyeta,tana birgeshi akwai son wasan tsiya wajen Iklas kamar yarinya yar 5yrs.


    Kafafunta ya hade waje daya ya dagesu ya matsa su da karfi saida ta saki Kara tana bashi hakuri,dankwalin Mama ya dauko ya daure kafafun Iklas tam,

      Ya jata jikinsa fitinanniya muyi baccin to gobe zakije schl, yau kuma da dare kin San ba bacci dai.

     Murmushi Iklas tayi yawwa honey irin na jiya za muyi style din kwai sweet,daria sosai Omar yayi yace to karfa ki Tara min mutanen unguwa da ihunki,haba wa ya isa ya toshemin baki dole in sakata in wala wlh harda kukan sweet idan ta kama.Omar ya Riga Iklas bacci lallabawa tayi ta dauki gyalenta ta daure kafafun Omar,dankwalin kanta na atamfa ta cire ta kara daure masa hannaye ta koma jikinsa ta makale sai bacci.

      4:30 Mama ta dawo ganinsu tayi suna ta bacci kowanne kafa daure da dankwali,shi Omar harda hannu ma.


      Dariya suka bawa Mama tana lallai yaran nan naga Alama ciwon hauka ya shigesu,sallah tayi ta wuce kitchen domin shirya abincin dare still su Omar baccinsu sukeyi.

   Ummi ce dake taya Mama girki tace bari na  yaran nan suje suyi Sallah su leka wajen Haj Rahina su gaisheta. Yayi kyau hakan cewar Mama.







AsmaBaffa 


   

    Godiya gareku masu comment. Allah saka muku da alkhairi,ina jin dadi.

[9:18AM, 4/21/2018] ‪+234 903 944 2971‬: ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR

         GOMNATI

          ⓂⓂⓂ


          170-175




By

AsmaBaffa.




    Tashinsu Ummi ta shiga da niyyar yi amma sai ta saki baki tana kalonsu kowanne daure da dankwali,toilet din Mama ta shiga ta ebo ruwa kadan ta watsa musu da sauri suka bude ido,sai yanzu suka tuno a gidan Baffa suke fa

     Ku je kuyi sallah fetsararru  ku shiga sashen Umma Rahina ku gaisheta tana fadin haka tayi waje,Omar kallon hannunsa da kafafunsa yayi yasan aikin Iklas ne ,murmushi ya watsa mata sai ki  kwance ni yarinya, hannun daya daura ya kwance,wai yaushe ma kika daureni ban sani ba,murmushin dake kara mata kyau saki masa kana ta bacci ta fada tana kwance masa sannan itama ta kwance nata kafar,


       Sallah sukayi sannan suka nufi sashen Haj Rahina,dukkansu yan matan Umma suna palonta har Sadiya da Aisha sunzo gaida Ummansu,Iklas sai da ta kara cin Uban kwalliya me kyau,ta kashe dauri tare da kara fesa turaruka,hannunsu sakale da juna sukayi Sallama palon Umma,yuuuuuuu suka zuba musu Ido,Najja ce ta maka uban tsaki tare da Hararar Iklas da Omar,

     Suma kannensu su biyu su Amina harara suke kawai aikowa da Iklas,Sadiya da Aisha sun Lula tunanin duniya,a ladafce suka gaishe da Umma ta amsa kadaram kadaham,ba yabo ba fallasa,duk sauran kannen Sadiya iya Omar suka gaisar,Iklas tana kallonsu bata kulasu ba itama,


    Kallon Amina Iklas tayi tace yan mata an girma sai aure,haka kika kara girma,kallonta ta mayar kan Sadiya da ta yamushe a gefe daya,tace a'a  Ashe kina nan ya kk,ga Maman yan biyu ma,gaskia Aisha kinyi saurin samun ciki,daga kaiki sai ciki.duk wannan maganar da Iklas ke musu Amina karama ta girmi Iklas bare su Sadiya,


      Gaba daya su Sadiya ganin yanda Iklas ta kara komawa,ta mirje ta kara yar kiba,ga kyau komai yaji duk sai suka raina kansu,musamman irin tsadajjiyar atamfar dake Jikin Iklas,sai kallon Takalmanta sukeyi,

     Komai na jikin Iklas unique ne,abin sai ya birge Sadiya da Aisha da suke jin jiki a dakin miji,shi yasa rainin hankalin ma da Iklas tayi musu basu damu ba Sam,sai su Najja yan mata da Amina su suka dauki zafi,ganin sun girmi Iklas amma tana raina musu hankali dan kawai tana auren yayansu,Haj Rahina kuwa sake sake takeyi Aranta gaba daya jikinta ya mutu taga lallai baza ta iya samun Nasara ba,amma zata nemi shawarar kawarta Haj binta.ko da wani taimako da zatayi mata.

    Umma sai mamakin rashin kunyar Iklas takeyi a ranta tace yarinyar nan jaraba ce naga Alama tafi karfinmu.

    Umma ce tayiwa Najja Signa da Ido kan ta rama abinda Iklas tayi musu,a masifance cike da rashin tarbiya Najja tace Ya Omar kayiwa matarka kashedin fada mana magana anyhow,duk cikinmu ba sa'anta,dan kina matarsa bazaisa ki samu damar raina mu ba,banza a banza yar matsiyata daga zuwa cin arziki an mallake mutum da tsafi,


     Aisha ce ta bige bakin Najja dalla rufe mana baki,Iklas tace nafi karfin na tsaya ja inja dake,ta karkace dauri taci gaba baki isa ki kirani yarinya ba,saboda na fiki sanin duniya,yarinya baki San komai ba tunda baki aure ba,Sadiya ce cike da sanyin jiki tace pls a bar zancen ya isa haka kiyi hakuri Iklas ki kyalesu yara ne basu inda duniya tasa gaba ba.daga har Iklas sunyi mamakin Sadiya da Aisha,sun canja kamanni da hali.


    Umma harara ta Dallawa Sadiya,Omar mikewa yayi tare da Jan hannun Iklas ransa bace,Najja ce ta biyosu a baya ta sha gaban Iklas tare da narka wata ashar uban me kika sani a aure, ke karamar yar iska ce, 

     Kallonta Iklas tayi ta dan saki murmushi yarinya kenan,Najja ce ta kara karfin muryarta mene abunda kika sani Wanda ni ban sani ba,me zaki nuna min?

      Iklas a nutse take fadanta silent killer ce,nasan tsayinta nasan kaurinta what of u?oh nasan zaki sani tunda ke taki ba Sadaki kika sani dole kinga da banbanc.....shut up a tsawace Omar ya furta,banza yar Tasha me tallan kwai da Apple cewar Najja,maganar ta konawa Iklas rai,wato Omar ya gama bazawa a danginsa ita tayi talla,ga zahiri kowa idan ya tashi yi Mata gori da yar matsiyata yar talla suke Mata, Sahar ma ta fada mata,a ina sukaji har ta saida Apple da Egg tabbas Omar ne zai fada,wani bakin ciki ne ya lullube Iklas,


     Bata San sanda ta cakumo Najja ba,Omar ya fara tafiya ya zata Iklas na bayanshi sai yaga wayam, hangosu yayi rukume da juna suna dambe, dama ga Najja garin jiki ne da ita narkekiyace ga tsayi ga kiba,Iklas kamar biri ta dafalfale Najja,Najja ce ta dage ta ciji Iklas a hannun da ta shaketa, fatar hannun Iklas ta dauke sai jini,Iklas ma bata bari an shata a banza ba,Najja ta gartsawa cizo a kunne sai jini Shar ta Kunnen Sadiya,

      Samu tayi iya karfinta ta lankwasa yatsan Najja na tsakiya ji kake rukus, da sauri Najja ta durkushe kasa tana wayyo ta ballamin yatsana wayyo Umma na shiga Uku,


     Omar da sauri ya karaso wajen bai wani tsaya bata lokaci ba ya fyallawa Iklas wani lafiyayyen mari,cik Iklas ta tsaya dafe da kunci,Najja na ganin haka tayi luf ta daina kuka sai dariar mugunta ma da takewa Iklas a boye,gwalo tadinga yiwa Iklas,Omar kuwa Najja ya kama ya Mikar ta tsaye,yana antaya mata zagi banza shashasha jaka,dabba wuce ki bani waje kafin na kwadeki,Baku da aiki sai jaye jayen fada da gulma,wlh idan Iklas tazo gidan nan kika kara tararta da fada sai na karyaki haka Omar yayiwa Najja tas,


     Ido suka hada da Iklas wacce har yanzu tsaye take kamar gunki,suna kallon juna Iklas ma tayiwa Najja gwalo ta rama itama harda itama dariyar duk abinda Najja tayi Mata sai da ta rama,Kafin Omar ya juyo Iklas ta Nutsu bai San me sukeyi ba,

     saida Najja tayi nisa ta juyo tacewa Iklas Apple and egg ta shige gida.Omar yayi Dana sanin Marin wifey dinsa da yayi yaga tabbas Najja yar iskace itama,ashe tuggu ta hadawa Iklas dinsa gashi ya jangwalo tsiya,taya zai lallasheta duk da yasan itama wifey din tasa tsokanar tsiya gareta.


      Matsawa yayi wajenta fuskarsa ba rahma yace muje ke kuma ai yana magana Iklas ta rushe masa da kuka ji kake Tim ta fadi kasa tana ta birgima da shure shure,wayyo wayyo wayyo zasu kasheni dangi sunyi min taron dangi,dama ba sona yakeyi ba,yafi son danginsa dani,an zalinceni,zai kasheni,miji me dukan mata aka aura min dama, ni gwara na koma titi talla na,baya tausayina wayyo Allah na tun ina yar mitsilata an fara yi min tabo ajiki akan dangin miji.

    Tsakaninta da Allah Iklas ke shure shurenta,Mama da Ummi sunji kamar hayaniya da gudu sukayo waje, su Umma ma dasu Sadiya duk sun fito,Iklas suka gani tana shure shure Omar na tsaye gefe guda yana tintsira dariya danshi dariya abin nata ya bashi.


      Ummi ce fara magana ke meye haka lfy?kunamace ta harbeki, Umaru mene haka?da Sauri Iklas ta kalli Omar still kuka takeyi,ido Omar ya mintsina mata wai ta rufa masa Asiri.


      Tana sheshekarta tace ba...ba...cinnaka bane ya cijeni,kuma Honey ya kwace min wayata,mene kuma honey inji Ummi, wani farin ciki ne ya lullube Omar shikam abin kunyane ace ya mari Iklas da hannunsa,

     Kowanne cikinsu tsaki yaja Mama tace naga ranar da zakuyi hankali, Ita Sadiya birgeta sukayi ita yanzu ta isa tayiwa Alhaji Balarabe haka.ai ranar sai dai gawarta,gata tana aiki tana daukan salary amma jin dadi da zaman lafiya ya gagareta,duk sun tashi a banza.


     Kowannensu part dinsu suka wuce,Suna shiga Mama ta kallesu Babana fada min gaskia me ya faru ban yarda daku ba,ganin Basu Umma Rahina Iklas tace Mama Najja ce fa ta zageni tace min yar tallar Apple and egg shine mukayi fada amma saboda Ya Omar yafi kaunar danginsa ya mareni a gabanta kalli inda ta cijeni Mama, su biyu suka rufarmin wai su ga yan uwa,Mama wai mutum ya daga hannu ya doki matarsa ta sunna  ai  ya fadi ba nauyi,

     Omar mukus yayi yace Mama..... rufemin baki shashasha sosai Mama taji haushin Omar,fushi sosai tayi da Omar,Ummi kuwa tasan dole Iklas Nada laifi a zancen nan amma Mama taki yarda,duk suna zaune Palo kowanne tsit kakeji in banda Mama da ta dage tana yiwa Omar fada, ka samu mace me sonka haka ka fara shirme akan Wanda basu da makiyi kamarka etc Iklas sai taji bata son fadan da Mama kewa Omar, sai taji ya bata tausayi gashi Mama na fushi dashi,Ummi sai Hararar Iklas takeyi, Omar ne yayi magana Mama kiyi hakuri haka mana,ai duk ita ta jawo baki San tsokanarta ba,duka Mama ta danawa Omar a bayansa, me makon aji Omar yayi kara Iklas ce ta gantsare ta saki kara,tare da cuno dan bakinta gaba Mama dan Allah Ku kyaleshi haka nifa kawai fada miki nayi ba dan ayi masa fada ba,sai dukansa kikeyi kiyi hakuri ki kyaleshi dan Allah mama kinji,Iklas harda marairaicewa,a hankali ta tayiwa Omar magana mu tashi mu tafi gidanmu kawai.hangame baki Mama tayi tana salati,Ummi kuwa daria tayi gwara da tayi miki kika gani,na fada miki yaran nan idan kina shiga fadansu kunya zakiji ba yan goyo bane.


    Mama tace ga zahiri na gani to wlh Ku tashi Ku tafi tun wuri, tunda sukazo suke samu magana kamar yaran goye cewar  Ummi. Da sauri Omar ya mike,Iklas ta dauki Jakarta da gyale  Omar ne yace kuyi hakuri  Mama....Ku je Allah raka taki gona marasa kunya. Iklas sumi Sumi tabi bayan Omar wai ita kunya.


        Sahar ihu takeyi tana kuka da Neman taimako tare da susar gabanta tana kiran Mummy, da Gudu mamanta ta fito tare da Daddy sukayi kanta a gigice,dan danan Mummy ta fara kuka ganin abinda Sahar keyi.

      Sunkutarta Daddy yayi ya sata a mota sai asibiti, sunje an basu gado tare da yiwa Sahar Allurar bacci, amma a banza sai da akayi mata Mayan allurar bacci har 3 sannan aka samu bacci ya dauketa.

      Tubeta likitoci sukayi wasu tsutsotsi farare birda birda cankam a cikin al'aurar Sahar kuka kawai iyayenta keyi, su Kansu likitocin basu taba ganin cuta irin ta Sahar ba.kowa saida ya tausaya mata domin da Allurar baccin ta saketa zataci gaba da ihu da Susa tana birgima, ba irin kudin da Daddyn Sahar bai kashe ba,magani sukeyi both na asibiti Dana gargajiya, amma abin ba sauki, Daddy ya gaji ya maidata Canada can ma ba sauki.


      Tun a hanya Omar ya tsaya ya siya musu gasassun kaji da kayan makulashe tunda suka taho Omar bai kalli Iklas ba itama haka kowanne da tunanin dan uwansa ya masa laifi.kowanne buri yakeyi aje gida ayi wacce za ayi.

    Iklas daya room din taje tayi wanka tayi Sallah tana jira ayi isha tana ta azkar dinta, Omar  kuwa yana masallaci sai da yayi isha ya dawo, Iklas kuwa wata kwalliyar ta tsantara ta hade cikin wando 3qtr fari da T-shirt ja,ta daure gashinta da Jan ribbom jelar gashin na lilo jambaki ma ja.

  Da Sallama Omar ya shigo fuska ba rahma,amsa masa tayi ciki ciki kafarta daya kan tana kallon wani American film a mbc 2,zama Omar yayi a wata kujerar wacce ke facing din tata,sai wani mayen kallo yake binta dashi na so da kauna tare da tsantsan sha'awa. Tasan yana kallonta amma taki kallon inda Omar yake bare ma yasa rai zata kulashi gashi so yake su hada ido amma taki yasan shima yayi laifi kuma mata sai da siyasa ake iya saitasu,dole sai da dabara musamman irin su Gomnati da sukeji da tashen kuruciya.

     Tasan Omar ita yake kallo tana sani ta dinga murguda Baki tana fari,sai murguda bakin takeyi taki dainawa, dariya ke Neman kwacewa Omar, suratul Fil ta karanta ta koma ayatul kursiyyu Omar ya ganeta waishi mayene shine take karatu kar ya cinyeta,

    Baice mata komai ba,ta wani Dora hannu saman dukiyar fulaninta ta kara dagosu Sama ta gyarasu ta kama rera tsohuwar wakar Hausa ta kwalele,ta dauki wayarta tana latsawa ba tare da ta kalli inda Omar yake ba taci gaba da wakarta wata kalar a hankali tace ka gani ka gani kwalelenka. Gani tayi Har yau Omar kallonta yakeyi mikewa tayi tare da yin wata mika wacce ta rikita Omar, tafiya tayi cike da yanga da karairaya ta je room ta jawo ledar naman da Omar ya siya.

      Omar shigowa yayi ya fisge ledar kajin tare da turata baya, a hankali yayi mata amma sai da ta fadi dama a zaune take, Omar kuma a tsugune,kuka ta farayi masa dama Omar hanyar yi mata magana yake nema,zuwa yayi da niyyar lallashinta,ai kuwa  Dane bayan omar tayi saida suka tintsire kasa ta shake wuyan Omar bada karfi ba ita a dole shakeshi tayi wai yaji zafi, chakulkuli ya fara yi mata tana hawaye tana daria,tsayawa yayi yana kallon dariyarta me matukar kyau da birgewa,tsawaya tayi da dariar itama sai kuma ta fara sheshekar kuka kwanciya tayi flat a kansa kamar ta hau katifa,ta rungumeshi kam kam taci gaba da rera kukanta bilhakki tana cewa ka.....ka....ka...mare...ni... Ni.... A...a....gabanta....am so sorry to ya isa indai akan mari kike ta wannan fushin tashi ki rama abinki,ba tare da ta dago ko daina kukan ba tace ai....ai...dan...ka...San...ba...bazan....iya.... Ramawa...bane....murmushi yayi kece wifey ba kya jin magana,yan uwana ne fa,ko ba komai suci darajata,dama....dama...haka zaka....ce mana...tunda....ni....ba...yar....uwarka....bace....lika....maka.... Ni...akayi....shine....ka... Min..... Wayo....ka....gama... Shanye... Min.... Zumata....yanzu....ka....tsaneni...yau Omar yaga ta kansa da Iklas taki shuru,taki tashi daga jikinsa kuma.ci gaba tayi amma..ni..a gabanka tace min...me Apple and egg....to baby am sorry tashi muyi magana haba yan matana, ninefa honey ki.




Asmabaffa



   Tnx alot readers

[9:19AM, 4/21/2018] ‪+234 903 944 2971‬: ⓂⓂⓂ

   MA'AIKACIYAR

       GOMNATI

        ⓂⓂⓂ


         175-180




By

AsmaBaffa






         Ci gaba da lallashinta yayi yanzu fa kika fansoni wajen Mama har dukana tayi kanki kinga kinji tausayina, a kaina kika kekashe idonki gaban Mama ki hanata yi min fada ko?

     Ni...ni... Ba tausayinka naji....ba....kawai...dan kar amana daria ne aji sirrinmu....murmushi Omar keyi tare da shafa bayanta yace a'a gaskia kin kara birgeni ba duk mace ce zata rufawa mijinta asiri haka ba kamar yanda kika min,na gode Allah miki Albarka,dadi Iklas taji tayi abun kirki wai ana yabonta.

      To tashi kiji wata magana,mikewa tayi ta zauna ta tankwashe kafafu kamar me zaman tahiya.


      Goge mata hawayen Omar yayi yana kinga duk kin bata min kwalliyar,hannayenta ya riko gaba daya fuskarsa ba alamar wasa,Wifey in tambayeki? Kai ta daga ae,kina sona kuwa anya?kai ta daga wai ae,magana zakiyi mun,mugun Sonka ma nice number 1 cewar Iklas,Omar ne ya nisa to dole kiso yan uwana,bai dace kina biyesu kuna fada ba,bayan kin San baki da gaskia,yes sun miki laifi kema amma ke kika fara tsokanarsu,ko ba komai duk sun girmeki fa last burn dinta ce kawai bata girmeki ba.


    Kina so ace na auri marar tarbiya da hankali,a'a amma ai dai kasan ni bana tsokanar mutum sai da dalili,kuma ai ma kai na tarewa fada tunda ba sonka sukeyi,to na gode sosai kin kyauta da kika tare min kinji,Allah tsundumaki a Aljanna,tana zuburo Baki tace Ameen,Omar yaci gaba bana son tsokana da jaye jayen rigima kin San fada dasu baya mutuwa fa,to ni tsoronsu nakeji ai ni in fada ma banki mu kwana muna yi ba,kasan sunana kuwa sanda ina jss case buyer ce ni,cewar Iklas


      Siyen fada nakeyi a schl na tarewa mutum a bani kudi,nayi business na fada,to ai naga ke ba karfi gareki ba kuma matsoraciyace tsokana kawai kika iya,dariya Iklas tayi tace lallai na waje baiga gari ba,baka San muguntata bane in na dinga hadawa mutum gadar zare sai ya raina kansa kaga dai yanda na tsillewa Sahar mazaunai ko? to ba komai nayi ba yanzu kawai a nutsatsiyata ka aureni ka godewa Allah da har kai zan hada a marin nan da kamin,yanzun ma kawai dan kai mijina ne kuma kaci sa'a ina sonka .


yanda take tawa Omar kuri sai tsoron tsiya.naji case buyer cewar omar yanzu dai Allah kinji na rantse na kuma ji ko a labari kinyi kokawa da wata musamman yan uwana zaneki zanyi ba mari ba,

        Bakwa son Zaman lfy,yan uwana daban ke matata daban,karama dake sai rigima,idan karfi kikeji,duk sanda kika ji kina jin karfi kizo ki nuna minshi on bed,kuma dole  ki so yan uwana idan basu sona case dinmu daban kema namu dake daban ne, na gama magana.kekebewa tayi zatayi kuka hannunta ya saki je kiyi kukanki ba a jikina ba.


     Ni kuma Marin da kaminfa?haushi kika bani kin bari anji miki ciwo a banza a hannu,jiba hannunki yanda aka cijeshi kin San yanda naji ne danaga jininki na zuba,kai dai kawai kace kafi son Yan Uwanka zaka min wani wayo, sai kiyi kuma ai Omar ya furta, insha'allah ni kuma bazan kara zuwa part dinsu ba,tana dan coko lips tace kayi hakuri Allah huci zuciyarka bazan kara tsokanarsu ba,in dai akan yan uwanka ne, amma bazan zauna dagalolo a dinga cin mutunci na ba,saboda  gani me hakuri,bazan dauki raininsu ba,ni tunda na aureka ai na zama Antynsu amma ko gaisheni basuyi ba,kai kadai suka gaisar,me yasa baka nuna musu muhimmancina ba?idan gaskia kake so a maganganunka,ka fadawa wannan me jikin talo talon indai ko kallona ta kara yi sai na zubar mata da hakoran gaba, daria Omar yayi lallai manya kalli hannunki yanda ta cijeki fa amma kike kurin zubar da hakora.


      Hmmm baka gani ba nima na cijeta a kunne naso na cire mata kunnen du ka wani zo ka bata min shiri.murmushi Omar yayi tashi ki koma yanzu ta balla miki kafa ba ruwana.....daria Iklas tayi tace Allah sai kayi jinyata,nifa a harkar nan banki a karya min hips bama,daria Omar yayi a'a wlh idan zakuyi ayi a ko ina banda hips salon a cuceni.

    Iklas dadi taji yaji tsoro tace ko a yanke min breast dina Hangame baki Omar yayi pls daina yi mana fatan tsiya,ana yankesu garin fada zan karo aure ta kwaceni amaryar,

    Ni kuma na rungume transformer.


      To naji kawai ki kiyaye ko ba komai suci darajata Gomnati case buyer.ga abincin nan to dauka kici ki barshi,fushi tayi tace na koshi,gwara ma kici kafin na miki duren iyamurai,gobe kuma schl zakije ki kwana cikin shirinki,

    Mikewa tayi zata bar dakin ina zuwa?cewar Omar kaya zan canja ok yau duk fushin ne baza a canja nan ba,bata kulashi ba ta wuce,tunda tayi wankan tayi shirin bacci kwanciyarta tayi a room dinta,sai fushi takeyi,Iklas zuciya ce da ita sosai idan aka mata abu bata amayarba sai ya tsaya mata a rai,amma ko bata rama ba indai ta fada ma ka Kasan ranta ya baci to shike nan ya wuce,yanzu ma gani takeyi Omar ya fifita su Najja a kanta,shine tayi zuciya take ta fushi a dakinta,


     Omar shuru shuru yaga bata dawo ba,har shima yayi wanka da komai,yayi niyyar kyaleta sai ya tuna bataci komai ba,kuma shi bazai iya kwana ba Iklas ba,har room din ya bita, ruf da ciki ya ganta ta gaji da fushjnta tayi bacci,tashinta yayi kin San ba a skipping meal gidana tashi muje,ni...a tsawace yace tashi muje ban son shirme,ba shiri ta marzaye tabishi kajin ya tura mata maza kici, kamar zatayi kuka take turawa a baki, sai dayaga taci sosai,brush tayi ya nunama Bed kusa dashi kwanta nan tana daddakirewa taje ta kwanta tayi shuru minti kadan tayi bacci,juyawa Omar yayi tare da makalkale Gomnatinsa.

      Washe gari kuwa tunda ta tashi taci gaba da fushinta,bata magana sai dole,har ya kaita schl da kansa driver ya dawo da ita,gani tayi Omar bai kulata ba shima,

     Tunani tayi kar a kwace mata miji,wayarta ta jawo ta tura masa message ya office?karfe Nawa zaka dawo?miss u.

     Dadi Omar yaji dama ya kasa tabuka komai saboda Gomnati na fushi dashi,Sam baya jin dadin fushinta.

      Shareta yayi baiyi reply ba,Iklas na ganin shuru tace shike nan maybe ya Omar fa yayi fushi dani,kanta ta zubawa rankwashi tana na cuci kaina,yanzu idan yayi budurwa fa,shike nan nice ma da abin haushi wlh,ni wata banza ce sometimes mene na fushi da ya Omar daga ya fada min gaskia,bari kawai ya dawo mu shirya.


     5pm Omar yasa password doorbell tayi kara,fitowa Iklas tayi sanye da wata Riga gaunt iya cinyarta peach color,ta zuba kyau sosai,lekawa tayi taga Omar ne, bude kofar tayi,kamashinta ya daki hancin Omar, Iklas ya karewa kallo ta gama hadewa,

     Fuska ba walwala wai fushi yakeyi shima,a hankali tace sannu da zuwa Honey,yawwa kawai yace zai wuce ta tare hanyar tare da rungumeshi ledojin shopping dake hannunsa ya zubar kasa,jikinsa na mazari ya hau tsotsar Bakin Iklas a haukace,baji ba gani,daukanta yayi har bedroom toilet ya direta wanka sukayi a tare ya kara dakko Gomnati har bed nan ya shiga sarrafata itama haka dan kullum Iklas a karanta yanda ake xxx kala kala take,browsing takeyi amma ba kallon bf ba karanta takeyi step by step shi yasa duk wani new style take gwadawa kan Omar.


     Mamaki Omar keyi yanda take kwarewa a harkar xxx tana iya style kala kala,bayan sun samu nutsuwa suna kwance Omar ya rada mata wai baby a ina kike koyo harkar nan ne?fari Iklas tayi da ido tace wasu a wajen arnan unguwarmu suke labari,wasu kuma browsing nakeyi yanda ake koyawa  theory shine nakeyin practical kanka,


     Daria Omar yayi to anjima practical Nawa zakiyi?kajika ya Omar kwai wayo yanzu fa ka bani wahala amma ai kinji dadi,ai Kaine kana wuta fa.Iklas sun gama Ssce exams sunyi candy,

     Yau watanta Uku Gidan Omar,frnds dinta su angel duk suna kawo mata ziyara watarana,itama Omar yana kaita,haka gidan Sultan ma,Saleem ma da matarsa Jannat suna ziyarar juna,


      yanzu Iklas Satinta 3 kenan tana fama da tashen zuciya sai kwadayi takeyi kala kala,tace wannan tace wancen, ta kara kiba da kyau,kirjinta ya ciko dam,Omar sai kwasar gara yakeyi, ya kara manne mata watarana ma baya zuwa office,

      Zazzabi Iklas ta dan farayi,hospital suka je aka aunata tana da ciki na 2mnths,murna sukeyi sosai,Iklas harda kunna kida tana rawa,tana oh wai nice zan haihu,yanzu zan iya haihuwa,ta kalli Omar dake shafa cikinta, honey ka min ciki,dan Halak dan sunna,gaskia dole dama nayi ciki, baka daga kafa ko na 1day,yanzu idan na haihu dawa zakayi wannan barnan On bed,kai gaskia ya Omar muna goge duniya.rungumeta Omar yayi yanaji kamar ya cinyeta du saboda so gashi zai ga jininsa a duniya shima.


     Washe gari Iklas cewa tayi Omar ya sauketa wajen Ummi,ai kuwa haka akayi yana sauketa ya wuce office,tunda ta shiga dakin Ummi take ta faman shafa cikinta tana murmushi,tabe baki Ummi tayi tace shashasha.

    Minti kadan Iklas tace wai Ummi baki ga komai ba?banza Ummi tayi mata,Ummi yanzu baki gane ba? A hankali cikin rada tace ciki ne dani fa,baki gani ba da akayi scanning daga ganin shape din sa nasan yaron me kyau zan haifo,kamarsa daya da ya Omar daga ganin Alama,Ummi taji dadin Iklas Nada ciki amma tace dama shi kikazo nunawa,to Ummi dan na nuna laifi nayi dan sunna ne fa ba na shege nayi ba,

     Kowa yasan cikin ya Omar ne,da aurena,saima ranar suna za a sha shagali sunan Baffa za a sa masa,to sai ki bari ki haihu tukun tun ciki bai fito ba ake wannan burin?haba Ummi ki mana fatan alkhairi kawai ba ki zauna kina wani kwane kwane ba.

    Allah shiryeki Iklas kinje wurin Mama ae tana kitchen bari naje ma na tayata girki itama taji dadin suruka,taji dumin surukarta,daria Ummi tayi ke naga kara fetsarewa kijeyi kullum.a kitchen ta Tarar da Mama, Suna aikin Iklas tana sani take yatsina fuska kamar zatayi amai,harda ficewa da sauri ta shige toilet din Mama tana kakarin amai wai dan Mama ta gane tana da ciki fa,Mama ce tabi bayanta wai kunya sai sunkuyar da kai takeyi,tana wanke baki wai a dole ta gama amai,Mama sai sannu take mata tana jin dadi a ranta dan ta fuskanci ciki ne da Iklas,

   

     Ganinda Iklas kewa Mama bata gane tana da ciki ba,dan haka tace Mama dan Allah ki sanmin yaji a plate zan sha,yaji a'a sai dai ki canja wani abun banda yaji,'yata Kodai ciki ne dake?da sauri tace ae Mama watansa biyu ma mun Ganshi a scanning kato dashi me kyau ne.


      Dariya Mama tayi Iklas kwai kuruciya naga dai ranar da zaki shiryu.murmushi Iklas tayi ta baje saman kujera ita game ciki,su Suhaila suna dawowa daga schl ta rada musu na kusa haifar muku baby me kyau kamar bature, sai tsalle sukeyi suna murna,Abdallah dake Russia su Suleim suka fada masa.5pm Omar ya shigo a gajiye Iklas ya gani tana cin taliya da manja da yaji,tana kasa zaune ta rarrafo wajensa barka da dawowa Daddyn Baby na,daria Omar tare da cewa na hanaki cin yaji ba kya ji ko,hmm Baby yau ita yake so yaci ba laifina bane.

   Washe gari Omar da Iklas sunje Hospital ganin likita,Sultan ne yace su jirashi yana fitowa yanzu yana duba wata,mutane suka gani damkam a waje masu son ganin likita, wajen mutanen Iklas ta karasa mata,tace bayin Allah sannimu fa,dan Allah Ku bani farar  kujerarcen na zauna abinka da mace me juna biyu bama jure tsaiwa,gaba daya matan wajen daria sukayi sukace amma Sabon aure ce wannan batasan radadin haihuwa ba,da gani ma auren wuri akayi mata yarinya ce.

     Kujera ta karba ta kawo wajen Omar Honey zauna ni na gaji,zama yayi ya jawota tare da dorata kan cinyarsa kowa na kallonsu,

     Basu Dade ba Sultan ya fito shegen gari kana harka suka tafa da Omar,ciki suka shiga amma Iklas tace dole a kara yin scanning taga ya girmansa yake,

    Sultan yace kai mutumina kana fama fa,harara Omar ya watsa masa ina ruwanka kai tayiwa malam kasa ayi mana scanning shine zaman lafiyarka,daria Sultan yayi mijin tace kawai. fadi ka kara Omar ya furta.


     Cikin Iklas ya cika 5mnths ya fito kadan,dawowa Omar yayi ya tarad da Iklas ta ebo yaji tana sha,kwacewar yayi ya zubar dashi yana ta mata fada kan ta daina shan yaji,gani tayi da Omar ya takura mata,komai in tana son ci sai ya hanata wai zai Mata Illa,sabo da wannan dalilin Iklas ta dauki Jakarta ta koma gidan su Omar wajen Mama wai tayi yaji baza ta koma ba sai Omar yazo yayi bikonta,Ummi tayi tayi taki komawa, kyaleta sukayi, 

 

     Kwana 1,2,,3,4,5 shuru taga Omar ko gaida Mama bai zo ba,bai nemeta ba ko a waya tun tana sa ran ganin Omar amma shuru.

    Washe gari sunday 7am tayi shiri tasa driver ya kaita gidanta wajen Omar. Tana shiga ta hau gyara gidan inda yan aiki basa shiga saida ta gyara ko ina kana ta fada  kitchen ta shirya breakfast tana shirya dining, kamshi ne ya tashi Omar wanka yayi ya fito ido 4 sukayi da Iklas tayi wani sabon wankan ta chakare.ina kwana ta gaisar da Omar, barka da zuwa wifey, yawwa cewar Iklas taci gaba I miss u Honey,me too dear nan tayi serving dinsu suka ciyar da juna,sai hirar love sukeyi babu Wanda yayi maganar yajin Iklas,

     Sai shagwaba takewa Omar Honey?naam wifey me kike so,kawai ni kasa naji dadina..murmushi ya sakar mata sai lashe masa kunne takeyi cike da salo,dama Omar kadan yake jira yau kwanansu 5 rabonsu da juna,kamar zasu cinye Kansu haka Duke darje juna a Palo ko bedroom kasa Shiga sukayi.


     Sai da suka gwangwaje da juna sannan sukayi wanka tare nan wani sabon babin murzar juna suka bude,sai wurin 4 suka samu nutsuwa tun safe ake abu daya,shiryawa Iklas tayi taci gaba da fushinta ta dauki Jakarta zata tafi,Omar ya zata Iklas ta dawo kenan Ashe bata huce ba,tafiya zaki karayi kuma?cike da fushi tace Allah kiyaye na dawo da kaina ai class dina ya zube sai anyi biko na ehe.ta fada tare da ficewa driver ya figeta sai gidansu Omar,

     Omar in banda dariya ba abinda Omar keyi akan wai Iklas yaji tayi.

  

     Tana komawa gida su Mama ma sun ganeta wajen Omar taje sai daria sukeyi a ransu,washe gari ma haka ta kara figar gyalenta driver ya kaita suka yini suna sheka love ta shirya tana cika tana batsewa tacewa Omar Allah bamu Alkhairi,yana dariya yace to ki gaida gida.

      Next day da gamma 5pm ta shigo palonta,Omar ta gani yana kallon news a jikinsa ta kwanta ai kuwa ya shiga yi mata tausa saida ta huta kana ta gyara ko ina yana kamshi, tayi musu girkin dare lafiyayye suka ci suka sha,suka shiga aikin Sunna ba ji ba gani,kusan kwana sukayi sannan Omar ya kyaleta badan ya gaji da ita ba,

    Itama Iklas haka bayan sunyi break saida tasa Omar ya kara xxx sannan ta shirya tace na tafi,Omar yayi yayi ta hakura ta zauna tace Sam wlh sai yaje bikonta baza ta dawo da kanta ba,

 

     Dariya Omar yayi sosai yace to ki gaida gida ya zaro bundle na 1k ya bata,tace Allah kara budi,na gode Allah ya kareka daka dukkan masu sharri,har mota ya rakata ta shiga driver ya figeta sai gidan Mama.suka bar Omar yana ta dariya.shima ya shirya ha bar gidan fes dashi.shi kam yajin nan na Iklas gaba ya kaishi ba bayaba, dan sosai take bashi zumarta.




    AsmaBaffa

ⓂⓂⓂ

   MA'AIKACIYAR 

       GOMNATI

        ⓂⓂⓂ


         180-185



By

AsmaBaffa





       8pm  na dare Omar yaga hakurinsa ya kare zama ba Iklas kusa bazai iya ba,gidansu ya wuce,a Palo ya samu Mama dasu Suleim,zama yayi tare da gaishe da Mama cike da fara'a ta amsa,haka su Suhaila suka gaisar dashi ya amsa yana tsokanarsu,Mama ina Iklas?murmushi Mama tayi sai yau kazo bikon? Kai anyi yaji kaki zuwa haka akeyi?

    Dariya Omar yayi wlh Mama rigimarta tayi yawa,bata ji ko kadan watarana sai tayi abu na manya me kyau watarana kuma ta dinga rigima kenan,Mama tayi magana haba Omar yarinya ce kasan fa kowa da lokacin da hankali ke zuwa masa,shi yasa ni bata bani haushi,Mama ni ba haushi ta bani ba dariya ma abin yake bani in ba kuruciya ba wake yaji kuma ya dinga zuwa kullum har girki da gyaran gida takeyi ta dawo,Mama dariya tayi sosai tace shi yasa muke nemanta mu rasa,kaji shiririta ko,aiki ya ganka sai ka bita a hankali,kasan dama yara da suke kan ganiyar girma haka yawanci za kaga sunayi,kaje tana dakin Umminta .


     Mikewa yayi cike da takama yana baza kamshi,a bed din Ummi ya hangota sanye da wata doguwar rigar lace,tayi kyau sosai, tana shan mangoro da wuka a hannunta,har kasa ya rusuna ya gaishe da Ummi,Iklas kuwa kin kallonsa tayi ta kara tamke fuska ita wai anzo biko da kyar zata koma,sai ta ja masa aji.

      A gefenta ya zauna bakin gado,Ummi mikewa tayi ta bar musu dakin,Iklas mangoro dinta kawai take sha,wifey ba gaisuwa Omar ya furta tare da gumtse dariyarsa,banza ta masa,kalar tausayi ya koma ya marairaice mata haba matar so kike na mutu ko?kin tafi kin barni bazan iya rayuwa ba ke ba,kece farin cikina ki taimaka min ki koma ko na sauki,banza tayi dashi haba Maman Babyna.


      Hannunsa yasa ya zuge zip din rigarta yana shafa cikinta kinga sai yau na gaisa da Babyna since how many days yau.

      Bakinta ta cuno gaba ba tare da tace komai ba,fuskarsa ya matsar saitin tata ba tare da ta shirya ba carab taji yana kissing dinta kamar zai cinyeta,kwace kanta tayi da kyar sai fushi takeyi sosai,Omar har ya fara fita daga hayyacinsa,ba wasa a fuskarsa yace tashi mu tafi gida,kafada ta make ya daka mata tsawar da ba shiri ta mike tsaye,duk iya shegen Iklas tana mugun tsoron Omar,hannunta ya kama ya hada mata kayanta a yar Jakarta data dauko ya sata gaba suka fito, ba Wanda ya kulasu sukayiwa su Mama sallama ya zaga ya bude mata mota ta shiga,shi kuma driver ya bude masa ya shiga,suna bayan mota driver ya jasu,Omar sai janta yakeyi da magana amma ita shuru shuru da kyar takeyin Magana sarauta ta motsa.


      Take away ya musu na abubuwan ci suka karasa gida,koda suka fito daga motar daukanta yayi kamar jaririya har bedroom ya ajiyeta bisa gadon sannan yabi lafiyar jikinta ya kwanta rabinsa na jikinta,har nishi takeyi amma batayi masa magana ba,wifey ki huce mana pls bana son fushinki, a hankali tace ni fa ba fushi nakeyi ba,ka dan dagamin jiki zaka kashe min Baby,murmushi Omar yayi ya saba da shiriritar Iklas ko ya idan ta nutsu sai yaga kamar fushi takeyi,baya son ya ganta shuru shuru,yafi so ya ganta kullum cikin nishadi da barkwancinta tana sashi nishadi,sabanin yau daya ganta ba yanda ya saba gani ba,komai in yace sai yaga ba wani surutunta ba labari kawai sai yaga ta yarda,

    Abincima yana sani yasan tana son kaza gashashiya fiye da sauran nama,ko ya kawo naman rago sai yaga taki ci,amma kaji tana ci sosai,

Ko a girki tafi yin amfani da kaji.


   Naman tsire na rago ya mika mata ya dauke kazar yace yau wannan zaki ci,sai yaga ba musu ta fara ci,da ace Dane da tuni ta turmusheshi a kasa tace zata kwace kajin.

    Kajin ya mika mata wasa nake miki ga naki,karba tayi ta fara ci nan ma,da kansa yayi mata wanka ya shiryata,har yau sai ya ganta taki cewa komai,kuma a fuska yaga bata fushi bare yace wani abu.

    Tunani ya farayi anya kuwa Gomnati lafiya take yau,kai da a kwai matsala gaskia.


      Har suka kwanta batayi magana ba,hugging dinta yayi sosai kamar zai tsaga mata kashi amma baiji tace komai ba,kunnenta ya riko da hakoransa ya dan cija kadan still ash...kawai tace tayi Gum.


       cikin salon rada a hankali murya can ciki yace Wifey yau lfy kike kuwa?meke damunki?mikewa tayi ta zauna akan bed din tana cije lips,Lfy wai mene ne?kuka ta barke dashi sosai wannan ba shagwaba,kuka takeyi sosai,

    Gaba daya Omar ya rude ya shiga damuwa wannan kukan na Iklas yasha bam bam da sauran kukanta daya sani ,bai taba ganin wannan kukan na Iklas ba.

    Shigarda ita yayi jikinsa sosai yana tambayarta meke damunta,sai da taci kukanta ta koshi sannan tace Wallahi na gaji da cikin nan,Dan Allah ya Omar kasa a cire min cikin nan,tana kuka tace wallahi ya isheni na gaji dashi dauriya kawai nakeyi.yanzu ma Chinese yake ta min a cikina har ciwo nakeji,duniyar tayi min zafi haka kawai nake jin bakin ciki.

      

       Wani azababben tausayin Iklas ne ya lullube Omar ganin iya gaskiyarta ta fada ba wasa ba shagwaba a cikin zancen.ga wani mugun sabuwar kaunar Iklas data kara yi masa dirar mikiya,

    Cike da lallashi yace kiyi hakuri kinji ai kin kusa haifoshi saura 3-4mnths an wuce rabi kinga an kusa,da ace nasan haka ciki yake wlh da bazan yarda kayi min ba,kayi ta yimin wayo na yarda gashi ni kadai nake shan wahala,Dana yi yaji ma kin zuwa kayi saboda ka samu abinda kakeso,baka damu dani ba,


dama Ashe su Ummi gaskia suke fada min namiji ba dan goyo bane, naki ji na dinga yi musu rashin kunya akanka,da na sani wlh da suka fadamin namiji ba dan goyo bane to da tuntuni Dana goyaka na shiga cikin rana da kai na zame zanin goyon na sakeka a tsaye ka fado ka kwala kanka da kasa ya fashe.sosai Omar ke dariya sai yanzu hankalinsa ya kwanta yaji dadi Gomnati ta samu saukin jikinta,dama shi haka ya saba da Gomnati,bai so ya jita shuru.cike da so da kauna ya dinga bata hakuri baije biko da wuri ba,da kuma cikin daya sa mata yana damunta,dole yasan masu ciki basa jin dadin rayuwarsu.

     Lamo 

tayi tana jin lallashinta da yake tayi da kalamai masu dadin gaske,har ta samu tayi bacci.


    Washe gari da safe bai iya zuwa office ba ganin Iklas kamar bata jin dadi,abincinma shi ya musu indomie suka ci,suna zaune a Palo suna kallon news Iklas na cinyar Omar yana mata tausa ko maganar kirki batayi,zumbur ta mike tsaye wayyo ya fara naushina yau harda kafafunsa yake ta min,dan Allah ka kaini asibiti bani da lafiya,shine lafiyar taki ai wannan naushin da yake miki wannan yana nuni lafiya yake Babyn cewar Omar, zama Iklas tayi tace kai wannan naushin da a fuska ya min da tuni ya fasa min hanci,murmushi Omar yayi ya shiga shafa cikin yana kanafa nausar min wifey daga yau ka dena in ba haka ba zaneka zanyi,dariya Iklas tayi yanda Omar ya dage yana yiwa yaron fada kamar an haifoshi.

    Gobe ne ranar zuwanki awo ma ai ba sai a duba lafiyarsa ba,OK tace Allah nuna mana goben,karar doorbell sukaji,Omar ne ya mike tare da bude kofar,mamaki ne ya bayyana a fuskarsa ganin Sadiya da Aisha yau sunzo gidansa a ransa yace Allah sa lafiya dai,

    Iso yayi musu suka shigo har palon,Aisha cikinta haihuwa ko yau ko gobe,cike da girmamawa Iklas ta tarbesu da fara'a, lemo da ruwa ta kawo musu sannan ta gaishesu,Omar sai dadi yakeji Iklas ta dauki nasiharsa akan yan uwansa,sosai suke hira,sun Dade a gidan,Iklas tayi musu girki sunci sun sha,suna ta jin dadi,Omar ne ya kare musu kallo da gani an San basa jin dadin gidan miji.


      Sadiya fatan dai lafiya kuke zama da mazajen naku,sunkuyar da kai Sadiya tayi cike da kunya tace Hmm kai dai ayi zaman hakuri kawai yaya Omar,amma batun zaman jin dadi babu,ganin maganar yan uwace Iklas mikewa tayi zata bar wajen suyi sirrinsu,Aisha ce tace ina zakije kuma?yanzu zan dawo,no kinga zo ki zauna ai an zama daya haba sai kace wata bare,

    Dole Iklas ta dawo ta zauna,nan Sadiya ta fadawa Omar irin Halin da suke ciki,daga Omar har Iklas sun tausaya musu matuka,dama shi yasa duk me Neman jefa wani cikin masifa kansa zai fada karshe,

     Omar yace amma kun San da haka kuka ki fada a karbo muku hakkinku,Aisha tace hmmmm yaya to ya zamuyi mudai munga rayuwa,Umma ce duk ta jefa mu cikin wannan Halin Dan Allah yaya Omar ka yafe mana,munyi kuskure Wanda a lokacin nutsuwa bata zo mana ba.karma Ku damu kanku ni bakuyi min komai ba,ba wata Matsala kuma zan nemi mazajen naku,haka sukai ta godiya sannan suka shiga motarsu suka tafi.


     Iklas ta kara darasi dama ance duniya makaranta gani ga wane ya ishi wane tsoron Allah.sai godiya take wa Allah daya bata miji Omar,a ranta tace dole na nemo makaman yaki na zaman aure na kara rike mijina,nan take ta buya a kitchen ta kira Angel da princess kawayenta nutsatsu wayayyu,duk da basuyi aure ba tasan suna da hankali,murya kasa tace dan ubanku kuzo akwai matsala dit ta kashe wayarta ta koma wajen Omar.

     Kallonta Omar yayi Gomnati ya akayi ne?yaushe kike so a nemo miki Admission a university? Kai ana ta kai wa yake ta kaya,sai na Haihu Kuma akwai wasu harkoki Dana ke so naga na gama saita su sun hau tsari tukun,

      Ba kya son Aikin Gomnatin ne yanzu,Honey dafa ba yanzu bace nayi hankali tun yaushe yaushe rabon da kaga na dauki jotter ina rubutu,gaskia da nayi shirme Honey.

     Omar daria yake a ransa matar da yanzu ta gama bashi dariya da shiriritarta amma wai kuri takeyi tayi hankali.


     Ibzzy Boy yau Monday sai da ya tabbtar Omar yana Office sannan ya hadawa masu gadin gidan wayo yace Frnd din me gidan ne sako yazo karba,.  

      A Palo yaga Ilkas da cikinta a gaba tana shan water melon da madara,kanta bako dankwali daga ita sai wata dangalgalar riga iya cinya me fadi, wani bakinciki da kishi ne ya kama Ibzzy, Iklas mutum kawai ta gani a kanta,abinda Ibzzy bai sani ba yana shiga ciki securities suka kira Omar a waya suka shaida masa,dama ya bar Office ya kusa da gida yanzu baya dadewa  saboda Iklas cikin yana damunta.

     Minti biyu driver sa ya kawoshi gida,Iklas a gigice ta mike jikinta na rawa ta dauko Hijab zata sa Omar yayi Sallama,Ibzzy da sharbebiyar wukarsa a hannu kamar sabon kamun hauka,da sauri Omar ya kamo Gomnati ya rungumeta kam,itama haka sai rarraba ido takeyi,securities Omar ya kira ya nuna ibzzy da yatsa tunda kai bakin jahili ne ko mahaukacine ban San nufinka kan matata da kake bibiyarta ba amma tunda naga karamin dan Iska ne kai zanyi maganinka,nanfa securities suka kama jibgar Ibzzy, Iklas tace naga dukan wasa kuke masa ku kara sosai,sai da sukayi masa jina jina,sannan Omar ya tsokani Iklas dan yaji kalar muguntarta da take fada tana da ita,wifey a kyaleshi haka?


     Ba ayi masa dukan tsoro da yasa naji ba,nafa firgita yaron cikina sai da ya yi tuntsira gudi gudi.

Omar matse dariyarsa yayi to yanzu me kike so a masa?a balla masa kafar left side,Hannun right side sannan ta radawa Omar ayi masa kaciya da fashashiyar kwalaba sai a kyaleshi sauran kuma Allah ya saka min a lahira.

  Lakace mata hannci Omar yayi yana dariya wifey muguntarki yawa gareta bayan wannan har na lahira kike nema a kara saka mini. 


police Omar ya kira sukayi gaba da Ibzzy Boy.Ibzzy yayi Dana sanin zuwa gidan Omar da yayi,yana kallon Iklas yana ki taimaka min dan darajar Allah ki bawa mijinki hakuri,juya masa baya Iklas tayi tare da kara shigewa jikin Omar tare da cewa gwara ka rufawa kanka asiri ka daina Neman taimakona dama ina jin haushin ka taba kadeni a mota,zan iya sawa a kwankwatsa ma kashin hakarkari,tuni police suka kara rankwala masa Kasan bindiga suka ja shi sukayi gaba dashi.


     Cikin Iklas ya cika wata 9 yayi kato da yawa,kullum sai Iklas tayi kuka da dana sanin biyewa Omar da tayi ta samu ciki,da kyar yake lallabata,ganin gaba daya Iklas bata da sukuni yasa Mama tace dole Omar ya dawo da ita gabansu,Omar haushi yake ta ji shi taya zai rabu da Iklas,bazai iya bacci ba ita ba,itace far in cikinsa rayuwarsa ma kaf saida Iklas yake jin dadinta,yanda Omar ke son Iklas da ji da ita ko kansa baya so.amma Mama tace a kaita gida kuma bama irin 1wk ba har sai ta haihu tayi arba'in,abinda ma yafi kona masa rai ma wai Mama tace bazai koma gidan da zama ba sai dai ya zauna a gidansa shi kadai.shi kam bazai Iya ba.shima dole ya zauna a can tare da wifey dinsa,

     Iklas anyi laushi in ka ganta kamar ba ita ba ta kanta kawai takeyi,ji takeyi kamar mutuwa zatayi,Ashe haka cikin yake da wahala,yau Omar ya hada musu kayansu zasu koma wajen Mama, Iklas tana zaune ta zumbula hijab har kasa don cikin yayi girma da yawa,tayi jigum da ita tana tunanin lahira.

      Duk iyayin nan an ajiyeshi gefe,komai akace tace sai Allah ya saukeni lafiya,amma batun daukan wanka duk har tayi dinkunan suna an ajiye su kala kala.

    Omar ma yakai dinkuna da yawan gaske na Iklas, Baby kuwa yasha ksiyayya wajen Omar tun kafin yazo duniya,suna hangar zuwa gidan Mama Iklas tace a kaita wuse market,Omar ya tambaya me zakiyi a kasuwa,hmmm kai dai kasa driver ya kaini,

    Umarni driver yabi har wuse market Omar zai bita tace kayi zamanka yanzu zan dawo,minti kadan ya hangota a shagon wata yoruba ,sai gata ta dawo da Leda a hannunta.

     Bude ledar Omar yayi ya leka mene wannan black,kwacewa Iklas tayi sabulun salo ne fa baka sanshi ba?me za ayi dashi?jariri akewa wankafa dashi Ummi tace yafi fitar da dirtyn jariri, murmushi Omar yayi lallai kaga me jego nan tanaji kikeyi?kai ta daga masa kawai wai ae.baza a wankemin yaro da wannan sabulun baki ba,in ba dirty zai kara ba wanne dirty zai fitar,cewar Omar.

    Kallonsa Iklas tayi yaronka ko nawa,na sha wahalata na dauki ciki 9mnth na haifi abuna ka nuna min iko a kansa, tsokanarta Omar yayi cikin kasa da murya ke kikayi cikin?itama a hankali yanda driver bazai ji ba tace tare dai mukayiwa juna tunda nima nayi gwagwarmaya,amma tunda kace haka u wl see  bari na haifoshi Allah sai naga dama zaka daukeshi gwara ka lallabani ka fara kamun kafa,dariya Omar yayi iklas abin dariyarta a jininta yake kawai, ta karfi Iklas ta maidashi yaro shima biyeta yakeyi,hannunsa ya sadada ta cikin hijab dinta ya rungumo dukiyar fulaninta,tare da kwantota jikinsa yana wasa dasu, kamshinsu ya cika motar,kallonsa takeyi sosai yanda Omar ke kara kyau kullum,a ranta tana gaskia Allah ya bani miji tab zuki.


       Wasa takeyi da hancin Omar ta lotsashi ta jawoshi,sai rada mata zafafan kalamai yakeyi masu rikita Hankali har suka isa gidan Mama.

     Mama ce tace Iklas da Ummi zasu dinga kwana,Omar bai so haka ba yafi so ace Iklas ta koma room dinsa na gidan inda zai dinga lallabawa wajenta

       Haba Mama room din yayi musu Kadan ta koma part dina,Harara Mama ta zubawa Omar nan take yayi shuru yasan Mama ta ganoshi,Iklas ya dan dungura da kafarsa yana mata signa wai tacewa Mama room guda za a bata ita kadai,kafada ta make wai taki din,Mama na kallonsu abinda sukeyi, kara tabo hannunta yayi wai ta fada,kafada ta make masa, ya nuna kansa wai ni din?kai ta daga alamar ae, tare da sa hannunta biyu a bayanta kamar jariri ta goya tare da taroshi irin kar ya fado ta sauke hanun tai masa alama da yatsa lalala,wai nufinta namiji ba dan goyo bane.

       Da Sauri tayi Inda Mama baza ta gani ba,bata San an ganta ba,Mama a ranta tace ikon Allah yarinyar nan ta fara kunyata ta fara girma,bata San Iklas kawai da dalilinta na yin hakan ba,dan tasan Omar wuya yake bata ne, cikinta ya girma kuma shi bai San kadan ba,ga wahalar cikin dake jikinta ba wata cikakkiyar lafiyace gareta ba.


        Mikewa Mama tayi,yana ganin haka ya matsa Kusa da Iklas yana rokonta ta zabi room ba lallai nasa ba,amma ta zauna ita kadai,hmm dear kenan ka bani tausayi,langabewa yayi  sai rokonta yakeyi ta canja room, saida da ta kalli gabas da yamma kudu da arewa taga ba kowa sannan ta matsa jikinsa tana shafa fuskarsa kayi hakuri baby this time around bazanwa Mama gardama ba,kayi hakuri zaka dinga zuwa wajena kullum muna gaisawa.


      Cike da jin haushi Yace kice kawai baza ki fada ba,amma mene a ciki, su Mama fa wayayyun iyayene, to nidai yau bazan iya ba dan Allah ka dinga salalawa honey cewar Gomnati, a zuciye Omar ya mike ya bar gidan gaba daya.


Iklas tace ka dawo ma ka samenii ,Iklas kanta ta tambaya a fili wai ni mene yake damuna haka ne?wai sai inji  ina ta hankali kullum,yanzu jibi irin  kunyar Dana nuna gaban Mama, lallai idan na haihu haka zan d

 yi,ina share jaririn ina basarwa watarana na hanashi nono,yayi ta tsala ihu sai an hadani da Allah da Manzo.




AsmaBaffa 

  

   Tnx alot, love u all

ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR

        GOMNATI

         ⓂⓂⓂ


          185-190




By

AsmaBaffa.





    

      Omar tunda ya tafi cike da bacin  Rai a zuciyarsa,haka ya koma gida yaji gidan ya masa fadi wayam ba masoyiya, nan ma yaji ba sauki bazai iya rayuwa haka ba,mikewa yayi ya fesa wanka 3qutr yasa da riga T-shirt masu matukar kyau sun dace da jikinsa,gashin nan sai kyalli yakeyi,Omar ba dai kyau ba ,karshe wajen kyau

     Yau da kansa yayi driving shopping mall ya shiga duk abinda yasan Gomnati na so shi ya jidar mata ya siyo mata lafiyayyun gasassun kaji da ice cream ya wuce gidan.


      Sallama dauke a bakinsa ya shiga palo,Ummi ya gani da su Suhaila,Mama na gefe tana waya da Baffa,da Ummi suka gaisa suna ta hira har Mama ta gama wayar,cinyar Mama ya kwanta sai shagwaba omar ke zuba mata kan ta barshi ya zauna gidan,amma Mama bata kulashi ba bare ta bashi amsa,


 Ya rasa me ke masa dadi a duniya,daurewa yay ya cije tare da mikewa,nasu kajin da kayan ciye ciyen ya mika musu,ya kwashi na Iklas yayi dakin Ummi kai tsaye,Iklas na zaune tana bincike a wayarta ya shigo da Sallama yana ta wani cin magani,kamar zai maketa,daria ma ya bata 

     Kallonsa takeyi yayi kyau sosai,sannu da zuwa zumana,ko kulata baiyi ba yayi zamansa gefen bed din yana fushinsa,tana sani tace waya taba min kai ne my soul?a office ne? Harara ya dalla mata,

     Allah huci zuciyarka Ogana idan ma wani ne ya bata ma,zaki sani ne indai nine zan rama,yanzu nan tun akan

Maganar room ce kake fushi haka?kayan ya tura mata ya mike ya koma wajen su Mama ko cikakken minti 5 baiyi ba ya dawo dakin Iklas a fusace cikin fushi yace ke dole fa ki zabi room guda naki na fada miki,

      Kin San Halina a gaban Ummi ba ruwana zan iya hugging naki da wasu abubuwan gwara ki rufawa kanki asiri ki koma wani room din da zama,


    Kallonsa Iklas takeyi da cikinta a gaba har ya gama fadansa,dariya tayi wacce ke kara mata kyau,sai kallonta Omar yakeyi da sha'awa komai na Iklas me kyau ne,baya gajiya da ita,tsayawa tayi da dariyar tace to kullum kullum da katon cikin ma baza ka bari a huta ba,ko tausayina baka ji zama da kyar tashi da dabara amma kai ba ruwanka,yanzu an dawo dani dan na huta jiba yadda kake min rigima,kayi hakuri na haihu nayi Arba'in,a fusace yace au harma arba'in Ashe kece mijin ma,to Honey zoka danneni ka kwata,


     Murmushi yayi Iklas rigima kenan,zaki ga sanda zan danneki ne ai,dan kawai yanzu kinyi nauyi ne dole a biki sannu amma da sai kinyi bayani,nasan zaka iya ai oya zo muci abinci ka daina rigimar kai kasanni bazan bar mijina cikin Matsala ba dole akwai mafita ka daina bata bakinka,nayi yaji ma na nemoka baka zo biko ba bare yanzu da dole nima su Mama sukayi min,Ummi kakata ce ba wata kunyarta nakeji ba,


     Sai yanzu  ya dan samu nutsuwa da farin ciki,matsowa yayi tare da zama gabanta murmushi dauke a fuskarsa zama yayi sosai a gaban yana shafa ckinta,daga bisani ya jawo naman yana yankowa ya sa abakinsa sanna ya hade bakinta da nata yasa mata naman ta cinye tana kada kai uhmmmmm kaji dadin bala'i kuwa,

      Haka ya dinga ciyar da ita har ta koshi,yau Omar a part dinsa ya kwana gidan Mama ba tare da kowa ya sani ba,Iklas kuwa tayi tunanin dama Omar dakinsa zai kwana,dan haka gaba daya tausayinsa takeji hade da wani sabon sonsa,da sassafe ta shirya kanta cikin doguwar rigar a tamfa,sama ya matse kasa ya bude sosai ya boye cikin ta,fitowa tayi sadaf sadaf zata shiga dakin Omar,suhaila ta gani da suleim zazu tafi schl,Anty ina kwana suka gasheta sukayi gaba da gudu,ita kuma ta fada room din Omar a kan bed ta hangoshi yana ta baccinsa cike da nutsuwa,komawa tayi ta sa key a kofar saboda tsaro.


       Tana dawowa ta haura saman bed din tare da rungumeshi kam tana shakar kamshinsa tare da manna masa kiss a goshi,a hankali ya bude idonsa masu matukar kyau,ganin Gomnati a jikinsa ba karamin farin ciki yayi ba.


       Ba tare da bata lokaci ba shima ya Kara manneta a kirjinsa wifey I miss u da kyar nayi bacci jiya,baki zo ba har jiranki nayi,miss u more honey nayi niyyar zuwa bacci ya sace ni,cikinta ya Shiga shafawa ya gudan jini na lafiya yake?haushi Iklas taji yace gudan jininsa wato ya kwace mata mijinta,

      Shinema gudan jinin naka,ni wlh shi yasa banso haihuwar nan ba,yanzu sai ka dinga daukansa ni kana shareni,dariya Omar yayi me kishi da danta haka akeyin Maman babyn?ta tsani danta? Kece fa zuciyata gaba daya,cike da shagwaba tace to ai jini yafi zuciya muhimmanci shine zaka ce masa gudan jininka ni a bani zuciya,saboda ka samu da,fari tayi da ido Wanda ya susuta Omar lokaci guda tare da cewa dadin abin ai kafin ayi dan ni aka samu,kuma ai da nane.


      Dariya Omar yayi kinsan me kike cewa kuwa wifey? Wannan shine ba kano ba birni,ba cinya ba kafar baya, shi yasa tunda ke danki ne kinga shi gudan jinina,ke kuma zuciyata kinga ai kun kwaceni du ke da baby,ni dai Allah ban yarda ba cewar Iklas ,ok to a bashi zuciyar ke gudan jini ko?kafada ta make abinda nafi so zuciyarka shine zaka ce a bashi ita,dariya Omar keyi yace to na bashi liver ta,da Sauri tace tab bai isa ba bazan yarda ba,Kasan kuwa muhimmancin liver da zakace a bashi ita yama fini kenan sosai fa ina laifin ka bashi yar madaciyar jikin hantar taka tunda shi yaro ne,ko ka bashi timbi ko hanji,


Fashewa da dariyar  shiriritar Iklas yayi tare da kara kankameta sosai abin dariyar Gomnati da yawa yake, tafin hannunta ya mannawa kiss yana bin hannun da kiss ya gangaro wuyanta nan ya fara lasar wuyanta cike da salon kwarewa tattare da nutsuwa a hankali ya dinga sarrafata tunaninta ya gushe nan fa suka dinga baje harka,bayan sun nutsu wanka sukayi cike da nishadi,Omar na ta zuba mata albarka, Iklas dinsa dabance,tana shagwaba shi sai abinda yake so,gashi tana fahimtar matsalarsa ko bata so sai ta faranta masa,yanda yake bata wahala bata taba nuna gazawarta,

     Burinta taga Omar kullum hankalinsa kwance,gaban kowa tana nuna rashin kunyarta dan ta faranta masa.


      Har kaya ita ta sawa Omar tare da shiryashi suka fito fes fes dasu,Ummi bataga Iklas ba tunda taga haka to lallai Omar yana gidan,Iklas ta birge Ummi da take kula da mijinta,

      Suna hirarsu kasa kasa murmushi dauke a fuskar Iklas suka shiga wajen Ummi suka gaisheta Ummi tana in kaga Zara kaga wata,suna ta murmushi suka je wajen Mama, tana ganinsu haka taji dadi a ranta amma sai ta tamke fuska ta fara yiwa Omar fada Dama nasan baka jin magana Babana saida ka kwana a gidan nan sabo da mun dauko matarka, ka kiyayeni fa,jikinta ya fada haba Mama nifa gwara ki hakura ki kyaleni dan Allah,Iklas ce tayi magana cike da marairaicewa Mama kiyi hakuri ki kyaleshi.ai na kyaleshi Iklas ya zanyi da shi ya fiye rikici,that's my Mum cewar Omar.


        Kuje ga breakfast can a dining,Mama ta kara da cewa Iklas yan uwanki na kasar Libya jiya sunyi mana waya ni da Ummi,nayi magana dasu cikin harshen turanci duk da ba wani iya turancin nan nayi ba sosai dama Abdallah ke koya min,sunce zasuzo ganinku nan da 3days sai Ku kirasu kuji komai,number tana wayar Ummi,sosai Iklas take Murna ko ba komai yan uwansu zasu zo dangin mijinta su gansu asan suma suna da gata.


Omar ne ya kira yan uwan Iklas a wayarsa suka tabbatar masa nan da 2days gasu nan ganin yaransu,ai kuwa Saturday na zuwa aka tura driver ya daukosu maza su biyu mata biyu,dayar macen Babba ce sosai ta manyanta,dayar kuma budurwa ce yar gidan best Frnd din Baban Iklas     me suna KHAIRAT.

      zankadediya itama,part guda Baffa yace a ware musu shima yana nan zuwa next day zaiga yan uwan matar dansa, Iklas ta rasa inda zata sa kanta sabo da murna,su Sadiya ma sunzo sun gaishesu,bangaren Hajiya Rahina ma an rakasu sun gaisa,ba tare da ta nuna musu wani dan hali ba,su Sultan,Raj,yan uwa da abokan arziki duk sun zo sun gaishesu,haka frnds din Iklas suma,Maman saleem,saleem da matarsa duk sun je.

    Su Kansu mutan libiya sunji dadi sosai,

   

      Khairat tunda Allah yasa tazo gidan tayi tozali da Omar mijin Gomnati taji duk duniya ba Wanda take so da muradi sai shi,dan haka ta like masa ta manne masa,shi kuma ganin yan uwar abin kaunarsa ce Gomnati Iklas sai yake kulata yana karramata,itama Iklas data ga haka bata damu ba tayi tunanin kawai saboda mijinta ne shi yasa take matukar ji da ya Omar,Wanda ita Khairat balarabiyar kasar libiya Sam ba haka bane a ranta tsabar son Omar ne yayi mata yawa,Wanda tana jin baza ta iya rayuwa ba sai da shi,dole sai dai itama ya aureta tunda musulunci ya bada damar auren mata har hudu,

    Shi yasa take Neman hanyar da Omar zai fada tarkon sonta, ita tasan Iklas din Omar ta fita kyau amma dole ne ta sameshi ya aureta.


        Shi yasa khairat Sam bata zama a bangaren da Baffa ya basu kullum tana wajen Iklas saboda taga Omar kullum yana manne da matarsa,shi yasa take nacewa kusa da Iklas,Khairat taga Iklas yarinya ce shi yasa take so tayi mata wayo ta kwace mijin,dan burinta ta dauke Omar su koma kasarsu da zama,Khairat shekarunta 28 dan haka ta girmewa Iklas wacce kwanan nan ta cika 17yrs kwata kwata.


        Shi fa Omar Khairat ta fara damunsa tana shiga rayuwarsa shi da Iklas, ba dama su kebe waje daya sai tazo ta takura musu,dan dai kawai dangin Gomnati ne da tuni yaci uwarta an wuce wajen,

        Amma dannewa kawai yakeyi yana biye mata ganin Iklas bata Nuna damuwarta ba,


      Idan sauran bakin sunce time yayi ya kamata su koma kasarsu fafur Khairat ke hanasu wai a bari suga yar uwarsu ta sauka lafiya wato Iklas,Ummi da Mama sun gano take taken Khairat.

      Omar yaje gidan Sadiya da Aisha ba tare da ya Sanar da kowa ba,ya musu Sulhu sosai da nasiha sosai sun samu yanci mazan nasu sun fara canjawa inda suma  su Sadiya suka kara jajircewa wajen kula da miji,har makaranta ta koyon girki da dabarun zaman aure suka shiga. Har sauran kannansu sun biya musu sun shiga kuma suna ta kula da tarbiyar sauran kannensu tare da yiwa Ummansu Nasiha kuma ta dauka.

    Har wajen Baffa suka je gaba dayansu har Umma Rahina suka bashi hakuri kan abubuwan da suka shuka.


      Haka Maman Omar ma sun bata hakuri Aisha ta haifi yarta mace me suna Mufida, Sadiya kuwa anayin Hutu tazo ta dauki Suleim da Suhaila Suna gidanta suna jin dadinsu dan Alhaji balarabe kashe musu kudi yakeyi yana shagwaba su.


      Mijin Aisha ma Nasihar iyaye data  Omar  sun jawo ya nutsu ya canja hali,sai kiba da kyau da su Sadiya suka karayi. Kullum sai sun Sawa Omar albarka, har Baffa da Umma Rahina suka fadawa abinda Omar yayi musu,haka Mama har Godiya suka Mata.


       Iklas ta shiga damuwa akan Khairat tana shigewa mijinta tayi hakuri tayi kawaici ta gaji haka.musamman da taga Omar na biye mata,shima Omar Haushin Iklas yakeji yaga kamar ta daina sonsa bata kishinsa,tana ganin yanda Khairat ke manne masa amma bata nuna komai,shi kuma kara yake mata kawai,baya ga haka da tuni ya kwadawa Khairat maruka yanda take zama tana goga masa kafardarta a tasa, tana taba jikinsa ko ta rike hannunsa in tana masa magana.ga shi kullum shigar banza takeyi a gidan ko kunyar su Baffa bata ji.

      Kamar kullum yau Omar da Iklas suna zaune a palon Mama sun baje suna cin abinci Khairat ta fito taci kwalliya ta matse cikin Riga yar fingila da wando sai kamshi takeyi, wajen Omar ta nufa tare da zama kusa dashi tana gugan jikinsa, ran Gomnati yayi mummunan baci


    Kishi ya tashi dama ta gaji da halin Khairat,Iklas  wani azababben kishine ke azalzalarta kwakwalwarta ta dau zafi, zuciyarta tafasa kawai takeyi,Omar ya ga halin da Iklas ta shiga amma yace me yasa tun farko bata dakatar da abinba.

    Iklas tana so taga Omar ya matsa amma taga cin abincinsa  ma kawai yakeyi. Iklas a ranta tace kut inama ina da lafiya da billahillazi  sai nayiwa matar nan abinda ko a mafarki baza tayi sha'awar zuwa Nigeria ba,amma zanyi maganinta, maganin shege sai dan banza.

     Gani tayi Khairat ta zuba lemo a glass cup za ta kai bakin Omar,cikin Zafin Nama Iklas tasa hannu ta fisge cup din tare da watsawa Khairat lemon a fuska, ta mike tsaye tare da nunata da yatsa a tsawace tace get out before I scatter your skull into peaces, dama ga su da tsoro Da Sauri Khairat ta fice,Omar zaiyi magana Iklas ta daga masa hannu ya Isheka ya Ishe.....bata karasa ba mararta ta mirde,ta kulle tare da zamgewa da cakudewa. Rawa jikinta ya fara Kar kar kar....... Gumi ne kawai yake keto mata,wani azababben ciwo taji Wanda ko a labari,,films,da mafarki bata taba sani ba,mararta ta dafe ta daddage iya karfinta cikin siriyar Muryarta ta tsandara Ihun daya fito dasu Mama da Ummi daga kitchen a guje.

        Sulalewa kasa tayi tana kuka wayyo Allah na Ku taimaka min,a kaini asibiti na mutu acan,tuni Omar yana kanta shima hawaye yazo masa yana tunanin idan ya rasa Iklas tasa ta kare.


          Iklas ta rike Omar kam yana kiyi addua pls yanzu za a tafi asibiti,tana kuka ta fara La'ila ha illalla la'ilaha ilallah taana rerawa ita kadai yanda zakuru sukeyi kawai kirjinne da bata duka,tuni su Ummi sunyi waje kiran driver,Mama na hada kayan haihuwa,

     Suna cikin mota tana cinyar Omar  kwance su Mama a gefe,Ummi tace dan Allah Iklas ki rufemana baki haka akanki aka fara haihuwa,Omar shafawa Gomnati marar yakeyi yana lallashi tare da tofa mata addua.


         Ciwon ne ya lafa mata suna mota driver na tsala gudu, mikewa zaune Iklas tayi tana goge gumi  tana wash naji salama,suna shiga asibitin ciwon ya dawo yafi na da,cije baki Iklas tayi tana Bala'i.....Bala'i....gashi......nan.....Omar sai hawaye yakeyi yanda Iklas ta haukace gaba daya gashin kanta kamar daga bakin kura ya fito,yanzu bata ma San me take cewa ba,kuka  takeyi tana nishi tana Ku miko min danwake na kwandala,abani ko dan malelene,haka aka turata a gadon  asibiti har dakin da aka kwantar da ita,patients da malaman asibitin  kowa dariya sukeyi da tausayin Iklas yanda take fadan abu barkatai.


    Ummi ce ta kalleta tace yar bantan Uba taji wahala, Mama tace sannu yanzu Likita zaizo, Iklas ta Kalli Mama ta fara tooooooo.......yayi sauri yazo yamin Allura ta kwandala. Shi kansa Omar ta bashi dariya dannewa yayi.


        Ummi ce tsuguna a jikin gadon ai kuwa Iklas Neman abin rikewa takeyi ta tugewa Ummi dan kwali ta jefar,da Sauri Ummi ta matsa ta dauki abinta tana daurawa tace harda ciremin dankwali?Iklas tana cijewa  tace idan....dan kwalin na kwandala ne to a bani......lallai.... Nace a bani.

   Nurses da likitoci sunzo sunce Kaine mijinta? Da sauri Iklas tace yana ina bakin mugu azzalimi,ta fashe da wani  irin kuka me karya zuciya.Omar hankalinsa ya kara tashi gashi kusa da Iklas hannunta cikin nasa amma take  nemansa bata ganeba.





AsmaBaffa 

   

      Ku kwashe min da tafi readers.



Tnx all nayi delay ban cika alkawari ba, amin afwa nima ko ta kwandala ce.

ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR

        GOMNATI

         ⓂⓂⓂ


          190-195




By

AsmaBaffa





    

       Ciwon daya taso ne gadan gadan yasa Iklas ta daina kuka sai muzurai da cijewa kawai kuka ya gagara,likitoci sun bazu a kan Iklas yayinda Gomnati ke sambatu karfinta ya kusa karewa a hankali tace doctor kayi min Allurar guba tunda dai haihuwar nan baza ta zo ba,Omar ya rude addua kawai yake tofa mata,

      Iklas tace Ku fadawa mijina ya yafemin bazan warke ba,irin wannan ciwon nasan sai dai na tafiya lahira,Omar ne ya rungumeta yana hawaye am sorry wifey insha'allah zaki tashi,kan Omar ta shafa tace kamar Omar dina,nine matata Honey dinki ne,kayiwa Mama biyayya sosai,idan baka bita ba dole kaci wutar jahannama,domin bakusan Haihuwa ba.

    Sakinsa tayi,likita yace ya basu waje ga wani sabon ciwon daya taso mata,Ummi tace kiyi fa a Hankali Iklas Maza suna jinki, da karfi tace Maza? Maza basu San Haihuwa ba....wayyo Maza basu San Haihuwa ba.

     Likita ne yace su Ummi su fita duka zasuyi Aiki,Omar yace bazai  yuwu namiji ya duba masa mata ba,dole suka kawo mace da mata nurses,harda shahararriyar nurse din nan Subby,Maman waleeda ma anyi mata Transfer Hospital din ita ce ta karbi haihuwa da gaggawa,Subby ta Daura drip,Hajiya Jamila,Jamila Sule duk a asibitin suke aiki sai kaiwa da kawowa sukeyi wurin Iklas,

   

     Tun safe ake abu daya Har yamma Iklas bata haihu ba,bakar azaba take sha kawai,Subby tayi gumi sosai,Iklas kuwa da taji shuru sai tace kuji na fada muku bazan Haihu ba kawai kuyi min Allurar guba,Omar ya rasa Inda zai sa kansa,Sallah sai da yayi rafkannuwa da yawa,

      Babbar likita King ita ta zo ta kawo wasu dabaru cikin Ikon Allah 5pm kan yaro ya danno kai,Iklass ido yayi jajir yayo waje,ansata nishi ana fush,babu bakin magana ya mutu murus,nishi ake ta sata suna taimakawa,Rabin Rabin jikin Baby yayo waje aka taimaka ya fito du da komai a hannun Subby,

       Zukeken Namiji ta santalo me kama da Ubansa,lafiyayye katon gaske, yaro na fitowa Iklas ta sume, sai da tayi 5mnt ta farfado,nan akayi mata Allurai kala kala,nan danan nurses suka gyara yaro tsab,sannan aka fara yiwa Iklas aikin fito da jinin cikinta tas,tare da gyarata ta Huta sosai sannan Ummi ta shigo ta taimaka mata a bayi tayi wanka sosai ta gasa mata ko ina nan ma Gomnati harda kukan ruwan zafi,kafin su fito room din sai kamshine ke tashi,abinka da private hospital me tsadar gaske kai ka rantse Hotel ne,baza kace a asibiti kake ba,Iklas ita kadai ce a room din ba a hada mutane room daya,kowa da nasa.


         An canja bedsheet ma sabo,tana fitowa suka fada toilet ma'aikata suka gyara shima,kamshin dadi ne kawai ke ratsa ko ina,

   Iklas ta hana a fadawa Omar ta haihu wai sai ta shirya,a cikin jakar kayan haihuwa harda body lotion da su turare,da man gashi da handdrier,wata nurse da tazo domin sauran sun tafi,tace lallai haihuwar fari ce wannan shiri haka.

   

       Aikuwa Iklas ta busar da gashinta da hand drier ta tajeshi tsab ta shafeshi da man gashi me kamshi,da turaren gashi ma aka shafa,tea ta sha me kaurin gaske,sannan taci kaji da sakwara miyar egusi,Omar kuwa tuni Subby ta fada masa ta Haihu lfy amma ance ya jira za a kirashi,ai kudi ya zaro wanda bai san yawansu ba ya bawa Subby yar Albishir,sauran nurses ma kawai kudi yake ta fella musu,


har yau shuru,har yayi Sallar isha yana jira,Iklas zama tayi ta shafa body lotion dinta me arnen kamshi,

      Ta sa Wani Sabon dinkin doguwar rigar material black and milk yayi mugun mata kyau,sama ya dame kasa ya bude,Gomnati fa ta gaji amma haka ta dage tana kwance ta shafa powder ta,ta sa red jambaki,kamar ba ita ta haihu ba,

       Dagwas da ita tana kwance Ummi ta mika mata turaruka ta shafa wasu ta fesa wasu,kamshi takeyi na fitar hankali,jariri kuwa tuni Mama ta goge masa jiki da zaitun bayan ya dan dade akayi masa wanka tas dashi aka shafa masa lotion irin na jarirai masu matukar tsada da kamshi Omar ne ya siyosu tun cikin Iklas na 7mnths,kaya masu kauri da pampers aka sa masa suma kayan sai da Mama ta shafa musu turare kafin a sa masa


        Yaro gwanin sha'awa,sai da komai ya zama normal sannan a hankali Iklas tace Ummi a kira min ya Omar, Mama sabo da Murna duk ta kira mutane ta sanar musu,Iklas ma haka,Omar kuwa bai kira kowa ba yafi so yaga Halin da matarsa ke ciki.

     Yana zaune Ummi baki har kunne tace shigo Umaru,ai Omar ya Riga Ummi shiga dakin,mamakine ya cikashi,bai zaci haka zaiga Iklas ba.shi gani yayi ma ta kara kyau,sai yar ramar wahala da tayi kadan,ga kamshi da take zubawa,tuni Mama da Ummi sunyi waje sun basu waje,Omar ya rungume Iklas murna ta hanashi sukuni,sannu my sweet heart,kinsha wahala,har mamakin Murnar Omar tayi.

      Kisses ya dinga manna mata tako ina,kamar zai cinyeta sai sinsinar kamshinta yake tayi kamar zai zauce,yaron dake gefe ya dauka yayi masa Addua sosai sai kallon sa yakeyi ba kifta ido,zama yayi gefen Iklas yaron na jikinsa Kara kallon yaron yayi ya kalli Iklas tare da cewa amma wannan yaron na Kwandala ne ko?dariya sukayi gaba dayansu,tana dukan Omar a baya cike da shagwaba,


      Sai kunyar abubuwan dayi takeji a gaban mutane,yaro ya dara alamar Neman Nono,wifey nono za a bawa intestine tunda kince a bashi hanji,murmushi tayi tana shagwaba tace ni... Sai..na huta bacci nakeji,ki bashi mana yasha sai kiyi baccin, a'a ruwan nono bai zo ba fa,a bashi zam zam yasha kawai,dole Omar ya bashi Zam zam.ita kuma tana ta baccinta.


      Sai da ta kwashe 8hrs tana bacci,Omar har yaje gida yayi sabon wanka ya dawo,Mama tace Tunda kinci abinci yanzu ki bashi yasha mana kinga har ya fara kuka,a bari na kara yin wanka Mama, wanka tayi ta canja wata shigar ta lace Riga da skert cib ita,kamar dazu haka ta kara hadewa,

 

       Yaro sai kukan yunwa yakeyi,Omar ya shigo room din me ya sameshi haka?Ummi ta bata fuska gata nan taki bashi nono, daga tace wancen sai tace wannan,Mama ce tayi waje tana amsa wayar Baffa,cike da Fushi Iklas ta kalli Ummi ni... Nifa.. Nonona zubewa zaiyi ya lalace,kuma mijina fa?salati Ummi tayi,Omar kuwa dadi yaji ana ji dashi,ya zauna gefenta da sigar lallashi yana Haba wifey ai duk daya ne ni da shi,kinga shima yasha Nima a boye min nawa,bazai yi komai ba in dai ana kula dashi,


      Tana kunkuni ta dauki Baby ta saka Hijab ta boye sannan ta fara bashi,yana zuka tace wayyo Allah,Omar yace mene rada masa tayi a kunne tana cije lips wannan da zafi wahala yake bani ba irin naka yakeyi ba,dole ayi masa fada,murmushi Omar yayi yace yes ai ni na musamman ne kalar nawa daban,,Iklas tace cikin rada shi yasa nace kar a bashi gudan jini ko heart a kaishi wajen madaciya,ko hanji.


      Haka ne my love,Ummi ce tace munafukan banza aikinku kenan,ke harda boye nono kar a gani ko,Iklas tace ae Ummi abina me daraja ne,nufinki in dinga kwayeshi gaban kowa nasan muhimmancinsa.


        Ke ni kar ki isheni da Surutun tsiya dazu kika gama kururwa da kuka,sambatu ba Wanda baki ba kin samu kanki yanzu kin ishe mu,Omar waya yake ta kira cike da zumudi an haifar masa a bouncing Baby Boy,

        Mama tace kar a sallamesu sai gobe Iklas tayi bacci ta huta.


       Ibzzy Boy yan  sanda sun masa jina jina yayi nadamar halinsa,yayin da ya shiga taitayinsa,da kyar aka karbeshi.ya tafi cike da nadamar rayuwarsa ta baya,sai Istigifari yakeyi.

       Sadiya ta samu kiran gaggawa daga Office dinsu tana zuwa aka mika mata takardar sallama daga wajen aikinsu,saboda taci bashinsu masu matukar yawa na company taki biya,Sadiya tayi nadamar irin karyar da suka shirya a bikinsu domin da kudin ta ranta ta kara,

       Tayi kuka ta gode Allah,tana Oh nasan wannan hukuncina nake karba sanadiyyar abubuwan da nayiwa su Ya Omar,ya zama dole na fada musu abinda muka shuka.

      Aisha kuwa yarta da ta Haifa yanzu an gano tana da sickle cell,wato cutar sikila,kullum a hospital suke suna kashe kudi,basu da kwanciyar hankali.


     Dama shi laifi in kayi watarana ma sai ka shiryu ka daina sannan a fara jefo ma kaddarori,to su Sadiya karba tasu sukeyi tako Ina,addua kawai sukeyi,sun tabbas hakkin Mama,dasu Omar ne yake binsu,

         Dan yanzu haka Sadiya hawan jini ya shigeta,an dorata akan magani.Hajia Rahina da kawarta Hajia Binta sun shirya zasu je ayi musu wata addua wurin malam ,saboda abinda ke fadowa Kansu na masifa.

    Suna hanyar Nijar wasu yan fashi suka taresu a mota suka karbe kudaden tare da yi misu fyade sannan suka harbesu a kafafu da Hannu,driver kuwa basu kulashi ba ganin shi talaka ne,shine ya buga waya ya fadawa Baffa yayin da saura 4days sunan Baby na Omar.haka aka kwasosu ranga ranga rai a hannun Allah.


      Asibiti aka wuce dasu ,a wulakance,rai a hannun Allah,dama ita duniya dai dai take da kowa,mutum yayi ta shuka tsiyarsa,rana daya Allah ya maidashi ba kowa bane,kyashi,hassada,bakin ciki,gulma,cin amana ta ko ina sunyi yawa a alummarmu ga jarabar son abin duniya,kowa burinshi yaga yafi kowa.Allah kyauta.


      Sahar kuwa an gaji an dawo da ita gida,ta fige,ta yage,tayi baki,kai ba Wanda ke gane Sahar yanzu ta dawo kamar kwarangwal,tsoron zuwa dubiyaa akeyi ma,malamai sai aiki sukeyi a kanta ba dare ba rana.dama duk wani iskanci da mutum keyi lafiya ce tayi masa waya,yau gashi halin da suka fada.

        Muji tsoron Allah don yanzu tun a duniya ake karbar saka mako.


      Bayan an sallami su Iklas,suna gida an cika ana zuwa barka kungiya kungiya,Omar yana dakin da aka bawa Iklas kullum yana tsakiyar Bed shi yake mika jariri,Mama ce take korarsa amma ya nace a room din.

      Masu ganin jariri sunyi saukin zuwa,Baffa yazo Room din Iklas ya daukeshi cike da farin ciki,sai addua yake zuba ma jaririn.Iklas yanda take daukan wanka kamar zata party kullum,kai kace bata haihu ba,kullum sabon kayan da Omar ya dinka mata wajen set 20 dasu take cakarewa.kamshi na gaske ke fita a ko ina na jikinta,haka Baby ma kana gani kaga yan gayu ne iyayensa.

       Kullum Ummi ke yiwa Iklas wanka ta gasata sosai,ita kuma Iklas anayin wankan tana kuka,tun kafin ma aje wankan take fara kuka.

     Me gyaran jiki ta biya kudi ake mata kullum,sai kace zatayi bikin aure,

     Khairat suna nan suma sunga jariri,ganin Iklas na busy ta kara likewa Omar,Iklas kuwa hankalinta na kan mijinta tana kallon abinda Khairat keyi.

     Angel kawar Iklas ce tazo ganin jariri tace Gomnati ya haihuwar?kallonta Iklas tayi tace keeeeeee Marododo kenan,kinji azaba wlh kubi uwarku na fada miki ki dage da yiwa mamanki biyayya,sai yanzu naga muhimmanci uwa,ke ni yanzu da Mahaifiyata tana da rai ai da taga biyayyar da bata taba gani ba.

    Duk inda ake tunanin ciwon ya wuce tunanin me tunani,duk inda zan miki bayani baza ki ganeba Angel,ki bari sai kinyi kya ji.

     Wani duhu duhu na dinga gani,ke nifa ban San sanda na koma ganin Hoton kwandala a idona ba,Angel tace kwandala?abinda ba wani amfani ake dasu ba yanzu amma kika ga pic din kwandala,Iklas ta gyara zama tace to wlh kwandala na dinga gani a cikin idona kawai,sai kuma naga danwake da danmalele,ke harda dankwali Ashe na Ummi ne.


      Kinga da dan nan ya fito wani duhu na gani duf sai naga wani kwan fitila yayi flashing wall wal,kinsan irin fitilar da can da tsofaffi suke durawa kerosine?Angel tace yeah tace to irinta fa na gani Dana fara farfadowa,Ashe kwan nepa ne.Angel sai dariya take mata.


      Omar ne ya shigo da jariri ya mikawa Iklas lokacin Angel tana sallah,zama yayi zai fito da nono ya bawa jariri Da sauri Iklas ta dafe Rigarta miko min Hijab,ke wifey kawarki ce kawai a room dinfa kuma sallah takeyi,ae ni dai ka dauko min,dakko mata yayi tasa ta fara bawa jaririn nono, Omar dage hijab din yayi ya shige shima ya kwanta a cinyarta,Jariri na shan nono Omar na kan cinyar Iklas tana shafa masa gashinsa.

      Da dare Iklas ta fesa wanka ita da jariri ta sashi gaba cikin haske ta kura masa ido kurrrrrrrrr ko kiftawa batayi,har Ummi ta shigo bata San ta shigo ba,tana ta kallon Baby tana murmushi ita kadai,afili ta fara maganganunta Kai yanzu Allah ni na haifeka?kato dakai amma ka fito ta wannan yar kafar kofa?kalleka me kyau,gaskia Ina sonka,ina sonka,nafi kowa kaunarka a duniya,Allah raya min kai,ka zama dan albarka,dagashi tayi sama tana ta kissing dinsa ta ko ina ba ji ba gani,Ummi ce ta katseta ina jin dai Aljanu sun shigeki ko?Murmushi Iklas tayi tare da kwantar da yaron,Ummi Allah dan Boy din nan yayi kyau da yawa,kalli hancinsa irin na honey. Ummi wai kamar ni amma ina da haka,gaskia na samu abokina,rufemin baki sakarar banza cewar Ummi.


      Shi Omar yanda Iklas ke chake gayu ne yake birgeshi,ta haihu kullum busy amma tana kula da kanta,shi gani yakeyi har tafi da kafin ta haihu daukan wanka da komai da komai.

     Kasancewar Hajiya Rahina na asibiti Iklas batayi taron suna ba,yaro yaci Sunan Baban Iklas wato Abubakar suna kiransa Prince,raguna 2 da katon Sa Omar ya yankawa Iklas.


     Gomnati so takeyi kawai ayi Suna tayi maganin Khairat.


     Baffa sunje asibiti kowa da kowa na family Suna Gaban Haj Rahina wacce take rai a hannun Allah.kuka sukeyi ita da Binta, Binta tana ki yafemin kawata naci amanarki,Ita kuma Haj Rahina tana ke ki rabu dani Binta tsinaniya,so take ta ce Allah na tuba ka yafemin maimakon haka sai zafin ciwon yasa ta koma fadin Alhaji Mohd Inshaa'Allahu......insha'Allahu,sai ta koma cewa nashiga uku mun godewa Allah mun yabi  Annabi. Sai rerawa takeyi  da wanka.


      Bangaren Sahar kuwa ta dan samu sauki amma ta haukace domin duk namijin da ta gani ko yaro ko Babba,ko karami ko babantane  da taga da Namiji sai ta bude masa zaninta gabanta ya fito fatsar tace Malam Zaka siya?


      Babanta yasa  an kulleta a daki na musamman, ammma ko Daddy ta gani sai ta bude  masa tace Daddy Na siyarwa ne fa,kan haka wata rana Daddy yayi mata dukan tsiya ya farfasa mata jiki.yana ta kuka shi da Mummy tare da Nadama.

   Omar ba abinda ke damunsa irin sha'awar  Iklas, wankan da takeyi  shike kara rura masa wutar sonta da sha'awarta, ya gama  gama sawa Iklas ido, tare da Dana mata tarkonsa ba tare da ta ganeba.burinsa ya samu Iklas ta fara Sallah,bazai iya zama cikin wahalaba ace har sai tayi arba'in. Ga shigar da takeyi me Jan Hankali. Iklas kuma yanda taji wahalar haihuwa tace baza ta kara yarda da Omar ba sai tayi 3mnths ta murmure, kuma hakan ma sai an mata family planning.




AsmaBaffanku ce readers. Tnx  all for d comments.ayi min Afwa da typing error ba time ne.

ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR

        GOMNATI

        ⓂⓂⓂ


        195-200




By

AsmaBaffa




      Haj Rahina tana sambatun wahala tace Alhaji Mohd ka yafemin,ina Omar a nemo min shi na masa laifi na jefa masa cuta,Mama ki yafe min,tana nishi taci gaba ni...ni....nice....na..je....wajen...boka...ya sawa Omar cutar da ya bar gida kwata kwata,kuma....kuma...na jefa masa lalaura da dama Wanda bai sameshi ba,Nan dai ta tonawa kanta asiri kaf,

   Ita kuma Haj Binta tace ni...kuma...kece zaki yafemin Rahina....naci...amarnarki...kin bani kudi...naje wajen....boka...amma na naki zuwa....na dinga shuka miki karya....na cinye miki kudi...na gina kaina.....sabo....sabo da Bana so kici gaba.

     Haj.Rahina ce ta fashe da kuka tace wa Binta ke annamimiya ba take nakeyi ba....ki kyaleni inji da kaina...kowa yana gabansu both family Binta da Rahina sai kuka sukeyi.Omar da Iklas sun shigo suma,nan take Omar yace kanku kuka yiwa na yafe.....da sauri Iklas ta rufe masa baki,cike da shagwaba ta rada masa a kunne  Allah ni baza ka yafe musu ba,da ace da hali ma gwara a karasa datse musu kafafunsu


       No wifey cewar Omar,to shike nan a datse musu hannu ko daya ne,kuma baza a yafe musu ba masu shirka,suka cucemu mijina yayi ta shan Wahalar kuka nima aka sani kuka

     Na dinga tausauyin Omar Ina kuka to kukan da suka sani bazan yafe ba.

Omar ne dauke da prince a kafada ya karasa jikin Bed din yace sannu Allah Baku lfy,da sauri Haj Rahina tace ka yafemin da yarana mun zalinceka,na yafe muku komai wlh,Mama ma ta yafe,Baffa kuwa tunda yaji lafazin Rahina ya fuce cike da takaici

     Su Sadiya sun cika wajen da kuka ba ji ba gani suma suna rokon a yafe musu.


      Iklas tace honey na gaji kasan fa yau 2 days da yin suna ni na gaji kazo mu tafi gida,Ummi ce ta harari Iklas,Mama tace kuje Omar tunda ka yafe ba matsala ,ni zan zauna dasu tare da Ummi.

  

     Baffa anyi anyi yaki ya yafe musu da kyar Mama ta lallabashi sannan yace ya yafe musu,Omar mota ya budewa Iklas ta shiga shima ya shiga yau shine driver prince yana Bayan mota a kwance,Iklas ce ta kalli  Omar da harara tare da dauke kai,hannunta ya riko yana mirzawa lfy ke kuma?me nayi ake hararata.Kaine ai Honey ragon maza kawai,daga anyi Abu sai zuciyarka tayi Rauni ka yafe musu,yanzu mene abin yafe musu anan,ko kukan da sukani na tausayin cutar da ke damunka sanda kana gidanmu baka duba ba ka wani je gabansu Na yafe muku Allah yafe mana gaba daya,ta kwaikwayi maganar omar,shi kuwa murmushi kawai yakeyi,ta kara cewa wannan idan suka warke na hango rabaka dani Za suyi kaje kai ta yafe musu ,mashirka dasu Indai mutum a rayuwarsa yace malamai zai rike,komai mutum bazai tsarkake zuciyarsa ba ya yarda da Allah yana addua to wlh yana tare da wahala duniya da lahira,shirka honey bafa karamin Abu bane,kuma malaman suyi ta cinye musu kudi suna musu wayo,Allah shi keyin komai,babu Wanda ya isa yayi ma abinda Allah bai bai yi ma ba.

 

     Amma a yanzu da yawa mutum bazai Dage da addua wajen Allah ba,ya mike ya roka da kansa,sai dai ya dinga kai kukansa wajen malaman bokaye,maybe ma mutum yafi malamin da yaje gunsa daraja wajen Allah.amma yaki rokarsa. Ana fa kuskure,yan kasuwa,matan aure,yan mata,zawarawa,ma'aikata,etc kowa yanzu da yawa za kaga malamai sukeyi kala kala,malamina.to wlh mutuwa bata sallama,ba sai lallai da ciwo ba za a wuce,idan ma baka mutu ba ka tuba baka da tabbacin an karbi tuban naka ko ba'a karba ba?yanzu honey ni kaina sanda nake nakudar nan ai na zata wucewa zanyi.


      Dariya Omar yayi my heart ta Girma jibi wa'azin da kikeyi haka inda kike birgeni watarana zancen manya kikeyi idan Abu yazo serious kike daukansa,amma idan rigima da darunki suka tashi ba sauki da kyar ake shawo kanki.

   Murmushi tayi cike da shagwaba ta fada jikin Omar dake tuki, ni....ka daina cemin rigimammiya wannan ai sai prince.wani shock ke fisgar Omar na tsananin sha'awar Iklas.murya a dishe yace Wifey yaushe mace take fara Sallah in ta Haihu?cike da dabara Iklas tace idan Wanda sukayi haihuwa uku zuwa hudu ne to 40days sukeyi suke fara Sallah, wasu 1wk ma,wasu 2-3wks kai wasu ma sai su wuce 40days din etc ya danganta da yanda mace take.


     Da Sauri  Omar yace to irinku fa masu haihuwa daya,tamke fuska tayi ba wasa, tace masu haihuwar fari musamman irinmu da muke yan yara to sai munyi minimum 3to 4mnths,kai irinmu da muke 16yrs to 17yrs har 5mnths munayi kafin jini ya dauke mu fara Sallah.

     Bare ni da nake ta dabance kasan dai ko period tsuuuuuuuuuuuuu yake zubo min kamar an bude tap,dariya Omar yayi sosai yanda da girmansa da Ilminsa Iklas sai raina masa hankali takeyi zata wai yi masa wayo.


     A fili kuwa nunawa yayi ya yarda da zancenta Omar ya kara mata haske da tab ai dama na sanki wajen period bare wannan ai nasan flowing zaiyi like a river. Da sauri tace kamar ka sani kuwa,a river dinma bafa karama ba babban kogi,ko Dam.

     Harda kara kankame Omar saboda murna wai tayi masa wayo.


    Omar kuwa rungumeshin da tayi shi ya jawo Omar yaci birki kiiiiiit tare da gangarewa kasa.cikin zafin zafin nama ya hade bakinsu wuri daya, a haukace yake rikitata da salonsa,Iklas ta fara hargitsewa Itama musamman daya fara wasa da dukiyar fulaninta,itama biye masa tayi suka haukacewa juna da gani sunyi missing din juna,kawai I miss u suke furtawa juna.


           Iklas gani tayi abin na Omar yayi yawa, idan ta bari itace zata kwana ciki,dan sai ta kuma samun ciki ta Shiga uku. Da kyar ta kwaci kanta,da taga yaki kyaleta kuka ta saka masa, sannan ya kyaleta cike damuwa.yaci gaba da driving.


      Iklas taji wahalar Haihuwa Mama ta samu a room dinta ta je ta gaisheta kamar zata mata sujjada tsabar biyayya wai ita a dole tasan zafin haihuwa yanzu,lfy Iklas naga kamar kina da magana cewar Mama, Iklas zama ta gyara cike da ladabi tace Mama dan Allah kar ki bari Yaya Omar ya mai dani gidansa idan nayi Arba'in,Mama ta gano Iklas,amma sai tace sabo dame wani abin yake miki?yi gaggawar sanarmin nayi maganinsa,a'a Mama baya min komai wlh,kawai firgitani akeyi a gidansa sai na dinga ganin dodo a jikin bangon room dinmu,dariya Mama tayi karki damu za a kai malamai suyi karatun Qurani,ai Mama musulmai ne dodon basa ji,sun iya karatun suma,idanfa ina karantawa sai dai kiji sunayi suma,kuma Omar bai fada min cewar mama,ai mama ni kadaice na san dasu,a'a wannan za ayi maganinsu cewar Mama, Iklas tace asarar kudi zakuyi gwara Ku barni a nan gidan, Mama tace jeki za ayi bincike,amma bamu da iko sai abinda mijinki yace

    Da Sauri ta juyo tace Mama dan girman Allah Ku taimakamin,wlh idan kuka fada masa bazai yarda ba,ni dai kar kuyi masa zancen to.

     Murmushi Mama tayi jeki kinji za asan abinyi,kuma baza a fada masa ba,to Mama na gode ta kara jaddawa Mama dan darajar Allah kuyi min Rai,Ku duba lamarin nan,Mama tace Insha'allah. 

ta fita tana murna,


 Palo ta koma ta Iske Khairat ta cakare kusa da Omar.a fusace Iklas ta dauki katuwar kwalabar wani lemo me tsada ta daki jikin bango nan take kwalabar ta tarwatse Rabin kwalabar da tsini a hannun Iklas, gashi har wata ta yanketa a tafin hannu,amma a haka tayi kan Khairat gadan gadan zata buga mata kwalaba, Omar ya riketa kam sai zullo takeyi sai ya saketa,sosai Iklas take son kwacewa tare da nishi ka kyaleni pls honey, Omar kuma ya rungumeta ya hanata Motsi,sai huci takeyi tana wlh idan na kamata sai ta gane kurenta,

     Yer uwarki ce fa cewar Omar?ina ruwana da ita,na tsaneta bana sonta,da gudu Khairat ta tafi part dinsu tana rokon sauran suzo su bar Nigeria, da kyar a ka lallasheta cewar gobe za a tafi, sai kuka takeyi wiwi

       Omar kuwa da kyar ya kwace Kwalabar daga haannun Iklas sai lallashinta yakeyi tare da kwantar mata da hankali,yana shafa gadon bayanta tare da dan bubbugawa,yana rada mata a kunne relax wifey bana son saurin fushin nan naki, ki dinga hakuri, yanzu laifina ka gani?cewar Ikla taci gaba tunda taxo takeyin Abuwa bad a kanka ina kallon nake sharewa, kai kuma sai biye mata kakeyi, wlh hakurina ya kare da ace ta tsaya sai na mata bille a kirjinta da fuska,Kasan kuma zan iya danma na canja halina da ace ni din ta dace da tuni kaima Kasan nayi maganinta,gwara in tazo ka dinga matsawa dan next time ka kara barinta har da kai zan hada.


    To ai kinga dai bani naje wajenta ba ita tazo wajena,kuma ni sabo dake nake kyaleta,naga yar uwarki ce shi yasa na miki kara,kar kice bana son yan uwanki,shi yasa am sorry.ba komai Babyna nasan baka da laifi,amma ka kiyaye nan gaba kaima naga fa kamar zaka zama mayen mata ba mayen Gomnati ba,nafi so ka zama Mayen Gomnatinka.

     Dariya Omar yayi yeah ai shine dan yanzu kin daina kula dani sai ta yaronki kikeyi,haba my heart,my liver ,my blood.

   Murmushin jin dadi Iklas tayi tace kai da ace na fara Sallah yau da kwana zakayi cirrrrr kana shakaka dani.


     Idan da gaskene ki bani nayi romance mana,wayancewa Iklas tayi hmmmm ni dai ka daina zama kusa da wata,duk inda Omar yazo da zancen sai Iklas ta canja zancen.

     Washe gari da sassafe yan Uwan Iklas suka fito domin tafiya kasarsu,anyi musu sha Tara ta arziki driver ya kaisu airport,

     Khairat kuwa tsoron Iklas yasa ko kusa dasu bata matso ba daga nesa can bakin kofa ta dago hannu tace musu Ilallikha......


     Bayan sun tafi Iklas dauke da prince tana jijjigashi yana rigima,Omar ya zauna a jikinta shima yace Baby kin kori bakinmu saboda masifarki, ko kulashi batayi ba sai jijjiga yaronta takeyi tana masa rawa,

       Shillashi takeyi sama tare da juyo dashi ya kalli Omar kaga Daddy,irin rigimarku daya, Omar kuwa kwanciya yayi kan cinyar Iklas,yaron kuwa sai Kwalla kuka yakeyi yana tsala ihu,waka Iklas take masa tana shillashi tana eh...eh...ehh..kaga na kwandala.... Kwandala...kwandala......dan albarka.....dariya Omar yayi yace inye kaga su Gomnati anyi yaro,


      Omar yana kwance a cinyarta ya fara zura hannunsa a Rigarta yana shafa Dukiyar fulaninta, yer aiki ta aika da yaron ta kaiwa Ummi,ba a Dade ba Ummi ta dawo dashi tace ya isheni da kuka ga danku,

    Mama ma haka ta dawo dashi, haka yan aiki da su suhaila ma,

   Duk yaron ya ruda Iklas da kukansa,ya gigita gidan,sai ihun kuka yakeyi,Gomnati ta rasa inda zata sa kanta da rigimar prince.

    Omar kuwa ko kukan jaririn bayaji sai tabe tabe da lashe lashe yakewa Iklas a jikinta ya hanata sakat,kuka ta fashe dashi sosai baji ba gani,yaron na kuka itama tana kuka sun hadu sai yi sukeyi,kuma still tana ta jijjiga Prince, Omar bai kula dasu ba sai ji yayi Iklas ta gartsa masa cizo a bayansa


     Da sauri yace ouch......yana shafa wurin,sannan ya leka fuskarta ya sai kuka takeyi itama ga prince yanayi shima,ohhhh no wifey why? Kuka kikeyi to mene na kukan,prince na kuka ke kinayi am sorry ki daina bana so,

     Hawaye ya share mata tare da karban prince yana lallashinsa,mikewa tsaye yayi ya lallasheshi yayi shuru kuwa kuf a jikin Omar bacci ya daukeshi,

     Wajen Mama ya kaishi ya kwantar dashi a wajenta sannan ya dawo wajen Gomnatinsa yana lallashinta,sai shagwaba take zuba masa tare da narke masa,tana kwance a jikinsa tana shafa inda ta cijeshi tana kayi hakuri sweet heart wahalar raino naji,

   Gashi kowa yaki kulani kuma sai lasar min jiki kakeyi.to ya isa na daina kinji.


      Washe gari Allah yayiwa Haj Rahina rasuwa,Iklas harda kuka tana Allah sarki gwara da Ya Omar ya yafe musu Allah musu Rahma,sai da ana zaman makoki Iklas tana tare da su Sadiya tace Ohhh Allah jikan Umma na tuna sanda  ina da cikin prince   har hallaka kwabo da dan tamatsitsi take siyo min nasha naji dadina.Allah mata Rahma su Aisha suna ameen suna kuka.

    Anyi jimami yayin da akayi sadakar bakwai kowa ya watse.su Sadiya yanzu basu da wacce tafi musu Mama,da ita suke shawara,Omar kuwa da matsala ta taso zasu ruro wajensa,Baffa ma yana tausaya wa yaran nasa irin jarabawar da suke karba,daga wannan sai wannan.Duk abinda sukeyi yau gashi ba uwar tasu a duniya,duk burin Ummansu yau gashi ta tafi tabar duniyar.

      Shima wannan ya jawo Su Sadiya sun kara darasi a duniya.kwanan Rahina takwas da rasuwa Haj Binta ma ta cika itama,sosai akayi jimami da ta'aziyya nan ma ansha kuka.duk son duniyarsu yau gashi Allah ya kirasu sun bar komai sun tafi.nan make Tarawa nan ake bari duniya kenan.


     Sahar abin nata ba sauki,wata ranar juma'a ta fita waje ba tare da kowa ya sani ba,wani babban mutum ta gani a hanya ta cire zaninta tare da cewa Alhaji zaka siya,bata san liman din Unguwarsu bane ai kuwa limamin nan  a fusace yayo kanta dan ubanki tsinaniya tambadaddiyar karuwa,ni zaki mayar dan Iska ni zakiwa maganar banza,ya fara jibgarta ina liman zaki mai dani dan iska,da kyar aka kwaceta,ita kuwa sai gwalo take wa liman,yana kallonta idan suka hada ido sai ta zaro masa harshe ta mayar.

    Sai da wani mutum yazo yayiwa liman bayanin yer gidan Gomnace daya sauka last yr,ai kuwa nan liman ya fara yi mata addua ya daina masifa yaji kudi.

     Kamata akayi tare da mayar da ita gida. Allahu Akbar duniya,da ace da ne liman bai isa yaga Sahar ba bare ya iya yi mata ko da kallon banza ma.sai gashi harda duka.


     2wks da haihuwar Iklas jini ya dauke mata ta fara sallah a boye dan kar Omar ya gani bata San Omar tuni ya hada CCTV a computer dinsa ba, in ya dawo daga Office yana kunnawa ya kalli duk abinda Gomnati keyi a gidan,


       Rannan yana dawowa ya kunna yana kallon Iklas,katsam yaganta sadaf sadaf ta sa key a kofar,sadaf sadaf ta tayar da Sallah,wani dadine da farin ciki ya lullube Omar. Ya furta today is my day.Iklas kuma tunda Mama taga yau ta fara sallah  sai tace wa Iklas tattara naki ya naki kaf ki koma dakina da zama,Iklas cike da murna ta koma room din Mama.



AsmaBaffa.


   Mom walida name sake with maman waleeda na gode naga comment naki.


    Jinjina gareku mutanena.

ⓂⓂⓂ

    MA'AIKACIYAR

        GOMNATI

  

          200-205



By

AsmaBaffa



  

    SAFEEYA AHMAD,MAMAN ABBA, wannan page din nakune 

    




          Omar shigowa yayi gidan a gajiye,ko wanka baya jin zai iya yiwa kansa shi yasa ma ya aiko Suhaila ta kira masa ita,Iklas an cakare da kwalliya kamar wata queen tsabar kyau,ga mama da Ummi gyarata sukeyi sosai,itama Iklas kullum sai taje gyaran jiki wajen Mero Lallausa,kamar wata Amarya haka ake gyareta,jikinta ya murje sai sheki da kyalli takeyi,gashi abinci me rai da lafiya Mama ke bata,

      Koda Iklas taji sakon Omar firgita tayi,mama ce ta bada Amsar je kice aiki na sata. 1mnt da fitar Suhaila kiran Omar ya shigo dankareriyar wayar Iklas,sai da ta kusa tsinkewa ta daga tun kafin tayi magana yace in kin gama kizo am so tired ko wanka bazan iya ba,kuma yunwa nake ji,kamar zatayi kuka tace to am coming.

      10mnt kiransa ya kuma shigowa wai har yau me kikeyi haka?tana Ina ina tace I...I...will..be on my way, better dit ya kashe wayar

     15mnt ltr call din  Omar ya kuma shigowa still dagawa tayi idan nazo room din baza ta miki kyau ba bring ur self to my room quietly nasan abinda kike gudu ki daina tsoro ni ba abinda zan miki sai nan da 2mnths maybe ki saki jikinki ki daina bata lokacinki.


       Mama ta kalla kamar zatayi kuka,jeki kinji idan kinga wani abu da bakya so ki gudo,kamar kwai ya fashe mata Iklas ta fita tana sake sake a ranta,ita wahalar Haihuwa take tunawa.

      Omar kuwa Ransa ya matukar baci da Iklas,tana shigowa room da masifa yaso Tatar ta sai yaga wani uban kyau da ta zuka kamar ya lashe ta haka yakeji,dan danan ta kwacewa Omar Imani,yama rasa me zaice sai binta da kallo yakeyi,


      Gefen bed din ta zauna tana cin magani,sannu da zuwa me zanyi ma?Iklas ta tambaya,jiki a mace yace tashi kije bana so sai wani fushi kikeyi akan nace kizo jeki ki bawa Suhaila ta kawo min Prince,

     Gomnati taga da gaske Omar fushi yayi sai taji bata kyauta ba,batayi dai dai ba ta batawa mijinta Rai.


     Sumi sumi taje ta dauko Prince da kanta ta kawo masa,a hankali cike da nutsuwa tace masa me zanyi maka dazu?nace ai na fasa  bana so cewar Omar,kai dai kace kawai kayi fushi dani banzo da wuri ba kayi hakuri to,

      Gani kikeyi wani abun zan miki,dama wanka zaki min ki bani abinci kuma zanyi da kaina.mikewa tayi ta hada masa ruwa wankan.


       Dawowa tayi ta karbi Prince da ke hannunsa ta ajiye a kan bed sannan ba tare da tace kala ba ta shiga cire masa kaya sai dadi yake a ransa,amma a fili sai shagwaba yake mata yana gocewa yaki tsayawa kamar yaron yaye, 

 

       Pls ka tsaya mana mutum sai rigimar tsiya,sai da ta gama ta daura masa towel tare da kare masa kallon birgewa,dan ita dai a rayuwarta kirar dirin Omar,skin da komai na Omar suna matukar birgeta tare da bata sha'awa,a ranta sai zancen zuci takeyi yanda Omar kullum yake kara kyau da haduwa.

    Hannunsa me matukar laushi ta kama ta kaishi har Toilet,wanka tayi masa sosai,sannan tazo ta shiryashi,harda sa masa jallabiyya fara Sol,ka Dade baka sa jallabiya ba kasan kuwa yanda take ma kyau,yau ita nake so kasa min a gidan nan, tsokanarta Omar yayi ai kuwa fita zanyi ni,haba dai duk gajiyar nan da ka kwaso ,sai da ta gama ta kalleshi tana murmushi tace Honey dan Allah Kasan kai me kyau ne kuwa? kana kallon kanka kuwa yanda kake da kyau

   Hancinta ya ja ai kinfini kyau wifey,duk Inda ake Neman kyau to azo wajenki,

     Ranar Dana fara ganinki a gidan kaji tun a ranar na tabbatar ke me kyau ce wacce ban taba ganin irinsa ba, 


Hugging dinsa tayi tare da shakar kamshin juna,tare da cewa hmm wai a gidan kaji dama ka kalleni? Ko mutum baya so sai ya kalleki yanda kika haske gidan kajin gaba daya,ke ake fara gani a ciki da tsangalalliyar rigarki gwiwowin ki da kafafun masu kauri da kyau duk waje suke,kallonta Omar yayi wai don Allah a lokacin ba kya jin kunyar mutane?


 Dariya Iklas tayi kai nifa idona a lokacin tar nake ganin kowa,na saba da shiga cikin maza dasu nake gogayya kullum,kaga kuwa ai dole ido ya bushe,

      Wai kai ai kadan ka gani danma baka ganni a tsakiyar yan wiwi ba mun kafa daba guga suna zuka tare da bulbula hayaki,to can kuma me ya hadaki da yan wiwi? Dariya Iklas tayi tare da boye fuskarta a kirjin Omar,kasan me a time din babu wanda ke birgeni irin dan wiwi,ni idan baka zuka hayaki ba ruwana da kai,kawai naga ana feso hayaki ga wani kidan Bob marley yana tashi ko wakar ganja fama,ka harde kafafu kawai ka fuske kana bulbulo hayaki malam,

 

      Dariya Omar keyi sosai,amma dai basa cewa suna sonki ko?ai kasan duk wani dan wiwi idan ya shahara ya cika dan wiwi to baya mu'amula da mata,basu fiye neman mata ba,ko budurwa basayi,idan na samu ribar tallana har hamsin nake raba musu a zuka hayaki,ni kuma inyi ta kallo ina jin dadi,


A kunna wakar ganja farmer subhanallah kai kanka zasu birgeka yanda ake zana love da hayaki,murmushi Omar yayi lallai Allah ya kare min matata shi yasa ba a son daurawa yaro talla,idan ba wanda Allah ya tsare ba lalacewa sukeyi,Iklas tace wlh kuwa honey kafin kaga yar talla wacce ke fita tasha,ko titi ta gari sai an tona,duk a tallan maza ke lalatasu,ga shaye shaye yanzu wasu sun waye da sha banalin,codine,da sauran kwayoyin maye duk a sanadin talla,nima Allah ne ya shiryani kuma Ummi tayi mana tarbiya,ga addua ina dagewa amma da tuni nasan nabi duniya.


  Za kaga manyan masu kudi suna parker motoci suna neman yan talla,su kashe mata kudi,shike nan idan ba ayi sa'a ba tabi duniya,rayuwarta ta lalace,sai kaga yan majalisu,senate,com,yan kasuwa da manyan masu kudi suna bin yan talla,kafin kace me an rude ta da kudi


  Kaga suna tayi mata maganar batsa tun bata yarda har ta yarda,wasu kuma ayi musu fyade,watafa honey me chemist ta kaiwa talla amma ya bata kwaya yayi mata fyade,

Wasu a shaguna,wasu kango,wasu su koma karuwanci,kai alot fa,talla bashi da afani ga mata kawai sai dai wasu sabo da talauci ba yanda za ayi,wasu kuma son abin duniya,wasu kuma rashin gata kishiya ko dangin uba suna rikesu sai su dinga tura su talla suna cin amana,ba Arabic schl bare boko,Allah ma ba a sani ba bare a bauta masa.

       Allah kyauta wifey gaskia ya kamata ki fara yiwa mata wa'azi a kasar nan, ta kyalkyale da dariya tare da dan dukansa a kirji cike da shagwaba tana turo lips dinta tace kai honey ba dama nayi magana sai ka ce wani wa'azi,ina fada maka abinda na sani ne kuma kaddarar rayuwa ta kaini kasan ba dadewa ce a duniya take sawa asan rayuwa ba,kaddara ce da mutum zai cinci kansa yake sawa yayi nasa karatun duniyar, 

     Amma da nayi maga......ba tare da ta ankare ba ya fara kissing dinta a wuya,daga nan ya gangaro lips dinta,tare da shafa mazaunanta masu matukar raushi, kafin kace me wasa ya canja salo,sosai Gomnati ke enjoying, sai da ya lugwigwitata son ransa tana biye masa,sannan ya kyaleta itama ji tayi tana matukar bukatar Omar gaskiya,

    A ranta tana anya zan iya 1mnth ba tare da na yarda da Omar ba,can ta tuno wahalar haihuwa,sai kuma tace kau dan wuya ai ba a bar dadi ba.


       Omar kuwa da kyar ya saita kansa so yakeyi ta hanyar wayo da salon dabara Gomnati ta bashi abinda yake so,idan ya nuna ta karfi ko yayi mata dole to zata ki yarda ko su sami sabani tunda irinsu Iklas saida lallabawa.

     Kallonta yayi cike da sha'awa sai Mirza yatsunta yakeyi, cike da shagwaba yace my heart yunwa,au na manta bari na kawo abincin ta fada tare da mikewa ya jawota a hankali ta fado jikinsa kiss ya manna mata a goshi tare da cewa jeki dawo ki sanmin milk din Prince,bata gane me yake nufi ba tayi waje.


   Abincin ta dauko jere a katon tray me mugun kyau na yan gayu ta ajiye  a kasa tare da shimfida katon carpet me tsananin kyau da birgewa ga duk Wanda ya gashi,

     Zama yayi a kai sannan tayi serving dinsa ta fara ciyar dashi tare da yi masa kalamai masu matukar sa nishadi da jin dadi Wanda ke kankarowa mace daraja a idon mijinta,me kara sa miji yaji gaba daya ya narke,ya tsunduma,tare da cabalbakewa cikin kogin son matarsa,

   Shagwabashi Iklas keyi sosai kamar wata Mamansa,shi kuwa Omar jinsa yake kamar yaron goye a wajen Iklas,yaron ma irin danye cakal din nan.

     Bayan ya gama cin abinci Iklas tana kasa ta mike kafafunta kusa dashi kanta yana kafadar Omar tana wasa da zaren jallabiyarsa da ke lilo a wajen wuyansa,

      Zamewa yayi tare da daura Kansa a saman cinyar Iklas ya kwanta kamar zai sha nono,a hankali ya dage rigarta dukiyar fulaninta suka bayyana farare tas dasu,nipple din jajir dasu,kansa yasa a tsakitarsu wani azababen kamshi ya rikitashi sai fisgar numfashi yakeyi tare da shidewa,

     Iklas kuwa lumshe ido tayi tare da zama dagalolo kamar wata doluwa Omar ya fara kaita karshe da salonsa,idon sa jajir yace wifey ki sanmin milk din prince kinji,baki ta bude ta firgice,da karfi take son Jan rigarta tana so ta rufe amma Omar ya rike rigar gam ta kasa,

     A rude tace me...me zaka sha nonon Prince kayi dashi wannan ai kazantar taka ta kai karshe,ni ban taba ji ba a duniya,idan babu kyau fa?ni bani da Ilmi a nan,amma ko ya halarta baka kyankyami me zakayi da shi,kuma ma ai shanye masa zaka yi,


     Ganin yanda ta rude kamar zata zura da gudu yasa Omar cewa calm down Baby relax kiji mana,shuru tayi tana saurarensa ba a koya muku a Islamiyya ba?baki da ilmi a kansa ni ina dashi,matukar miji bazai shanyewa jaririn ruwan nonon ba a barshi da yunwa,yazo ya cutu ko ya shiga wani hali to ya Halarta miji yasha milk din matarsa,idan kuwa zai shanye masa abarshi da yunwa to bai halarta ba,

     Wa'azi ya kunna mata inda akayi wa malaman sunna da dama tambayar kuma suka ba da amsar a haka cewar ya halarta,honey kinga mutanenmu da yawa basu San wannan ba,turawa ne da larabawa da sauran yare suka San da wannan,akwai hausawanmu da yawa basu sani ba.

    Shi yasa Neman Ilmi yake da dadi,ya kamata a dage da nemansa ta ko ina.

 

     Yanzu kai baka kyankyami?murmushi Omar yayi muke shan na rakumi,na Saniya Dana akuya ma bare abinda Prince dina ke sha,kuma milk din my heart,liver and my blood.ni ba wani kyankyami sai dai idan baza ki bani ba.

      Ni ba ruwana kai kaga zaka iya.

      Ai kuwa Omar kamar jariri ya kama zukar milk din dukiyar fulanin Iklas ji kake makwat,harda yin wasa da dayan, dan kadan yasha Iklas ta kwace abinta ta rufe tare da cewa Kazami zaka shanyewa Prince kalli yanda kake lashe lips,to kaga dai a jikina yake ko?to wlh bazan iya sha ba.

     Ke kika ce ai,ni as from 2day kullum ki dinga ajiye min milk dina.a'a bazan iya ba kato dakai ga prince kunyi min yawa ai sai kusa na rame.Ummi ce ta sa aka kira mata Ikkas,


     Da sauri ta sami Ummi a room dinta Ummi gani lfy?ina fada miki ki kiyaye shigewa miji kinki ji ko? Yaufa satinki biyu da Haihuwa amma ke bakya gudunsa,so kike ki samu wani cikin ko kiyi kwanika.

      Dire diren kafafu Iklas ta fara tana make kafada,ni a gaskia abinda kikeyi Ummi bakya kyautawa,kun cika fassara mutum Ku tsofaffi Ku ke jawowa wasu kaga daga sun haihu sai aure ya mutu idan kuka kawo yarinya gida wai goyon ciki sai Ku hana mace ko mijinta tayi hirar kirki dashi,ba kula da miji,ba zance me dadi,kullum ta dinga gudunsa har sai kiga a haka aurenta ya mutu ko kuma ta jefa mijin ya kasa daurewa ya fada Neman mata.ni kinga ina tsoron kara haihuwa amma wlh akanta bazan kasa zuwa na bawa mijina kulawa ba,to naji magana uwar yan wa'azi da an tabaki yanzu kya fara nasiha,naga yanzu tunda kika daina son aikin Gomnatin nan kika daina rubuce rubecen iska sai kika koma wa'azi,ke a dole kinyi hankali kinyi aure ke ga me miji ko,?


    dan ubanki jeki ki bashi kanki ke zai bari da wahala,baki Iklas ta turo gaba Ummi pls ki dinga ganewa kina yawa fa Ummi ya za ayi ki dinga kwafsawa ke kullum harkar daa can zamaninku kike kawowa,Iklas tana fada tana yarfe hannu tare da yatsina fuska,ki gane Ummi ba cewa nayi zan bashi kaina ba,nimafa ina da hankalina ba sai kin dinga sa min ido ni da mijina ba,Ummi ce ta jefeta da cokalin da take cin dambu ai kin gaji Ubanki haka yake shima kan matarsa bashi da kunya,jininku haka kuke ai, dariya Iklas tayi tana daga jikin kofa tace Ummi hardake fa haka kenan kika kula da tsohon mijin nan naki ko? Dariya Ummi tayi Ohh ni jikar Hauwa'u naga ta kaina da Iklas


      Ummi ki daina damuwa akwai solution ba wani ciki ki daina samin ido yanzu kai ya waye bazan jira haka kawai Ku jawo min salalan tsiya mijina yayi fushi dani,ko aure na ya fara tangal tangal,ko mijina na jefashi hanyar bin mata ba,domin ni Kadai ta shafa,iyakaci idan na kawo kararsa kunyi min mutunci Ku bani hakuri kuyi addua ko Ku lallasheni. Kinga yaushe zan yarda da shawararku.ni nasan halin mijina Ku barni inji da abuna.to Gomnati Allah taimaka fita ki bani waje na gaji.


      Ummi ce tace au na manta ban fada miki ba Mama zata tafi Umra ita da Baffa,suleim,da Suhaila wani watan me zuwa,sosai Iklas ke murna,tace kuma Baffa Nima ya biya min aikin hajji bana dani za aje idan muna da Nisan kwana,ke kuma yace ke mijinki yace tare zakuje dashi kafarki kafarsa da Prince. Tsalle Iklas Ta farayi tare da rungume Ummi sai murna sukeyi.kamar ba Ita ta haifi Prince ba sai tsalle takeyi, lafiya kenan inda ita komai mutum gani yake dai dai dashi ne,Iklas ba a Girma cewar Mama da ta shigo ta kama Iklas na tsalle.

   Sai godiya Iklas ke wa Mama taji labari.


       Ibzzy Boy ne tare da WANKAN TSINKE sun cakare suna shopping a wani katon Mall,wani Babban abokin Ibzzy ne ya shugo suka tafa yana karewa Ibzzy kallon,man kana shanawafa kayi aure ka barmu,ango ango.Wankan tsinkece tace ina yini cike da ladabi,daya saurayin ya leka fuskar wankan tsinke tare da cewa kardai Wankan tsinkece Amaryar? Ibzzy yana washe baki yace yeah,Allahu Akbar cewar abiki,yanzu wankan tsinke ka aura Ibzzy?duk irin ta a sar da kuka kwasa kace baza ka aureta ba ka gama da ita lallai Allah ne me shirya bayinsa a lokacin daya so


     Ibzzy yace Bari dai Frnd sai dai Allah ya yafe mana,shi yasa muka tuba muka rufawa kanmu asiri muka auri juna ina ganinta a biri tana ganina a ayaba, ba ruwanmu da duniya.naga darasi kala kala Man,duk da inda ka dauki duniya to dai dai take da kai.Frnd shi tsiyar karatun duniya idan ta tashi koyama. darasi dole sai ka dauka,kuma wlh ba a kunne akeji ba.......kafin ya karasa wankan tsinke tace dukkan gabbai da ji sai yaji,ciki da waje ko ina sai ya shigeka.nan dai suka bar Zak's abokin Ibzzy da alajabi da mamaki wai Ibzzy ne dake kashe musu kudi dan suyi Iskanci

     Gashi wai ya auri wankan tsinke kawaliyarsa abokiyar masha'arsa. Allah me Iko kenan.


     Misalin karfe 9:30 na dare kowa na gidan yayi bacci tsuuuuuuu yakeji,wani hadarine ya taso yayin da ruwan sama ya kece me karfin gaske,Omar dake kwance shi kadai kwal wata muguwar sha'awar Iklas ce ta taso masa ga kuma son yaji dumun jikinta dan burinsa kenan idan ana ruwan sama ya jishi tumbir Iklas ma haka lol suna manne da juna suna baccinsu,

    Kasa bacci yayi ya mike tare da saka jallabiyya sadaf sadaf kamar barawon tukunya ya nufi dakin Mama, tunaninsa Mama tana dakin Baffa bai San Baffa yayi sammako zuwa Adamawa state zasuyi semina.


      Yana zuwa ya tura kofar a hankali ya Shiga dakin,itama Iklas tunda taji ruwan sama ya tsuge shaaaaaaaa sai ta fara kewar mijinta tare da son kasancewa dashi,

    Hangosu Omar yayi Mama a kan katifa a kasa tana Baccinta,Prince kuma a dan Bed dinsa yana bacci,Iklas ita kadai a bed din Mama tana kallon pics din Omar a wayarta,Omar ne ya karaso kan bed din a hankali,kamshinsa ne yasa Iklas ta gane shine tun kafin yayi magana


     A hankali ya lalubi kunnenta tare da kashe wayar hannunta ya ajiyeta gefe can,a hankali kamar munafuki ya rada mata tashi wifey muje room dina,karkiji tsoro ba abinda zan miki bacci kawai zamuyi,dama Iklas ma baccin take so suyi tare, Omar kuwa murna Ta kamashi yau zai wa Iklas wayo ya sharbi Zumarta.

     Iklas kuwa ta yarda cewar bacci kawai zasu sha da Omar harda sa yatsa akan lips dinta tacewa Omar shiiiiiiiii wai yayi shuru kar  Mama tajisu tare da sakala hannayenta a wuyan Omar wai ya dauketa

    Ai kuwa ya dauketa kamar jaririya hannunta a wuyansa, sadaf sadaf yazo zai wuce ta kusa da katifar Mama Ashe Omar bai sani ba ya take jallabiyarsa da daya kafar, yana takawa kafarsa ta harde ji kake rikica sun Fada kan katifar Mama, Allah ya kiyaye Kadan suka bigi jikin Mama  da badan haka ba da tuni Mama ta balle baras,amma duk da haka sai da kashinta yayi kara,

   Zumbur ta mike tana rafka salati zata zura a guje tabar dakin sai ayatulkursiyyu take fada  a bakinta a maimakon ta karanta,Sam bata kula dasu Omar ba tsabar rudewa

  

    A garin haurowa daga katifa zata bar dakin a tamanin ta make goshin Iklas ta taka hannun Omar,kwalla kara sukayi a tare Wanda yasa Mama ta banka waje a guje,a hankali suka leka waje suka ga Mama ta fada dakin Ummi sun maida key kyaras sun rufe kofarsu.


    Dariya suka dinga yi sannan Omar kawai  ya kulle dakin Mama da key shima suna ta dariya suka haye kan gadon Mama hankalinsu kwance.

    Sunfara romancing juna suka ji Ummi da Mama suna murda hannun kofar kamar zasu karyata  Mama tana mun shiga Uku Ummi Iklas da yaro suna ciki fa.


    Ummi harda kuka muje mu taso Umaru yazo wajen Nan ya gani,Mama tace wlh abin   Babba ne, Riiiiii suka juya  dakin Omar,Mama tana cewa da na sani da ban kashe light din dakin ba naga mene haka me uban nauyi.

      Dakin Omar suka dinga bugawa Suna kwala masa kira,ka fito Umaru tashin hankali ya samemu.


   Omar kuwa murza juna sukeyi suna jin su Ummi sama sama sai dariya sukeyi Iklas tana cire masa Riga cikin zafin nama shima yana cire mata nata amma fafur ta hana ya cire mata dogon wandon da tasa na bacci,tace jini bai dauke ba ayi iya romancing kawai, haka Omar ya sani amma ya kyaleta kawai a ransa yace kinci sa'a kawai a dakin Mama muke shi yasa,da sai na nuna miki CCTV na kureki.kuma dole ki bani.amma a jira next time yanzu muje a haka.

    Ummi fa sunga Omar ma shuru,fita sukayi nemo security harda kunna touch light suna haska lungun da wutar nepa batayi haske a wurin ba.






AsmaBaffa


 Tnx all

ⓂⓂⓂ

   MA'AIKACIYAR 

       GOMNATI

        ⓂⓂⓂ



        205-210




By

AsmaBaffa






       Mama da sauri suka kira securities har mutum uku suka zabo Wanda suka fi kowa karfi da murdedden jiki a cikin securities din da suke gidan,da sauri suka hawo sama har kofar room din Mama suna muzurai,nan suka fara kokarin bude kofa,kamar kofar zata balle haka suke dukanta,Omar da Iklas da sauri suka maida kayan dake jikinsu,suka shirya tsab harda gyarawa Mama bed dinta  don sunyi enjoying yau.

    Omar a hankali yacewa Iklas zafa su balla kofar nan,Iklas hannu ta Dora akai tana zagaya dakin ba solution,tace wa Omar ni wlh kazo ka jawo min ina zamana lfy,yanzu Mama inda kashinta yayi kara haka rukus ta kama mu mune muka firgita ta ya kake zaton zatayi mana?


     Dariya Omar yayi ki daina tuno min yanda Mama take gudu hhhhh sukayi dariya gabadayansu kasa kasa,wlh kamar tolo tolo cewar Omar,ba ruwana Mama ce dai cewar Iklas,

      Yanzu solution Gomnati tuno tsohuwar dabararki sanda kina yar talla,yawwa shiga toilet sai na kulleka ciki idan ta yi bacci sai ka fito,kaji fa wlh zasu karya kofar nan,

    Da sauri Omar ya shige toilet Iklas tasa key,yana daga toilet yace Wifey idan tace toilet zata shiga fa?na tabbatar idan Mama ta shigo sai ta shiga toilet yanda ta tsorata dole ko fitsari ne sai tayi,

   Dariya Iklas tayi ka jawo min jin kunya wlh,see u kar ki raina min hankali anji dadi dake wahala tazo zaki zame kanki,kinfi kowa jin dadi na tabbata cewar Omar,to fito ka shiga cikin sip,bude Omar Iklas tayi ya fito daga toilet yana hada zufa,

    Ke na gaji su kamani kawai na shiga sip kamar kwarto nida matata,kawai a fada Mata gaskia.

     Wlh ban yarda ba laifina zasu gani suce nice jarababbiya na manne maka,da masifa Omar yace ohhh da nazo ban taimaka miki ba?,itama Iklas ta harzuka cikin bacin rai tace ni na kawoka ko naje dakinka eh,da kazo na fada ma mu bari mu samu waje secret kaki ji,then zaka lullubeni da fada,


      To anzo din ba hakkina bane cewar Omar kasa kasa suke fadansu. Dan kar aji muryarsu,yaci gaba ki kiyayeni da yimin rashin kunya,kar ki jawo na zaneki ko yanzu na kwaci hakkina ta karfi,bismilla kwaci cewar  madam Gomnati,

    Gadan gadan Omar ya fisgota ya ajiyeta a Bed a hankali dan kar su Mama suji nan Iklas taga da gaske yakeyi kuma asirinta zai tonu cewar ta fara sallah,

    Cikin Rada tace haba honey kayi hakuri su Mama fa suna bakin kofa,kokawa suka fara tukuri suna bige bige da magana kasa kasa omar yana zan Nuna miki yau ni ba sa'anki bane,sai nishi da hakki Iklas keyi, 


Tana kokarin tashi tana fadin bazan bayarba ka kwata  din cewar Iklas,

    Ummi ce ta daka tsalle tace mutanen boye ne a dakin kuyi shuru kuji wlh kusur kusur akeyi kamar beraye,Mama ta kara ja da Baya tana kuyi shuru kuji maganganu a ciki,kasa kunne sukayi har securities sukaji maganganu a cikin dakin amma ba a gane murya kuma ba ajin me ake cewa,

    Ihu sukaji kadan can kasa shima ba a gane muryar ba,can sukaji ana yin kamar jifa an daki sip,kofa sukaji tayi kara,an jefar da wani gwangwani yayi kara kwararam, ai securities da gudu suka sauka kasa suna kuyi Hakuri a nemo malamai manya wannan ba aikin mu bane, Mama ma suka rufa musu baya,

          har su Ummi sun sauka suka kuma dawowa suka wuce kofar suka Ruga dakin Ummi,zasu sa Key Ummi tace Iklas da yaro,komaawa sukayi riii cikin Sanda suka dinga Iklas Iklas suna buga Kofar,

     Omar ya toshewa Iklas baki sunyi luf jikin kofar toilet Suna saurarar su Ummi,Iklas ce tayi gurnani Uhmmmmmmmm saboda Omar ya toshe mata baki yaji zata tona musu asiri, cikin rada yace kiyi shuru na fasa yi ,karki tona mana asiri,na tabbata Mama sai ta tsinemin idan ta kamani,

    Yanzu muyi kokari subar wajen nan,kokawar da mukayi dazu da Alama ta tsoratasu mu karayin irinta,


       Bakinta ya bude mata tana fushi dan ya bata wahala a kokawar da sukayi dazu.

     Jikin kofar taje tare da canja murya ta fara kukan saniya,Omar ma wajen kofar yazo yayi kukan akuya,ya canja murya yace bil'adama Ku kiyaye mu,kuna takura mana nan kasuwarmu ce ta kayan miya,

        Iklas ta makale murya anan har hanjin tururuwa muke siyarwa, dariyarsu kawai suke dannewa,Omar yace daga yau sai karfe 10 na safe zaku dinga amfani da dakin nan,Ku tabbatar kun bar dakin nan idan 9 na dare yayi,kuma baza mu illata muku jaririnku da Iklas ba domin sunfimu power,su mun yarda su dinga kwana a dakin,amma banda Ku.


     Iklas ta kara canja murya tare da cewa nasan Iklas wacce da take saida Apple da kwai mun San tarihinta yanzu sai mu fada muku,har kwandala ta furta lokacin da take nakuda,Omar shine Wanda akayi masa asiri ya bar gida dan a zalunceshi.......


      Mama ta kame a jikin kofa jikinta sai bari yakeyi kamar mazari,Ummi tace wlh mutanen boye ne,kara sukaji an kwalla Iklas sai Chinese sukeyi da Omar tana lallai yau zan sha jinin biladama.


    Ai su Ummi suna jin haka suka zura da gudu dakin Ummi tare da danna key,suka fara lazimi kala kala bayan sun dan nutsu Mama tace kinji wani gurnani da sukeyi,Ummi tace har tarihin Iklas da Umaru sun sani kaf idan ba mutanen boye ba wa zai San wannan.sai tattaunawa sukeyi kan aljanu,Mama tace uhm muyi shuru kin San zasu iya jinmu.


     Omar da Iklas dariya sukeyi har kasa tare da  tafawa,wlh kin kawo solution gobe mu nuna bamu San komai ba,kinga 9pm Mama zata bar room din sai na zo mu rufe kofar muyi aljanun karya mu na kwasar sweet.

     Su Omar kwanciya sukayi makale da juna suka sha bacci,Mama kuwa tun a Daren ta sanarwa Baffa abinda ke faruwa,

    Gari na wayewa da asuba Omar yanayin Sallah ya fice daga room din ya koma nasa,


        Yana fita Iklas ta mike tayi tata sallar da azkar wai dan kar Omar ya gane ta fara sallah,shi yasa sai da ya fita tayi tata,su Mama har 11 na safe basu bude kofa ba,sai da rana ta fito sosai sannan suka fito,tare da zaman jiran Baffa dan yace yana hanya,

     Omar ne ya fito sanye da shiga ta alfarma,yasha farar shadda,yana kasaita sai kamshi yakeyi,su Ummi ya gani a Palo sunyi jugum kamar masu zaman makoki ko breakfast Mama bata yi ba,

     Har kasa ya tsuguna yana danne dariyarsa ya gaishesu,sannan yace lfy wai na ganku haka?inafa lafiya Umaru cewar Ummi, jiya mutanen boye sun hanamu bacci, tamke fuska Omar yayi da alamar tsoro a ina kenan Mama,? dakina Babana da farko ina bacci naji wani abu kamar buhun shinkafa an jefamin a jikina,za a karyani,

    Hangame baki Omar yayi tare da dudduba jikin Mama yana mata sannu,kar kaso kaji yanda aka dinga buge buge da ihu a ciki,murya kala kala,Omar yace tab wannan sai ifiritai,


    Ummi tace har tarihinku suka bamu jiya wata dariya ce ta kama Omar da kyar ya iya dannewa, a firgice kamar gaske yace ummi Prince, da matata ta? Mama tana jimami tare da karkada kai tace kayya Babana sai abinda Allah yayi dasu,dan ciki suka kullesu da kwado,securities ma kasa komai sukayi.


  Kafin Mama ta karasa amma Baku taso ni ba?cewar omar, ina daki ina bacci,kai umaru har wajenka munje bamu ga kowa ba,Omar yace kundai firgice ne kawai amma ni ina bed ina baccina,Mama tace gaskia a tsorace muke baza mu gane ba.

  Fiya fiya kamar Omar zai tashi sama ya haura sama tare da cewa yarona da Mamatata,


       Iklas tana labe tana jinsu sai dariya takeyi a hanya suka hadu da Omar itama sanye da farin material sai kamshi takeyi tasha kwalliyarta,hugging dinta Omar yayi tare da sheka dariya,yana ina prince?yana wajen karime tana masa wanka,

    Rike da hannun juna suka sakko kasa, da sauri su Ummi suka tari Iklas suna me ya faru ince ko jiya basuyi muku komai ba?Iklas ta kallesu mene ya faru lafiya? Mama tace jiya ke baki ji komai ba? nifa ban gane ba Mama abinda ni ko farkawa ma banyi ba,saida na makara a sallah ma,Allahu Akbar Cewar Omar,Ina yaron?cewar Mama yana wajen karime tana shiryashi,


        Alhmdllh Mama take maimaitawa,Omar yace wifey muje yau mu zamuyi abincin Breakfast, Mama tunda tsoron room dinki kikeyi ki koma na Baffa kawai,haka za ayi Babana cewar Mama, Mama har tausayi ta bawa Omar da Iklas yanda take a tsorace.

    Wani Daren ma haka suka taru a kofar room din Mama, Omar dauke da Prince, Iklas,Mama, Ummi, Baffa da sauran securities tun 9pm suke jira har 12am basu ga komai ya faru ba a dakin Mama,Baffa ne yaja tsaki yace kai kowa yaje ya kwanta kun bata mana lokaci,baga Iklas nan ba mene abun tsoro?

  Da kyar Baffa da Omar suka kwantarwa da Mama hankali ta yarda ta koma dakinta,

    Iklas ta matsa kusa da Omar can kasa tace Allah kiyaye Gaba, mintsininta Omar yayi kadan a cikinta,yayin da kowa ya watse ya barsu,lips dinta ya kamo tare da tsotsa kadan ya mata Good night ta karbi Prince tayi cikin room din Mama.wanka Mama tayi ta shirya sai wajen Baffa,ta zata Iklas tayi bacci,harda sanda.


       Tana fita Iklas ta kunna wayarta za tayi karatun novel kiran Omar ya shigo,tana dagawa yace ina Prince dina?wato prince ma kazo nema ko?yayi bacci tun dazu,mama fa? Ta fita cewar Iklas,a firgice yace tsoro ne har yanzu?calm down tana wajen baffa har wanka ma tayi,

    Murmushi yayi yace hmm to ko nazo? Cewar Omar da sauri Iklas tace no karka jawo min pls kayi bacci.matsoraciya kawai,ae naji din,to yimin wani abu nayi bacci,nan Iklas ta dinga zuba masa sweet word masu girma da tsada,wasu ma kunne bazai dauka ba shima haka,daga cewa za ayi bacci sai da suka kai 2 na dare suna waya.


    Police ne sukayi sallama a gidan Sadiya tare da tasa keyarta zuwa station saboda an samu nasarar cafke yan ta'addan da ta taba sawa su kashe mata Omar, ana kamasu suka kala mata sharri cewar itace uwar dakinsu,dan haka aka kama da ita.kwanan Sadiya 5 a sell Omar ya biya kudi me yawan gaske aka saketa da kyar.

   Mijinta ma yayi nasa kokarin wajen kareta akan case din.

    Bangaren Aisha kuwa mijinta yace tunda Allah ya shiryeshi ya daina harkan banzan da yakeyi zai kara aure, mace daya baza ta isheshi ba,ya nemo wata yar santaleliya zai aura me suna Zakiyya.Aisha tayi kuka tayi bakin ciki ta gaji.ta saduda ta fawwalawa Allah,Baffa ya nemo su ya hada kan yaransa tare da yi musu Nasiha me ratsa jiki.

    Najja kuwa cewa tayi Baffa nima ance za a turo,ok ko me ake ciki ki fadawa Mama cewar Baffa,a nutse tace to Baffa. Su Najja anga duniya ta fito da miji itama kwanan nan za a sha biki.


     Yau Iklas kwananta 35 tayi arba'in,gyaran jiki ta shashi in and out,ta kara kyau kyan diri ta karashi,yayin da Omar yake Neman zaucewa sabo da Iklas bata yarda yayi xxx sai dai romance kawai,suyi fada su shirya,yayi fushin ya hada dabara da salon wayo har yau bai yi aiki akan Iklas ba,yanzu ya canja shawara.ya gaji ya matsu Mama ta bashi matarsa su koma gidansu,gashi taki yarda dan Mama ce masa takeyi sai Iklas tayi 2mnths zata bashi ita su tafi.shi kuwa yace bazai yiwu ba gaskiya.


 Yauma kamar kullum Iklas tana baccinta dakin Mama yanda suka saba,Mama na bisa katifa tana Bacci Omar ya lallabo dakin daga shi sai boxers dan firit,ba tare da bata lokaci ba ya sunkuci Iklas tare da toshe mata baki sosai,

     Zai tafi jin kamar taku yasa Mama ta farka,ga duhu a dakin kafafun mutum kawai ta Iya ganewa sai ta daga kanta ta kalli sama,sabo da duhu Sai taga mirjejen katon namiji tsaya a kanta,

   Dan danan Mama ta tuno da Aljanun kwanaki da rarrafe ta fita waje tana fita ta mike tare da gudunta tako tako tayi dakin Ummi,karar Iklas taji tace wayyo Mama Ki dawo wlh Omar ne yazo zai saceni.

    Omar takaici ya rufeshi yanda Iklas ta kwace bakinta daya toshe ta tona musu asiri,yanzu Mama zata gane sune aljanun baya,watakil tayi fishi ta hanashi matarsa,amma da ace zata bashi matarsa su tafi da fine and Good.

     Kunya yaji kar Mama ta ganshi cikin sauri ya saki Iklas a kasa da sauri ya bi hanyar part dinsa,Mama na shawo kwana shima yasha tasa kwanar,kawai hango bayansa Mama tayi ya shige room dinsa,

    Cikin fushi Mama ta shiga room dinta,a ranta tana da alama yaran nan ne suka firgita mu rannan amma suka raina mana hankali,ita da kanta Mama da ta tuno sai da abin ya bata dariya,wato Iklas ce tayi Muryar mace nan har Hanjin tururuwa muna siyarwa.

     Mama a ranta take zancenta tace Allah kaimu gobe zaku bar gidan nan da sassafe ma kuwa.


    Iklas ta koma kan bed tayi luf,tunda taji Mama shuru to tasan tabbas ta ganosu.

    Sai juyi takeyi tana sake saken da wanne ido zata kalli Mama gobe.

     Gari na wayewa Mama tana idar da Sallar asuba ta hadawa Iklas kayanta da tasan suna dakinta kaf,

    Wajen Ummi ta shiga ta sanar mata,Ummi ma dariya takeyi sosai nan ma ta hada kayan Iklas kaf,


      Duk wani kayan Iklas saida suka hada tun kafin garin yayi haske,dakin Omar ma mama ta tattaro nasa duka gaba daya.

   Wasu yan aiki Mama ta tura Gidan Omar duk da neat yake saida tasa su suka kara gyara gidan,ko ina ya dau kamshi da kyalli sannan suka dawo,


      Kayan Iklas dana Omar duk an zubasu a mota tasa  driver ya kai can gidansu,

 Omar yayi wanka sai mamaki yakeyi ba kayansa har turarukansa,komai sai guda daya aka bari na sawar yanzu.

    Haka ya shirya cikin wani danyen yadi Milk color,ya fesa turaren da mama ta bari,ya sa takalminsa ya fito sai soshe soshe yakeyi na kunya,Ummi,Mama, Baffa dasu najja gaba daya suna palon suna hira,

   Iklas ma haka ta sanya sabuwar red atamfar da mama ta bar mata,jiya me dinki ya kawosu,gyale da takalmi,sai kayan kwalliyarta,haka ma Prince,shiryawa sukayi ta fito itama,prince dauke a kafadarta,ta sha uban kyau sai kamshi sukeyi


     Sai kunya takeji haka suka gaisa ko kallon Omar batayi ba, shi kuwa kamar zai hadiyesu,mamace tace ga breakfast can sai kuje kuci,ko hanjin turuwar zaku soya abinku?

   Baffa ne yayi magana yace a'a kar ki damar min yara,ki bari suci su tafi kinzo kina tsokanarsu bayan ke kikayi abin tsokanar.

   Mukus su Omar sukayi,Ummi tace da kin sani baki basu abincinba wlh.

     Ku wuce kuyi sauri kuci ku tafi kuje gidanku kuji dadin yin aljanun a can cewar Baffa.

   Najja ce ta karbi Prince a hannun Iklas tana masa wasa tana Anty Iklas kinyi kyau wlh,murmushi Iklas tayi tare da cewa tnx tawajena.


     Omar kuwa farin ciki ya cika shi yayin da Iklas ta fara hawaye tana cin abinci Omar na kallonta tana kuka.kallonta yayi kuma karki yi tunanin ni sai dare zanyi abu kin San ko first night banyi ba sai first day dan haka ki zama ready bana harka sai dare.

   Kuma zaki San kin min laifi duk sai na fanshe,


   Kuka Iklas keyi Mama tana kuyi sauri fa,Har wajen Mama Iklas tazo tana rokonta,Mama tace ki rufawa kanki asiri kafin na miki hukunci me tsauri ku bar gidan nan.

   Omar ma yana gamawa yace Mama zamu tafi....dallah rufe mana baki cewar Ummi, Baffa yace kaga ku masu laifi ne ku tafi ya fi muku sauki,

    Har mota Najja ta rakasu da Prince driver ya ja su sai gidansu,Iklas hawaye wani na bin wani,tace to....to....dan...Allah...kasa ....ayi min...Allurar family planning.





AsmaBaffa




Tnx alot

ⓂⓂⓂ

   MA'AIKACIYAR 

       GOMNATI

        ⓂⓂⓂ


         210-215




By

AsmaBaffa



My best fan ever MAMAN WALEEDA Allah baki lafiya ameen.kullum muna miki addua missed u much more, wish u quick recovery.




    

        Pls ka kaini hospital ko Allura ayi min,kar na samu ciki da Wuri kaga Prince ko girma baiyi ba,kar muzo a sami matsala,I knw kana da ilmi kan hakan,sai kaga an samu ciki ga yaro na shan nono yayi ta cuta ya samu matsala ko mu rasashi gabaya gashi bamu da tabbas da Wanda zamu haifa gaba.

    Omar ya nutsu yana jinta,maganarta gaskiyace amma shi yasa son yara,musamman da ya Dade da yin aure bai ajiye ko daya ba,

   Kallonta yayi tare da lumshe ido,jawota yayi jikinsa yana share mata hawayen yace bari muje hospital muji shawarar Sultan.


   Driver yayiwa umarnin zuwa asibitin Sultan,a office suka sameshi,Bayan Omar ya masa bayani,Sultan yace is Good ayi mata,kasan ta masu tsohuwar haihuwa daban ta masu sabuwa daban,za ayi mata Allura,idan bata karbeta ba sai a canja wani kalar,idan tana so ta samu ciki sai a daina,haka kuwa Sultan yazo tare da zuko ruwan allura zaiyi mata a hannu,

   Omar yace hey dakata malam ka nemo mace tayi mata baza ka taba min mataba,dariya Sultan yayi to sir ai ba taba ta zanyi ba kawai yi zanyi ba tare da ko yatsa ya dangwala jikinta ba,

   A'a wlh a nemo mace salon kaga kalar skin dinta cewar Omar,Allah shiryeka Frnd da wannan bakin kishin cewar sultan.

    Mace aka nemo tayi mata ya basu date a rubuce time inya cika ta dawo,Iklas sai murna takeyi tare da cewa a gaishe min da Yasmin ina nan zuwa insha'Allah,kuma kacewa Raj kwana biyu ko leko prince dansa baizo ya ganshi ba,nayi fushi.to Allah kawoki lfy,kuma zan fada masa,Ina Babyn namu?cewar Sultan.

    Da murmushi Iklas tace yana mota.OK ai gaidashi, zaiji tnx a lot.

    Sallama sukayiwa Sultan suka wuce cikin mota hannunsu rike da juna,sai kallon hadaddu akeyi a wajen,duk inda sukayi idon mutane kamar zai fado.

    Mota suka shiga sai wani suya sport,Gomnati ta kalleshi da mamaki me zaka siya?yanzu mukayi breakfast,da sassafen nan me zamuyi dashi?murmushj yayi wai ke baki san ke amarya bace yau?to amarya da ango ne a motar nan idan kin manta na tuna miki,

   Baki ta tabe tare da yatsina fuska awai abinda ka shanye amarcinka,wannan me jegon da batayi arba'in bace,ke kike ganin haka,amma ni kinfi budurwa a wajena,Iklas wani dadi taji amma a fili harda dauke kai tana yatsina fuska,yatsunta Omar ya fara murzawa yana ko kin San duk duniya sun tabbatar virgin bata da sweet sai dai ma wahala da zata sha shima dole zai sha wahala,duk da namijin zaiji dadi.amfanin mutum ya samu virgin shine idan dashi ta fara shi zai iya bi da ita,amma misali ka samu bazawara ko wacce ta nemi mazan banza dama ba dakai ta fara ba,maybe Wanda ta sani ya fika zama active ya iya gingering dinta,wani kuma ta saba da lazy ne kai kuma gwarzo ne sai ki ga ka kasa control dinta,tana samun matsala,but idan virgin ka aura baka da matsala,Kwanciya Iklas tayi a jikinsa tare da cewa to Allah ya shirya mata masu bada Kansu tun a waje,sabo da rudun duniya,da rashin yin addini,zakaga da yawa mata musamman yanzu addini bai damesu,ga ilmin ba a amfani dashi,sallah a dinga sha ruwan dai dai,wasu basayi budurwa katuwa bata sallah bare sauran addini,shi yasa shedan yake saurin samun nasara Kansu,amma in mutum na daurewa yayi sai kaga ko yanaso Allah ya kareshi bai aikata,idan ma yayi sai Allah ya shiryeshi ya daina.

    Wooooh sai wifey akwai wa'azin duniya,na fada miki da Arabic schl kika dace,ko na samo miki kiyi degree?boye fuskarta tayi ajikinsa a hankali tace ae inaso,angama Gomnati ikon Allah,


     Suna zuwa gida Iklas ta kwantar da Prince a bed dinsa ta fara shirya kayan sawarsu nata Dana Omar, Omar kuwa kayan jikinsa ya cire daga sai short ya karaso wajen Iklas,Yan matana a ajiye shirya kayan nan kizo muyi baccin rana pls,na gaji yanzu hutawa zanyi,

     Yanzu fa ka tashi daga bacci karfe nawa yanzu da barin gidan mama?to ni baccin hantsi zanyi kuma kin San ni bana iya bacci ni kadai idan kina kusa,

     Muje manniru cewar Iklas,Omar kayanta ya cire mata tare da shigewa da ita blanket,ya haukace gaba daya,itama ya gama gigitata,kawai shagalinsu sukeyi,yana gab da samun abinda yake so wayarsa ta fara ruri,ko saurararta baiyi ba,nacin kira aka dinga yi cike da jin haushi yayi tsaki tare da dagawa ko duba wa ya kira baiyi ba yace hello cike da dashewar murya,muryarsa sai rawa takeyi,duf yaji ba a ji magana ba,cike da masifa yace wai who is on the line,Sadiyace ta fara ina..ina ya..ya..Omar nice Sadiya sis fa,

    Kamar zai daketa yace to kuma ke baki da hankali ki dinga kiran mutum cikin tsakar dare ko kunya ba kyaji,sauri ki fada min abinda zaki fada min kafin na kashe wayata,


     Yaya yanzu fa 11am zaka kace tsakar dare lafiya kuwa,dama shirmen daya sa kika kirani kenan?no dama kira nayi mu gaisa,da Sauri yace to na gode I wl call u back,ya kashe dit ko ajiye wayar baiyi ba kiran Raj ya shigo shima dagawa yayi uban mene kuma?zan kiraka back malam ya kashe .

 

      Yaci gaba da harkoki waya sai kara takeyi nan ma Raj ne still a fili yace jakai sai kuyi tayi,ranar Iklas tasha wahala karshe wanka kawai sukeyi suyi Sallah Omar ya Dora daga inda ya tsaya,kamar engine, sai da ya cinye yinin tas,har kuka Gomnati tayi,yace dama na fada miki duk rashin kunyar da kika min da karyar baki fara Sallah ba sai na fanshe,


    Haba wacce karya nayi?kina musu?cewar Omar bari ki gani,labtop dinsa ya dakko ya kunna mata video dinta tun daga ranar da ta fara Sallah,shuru tayi tare da mamakin abun,a kiyaye gaba cewar Omar,murmushi tayi lallai honey ka iya wayo,shi yasa ka jawo Mama ta koremu gida.

   Kwanan su uku Omar ya kai Gomnati yawo suka dinga yawon gaida yan uwa,frnds da abokan arziki sai da sukayi 1wk kullum sai sun fita zuwa gidan wasu.


   Admission Omar ya samowa Iklas a wata private university tana karanta Arabic English, Iklas fa an kara girma da kyau,Prince ma haka,yaro jajir dashi,zai wayon tsiya.

   A kwana a tashi Iklas ta gama level 1 sunyi Hutu Omar ya biya musu aikin hajj,suna gama hajj ya kaita kasar libiya wajen yan uwanta,daga can suka wuce Russia suka kwashi amarcinsu sannan suka dawo gida Nigeria, Omar yanzu har Office yake zuwa da Iklas yana nuna mata yanda aiki yake,har tayashi tanayi,idan taje schl ta dawo sai ta biya wajen Omar a Office,duk wani company da aikin da Omar keyi,da meeting ko wani abu indai Omar zaije kafarsa kafar Iklas,


     Iklas yanzu rubuce rubuce ya dawo,ga buga Lissafi nawa ne ya shiga company nawa ne ya fita,kaza yana bukatar kaza,watarana kuma harkar boko akeyi,Sadiya ma dasu naja an basu wasu companies na Baffa suna kula dasu kuma sosai suke kawo masa ci gaba.Baffa da Omar sun yaba da aikinsu,


     Sahar kuwa har yau abin ba sauki domin yau ma Daddy zai fita ta fito da gudu gaban driver Daddy ta bankade zaninta duk da Mum ta sa mata dogon wando saida ta cire wandon ta karasa wajen driver tace malam zaka siya,

   Ko kallonta driver baiyi ba a ransa ya dinga fadin Aradu bani son kalar naki,wannan in banda tsamin dauda me zaiyi wannan sai dai abokina SULE SHAGALI nasan shi kowa tasa ce,da shine da tuni aikin gama ya gama.Daddy ne ya katse masa tunaninsa yanda ya zage yana kuka yana dukan Sahar tare da nadamar irin tarbiyar da suka bawa yarsu gashi su abun yake damu,Tunda Daddy ya fara dukan Iklas bai tsaya ba saida ya karya mata kafa.da kyar aka rirrikeshi,Mum ma sai kuka takeyi tare da daukan Sahar ta wuce asibiti da ita.

    Satin Sahar Uku  a hospital ta warke, sosai Mum da Daddy suka koma ga Allah ba dare ba rana suna addua Allah bawa Sahar lfy.


      Ai kuwa ba a Dade ba Allah ya amsa Adduarsu Sahar ta warke ta daina komai da takeyi,tayi nadamar halinta,Daddy Mum da Sahar Har gidan  Omar sukaje tare da Neman gafararsa,ya yafe mata sannan Daddy ya daura auren Sahar da driver dinsa MUSA KASHE KALA.

    driver yanzu yaga Sahar tana cakarewa ya like mata ya manne mata.. 

   Sahar kuwa sai kuka takeyi tare da Nadamar abinda tayiwa Omar, gashi yanzu ya ta auri driver,kalli kyan hali,kyan sura,kudi irin na Omar amma tayi watsi da damarta,gashi ya samu wacce ta fita, ita kuma ta kare a wajen MUSA KASHE KALA, Allah ma ya taimaketa musa ya dan waye,gashi dan 39yrs ne kuma dan wanka ne shi yasa ake ce masa Kashe Kala.Iklas sabo da taga kwakwaf har bikin saida taje tare dasu Jannat,Diyar,khady chafe etc


     Daddyn Sahar gida da jari ya bawa Kashe kala,Sahar kuma ya gina mata hospital dinta na kanta,ko kadan bata kaunar kashe Kala,saboda gara ne amma ba yanda ta iya haka ta godewa Allah tare da yiwa kashe kala biyayya.

   Kashe kala kuwa baya daukan raini kuma bashi da hakuri shi yasa kullum cin uban Sahar yakeyi ya zazzageta tas.yana cewa ya taimaka mata an lika masa ita.sai dai tayi kuka ta ce Duniya kenan.


    Sahar ta jawowa kanta akan son zuciya ta dauki aikin Gomnati yafi mijinta da aure daraja gashi ta koma Neman maza da aurenta yanda kuma take abubuwa da yawa Wanda bai dace matar aure tayi ba,koma budurwa ce bai dace ba,Batsa da mazan wajen aikinsu,shigar banza da nuna tsaraici,da mu'amula da kawayen banza,gashi yanda ta kare mata a wajen kashe Kala da kullim bata da daraja a idonsa sai zagi da cin mutunci,kullum cikin kuka take,gashi bata son Musa kashe kala kuma dole ta zauna dashi,

      Shekara daya da aure Sahar ta haifi yarta mace me katon hanci da rankwalelen Kai me kama da kashe Kala sak kamar Ubanta.lol


    Jannat ma ta Haifi danta namiji rangadede,yayinda Sultan yarsa take tafiya dagwai dagwai,Raj na nan da Amaryar da tsohon cikinta,Mama kuwa sun tafi Russia ita da Baffa tare da suleim da Suhaila sunje Hutu can,Ummi ke kula da komai na gidan.


    Iklas kwance jikin Omar,Prince yana gefe a kan dan kekensa yana wasa,Omar ne ya kalli Iklas my heart ya kamata tunda kin yaye Prince kin kusa gama schl a haifo min wani Baby girl din,turbune fuska tayi tare da shagwaba ni..ni Allah ba yanzu ba,yau she na yayeshi?ka bari na karasa schl,shikenan bari sai na karo aure cewar Omar,tasan tsokanace tace baka Isa ba yaro ,murmushi Omar yayi tare da cewa nine yaron naki?nawa kake? Da nawa ka girmeni?dariya Omar yayi lallai kin isa wifey,

     Murmushi tayi kaima kasan ba wani girmata kayi ba,shike nan za ki gani za a tantance cewar Omar,ya dauke Prince ya kaiwa Karime me kula dashi tare da daukan Gomnati cak yayi cikin bedroom da ita, dama tsokanarka nakeyi ni din banza,nawa nake,kwananan na daina shan nono wajen mamata,kai ai babban yaya ne.Dariya Omar yayi tare da cewa ai baki isa ba yarinya sai an banbance dole Iklas ta bada hadin kai ranar ai ta gogu wajen Oga.


     Omar ne ya fadawa Sultan cewar idan sunzo Allurar Iklas da ake mata ta planning su dinga yi mata Allurar Paracetamol a cewar ta Planning ce sai dai ta ganta da ciki.




AsmaBaffa 


      Readers gobe zai zama last page na wannan novel insha'allah

ⓂⓂⓂ

   MA'AIKACIYAR

        GOMNATI

     

          215-20




By

AsmaBaffa





         FINAL(KARSHE)





      Sai da Iklas ta kwashe  3mnths tana zuwa Allurarta amma sai Sultan ya bada paracetamol injection ayi mata ta dawo tana ta murna,Omar kuwa yayi luf,

 1mnth da akayi mata ta Paracetamol sai taga tana period,da kuwa bata period,amma jin ance ai wasu komai planning basa daina period sai ta dauka itama haka take

  Ko da ta yiwa Omar magana yace ai haka kike Gomnati,kalarki ce haka.


    Yau ma date ya cika zata je Allura,malama Iklas sai dadi takeji ganin Omar ya yarda ya share zancen haihuwa ma kwata kwata ya daina cewa yana so ta haihu,sai dai ma ya dinga kara mata haske akan ingancin Family planning,Iklas kuwa har wani nishadi take ji,dan haka da safe 11pm bayan tayiwa Omar breakfast ya wuce office bacci ta koma,sai 2 ta tashi tayi sallah tare da gyara inda masu aiki basa shiga,aka shiga kitchen ta shirya girke girkenta,

    prince tafiya yakeyi ko ina,bashi da fara'a ko daya sai a wajen uwarsa da Daddy nan zaka ga dariyar Prince,ubansa ya gado wajen hade rai sai gaban Iklas da su mama xa asan ya iya dariya,

    Ga masifa yaron irin uwarsa Iklas,baya Barin ko ta kwana,abin yayi masa yawa,gashi comedian ne idan yaga dama kajifa dan yaro .

    

    Karime ce ta shirya Prince,cikin jean blue pencil da farar Riga yasha kyau.

  Iklas ma an dau wanka tasha wata arniyar shadda light blue doguwar Riga taji aiki,su Gomnati an girma tayi tsayi da yar kiba,ga hasken data kara.

    3pm Omar ya shigo,Gomanti ce ta hana Omar shigowa palon tare da kwalawa Karime kira,zo ki dauke prince baba Karime.

    Da sauri Baba Karime ta dauke Prince suka bar palon,Iklas harda zuge labile tare da danewa jikin Omar ya kusa kaiwa kasa,sabo da Kyan da Iklas tayi ga kamshinta gashi ta bashi wawar runguma,kamar ya sume haka yaji


    Gomnati harda Oyoyo honey,sannu da zuwa honey,an siyomana Banana?yanda take rerawa kamar irin yaran nan,sai murna takeyi kamar yau ta fara ganin Omar a duniya,kullum haka takeyi kamar ranar ta fara ganinsa kamar zata tashi sama,

         Omar kuwa wani mayen kallo yake mata tare da lumshe ido shi kam yayi dace. Suna rungume da juna a bakin kofar ya tallafo mazaunai yana shafasu Wifey naji kinyi nauyi da kiba,kibarki yanzu kin tashi daga Balarabiya kin koma baturiya,ko dai cikin ne?murmushi tayi wasa kakeyi honey kasan bama wasa da Allurar nan fa,gaskiya ni kaina nafi so ki huta da yawa kar a kuma kira mana kwandala cewar Omar.

     Kaga oya muje ayi wanka kaci abinci muje hospital,kamar gaske Omar harda saurinsa sharp sharp yayi wanka, ya shirya shima light blue shadda irin ta Iklas ,da yazo cin abinci ma harda turawa da sauri da sauri,

    Iklas kuwa an dauko takalmi jaka da gyale tare da kulle kofofin bedroom,

    Prince ta karba, Omar ya jefa cewgum orbit a baki sukayi gaba tare da daukan Prince,Prince yana Daddy a caukeni,basu kulashi ba,jakar Iklas ma tana hannun Omar ya rike mata,

    Yau Omar ne driver,Prince yana baya,Iklas an kame a gaba,sai asibitin Sultan,Suna zuwa Sultan sai dariya sukeyi da Omar suna magana kasa kasa,Iklas ta zata labarine yayi dadi,Sultan ya karbi Prince yana masa wasa,yace madam zamu gwadaki muga ya yanayin Allurar take a jikinki,je toilet din can ki bamu fitsarinki,

   

      Yana aunawa yaga Iklas tana da cikin wata daya,a sirri ya fadawa Omar,ita kuma yace Madam gaskiya allurar ta karbeki kwarai,baki da matsala,nan yasa aka yi mata paracetamol dinta cewar ba matsala.


     Gomnati sai murna har suka dawo gida tayi wanka tasa rigarta iya Rabin cinya me siririn hannu,Omar already yana Palo shida Prince suna wasa,

     Iklas na zuwa tace kayi wanka baka bada Prince an masa ba,Karime ta kaiwa shi maza a shirya shi Baba.

   Ta dawo wajen Oganta,a kasa suka kwanta kanta yana kirjin. Omar,sai wasa yake da dukiyar fulaninta,kai my heart kamar ciki komai ya ciko,mika Iklas tayi lafiyayya tace jin dadine kawai,karfa Allah ya nuna mana ishara ya baki cikin kuma ana Allurar,hmm Honey kenan ka kwantar Da hankalinka ba wani ciki,haka ake ciki ba cuta r laulayi?ni rawa ma nake son yi,remote ta dauk tare da danna kida,

    Omar ne ya karbi remote ya canja waka tare da karo vol na speaker yace oya tashi kimin wannan rawar, to ai slow music ne sai dai in ka mike tsaya saboda wannan rawar kalarta kenan ya dace ace da namiji,


      Kawai kimin na gani pls cewar Omar nanfa Iklas har bending down takeyi a slow,omar ya tuna tana da ciki kar ya zube,ya kashe kidan du,Gomnati zo kiji wata magana?tana zuwa ya dauketa yayi ciki da Ita suka Lula wata duniyar ta ma'aurata.

 

     Omar ya kara mannewa Iklas saboda cikin ya kara sa mata wani sweet din daban,Iklas ta kammala degree dinta,yayinda take zuwa office din Omar yawanci tare sukeyin aikin,aikin Hajji da Umrah sunje da yawa,yau Omar yana Office Iklas ta hade cikin wani unique material kamar yan mata,ta shirya girkinta a dan wani basket me tsananin kyau,prince yana wurin Baba Karime,driver ne ya kaita Office din Omar,tana zuwa building din mutane sai gaisuwa ake kaiwa,yayin da Omar yace sunanta Gomnati,kowa da Gomnati yasan Iklas,ya fito mutane yaransa suna take masa baya zaije Sallah,ya hango motar Iklas an kawota,da Sauri ya sallami mutanen ya karasa wajen motar cike da takama,dakansa ya bude mata ta fito,hugging dinta yayi,wata siririyar sukaji tayi musu sallama,juyawa sukayi dan ganin ko wacce,wata yar budurwa ce zata kai 25yrs sai mayen kallo takewa Omar tare da cewa sunana xahra Eabraheem,ina aiki a company ka,pls ko zan iya ganinka,

     Wani matsiyacin kallon Omar yayi mata tare da Kallon Gomnatinsa sannan yace ki tambayi my heart idan ta yarda fine,Iklas wacce ta gama kumbura sabo da kishi matsawa tayi jikin Omar har dagen kafa takeyi wai dole sai ta kareshi Xahra na kalle mata miji,Da masifa Iklas tace u r fired from ths company as from 2day kar na kara ganinki,


     Allah sarki Xahra ta jawowa kanta kuka ta farayi tana ba da hakuri,Omar yace my peace a barta pls,ba tare da Iklas ta kalleashi ba tace baka da wannan damar yaro,dariya Omar yayi yanda Iklas ke kuri da nuna takama kamar company ta

       Yace kalli mutane yanda suke bina suna biyayya ke kuwa yar cukula dake sai ki tamin tsiwa,baki ta turo cike da shagwaba ni a haka kake zuwar min? zigidir kake zuwa duk wani tabo dake jikinka na sani,su kuwa fa sai ka dau wanka,

   Hanci ya lakuce mata tare da mika mata key din Office bari nayi Sallah kar na rasa jam'i,kiss ya manna mata a goshi sannan ya wuce,


    Xahra ce ta karaso wajen Iklas tana rokonta akan a yafe mata,karki damu amma dole na canja miki Company,gaba Iklas tayi da basket dinta na food tace wa Xahra follow me,

     A kujerar Omar ta Office ta zauna tana juyaya da ita nan take tayiwa Xahra transfer zuwa company da Sadiya ke kula dashi,sai godiya take.

     Tunda Iklas ta zauna take faman shigar da kudi ta computer tana calculation,Omar yana shigowa ta nuna masa komai sai murna yakeyi Gomnatinsa wise ce,


         Iklas yanzu ta mallaki kadarori da dama,sosai take juya kudade itama,Suhaila da Ummi sai abinda suke so take musu,frnds,da dangin mijinta du tana kyautata musu da arzikinta da karfinta,har tallafi take kaiwa gidan marayu tare da Dora Omar akan harkar taimakon talakawa sosai,

     Gidan Kajin Mama wata rantsatsiyar mota ce ta shigo bayan mintuna Omar ya fito cikin shiga ta Alfarma kamar wani sarki,budewa Iklas yayi ta fito wow Iklas ta gama zama queen,handbag dunta na hannun Omar,Prince ma yana gabansu ya hade sosai,Iklas da yaron cikinta Wanda batasan tana dashi ba,

    Ma'aikatan sun San Iklas amma basu ganeta ba sun zata bakuwa ce tazo daga kasar larabawa,yanda suka ga Omar yana hugging dinta yasa suka gano matarsa ce,wani cikinsu yace daga Kuwait naji ance ya auro matarsa

    Sai da Iklas ta sanar dasu cewar Itace Gomnati me siyan Kwai da Apple,sai mamaki sukeyi suna tayata murna da farin ciki,wai dama Ashe Allah yayi itace matar Ogansu kamar wasa suka taba haduwa a wajen,har fada sukayi ranar,gashi Ashe har sun haifi Prince,

    Iklas Karin Abashi tasa Omar yayi musu,ita kuma ta raba musu kyautar kudi,sannan suka bar wajen,Ma'aikata sai Albarka suke sa mata sosai,tare da mijinta,ranar sunsha Addua.


    Iklas tana gidan Mama Omar ya barta ita da Prince suje su kwana daya,zai je gobe ya daukosu,Gomnati an baje  suna musu dasu Najja da Ummi sunce ciki ne da ita Gomnati tace lallai kuna bata bakinku,dan kunga na canja jin dadine mijina yana kula dani,ba wani ciki Omar yace sai nayi 5yrs zan kara haihuwa,gwara ku kyaleta cewar Mama.


    Shuru sukayi suka kyaleta,sunyi shirin kwanciya sai ga kiran Omar a wayar Iklas, hello honey? Kinga ba wani honey Ina compound fito mu tafi gida,kaifa kace na kwana honey, ae na sani ai na fasa yanzu,amma saida ka bari na fada musu,in ba so kike raina ya baci ba kawai ki bar musu Prince kizo mu tafi gida ko kuma nazo cikin gidan na daukeki,,


    Shagwaba ta fara yanzu dan Allah ka kyauta min?hmm zo muje gida kyayi shagwabar a can,dit ya kashe wayar,Kinga ki tashi kibi minji kar yazo yana yi mana rashin kunya da tijara a gidan nan akanki nasan yanzu kwa zama Aljanu cewar Ummi,

   Ikkas tana fushi ta dauki Jakarta da kayanta,ta barwa Prince nasa tayiwa Mama Sallama ta fita,


    Shiga motar tayi tana kumburi,Sorry my heart na kasa bacci ne shi yasa cewar Omar, Gomnati tace muje kawai nasan me kake so,amma baka kyauta min ba ka sani ko?haka kake min sai ka amincemin naje Unguwa yini ko kwana sai kace ka Fasa ka dawo ka daukeni,ko ka turo driver ya daukeni,

    Baza ki ganeba my liver bana gajiya dake ne,bana iya hakurin rashinki kusa dani, nima ai bana iya hakurin dakai kawai dai ina daurewane,ke kina iya daurewa ni kam ban iyawa wlh,na gaji ma Hutu zamu dauka muje london, a'a muje saudiya kaga an kusa aikin hajj  cewar Iklas, duk inda kike so ai nan Zamuje Gomnati ba a ja dake,

    Dukan wasa tayi masa kadan a kirji,ka gani ko ban son Tsokana,suna shiga gida da kyar suka iya shiga bedroom kamar zasu cinye juna tun daga compound,sun kwashi sabon Amarci a ranar.

   Abdallah an zama katon saurayi ya gama degree ya dawo,yayinda ya like shi Suhaila zai jira tayi Candy ya aureta,Itama Suhaila tana son Abdallah sosai.Suleim kuwa tace karatu zatayi me zurfi kamar Yaya Omar.Najja kuwa ansha bikinta Iklas sune kan gaba,amma Omar ya hanata sakewa,kullum yana like da abarsa, an kai najja Sokoto,ta auri wani local gvt chairman.

   Aisha ma ta kara haihuwar lafiyayyen da Namiji,Sadiya kuwa yanzu Allah ya bata ciki wata 2,mijinta kamar ya cinyeta,sauran kannensu su biyu suna part din Mama tana kula dasu.


    Iklas taga cikinta yana ta girma,gashi kamar alamar ciki take gani,tabbas su Ummi sunyi gaskiya,lallai maganar Omar cewar Allah ya nuna musu Ishara gata ana mata allurar planning gata da ciki yanzu,

    Kuka ta sakawa Omar daya dawo,wlh honey ciki ne dani na shiga Uku,

  Har asibiti Omar ya kaita aka tabbatar ya wuce 3mnths,Omar da kyar ya kwantar mata da hankali ta hakura,tasha kuka kuwa,Omar Sam bai nuna yasan tana da ciki ba tun tuni.biyeta ya dingayi yana lallashi da salon wayonsa harta hakura.


     A airport na Abuja Omar da Iklas suna manne da juna wannan tafiyar an bar Prince wurin su Mama,Jannat matar Saleem da tsohon cikinta zasu tafi egift suka gaisa da Iklas tare da wucewa wajen nasu screening din.

    Omar tun kafin a fara yi musu screening domin zuwa kasa me tsarki,yana wajen Iklas dinsa,minti 1,2 yazo ko kina bukatar ruwa?juice?snacks etc haka yake tayi ko yazo ya danyi Hugging dinta yana kissing dinta,a chair  ma daya zauna tana kan cinyarsa, yana ta lallabata,sai shagwaba take masa,tun mutane basa kallonsu har suke kallonsu suna sha'awarsu kamar wasu turawa ana zuba love,

    Tashi Omar yayi tare da dawowa wajen Gomnati dauke da ruwa Faro ya mika mata,kiss ta bashi a kumatu,wata tsohuwa ce ta matso kusa dasu ta fara zazzaga musu masifa,wannan aikin hajjin zakayi kuwa dan nan,wannan baza ka barta kuyi Ibada ba,kabi ka like mata,wani Iskanci ne wannan kana lasheta da tsotsa kamar tsohon maye,


    Kema da laifinki munafuka ke kike bashi hadin kai wannan bazai barki kuyi addini ba,,ka hana kanka ka hana wani ibada saboda Iskanci ya ratsaka, tsaki tsohuwa taja tare da komawa cikin mutane tana ci gaba,Maman Khayree ce tace dan Allah Iya ki kyalesu haka,irinkune kuke jawowa yara na muku rashin kunya,yo bazan fadi gaskiya ba fisibilillah yaran nan har karar tsotsa kakeji kamar suna shan alawa,mu bamu San wannan ba,ohh ni Delu karshen duniya yazo sai ta fashe da kuka,kaji fa tsohuwa da karfin hali.

    A jirgi ma Delu ta sawa su Omar Ido,idan Omar ya rungumo Iklas ko yayi wani abun sai Delu tayi masa dakuwa wato ambola,dariya take bawa su Omar ma

    

    Iklas ana Madina,ita kadaice yau ta koma hotel dinsu bayan ta dawo daga masallaci tayi Sallar Isha.

     Darul salam Hotel ta shiga har Room dinsu ita da Omar sai yatsina takeyi ta gaji,tana shiga Room dinsu Omar yana kwance yana hutawa da alama bai Dade da dawowa ba shima,Hi dear kawai tace tare da shigewa toilet,wanka da Brush tayi ta fito tayi shirin Bacci,shima Omar hakan yayi,tana zaune tana zuba kamshi tare da cin Apple,zuwa yayi ya zauns kusa da ita tare da rungumota jikinsa yace wifey najiki so silent,mene kara narke masa tayi tace wash na gaji massage nake so,

    Kwantar da ita yayi on bed flat ya Fara mata tausa me dadi,yaga ta fara masa bacci sai ya koma yi mata cakulkuli,nan ta fara dariya sosai,ba shiri ya tsaya tare da cewa me nake gani a hakorinki kamar Gold teeth guda daya a hakoran sama gefen right side?dariya Iklas tayi tare da cewa my King Hajiyayye kenan, na koma Hajiyayye nima,yau naje hospital aka samin,haba inta zuwa Sadiyya ko hakori daya babu,ya ka gani my King yayi ma kyau,idan baiyi ba baka so na cire,


    Omar Wanda ya tsaya ya kasa motsi saboda yanda hakorin makkan yayiwa Iklas mugun kyau,da Sauri yace no ina so kinga yanda yayi miki kyau kuwa wifey,I love it. Bakinta ya fara tsotsa kamar sweet,nan Iklas ta fara sarrafa Oganta Omar,kafin kace me sun zauce akan juna,nishin sweet tare da furtawa juna sweet words masu wuyar fassara da nauyin dauka ga me karamin kai.sunna suke daffakawa ba kama hannu kamar su hadiye Kansu.




      ALHAMDULILLAH


da Allah ya bani dama da ikon Kammala wannan littafi nawa,ina fata ya fadakar ya nishadantar tare da fatan kunji dadinsa masu karatu.


   Masu comments akan wannan littafin Ma'aikaciyar Gomnati,masu bibiyarsa kullum,da masu tambayarsa idan ba ayi posting ci gaba ba,duk kowa ma da kowa naga sakonku,bani da bakin Godiya Tsakanina daku sai Addua,naji dadi, nayi matukar farin ciki ba adadi.naso na sa Sunan duk wasu masu comment a Novel din nan domin karramaku readers amma ba time.gaba dayanku NA GODE NA GODE KWARAI 

  Allah ya biya muku bukatunku. Love u all.really miss u.kamar kar na daina typing wannan Novel wlh amma ba dama.Allah sarki Iklas da Omar dina.



Littafina me zuwa bayan sallah idan Allah ya kaimu da Rai da Lafiya shine:


     ✳CIRANIN AMANA✳


Ina fatan yafi MA'AIKACIYAR GOMNATI komai da komai Insha'Allah.


Allah sadamu da Alkhairinsa, Allah sa muyi azumi lafiya mu gama Lafiya.Allah ya Bamu lafiya me dorewa,ya Gafarta mana zunubanmu, ya Bamu Nisan kwana me amfani,ya samu a Aljanna,ya tseratar damu daga wuta,ya azurtamu da arziki me amfani duniya da Lahira.


     

   GODIYA DUBU DUBU MALALA GASHIN TINKIYA MUTANENA.




AsmaBaffa.

COMMENTS

Name

ADSENSE,4,Airtel,1,ANDROID,9,AQIDARMU Book 1 Complete Hausa Novel,1,AQIDARMU Book 2 Complete Hausa Novel,1,Arbitrade,4,Arbitrage,1,AUREN MU Complete Hausa Novel,1,Babban Yaya Hausa Novel Complete,1,Babu So Complete Hausa Novel,1,Bakar Inuwa Complete Hausa Novel,27,Billyn Abdul Novels,7,BLOGGING,13,Business online,10,Crypto currency,17,Dare Daya Hausa Novel Complete,1,Daudar Gora Book 1 Complete Hausa Novel,48,Daudar Gora Book 2 Complete Hausa Novel,95,DOWNLOAD,2,Duk Karfin Izzata Book 2 Complete Hausa Novel,34,Education,3,Email,1,Facebook,4,Finance,1,Furar Danko Book 2 Complete,9,Furar Danko Complete Hausa Novel,31,fyade hausa novel by maman teddy,1,fyade hausa novel Complete,1,Gidan Haya Hausa Novel Complete,6,Gidan Haya Complete Hausa Novel,4,Gidan Haya Hausa Novel,1,Gidan Kwarata Complete Hausa Novel,1,Glo,1,Google,1,GURBIN IDO Complete Hausa Novel,1,Hamshakiya Hausa Novel Complete,25,JARABABBEN NAMIJI Complete Hausa Novel,1,Jikar Maguzawa Complete Hausa Novel,23,Job,7,KASUWANCI NA Complete Hausa Novel,1,Layikan waya,2,Loan,8,MA'AIKACIYAR GOMNATI Complete Hausa Novel,1,Makauniyar Kaddara Complete Hausa Novel,70,Mufeedah Complete Hausa Novel,25,Namijin Zuma Complete Hausa Novel,26,nihaad complete,62,Nihaad Complete Hausa Novel,62,nihaad hausa novel,62,Npower,13,Pc Tools,2,Qamshi Hausa Novel Complete,14,Raina Kama Complete Hausa Novel,29,Sakayyah Book 2 Hausa Novel Complete,30,Sakayyah Hausa Novel Complete,60,SHAKUWAR YARINTA COMPLETE HAUSA NOVEL,20,Support,26,Tabarmar Kashi book 2,7,Teach and guide,8,TUMFAFIYA Complete Hausa Novel,1,TUMFAFIYA Hausa Novel,50,TUMFAFIYA Hausa Novel Complete,19,UNCLE DATTI Hausa Novel Complete,1,Watsapp,3,Waye Mijina Hausa Novel Complete,5,WEB LANGUAGE,1,WEB TUTORIAL,2,Yar Aikin Karuwai Book 1 Complete,1,Yar Aikin Karuwai Book 2,1,Yar Aikin Karuwai Hausa Novel,1,Yaya Mata Complete Hausa Novel,22,Zafafa Biyar Novels,7,
ltr
item
NAGARTA24 || job || npower || crypto currency || arbitrade || loan || teach and guide || support ||: MA'AIKACIYAR GOMNATI Complete Hausa Novel
MA'AIKACIYAR GOMNATI Complete Hausa Novel
https://blogger.googleusercontent.com/img/b/R29vZ2xl/AVvXsEjG65lcHKu9ef7VqM4hbIeoe5jimtxzT7pMG4e_sBOgVAtz5sTbNWWd4-JMl6VUoA-9gV2eSZWiyZHhA95cI7ZJBh09t2VZjg7anCAbCnGTxt4laip_KqZT5RbmA0yfOjmDBjfV46o2Yr8VWepY-A2StyjrRcFDYsMdm4hxpLXtviDx7HA1tfGM7qbqZwKL/s320/img_1696842015295.webp
https://blogger.googleusercontent.com/img/b/R29vZ2xl/AVvXsEjG65lcHKu9ef7VqM4hbIeoe5jimtxzT7pMG4e_sBOgVAtz5sTbNWWd4-JMl6VUoA-9gV2eSZWiyZHhA95cI7ZJBh09t2VZjg7anCAbCnGTxt4laip_KqZT5RbmA0yfOjmDBjfV46o2Yr8VWepY-A2StyjrRcFDYsMdm4hxpLXtviDx7HA1tfGM7qbqZwKL/s72-c/img_1696842015295.webp
NAGARTA24 || job || npower || crypto currency || arbitrade || loan || teach and guide || support ||
https://www.nagarta24.com.ng/2023/10/maaikaciyar-gomnati-complete-hausa-novel.html
https://www.nagarta24.com.ng/
https://www.nagarta24.com.ng/
https://www.nagarta24.com.ng/2023/10/maaikaciyar-gomnati-complete-hausa-novel.html
true
1779421581242976301
UTF-8
Loaded All Posts Not found any posts VIEW ALL Readmore Reply Cancel reply Delete By Home PAGES POSTS View All RECOMMENDED FOR YOU LABEL ARCHIVE SEARCH ALL POSTS Not found any post match with your request Back Home Sunday Monday Tuesday Wednesday Thursday Friday Saturday Sun Mon Tue Wed Thu Fri Sat January February March April May June July August September October November December Jan Feb Mar Apr May Jun Jul Aug Sep Oct Nov Dec just now 1 minute ago $$1$$ minutes ago 1 hour ago $$1$$ hours ago Yesterday $$1$$ days ago $$1$$ weeks ago more than 5 weeks ago Followers Follow THIS PREMIUM CONTENT IS LOCKED STEP 1: Share to a social network STEP 2: Click the link on your social network Copy All Code Select All Code All codes were copied to your clipboard Can not copy the codes / texts, please press [CTRL]+[C] (or CMD+C with Mac) to copy Table of Content