KASUWANCI NA Complete Hausa Novel

  [1/1, 10:17 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖 🌖🌖🌖🌖 COPY BY ZAINAB BUTALAWA    KASUWANCI NA

 


[1/1, 10:17 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖
COPY BY ZAINAB BUTALAWA
   KASUWANCI NA

  
              1



Official



By
AsmaBaffa




        BISMILLAH




     Alhmdllh fans Allah ya kara kawo mu sabon Novel dina KASUWANCI NA da fatan zaku bibiyeni muji yadda zai kasance,Fatana Allah yasa mu karu da juna,Allah yasa masa Albarka ya fadakar ya kuma nishadantar daku.ina matukar Godiya masoyana,masoya novels dina,masu sharhi musamman AsmaBaffa fans club,Taskar fiddausi sodangi,da kuma House of Hausa Novels ina miko dubun gaisuwa ta gareku na gode da Sharhi.
      
   Da fatan zaku ci gaba da Sharhi a kai Kai sabo da shine yake guiding writer ta rubuta muku me dadi da ma'ana,idan ba Sharhi baya tafiya dai dai,Dan Allah a dinga Sharhi fans ana nishadi musamman yan gp na.
    Akwai gps da dama da basa Sharhi ko tnx baza suyi ma ba,zaka ta musu posting shuru,sai ranar da ba ayi posting ba sai a fara neman novel ci gaba.duk gp din da basa cewa ko Hi zan daina musu posting wlh,da nayi daya biyu naji duf to shike nan sai suji duf nima🤣🤣

      Wannan page na farko na Sadaukar dashi gareki sweet frnd FLOWER.













         Kudin cinikin awarata nake irgawa duk da ba kudin arziki bane amma dukkansu daga yan goma sai yan biyar sai ko ashirin,kanwata na shiga kwalawa kira MEENAT wai baza ki fito ba sai na shigo na mareki,Maganar AMMA naji tana daga gefena a kwance saman yar tabarma tace Haba MUFEEDA ta wannan wacce masifa ce haka dan Allah ki dinga dagawa yaran nan kafa kannenki ne fa,Amma kina dai jin tun dazu nake jiransu su fito su tafi Islamiyya amma sai nauyi sukeyi kuma sun San cewar anjima zan soya Awara,gashi gobe zasu zo suna takura mana a basu kudin Break, to ai sai bisu a hankali dan Allah kinga ni ba lafiya ce dani ba kece komai nasu kece uwarsu kece Ubansu Mufeeda kece komai dinmu,Zuciyata ce tayi rauni nace to Amma ba komai na Dena kiyi hakuri Allah zai baki lafiya kinji,ga kudin nan Amman mu bari na gyara gidan na daura mana tuwo naga muna da ragowar garin masara,Murmushi Amma tayi tare da kallona tace Mufeeda Allah ya miki albarka Allah ya baku miji na gari,ya baku yara su rama muku abinda kukayi mana na alkhairi,Mufeeda yau shekarar babanku Sha uku da   bacewa,har yau ina Sa ran watarana zai bayyana da Zanfi kowa murna ya ganku Ku uku kun Zama yan mata gaku kyawawan gaske kamar indiyawa,musamman ke Mufeeda kunfi kama da Shuwa sosai mahaifinku kika biyo domin shine fari kamar balarabe haka yake har kin fishi Hasken fata ma,su kuma su Meenat sune masu kalata wato su ba farare ba su kuma ba wanda zai kira su bakake duk gaku Allah ya bani Ku kyawawa farare daku amma duk kyan nan sabo da talauci ko Sallama ban taba ji ance ana sanku ba,wanda na tabbata da masu kudi ne komai muni auruwa sukeyi,musamman ke Mufeeda kin kai har 16yrs amma nafi so na aurar dake tunda ba makaranta kike zuwa ba,Baki na turo gaba tare da sakin shagwaba ina shure shure kamar yarinya ina kukan sangarta Allah Nidai Amma bana son aure kuma ma nawa nake,hmmm Mufeena Mufee tawa ai gashi nan kin fara girma har da Irgan dangi,Ammah mene Irgan dangi? tace gasu nan a kirjinki Kin fara Nono Mufeeda akwai maganar da za muyi anjima idan yaran nan sunyi bacci,kunya ce ta kamani nace to Ammah Allah ya kaimu bari na gama aikin ko kina da bukatar shiga bayi na taimaka miki? Ae rikeni muje Mufeedata Allah ya miki albarka,

kama Ammah nayi da kyar tana rike da sandar karfe wacce a asibiti aka bata ita na kaita har bayi ta tsuguna tare da Dafe jikin bango,sai na fito bayan ta gama abinda zatayi ta kwala min kira na koma nace Ammah ko na goyaki? Dariya tayi tare da cewa na gode Yata baki ji me Doctor yace ba?na dan dinga takawa,murmushi nayi wanda yasa hakorana kanana farare suka bayyana,dimple dina ya lotsa riketa nayi muka fito tare,sai Lokacin kannena MEENAT da MA'EESHAH suka fito cikin shirin makarantar Islamiyya,na kallesu cikin tsafta kayansu yasha guga,sun bani sha'awa naji inama nima haka nake zuwa kullum amma ina bazan samu dama ba,amma Alhmdllh tunda kannena suna zuwa ba matsala.Amma ce ta kalleni cike da tausayawa tace Mufeedata? Da sauri na dawo daga tunanin dana lula na kakalo Murmushin dole nace Ammah ki huta bari na gama aikin naje na siyo kayan alewar madara,kinga gobe kuma da safe Kosai yana jira shima,amma ni naga awarar tafi riba ma,Ammah tace Mufeeda wannan satinfa naji zuku yi Allurar polio vaccine da kukewa yara,Mufeeda tace wlh Ammah ba sauki abin ni haushi na ma gidan masu kudi kantama kantama na GRA Ammah ayi ta wulakanta mu da kyar mukeyi muna Shan wahala,wani gidan ma kafin ka shiga tashin hankali ne ko ina securities ne,aikina naci gaba da yi muna hira da Ammah mahaifiyarmu,saida na gyara gidan tas na kunna turaren Wutar kamshi duk da gidan ba wani me kyau bane amma ita tsafta bata buya,Allah ya haliccemu da tsananin Tsafta wanda duk Bala'in mutum bazai ce gidanmu akwai digon wani abu na kazanta ba haka muke gaba dayanmu,miyar Kubewa busashiya na kada,na tuka tuwon masara na kwashe cikin wata tsohuwar Cooler dunmu,nayi wanke wanke da wanka na shirya cikin kayan gwanjo na Riga blue me layi layi na fari,tare da skert shima ruwan goro,farar Powder na shafa da Vaseline a lebena,Hijab me hannu nasa wanda ya wuce gwiwata nace Ammah bari na siyo kayan nan nazo na fara soya Awarar dare kinga magriba ta gabato,Fadada murmushinta Ammah tayi tace a dawo lfy Allah kiyaye hanya.

    Ameen nace tare da fita waje ina dan wasa da kudin dake hannuna cikin unguwarmu layinmu na bari nayi tafiya me Nisan gaske Allah yasa ma ba rana sai da na gaji sosai kafin na karasa wata yar kasuwa karama da ake saida kayan abinci da fruits etc, inda na saba siyen waken kosai da sauran kayan Sana'a ta na karasa da fara'a dukkanmu munyi sabo da juna sabo da yau da kullum,kudin na mika ina bi ko wanne layi duk na hada abinda nake bukata kaf aka hado min a wani katon buhun bacco na fito da kyar nake dagawa ina nishi haka nake tafiya a hankali, wani dattijo ne yace yarinya kawo a daura miki a kai ai zaifi ko? Murmushi nayi masa ya amsa ya daura min na masa godiya naci gaba da tafiyata da kyar,sai da nayi nisa na shiga wani layi wanda manyan gidajen masu kudi ne na gani na fada,GRA ce ta masu kudi nabi ta ciki sabo da kullum ta hanyar nake wucewa ko sabo da nasha kallon hadaddun gidaje tare da Lambu masu kayatarwa duk kuwa da cewa na saba shiga sabo da rigakafin polio na nake aikin dole muna neman Izni mu shiga sabo da tare da masu Unguwanni muke yin rigakafin dole su yarda a shiga ko Police su kama me gidan haka aikin yake.

    Wasu motocine a kalla sun kai guda takwas a jere dankara dankara ban taba ganin irinsu ba sai yau da suka shararo da uban gudu kamar zasu tashi sama cikin layin,dai dai wani gida suka Parker wanda gidan yafi kowanne kyau a layin da gudu na matsa tare da rakubewa a jikin ginin gidan ina kallon ikon Allah,

da sauri naga sojoji sun fito daga sauran motocin tare da zagaye wata uwar shahararriyar mota me kyau da tsada na fitar hankali,wani dattijo ne ya fito fari kar dashi yana sheki da Alama kudi sun ratsashi a matukar hasale ya fito daya bangaren ma wani wani mashahurin matashi ne ya fito da sauri a matukar hasale cike da isa hade da Izza Saurayin kamar balarabe ko Bature haka yake duk Haske da kyau na da ake fada sai naga wannan ya wuce nawa ya zartani a komai nan take na raina kaina musamman yanda na kalli shigata babu maraba da Almajira mara gata.

    Saurayin bazai wuce 35years ba ya kai karshe a haduwa gashinsa abin kallo kansa style din askinsa abin kallo ne abin birgewa da sha'awa,idonsa ya bude,ban San sanda nace wow a raina ba idonsa kamar madara yana wani lumshewa gasu Dara Dara,girarsa har kamar zata hade,ga wani dan saje da gemu masu matukar kyau da suka kawata fuskarsa,hancinsa me matukar kyau kuma baiyi tsini da yawa ba,dan bakinsa wow masha Allah ga wasu pink lips duk da cewa nima bakina kamar cokali bazai shiga ciki ba gashi lips dina jajir dasu amma sai naga wannan kam nasa sunfi nawa komai,kuma sai na tashi me duhu a kansa ko dan shi Hutu da Naira sun ratsashi ne oho, Kana nan kayane a jikinsa wandon pencil Jean brown color,rigarsa fara tas da top Brown ya daura sama takalminsa fari half cover flat shoe,shi ba gajere ba shi ba dogo da yawa ba,haka ba ramamme ba kuma bame kiba ba,kai masha'Allah da a mafarki na ganshi ba shakka Aljani zance.

     Dattijon cikin farar shadda kar cike da Fada yake magana da alama da Saurayin yake,AAYAN  will u hear me out pls,da sauri Saurayin ya bata rai cike da fushi yana shagwaba kamar dan yaro cikin muryarsa da ta girgiza ni sabo da dadinta yace pls Abbi I knew it just leave me alone For God sake,Hajja she is ur mother not mine so Abbi kaine ya dace kabi Umarninta ba ni ba,taya zata dinga takura min ni kadai ne jikanta gasu nan da yawa maza da mata,ko kawai dan ni bani da Mahaifiya bata raye,sannan mahaifina bashi da lafiya bakwa kaunata shi yasa ni kadai ake ma haka yanzu ina Abuja kace dole sai na dawo Kano da Zama kusa da Ku,ban taba wani rayuwa a kano ba ka sani sabo da kana matsayin mahaifina nake maka biyayya,sabo da gudun saba maka na bar muku gidanku,bana amfani da sisin kudinka,Allah ya bani nawa Abbi har na fika ma maybe kudin,But why me,why are u doing this to me,kowa a Family kaf maza da mata nine ba a so me nayi musu?idan sabo da Umma ne bata raye sai na huta,Abbi ban shirya aure ba kunsa nayi ba muguntar da ba ayi min ba,haka mun rabu,kun kara aura min wata itama mun rabu sabo da matsalar dake damuna na rashin lafiyar haihuwa Abbi kun San bani da lfy bazan iya Rayuwar aure da mace ba akan me zaku ce na kara auro wata so kuke mata su kasheni bazan iya musu amfanin komai ba,dalilin bacin rannan da nake Sha kasan yanzu Hawan jini gareni me karfin gaske ko wanne lokaci zan iya rasa raina,sannan kasan Ina da diabetes dalilin Hawan jini yasa ya kamani tawakali da addua nakeyi,Abbi why not bakwa tausaya min,bakwa tausayin rayuwata tun tasowata a wahala na tashi a duniya,wannan yasa na tsani mata wlh Bana kaunar duk wata budurwa komai kyau da hankalinta,dalilin haka bana Hulda da kowa family da frnds etc ni kadai nake rayuwata sabo da bakin ciki da halin da nake ciki shi yasa nayi nesa da kowa,gwiwoyinsa ya  dire a kasa hawaye na kwarara a idonsa kamar ruwa tare da rike kafar dattijon yace Abbi ka fadawa Hajja zan zauna daku amma pls kar ayi min aure again ko me kuke so wlh zanyi amma yanzu banda aure,Abbi ka tuna kusan mutuwa nayi yanda mata suka ci min mutunci.

    Kallonsa Dattijon yayi tare da cewa tashi Aayan,zan yi shawara da yan uwana, muyi deal duk abinda mukace zakayi ka yarda? Ba tare da yayi tunanin komai ba Yace ae Abbi na yarda indai bazanyi aure ba shike nan,Abbi yace an gama ko ka samu Lfy kana haihuwa sai na yarda zakayi aure ka tabbatar?Kuma ko kaga wacce kake so baza ka aureta ba har sai in mune muka yarda?cike da murna yana murmushi ya daga kai alamar yes ya Amince,Abbi yace Good for u,kar kaga bani na haifeka ba kace zaka min butulci zan iya yi maka abinda baka tunani,ka dinga tunawa da halina kasanni sarai zan iya yi maka ko mene ne ba ruwana,Shi dai Bayan murna yake yace ya yarda,Tashi muje daga yau ka dawo Kano gida daya zamu zauna sai dai jefi jefi kaje Abuja harkokin business dinka shima sai idan da yardata idan kuma kaki zan iya haram tama Business dinka gaba daya kasan nasan komai akan hanyoyin da zan lalata duk dukiyar daka mallaka,

Aayan ne yayi murmushi tare da cewa Abbi matukar baza kuyi min aure na zauna da mace ba zan iya mallaka muku komai nawa,na tsani mace a duniya ni bana son Zama dasu wlh ko yan uwana banso,kallon tsana Abbi yayiwa Aayan tare da cewa dan kawai baka da lafiya ne Man amma wa yaki mata?ai mata sune jin dadin duniya,kaga duk son kudina?Saurayin ya daga kai yana murmushin takaici,Abbi yace to duk kudin da nake nema sabo da mata nake nemansu,mata mutanenmu in ba su mene amfanin kudi.
   Kai Aayan baka da amfani a duniya fa da kai da gawa daya kuke Banga Amfaninka ba sam,to kai baka haihuwa,baka iya Yiwa mace komai me kakeyi kake wahalar da kanka wajen neman kudi,gaka a haka kamar Namiji Amma na tabbata in dai ba mune muka zaba maka mace ba irin almajira ko talakawa sune suke neman kudi sune yan wahala sune wahalallu wanda basu san kansu ba,basu san me duniya ke ciki ba,basu da wani amfani da irinsu ya dace a nema a aura maka sune watakil ka samu me son kudi tayi kasuwanci da kai ta samu kudi ta zauna da kai da hakuri.

    Aayan yaji matukar zafin kalaman Abbi wanda gaba daya ji yayi kamar ya mutu Sabo da bacin rai,haka ya hakura ya danne bakin cikinsa Amma idonsa ya kada yayi jajir,sai da Abbi ya gama gasa masa bakaken maganganu masu zafi sannan yace tashi muje ciki kasa a kawo ma motocinka kasan ko aron nawa ko na gida babu me baka kamar yanda kace kowa yayi amfani da kudinsa,Aayan yace ai duk new nayi Order an siyar da wancen saban yayi za a kawo min  gobe,dariyar mugunta Abbi yayi tare da cewa kana kokari fa wlh ni da kai da gawa haka nake kallonka baka da amfani a duniya me zaka amfanawa wani?ko mace baka amfana mata komai ba sai wa? Bakin ciki ya tokare zuciyar Saurayin yana tsaye a gate har Abbi ya bawa Sojojin da suke can gefe dasu Umarnin su shigo da motocin gida,nan suka bar Aayan wanda ya dafe saitin zuciyarsa da hannunsa,har suka shige da motocin gidan,suna rufe gate din ya fadi a wajen ya sankame kamar ya mutu,gashi unguwar shuru ba kowa bare a taimaka masa.

    Ni da nake Rabe ina jin komai da Sauri na jefar da kayan dake kaina nayi kan wannan Saurayi cike da tausayawa,tunani na sumewa yayi,na rasa ya zanyi na tasheshi robar ruwa dake hannunsa na Eva na fisgo da Sauri hannuna na rawa na bude tare da kwara masa a fuska Amma shuru bai tashi ba,hannayena biyu na daura saman kirjinsa ina dannawa kamar yanda nake gani likitoci nayi,yi kawai nakeyi ba ji ba gani danna kirjinsa nakeyi sosai ina nishi,a rude na kara kwara masa ragowar ruwan na sunkuya a kansa kamar zan shige masa ciki,kamshin turarensa yasa kamar na sume Sabo da dadi,fatarsa laushi kamar auduga lumis,wukil naga ya bude ido mun hada ido dashi kafin na kifta ido naji an sharara min uban Mari sai da na daina gani na wasu yan lokuta,kafin na dawo hayyacina yasa kafa ya harbar dani da mugun karfin da sai da nayi uwar Sufa na tuntsira naci ta ka na kife can gefe yaraf,nan take lebena ya fashe fuska ta ta kumbura,sabo da rashin Imani bai kyaleni ba takowa yayi har inda nake ya kara Sa kafa yayi ball dani sai da kaina ya bugu da wata yar bishiya,kafa yasa ya take hannuna dake yashe kasa ya murza,idonsa yayi ja da hannu daya ya damki wuyana ya shake tare da rabani da kasa ina kakari,Mari ya shiga yarfa min ban san iyakacinsu ba sannan ya jefar dani kasa kamar wani kayan wanki,Kuka me karfi na saki duk dauriyata ban san inda kaina yake ba,tunani na mahaukacine dama ashe,ina ta kuka a wajen Fuskata ta kumbura sosai jikina duk wani wajen ya farfashe Sabo da ball da ya dinga yi dani,tsorinsa ya shigeni ina nan wajen har ya shige cikin gidan da motoci suka shiga,Allah ne ya taimakeni wani dattijon kirki yazo wucewa a motarsa yace yarinya motace ta bigeki?Ban san me zance ba kawai sai nace kare ne ya biyoni shine na dinga faduwa,mutumin bai yarda ba Amma ya Kira Driver dinsa yace ka dakko mota ka kai yarinyar nan asibitina ka samu Sajeeda tayi mata dressing ka maidata gidansu kayi Sauri dare ya fara,godiya nayi masa ina kwance a kasa ina tunanin zalincin da Saurayin nan ya gwada min tare da rashin Imani daga taimako sai naci Dukan tsiya,
haushinsa naji sosai a raina ga tsoronsa da ya dasu a Cikin raina bana fatan sake ko kallonsa Sabo da tsoronsa nake ji yanzu.

   Ina tunani a kwance Dattijon Driver ya karaso tare da bude min mota da kyar na iya shiga motar,Driver ya saka min kayana a Cikin motar wanda na siyo a kasuwa,wani hadadden asibitin kudi ya kaini nan take akayi min komai da ya dace aka bani magunguna da Alama asibitin dattijon mutumin ne da ya Bada motarsa a kaini gida,Driver na gwadawa gidanmu ya kaini har kofar gida sannan ya miko min dubu biyu yace na sha Maltina inji Alhaji me gidansa,da kyar na yarda na karba,shima sai da Driver ya nuna baiji dadi ba sannan na karba tare da zuba godiya na dauki kayana na shige gidanmu shi kuma yaja mota ya tafi,ina shiga gida Kannena Meenat da Ma'eeshah har sun yanka awarar suna jirana da gudu suka taso suna Sister Mufee me ya sameki?lfy?hatsari kikayi ko motace ta kadeki,kinga yanda kika koma kuwa,Da Sauri Ammah ta fito da Rarrafe kamar zata kifa Sabo da rudewa tana Innalillahi wa Inna ilaihirraji'un shine Abinda Ammah ke furtawa tana Hawaye tare da cewa me ya samu Mufeedata?Me ya samu katangarmu? Kuka na fashe dashi me karfi tare da Rungume Ammah ina cewa ba komai Ammah a wani layi ne kare ya biyoni na dinga gudu na fada cikin kwalabati da kyar wani ya taimakeni ya kaini asibitinsa kinga an bani magani harda kudi dubu biyu na shan Madara da Maltina,Ammah tace wannan waye me kirki haka?Wlh Ammah wani  ne Doctor ne Babban mutum ya sa Driver dinsa,to ku dai kiyaye da mazan zamani a tsare mutunci,Alhmdllh tunda komai yazo da sauki,Meenat ki dafa mata ruwan zafi ta gasa jikinta taci abinci tasha maganin ta kwanta,ke Ma'eeshah jeki kofar gida ki fara soya awarar kafin yan siya su fara taruwa, mikewa mukayi tare da aikata abinda Ammah ta ce.

    Bayan nayi wanka na gasa jikina Mai na shafa sannan na Sa doguwar riga mara nauyi itama yar gwanjo ce,abinci na dauko tuwon da nayi dazu naci na koshi domin ni cuta bata hanani cin abinci,komai rashin lafiya sai naci na koshi nayi luf,bayan naci Ammah ta dinga ballo min maganin tana bani ina sha har na gama,tace kawo na shafawa na shafa miki,Ammah zan shafa ki barshi kinga ke ba lafiya gareki ba, bayan na shafa jikin Ammah na koma na kwanta ina tunanin Saurayin dazu tare da maganganun da naji sunyi nake ta faman tunani shi kuwa mene tarihinsa me mutanen nan suke nema dashi ne haka,tunowa da nayi irin rashin Imaninsa nan take na firgita tsoronsa ya kara shigata na kankame Ammah har bacci ya kwashe ni,. Washe gari da asuba da kyar na tashi na gabatar da Sallah tare da Azkhar kamar yanda muka saba gaba dayanmu,Bayan gari yayi haske naje da Sauri na hada wutar  itace na daura ruwan zafi yana tafasa na dama koko sannan na kafa daya kaskon gefe daban na fara suyar kosan siyarwa ta,ana sallama ana siya sai kuma ruwan zafi ya tafasa na kwalawa su Ma'eeshah kira suzo suyi wanka su wuce schl,da Sauri sukayi wanka suka shirya tsab cikin Uniform dinsu wanda yasha wanki da guga,Kokon dana dama musu suka eba tare da kosan suka ci suka koshi sannan suka kaiwa Ammah nata itama,Nima ina aikin Suya kosan siyarwa ta ina shan koko da kosai na ,Sister ya jikin naki gashi kumburin ya baje,murmushi nayi tare da cewa Alhmdllh kuje kar kuyi late ayi karatu da yawa banda wasa,bani da burin da ya wuce naga kunyi karatu sisters ku dage cikinku mu samu lauya da Doctor dariya suka dingayi Ammah ma tana tayasu cike da tausayawa Mufeeda,kudin Break na mika musu nace gashi yau ba ashirin za a baku ba Hamsin Hamsim zan baku kuci me dadi,murna suka dinga yi suna tsallen murna tare da godiya,Nace kuje mana Gashi karbi Meenat kece babba kuyo mana Cefane muyi miyar egusi da tuwon shinkafa ki taho da nama na dari Uku muma muci dadi ko Ammah? Murmushin farin ciki Ammah ta saki tare da kallona tace Allah ya muku albarka dai yaran nan,

bayan sun tafi na gama siyar da kosai na ya kare kaf ,ina ta faman murna na lallaba jikina na gyara gidan fes na tattaro kayanmu har na Ammah da kannena na wanke su fes na shanya,Ammah wacce ta rarrafo ta zauna saman tabarma tace Mufeeda me za a dafawa yan makarantar ne yau? Na gaji taliya zan dafa da mai da yaji kafin dare sai muyi tuwon,eh hakan ma yayi ai tunda muna samun na sawa a bakin Salati ba kamar lokacin baya ba,tashi ki kokarta ki gama ke ma ki kwanta ki huta idan sun dawo yau ba Islamiyya sai suyi girkin daren,amsawa nayi da to na mike nayi abinda ta Umarceni,na hada mata ruwa na kamata har Nayi tayi wanka fes na koma na riko ta muka dawo naa tayata shiryawa tsaf muna hira.

ina gamawa na hada yaji me dadi yasha hadi na soya manja,na gyar dan kitchen dinmu wanda yake na karfen langa langa ne,Ammah na zubawa na kawo mata tare da ruwa,taimaka mata nayi ta zauna nima nasa hannu muka ci muka koshi muna Bada dunkulen Maggi star,Sallah muka gabatar ta Azahar,sai ko mukaji Sallamar Yan makaranta su Meenat,da gudu suka shigo suna sallama suka rungumeni,Ido na waro mene hakan? Sis wlh wani ne yace yana son Ma'eeshah mu kuwa muka zabgo da gudu,ke kin ganshi wlh in banda wari ba abinda yakeyi wai yanzu Ammah duniya ta lalace me kudi bazai Hulda da talaka ba komai kyanka indai ku talakawa ne babu me kulaka sai talaka dan uwanka,Ammah tace ai duniya haka ta koma idan da gate a gidanku to me mota ne zaizo idan babu kuwa sai dai dan uwanka talaka,Yanzu kalli irin kyawu da Allah ya zuba muku Amma babu me zuwa wajenku talakan ma ya gagara sabo da talakan ma gudun talakawa yake Allah kayi mana magani,dan baki na na turo Ammah ke komai kice aure wai shekarunmu nawa,dan gidanku gata nake nema muku yanzu ko idan da kunyi aure ai kuna da yancinku ko ba komai sai kiga kun huta shine burina,Ammah wa zai kula dake to aini aure bai taso ba a wajena Ammah wlh Bazan iya aure na barki a haka ba ko da kuwa zan dawwama ba aure ne a duniya,ki daina zancensa indai kina so hankalina ya kwanta,Maeeshah tace Sis manya bari muyi girkinmu,harararsu nayi nace kuje dai ku cire Uniform kuci abinci kuyi sallah ku huta sai kuzo ku fara aikin,ni yanzu kun san kasuwa zanje siyo kayan da nake siyarwa citta,kaninfari,barkono,wake,kanwa,Sabulu,omo,maggi kala kala,har su Aya duk siyarwa nakeyi duk wasu kana nan Abu na amfaninmu kayan girki ina siyarwa a gidanmu,haka ina saida su Aya,ridi,kantu,alewar Madara,albishir etc su Ma'eeshah nake sarowa suna Tafiya min dasu makaranta su siyar min,ina kosai na siyarwa,da rana na siyar da su Zobo kunun zaki da dare kuma nayi Awara,ina kitso da zanen lalle sosai kudi idan sunzo zanyi na karbi kudina,sannan ina cikin masu polio rigakafi,duk wani neman kudi na Sana'a kanana na gida ina yi,kusan komai ma siyarwa nakeyi,kullum bani da lokaci bana zama sam sai neman kudi dashi muke ci muke sha,muke Sutura tare da makaranta,

biyawa Ammah kudin magani,yanzu kasuwanci a duniya shine buri na wanda har ya kai ga dasa min matsiyaci son kudi tare da tattali,iya lissafi da planning,sabo da yawan Hulda da mutane yasa na kara gogewa na waye sosai,akan kudi ba mutunci ko bashi ya shiga tsakanina da mutum akan dan Kasuwanci na to fa zan iya rufe ido dole a bani ma,kamar zanyi sata haka nake matukar neman kudi.

    Yau Monday Su Meenat suna schl na gama komai na fita naje wajen saro kayan Yara na sha,ina siyowa kala kala har su tuwon madara na wuce schl na kaiwa su Ma'eeshah domin su siyar,ina zuwa na hango Malam ya sa Ma'eeshah kamun kunne ya hanata ko shiga aji wai sun makara.


    Ina matukar Jaje gareku fans da raguwar shekaru da muka samu domin ba karuwa shekarunmu suka yi ba raguwar suka yi,ana ta happy new year a daina addua ya dace muyi Allah yasa mun shigeta a Sa'a tazo lfy ta wuce lfy,Allah yasa ta Zama shekara me amfani a Rayuwar mu,ta zame mana farin ciki da samun ci gaba a cikinta,Allah ka kara mana lfy da Nisan kwana me amfani,Allah ka kara mana imani,Allah yasa muyi karshe me kyau idan tamu tazo,Allah ya azurtamu da mutuwar shahada,Allah ya rufa mana asiri duniya da lahira Ameen.



AsmaBaffa
[1/1, 10:20 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

    KASUWANCI NA






              2-5




Official



By
AsmaBaffa







          

  Wannan page naki ne HUMAIRA Allah ya bar kauna.









       Wajen malamin naje da kyar na rokeshi ya kyaleta yace tayi Sauri ta karbi sakon ta shiga aji, nima ina mikata mata na kama hanya sai gida,washe gari kuwa da sassafe na shirya na barwa su Ma'eeshah suyar kosai da Komai nayi shirin Tafiya rigakafin Polio dama indai ina rigakafin nan to dole  Meenat ce zata zauna tayi dukkan abin da nake siyarwa har na gama Polio sannan taci gaba da zuwa,Sabo da Ammah bata yarda da talla ba shi yasa Sam bama fita talla a gida muke sana'armu,     Ma'eesha kadai ke zuwa yanzu kafin na gama Vaccine.

     Inda muke haduwa da ma'aikatan unguwar da mukeyi naje na samesu cikin Napep na sauka cike da fara'a da murna muka gaisa da juna,sannan na dauki akwatin da kwalaben Allurar suke ciki ga kuma supervisor dinmu da sauransu,sabo da box carrier ce ni ba a biyanmu da yawa dubu hudu da dari biyar muke dauka idan an gama,bani da ilmin da za bani Babban matsayi,haka mune da wahala mune muke daukan kudi kadan,a kafa muke Tafiya muna shiga gidaje ana house marking,sai 2pm muka tashi,washe gari ma bangaren unguwan da mukaje daban,a kwana na Uku kuwa da muka fara GRA din nan da na taba ganin Saurayi Aayan ya zaneni yau gidajensu zamu shiga aikin Vaccine duk da cewar ban taba shiga gidan ba,amma bana fatan shigarsa,ina ji ina gani muka zo jikin gate dinsu,

takadda aka rubuta sannan akayi knocking,Sojoji sunfi  biyar ne suka fito kamar zasu masgemu,sai da aka basu takardar cewar yan Polio ne suka zo ga me unguwa a tsaye kuma dole sai an digawa yaro dan kasa da 5years,takardar suka karba sannan suka koma ciki zasu nunawa me gidansu,tunda suka shiga muna tsaye a wajen gate har sai da suka kwashe fin hour guda sannan suka fito sukace ance mu shiga,ma'aikatan sai murna suke zasu gano haduwar gidan,ni kam cikina ya duri ruwa bana fatan shiga Amma ba yanda zanyi haka na fara binsu kamar kwai ya fashe min a ciki sanye nake da red hijab dina me hannu har kasa duk da cewa nayi kyau Amma sam na raina kaina,

   Muna shiga muka firgita domin ma'aikata da Securities ne ko ina,gidan ko ina kamshi ke ratsowa yana sheki,ga wasu motoci sunfi ashirin a gidan lafiyayyu,har round ne a gida kamar wani Babban titi tsakiyar youturn din ruwa ke tsiri sama yana shararowa a kasa kuma yana komawa kasan yana fesowa,a film ake ganin irin wannan gida jen,can gefe ga wasu sweeming pool har kala biyu,ko ina flowers ne a gidan,duniya guda ce a gidan domin wani part din ma ya dace ka hau mota sannan ka Isa in kuwa ba haka ba zaka gaji,wani soja ke mana jagora muna binsa a baya har muka zo wani garden ba abinda babu a garden din nan domin har da filin ball da Sauran wasanni iri iri,kida ne na wakokin Naija ke tashi har tsakiyar kai a manyan speakers,yan mata su Uku kyawawa yan gayu ne sanye cikin English wears Wando short da yar vest suna ta faman taka rawa ,hannunsu rike da kantama kantaman wayoyi,gefe wasu Yara ne sunkai su hudu mace daya da Maza su Uku sun sha kyau cikin kana nan kaya yan yayi suna ta faman buga ball, abin mamaki ko kallon inda muke basuyi ba kamar ma basu san mutane sun wuce ba, haka muka ci gaba da Tafiya muna yin gaba kadan sai ga wasu Maza zaratan samari suma hadaddun gaske baza su wuce 29 yrs ba su uku suna zaune a wasu kujeru masu malafa a sama game kawai suke bugawa suna dariya,ko wanne yasha kyau cikin kana nan kaya kamar a England,kaina nidai yana kasa Amma suma samarin inda muke ma basu kalla ba balle musa rai za a kula mu,tafiya dai muke muna bin Soja can wani wawakeken fili ne fetal yasha tsari da haduwa carpet dan gaske ne a kasan wajen da wasu manyan pillows ko ina yasha flowers ga wasu grass carpet wata mashahuriyar Dattijuwa tsohuwa tukuf muka hango kwance tayi kwanciyar Isa kamar sarauniya fatarta lumis fara kar duk da cewa ta tsufa Amma akwai hutu kayan marmari sun ratsata.

    Mu matan da muka shigo dama mu Uku ne,da hannu tayiwa Soja Umarni nan muka ga yace gasu nan yayi gaba abinsa,har kasa na durkusa na gaisheta cike da girmamawa,su kuwa sauran matan cewa sukayi ai ma'aikata ne wlh baza su durkusa ba duk wulakanci da akayi musu ba wanda ya musu ko sannu bare kallon arziki,gata ita wannan ta tsufa ma Amma bata saduda da duniya ba har wani jin dadi take.

   Kallonmu tayi tsohuwar ko amsa gaisuwata bata yi ba tana yatsina fuska tana kebe baki tare nuna Isa ta fara magana kuje dan Allah kun tsaya min a kai wari yana hawa min kai,da mamaki muke kallon ikon Allah,can ta jawo waya ta danna kira tana jan tsaki,sai ga wata da Alama yar aiki ce harda Uniform dinta dauke ta fito da ruwan roba tare da wani liquid soap me kamshi tace kuzo muje ku wanke hannunku sai a diga musu polio,Tsohuwar nan cike da izza tace wlh badan Hukuma da suke hadawa da ita ba baza a digawa jikokina ba sam,kazanta abinda ana kaisu asibiti ayi musu me kyau ko kasar wajene ma sai suje a diga musu Amma a dinga turo mana kazamai gidaje jasu can kuje,ina jin haka na daga kaina ina kallon sararin samaniya tare da kallon tsayi da girman building din nasu kamar baza a mutu ba katanga ma tayi tsiri sararin samaniya kai kace Mala'ikan daukan rai bazai iya tsallakawa ba,a raina nace to yaje har fadar shugaban kasa ma ya dauke Yar Adua,yau Ina sani Abacha?

      Ina wannan tunani sai ga wasu dattijan Maza farare suma su Uku sun fito harda Abbi wanda na taba gani zama sukayi kusa da tsohuwar suna magana,lokacin mu kuma an jamu part din yan aiki nan aka dinga dirje mana hannu sannan suka fito damu, wajen yaran dake Garden tare da yan matan nan masu rawa da Wando 3qtr muka koma,nan fa da kyar aka jawo mana yaran ana cewa Hajja ce tace ayi musu suka bude bakin su tas dasu cikin taka tsantsan na diga musu yanda akeyi sannan nace to Alhmdllh mun gama mun gode,me rubutu ta cike talley sheet din,muna jiranta tana rubutu yan matan nan dake rawa dauke da cup a hannu suna shan lemo suna rawa suna bige mu Amma ko kallon mu basayi bare mu Sa ran ko Sorry zasu ce,gefe dasu muka matsa,wata ce ta fito cikin shiga ta alfarma zata kai 40years da Alama da yaranta a ciki domin munga suna daga mata hannu bye Mum,tayi murmushi Tare da shigewa mota Driver ya jata ta daura kafa daya kan daya tana karanta Jarida,Numfashi ne ya kusa daukewa sakamakon wasu motoci da suka keto cikin gidan a kalla sun kai guda biyar suka Parker zunzurutun Securities ne suka fito tare da zagaye motar kamar wani Shugaban kasa ne zai fito,bude motar sukayi muna tsaye muna shan kallo Wani arnen takalmi ya zuro waje nan take kamshinsa ya cika gidan me dadi,ya dan jima a haka kafin daga bisani ya fito cike da takama kamar wani Sarki,cikin kana nan kaya yake yau ma farin Wando  pencil sosai rigarsa Silver color da Golden rubutu,takalminsa Silver yasha masifar kyau,duk wanda ya ganshi zai rantse ba mutum bane Sabo tsabar baiwar sura da kyau,ga iya daukan wanka yanda yake matukar kyau,yan matan nan ne muka ji sunce Hi Ya Aayan,ko kallonsu baiyi ba sai ma wani kallon Banza da muka ga ya watso musu kamar yaga kashi,sabo da nima gwanar mugunta ce a raina nace Allah ya kara shegu ga ubanku a girman kai gwara haka,

    Matar da muke aiki da ita wato Salima itace ta kalli yan matan tayi dariya wai irin ta tura musu haushi,ai kuwa ba zato muka ji karar Mari a fuskata domin suna rawa tunaninsu nice na musu dariya shine daya a ciki kawai ta daukeni da shegen mari wanda ya jawo hankalin wannan Saurayin da Sauran Ma'aikata kaina,Kuka na fashe dashi a wajen nan take na fadi a wajen na dinga shure shure,wanda muke Polio ne suke bani baki kan nayi shuru mu tafi,cikin kuka nace Wlh sai na rama mikewa nayi a hasale na cakumo daya a Cikin yan matan wanda ban san wace ta mareni ciki ba nidai na kama daya tare da makalkaleta na cisgo gashinta na murde na ja da karfi,sannan na dalla mata mari har biyu na sake ta na zura da gudu domin sunyo kaina da kwaben lemon me tsada da suke sha zasu fasa min a kai,daya ciki ta jawo Hijab dina ta baya,Securities sun taho Saurayin nan ya dakatar dasu cewar a kyalesu,suna kallo sun rike min Hijab na sunkuya tare da zare Hijab dina na bar musu a hannunsu na Arce jikin gate ina rokon a bude min,Saurayin nan yace kar wanda ya bude min,Har yan matan nan suka zo kaina na kara runtumawa da uban gudu amma saida suka kamani suka rufarmin suka dakeni sosai naji jiki sai da suka gaji dan kansu sannan suka tafi ina yashe a kasa,sai Hawaye nakeyi abokan aikina suka dagani da kyar sannan naga wannan Saurayin yace a bude mana mu bace a ganinsa ya tsani mata ko da yan uwansa ne baya kaunar ganinsu,sai da na tabbatar an bude mana nasa kafa ta daya ciki daya waje sannan nace kai yan mata?duk kuwa suka juyo suna kallona nace Allah ya Isa kuma sai na rama watarana idan kanwata ta zama Doctor ko Lauya,kallon banza suka min tare da tabe baki,nace zaku gani wlh kyaleki nayi dan ba a kan KASUWANCI NA kuka tabo ni ba,rigimar ba akan kudi bace Amma da akan kudi ne ai da sai daí a mutu a gidan nan shegu,tsinannu tambadaddu,arna,jahilai,dabbobi kuma dukkan yan gidan nan na zaga na nuna Saurayin nan dake tsaye nace harda kai da wannan tsohuwar dake zaune a carpet a sanar mata dazagina da iyayenku baki daya,sannan kuma ina tunatar muku Mala'ikan mutuwa na nan zuwa watarana,sojoji ne suka yo kaina na Arce da uban gudu tare da cewa Allah ya isa dana gaishe da tsohuwar nan kekakashashiya,na dinga zura uban gudu Allah yasa time din tashinmu yayi kawai na fada Napep ina haki sai gida tazarce kawai tun daga Cikin gidan nake gudu har nazo bakin titi na hau Napep,su kansu abokan aikin nawa dariya suke min da kyar wani cikin wanda ke jiranmu a waje ya karbi box din hannuna Sabo da uban gudun da nake kamar na fanfalaki.

     Bayan na koma gida sallah na gabatar tare da fara harkar kasuwancina har Awara nayi ta dare bayan na siyar na gyara komai tare da irga kudin na cire ribar na zuba cikin asusun da nake tarawa Ammah kudin asibiti na magani tare da ware na gida da yan abubuwa,washe gari haka muka je wata unguwar mukayi polio abokan aikina su Salima sun sani gaba suna min dariyar abinda ya faru damu a gidan masu kudin jiya,sai dariya muke muna Bada labarin,Salima tace ammafa sun hadu da yawa a gidan kowa me kyau ga iya kwalliya musamman dan Iskan da yasa aka dakeni domin ni tunanina shine yasa a Zane ni tunda shi ya hana a bude min gate,Salima tace lalle Mufeeda ashe haka kike da rashin kunya idan an tabo ki,kina da Silent falava wlh,u like too much falava,murmushi nayi kawai domin bana jin wani turanci ni kam,karatun Hausa da Arabic kawai na iya Amma Ilmin turanci sai dai kalmomi dai dai domin bani dashi,h akan ma don ina dagewa ne su Meenat suna koya min amma da ba karamar dakikiya za ayi ba ni kam.

      Yau cikin nishadi muka gama Polio na dawo gida da Sauri naci abinci na shirya sai kasuwa siyayya ina tsoron bi ta cikin GRA Kawai sai na hau Napep naje na dawo lfy, bayan mun gama suyar Awara mun siyar wanka muka kara yi tare da Sallar Isha,Su Meenat Assignment sukayi na schl tare da karatu nima na zauna suna koya min karatun turanci da rubutu haka Arabic ma duk da ina da Ilmi domin Uzu na ashirin cif haka wasu litattafan duk nayi wanda Kannena su Ma'eeshah sunyi Sauka tuni littafin da suka sani kam ko kafarsu ban kama ba danma ni gwanar jin wa'azi ce nasan duk wasu hukunce Hukunce na addini da dama Amma su suke koya min karatun,da badan haka ba da anyi kungurmar Jahila ni,

      Part of speach suke koya min common adjective sun sha fama dani kafin na iya fada Sabo da ba laifi kwakwalwata da saukin ja tunda ni dai iyakacin Jss 2 makaranta ta gagareni Allah ma yasa Makarantar Arabic da boko mukeyi a hade shi yasa muke dana addini,su Meenat kuwa ai akwai Ilmi,shi yasa da munyi fada zasu ce to Sis me kika sani ma in ba neman kudi ba musamman Meenat uwar iyayi da son kwalliya domin duk wata kwalliya ta yan Zamani ta iya ta komai nata na harkar son gayu,Maeeshah ma haka suyi ta faman iyayi ni kuwa sai dai na siya musu kayan yi suyi ta zuba kwalliya ina kallo tunda har cosmetics na talakawa ina siya musu iri iri,kayan wanke gashi na talaka ni dai barni da jarabar tsafta amma ba ruwana da wata kwalliya gani nake bata lokaci ce kawai kudi nake nema dan mi tsira da mutuncinsu,
ni kullum sai daí na labta Hijab na fita neman kudi ba sauki wanda yanzu Unguwarmu sun samin suna Yar Kasuwa,sabo da bani da lokaci sai na neman kudi akan kudi ba daga kafa.

   Duk inda naji wata Sana'a ko harkar samun kudi to fa yanzu zan cusa kaina ciki dole sai na samu domin mu samu na ci da sha tare da Sutura,ina da karancin wannan shekarun Amma na shaku da kudi,yanzu abinda ya dameni bai wuce kai Ammah Hospital ba domin dubu Sittin da biyar zamu je da ita za ayi mata wani aiki a Ciwon dake kugunta zuwa kafafunta shi yasa na gigice yaki Halak yaki Haram haka nake tara kudin,
    Akan wannan yanzu kam na koyi ha'inci a Sana'a ta domin Awara da ina yinta me kyau da dadi Amma yanzu dan na samu riba da yawa na daina alkintata idan na tashi tacewa Bazan matse ruwan da yawa ba,kadan nake dan matsewa kana ci zaka ji ciki lumtsum da ruwa da mai,haka yajin na daina me dadi sai na gabza uban gishiri a ciki dan yayi yawa,haka ake siye Sabo da tsaftarmu Amma sun daina karba da yajinmu,haka kosai na ma da wata taba da ha'inci ya taso min sai na siyo garin kwaki tare da jar kala bayan na dauko markaden saina zuba garrin kwaki a Cikin markaden waken kosan nawa tare da jar color yayi wani jajir sannan kosan ya kumbura yayi sutu sutu dan na samu riba na samu kudi sai kiga ana ta siye Malam kosai yasha kayan miyar color gashi har wani Danko yake Sabo da yaji garrin kwaki ciki ba a sani ba ayi ta siye ina samun riba tunanina dai dai duk kuwa da cewar nasan ba kyau sai daí nayi Istngifari domin ko Ammah da kannena basu san tabar da nake aikatawa ba gara awarar gida idan zan soya musu daban nake tace ta tas tsam ba ruwa sai su zata ma wacce ake siya haka take.

    Hattana Alewar madarata dasu kwakwimeti tare da kafi tsire in dai zanyi sai na san tabar dana yi a ciki Sabo da kawai na samu riba me yawa,gullisuwa idan zanyita sai na tankade garrin masarara me Laushi na kara a cikin Madarar Sabo da tayi yawa,haka ma Zobo na siyarwa sai na samu jar color na tafasa zobon kadan na narka uwar Color a ciki nayi hadinsa a ganshi kamar gaske ayi ta zuka ba a san rabi color ce kawai da ruwa ba,kuma bana sa sugar dan zaki wato sugarin nake dan yafa kadan sai kaji zaki cai.

     Ina zaune kusa da Ammah ina tufke mata gashinta muna sauraren Radio kawai sai muka ji cewar Gomnati zata raba tallafi ga marasa karfi Naira dubu sha biyar biyar tare buhun shinkafa da taliya sugar da man gyada tare da waken Suya a ja jari,nan take na mike zumbur naji kudi,Ammah ta kalleni tace sarkin neman kudi dan Allah ki hutawa kanki zafin nema baya kawo samu haka duk kin damu kanki Allah yana rufa mana asiri dan Allah ki rage takurawa kanki ayi amfani da abinda ya samu,baki na turo Ammah kina gani kudin maganinki har yau basu hadu ba fa,to ta wacce hanya zaki bi ki samo mana tallafin? Ammah wajen counsilor din Unguwarmu Adamu zanje na nemi Alfarma ya nemo mana hanya,ai yana da kirki Amma fa kija mutuncinki duk da nasan irin tarbiyyar da nayi muku ki kiyaye Mufeedata sannan kinga girma ya fara kamaki idan kika bari Namiji ya rike miki ko yatsa shike nan kinyi ciki an gama,da Sauri na zaro ido waje a tsorace nace Ciki Ammah?ae ai indai Namiji ya rike maka ko farcene to shike nan ciki ya shiga,da tsoro na firfito da ido waje,nace Ammah su Meenat nake tsoro bari su dawo na fada musu gaskiya kar suje su yarda da Maza su rike musu hannu.

    Su Meenat suna dawowa na taresu da Sauri tare da jansu dan Bedroom dinmu nace dan ubanku karku bari Namiji ya rike ko yatsanku,Meenat tace Sabo da me?ba kyau kuma Ammah tace ciki ake dauka,Dariya naga Meenat ta kyalkyale tare da cewa Allah ya bamu kudi Sis ki koma schl kema wlh ba haka bane ke baki da labarin abinda ake a aure ana samun ciki,ai Ammah wayo ta miki kar mu kula Maza mu lalace shi yasa ta fada haka Sabo da taga mun fara girma,shuru nayi ina Nazari Amma naki yarda da Meenat Sabo da nasan Ammah baza ta fada mana karya ba,kyalesu nayi kawai na fita abina naci gaba zuba kwakwimeti na à leda,bayan na gama na fara daura su citta dasu kanwa,kaninfari etc,kusan duk makwaftanmu a wajena suke siyen kayan miya,idan suka siya kawai sai su zauna a gidanmu suce bari su daka kayan miyar ko jajjage da sun shiga gida kawai sai daí su fara girki,sabo da son kudi na nace to daga yau na kafa doka cewar ko wacce idan zata yi daka a turmin gidanmu to sai ta bayar da Naira goma kudin turmi,ganin haka yasa Bazan basu tabarya ba sai an miko goma shike nan suka daina daka a gidanmu,Muna da wata Kura da yake gidan mu akwai rijiya idan guganmu ya fada da ita muke amfani mi Ciro gugan,mutane suna zuwa aro sosai nan ma nace kudin aron Kura Naira talatin wasu haka dole suke bayarwa suna dauko Guga,Ammah ta hanani Amma naki ji,su Meenat ma dole suyi abinda nace ko bana nan idan aka zo to fa sai an Bada kudin nan,komai nawa idan zaka taba na kudi ne.

     Haka na kama kafa naje har gidan Adam counsilor neman Alfarma a sani cikin masu tallafi,yace Mufeedata ki. Makara wlh an gama daukan sunaye amma na miki alkawari akwai na wani watan kizo Office ki sameni a secretariat zan sa sunanki a wasu da za fara bayarwa na manoma,ban kawo da wata manufa ba kawai na dinga Murna ina godiya cewar zanje in Sha Allah.

    Bayan kwana goma Zaune muke gaba daya tunda anyiwa Su Meenat hutun schl muna ta Hadin Zobo nan nace suje su ebo robobi a wanke suna Tafiya na watsa Maroon color tare da makawa Zobo ruwa na hadashi da su Flavour yasha uban Barkono a ciki,sabo da aji yaji sosai sai na zuba citta da kaninfari kadan na ebi Barkono na watsa a ciki na tafasa dashi Sabo da aji yajin ya fito sai ka rantse yajin cittane da kaninfari me uban yawa,gaskiya na iya taba sosai ni kaina ina jinjinawa kaina yanda nake tabka tsiya a sana'oi na ba a magana watarana nakanji haushin kaina nima ba da son raina nakeyi ba Amma Sabo da neman rufin asiri,su Ma'eesha suna kawo robobi Meenat tace sis wannan uban zobon fa dazu fa dan kadan ne bai kai rabin botiki ba amma yanzu ya cika botiki,Maeeshah ma tace nima haka na gani kamar na Aljanu,Harara na zabga musu sannan sukayi shuru.

abin takaicin da kyar na hada dubu Sittin da Bakwai kudin Ammah na asibiti,haka nace su shirya mu tafi,har kofar gida na kira Napep muka hadu tare da daukan Ammah muka sata cikin Napep muka kulle dan gidanmu da yar kofar da ta kusa ballewa ma haka na zarge ta muka shiga Napep Sai Asibitin Murtala na cikin Kano,Munje  Dr Naseer ya duba lafiyarta ya dinga fada me yasa ba a kawota da wuri ba tuntuni yace a kawota ayi aikin to gashi ciwon nata ya kara karfi yanzu dole wasu magunguna zasu rubuta mana mu siya na dubu Hamsim da biyar sannan idan ta shanye bayan sati Uku mu dawo da ita za ayi mata aiki.

    Bakin ciki da tsoro tare da firgici suka kamamu gaba daya,nayi Zuru Zuru kamar wacce ta shekara taana zawo haka na koma nace Doctor yanzu nawa ne kudin aikin? Yace ai kudinku da yawa,likitan da zaiyi mata aikin nan baya zama a kasar nan sam Sabo da aikinta zaizo yayi mata ya koma,don haka idan yayi muku sauki ku biya dubu dari takwas da  Hamsim domin ciwon ya girma,da ace tun farko kun kawota da tuni baifi ku kashe dubu dari ba Amma yanzu danma da wannan Doctor dinne Amma wannan aikin kasar waje muke tura mutane masu irin cutar ayi musu aikin anfi dacewa,a nan kuwa sai dai mu dage da addua,kuje ku dawo lallai nan da 3wks tare da kudade in ba haka ba kuna kallo wlh zata kasa ko motsa yatsa dake gabarta nan gaba sankamewa zatayi ku daure ku dawo ayi mata aikin kunji.

   Likita na bayani Hawaye na sintiri a fuskata tunanina ina zan nemo kudin nan ko kaina zan siyar wlh bazan yi wannan kudin ba,Innalillahi nake maimatawa Doctor kuma na kwantar min da hankali yana cewa cuta jarabta ce daga Allah,idan Allah ya jarabceka sai hakuri aci gaba da addua Amma tana cikin hadari,Meenat dake kusa dani itama Hawaye takeyi,da kyar na Lallashi kaina nice babba Amma kuma nice me raguwar zuciya bana iya rike Hawaye na saurin kuka gareni ammafa a bangaren abin tausayi,ko ya naga abin tausayi yanzu zan yi kuka,kanmu da Ammah nake tausayawa kawai,Meenat karki fadawa Ammah me Doctor yace kawai kiyi shuru da bakinki Sabo da bana so hankalinta ya tashi,muce kawai aiki za ayi mata nan da 3wks sai kudin zamu fada mata,amma karki fada mata Doctor yace zata iya rasa ranta ba lallai ta tashi ba kinji,ok Sis Bazan fada ba cewar Meenat dake shesheka,hawaye na share mata nace muje kawai muk ayiwa Dr sallama muka tafi,Ma'eeshah da Ammah suna jiranmu a can waje, magunguna muka siya sauran kudin na siyo mana wasu kayan abinci da Cefane,Su Meenat kuwa tuni na hadasu tare da Ammah nace suje gida zanzo daga baya,Ina cikin Napep kawai tunani nake ta ina zan samu kudin nan,lallai Zafin nema baya kawo Samu,gashi dai na gama Ha'incina a sana'ata na cuci mutane da dama ta hanyar siyar musu da gurbataccen abun ci kuma karshe kudin anfaninsu kadan ne a wajenmu abinda nayi don shi ba a dace ba,amma duk haka ban hakura ba kuma ban damu ba matukar zan samu kudin da Zan nemawa Ammah lfy.

     Tunani nake bana ganin komai bana ji har Napep ya saukeni a gida na shiga da kaya Niki niki,Meenat ta karba ta shigar dasu ciki,tsabar bakin ciki da muke ciki yau bamu iya daura kaskon Awara a kofar gidanmu ba,duk muna zaune kowa da tunanin da yake banda Ma'eeshah da yake ita ba wani girma da hankali tayi ba sosai bacci ma takeyi,abincin da muka dafa ba wanda ya iya kai ko loma daya bakinsa,musamman ni gaba daya na rude na rikice,idan kuka ya taho min sai na shiga toilet naci uban kuka na wanke fuskata na fito haka na kwana inayi kafin Safiya tayi idona ya kumbura yayi jajir, ga addua muna tayi, mura ta kamani muryata har ta dashe Sabo da Hawaye na kawo Mura yawan kuka,da sassafe kamar me aikin Gomnati 8am nayi shiri da kumburarren idona tare da jansa na maka hijab kowa ya ganni yasan ba lfy,tunani nake ina zanje neman kudi Office din yan siyasa ko gidajen masu kudi?ko kuma kasuwa zanje wajen masu kantina,domin   banyi tunanin kaiwa gidan Radio ba ko wani waje,kaf makwaftanmu haushina sukeji Sabo da kan Sana'a ta ba mutunci idan maganar kudi ce ba kawaici don haka ba da wanda muke shiri sai daí daiku duk sunfi jin haushina,don haka babu me bamu shawara ko gidan Radio ko wani waje to idan ba business ba babu abinda ke hada mu dasu Sabo da ba a kula mu ance dan munga muna da kyau sai mu dinga yanga mu ba yayan uban kowa ba,sannan tunaninsu ma ni yar Iska ce Sabo da yawan fita da nake kullum ina gantalin neman Kudi tunaninsu ai iskanci nakeyi kullum ina titi,haka suke zagina ba abinda ba ce min.

    A fusace na fito daga gida ka Rantse  mutanen garin ne suka min abin haushi domin kowa haushinsa nakeji kamar zan make mutane haka nake tafiya fuuuuuuu fuska ba annuri,duk motar dana gani sai na harareta na harari na ciki dake tuki irin ga mutane da kudi ba taimako,common arna ko church kaje a tallafa ma amma musulmai ko a masallaci basa iya bada Sadaka me tsoka sai biyar,goma,ashirin katon me kudi kaga ya mika Hamsim,mafi akasarin Hausawa haka suke bare har wani ya dauki nauyin karatun wasu ko ci da Sha bare na magani sai dai dai ake samun masu haka,amma arna sai kaga mutum daya ya kwashi yan unguwa da yawa ya fitar dasu kasar waje karatu etc.
  



AsmaBaffa
[1/1, 10:20 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

    KASUWANCI NA




             6-10





Official




By
AsmaBaffa





        AUTA kema wannan page Sadaukarwa ce gareki.





             Tafiya nake ina tunani har na Isa bakin titi ina jiran na shiga Napep shuru shuru ba taxi ba Napep kowacce a cike suke,wata dalleliyar motace tayi parking a gabana tunanina Namiji ne irin samari yan iska masu ragewa mata hanya a nemesu nan take na kara tamke fuska na dauke kaina na kalli can gefen hanya,wani kamshi naji ya cika wajen sakamakon bude murfin motar dake Saitina da akayi sai lokacin na kalli me fitowar ba kowa bane face yan matan nan na gidan Saurayi Aayan wanda suka min dukan tsiya sune su biyu suka fito a zafafe kida na tashi a motarsu sunci uban kyau ko ina zasu je oho,ina cikin wannan tunani sai ji nayi an sharara min ruwa a jikina me sanyi,a firgice na kallesu da mamaki,nan suka sheke min da Dariya dayar ta fusgo min Hijab tare da shakeni,dayar ta duro min ashar tare da cewa ubanwa kika zaga har gidanmu?dama nace wlh duk ranar dana ganki sai kin San wa kika yiwa rashin kunya wato har iyayenmu ko?

     Dayar data shakeni ta tsandara min mari tace Wai ke face to face harda zagin ya Aayan ke din banza kucaka yar matsiyata kin San su waye ubanmu har zaki bude rubabben bakinki ki zagi kakarmu who are u me kwakwalwar dusa banza gaja.

  Wani bakin ciki da bacin rai ya taso min duk saurin kuka na haka na danne shi,dama cikin haushin masu kudi nake ga bacin ran halin da muke ciki,nan take na kasa hakuri nima nace kune dai gajoji yan iska tsinannu na shaki wacce ta shakeni nima na zuba mata Mari me lafiya,nan take ta shakeni tare da Dafe kuncinta, dayar ta taso a fusace kafin ta karaso na tsuguna tare da kwaso kafafunta ji kake Tim ta fadi gefen titi,na bita kuwa tare da jawo kafarta kaiiiii kowa yana kallo ina janta a kasa tana ihu,na hau kanta tare da Zama daram na rufeta da duka tako ina,wacce na mara kuwa da sauri tazo kaina itama ta hau dukana,muna ta faman yi,ga yara da mutane sun taru ana kokarin rabamu amma Sam munki Hakura yi kawai mukeyi,
    Wata motace dalleliya ta kara parking a gaban ta yan mata wata budurwa itace wacce muka samu tare suna rawa ranar da muka je gidan Polio da gudu ta taho tana yiwa yan Uwanta magana Ku kyale matsiyata Ku zo mu tafi pls wannan ba Class dinku bace Ladies pls,babu wanda ya kulata da takalminta me shegen tsini,gani tayi babu me hakura kawai ta daga waya ta kira Babansu tare da fada masa Address din inda muke,Nan take sai ga arnayen Motocin Aayan sunyi parking sun kai su bakwai da securities,yana zuwa ya fito cikin Takun mashahurin Namiji yau sanye yake cikin farar shadda dinkin fitted dai dai jikinsa ya dau matukar kyau ga wani arnen glass  Brown a fuskarsa ba karamin kyau yayi ba,ganinsa yana tahowa nayi matukar firgita kamar zanyi fitsari sabo da na tsorata bazan manta da dukan da yayi min ba,ban San sanda na hantsilar da dayar daga jikina ba na tashi daga kan dayar da nake zaune na gyara hijab dina na kwashe da uban gudu kamar zan tashi sama,ina danyin nesa dasu na tsaya ina maida Numfashi,shi kuwa baima tunani ba Sam bai gane ni ba amma ya tabbata ya sanni.

    Ina kallonsa ya karasa wajensu ya kama yan matan nan ya dinka kwada musu mari ba ji ba gani yana ball dasu sai da ya canja musu kamanni sannan ya fada mota yace Securities su kamo ni,banyi tunanin wajena zasu zo ba ina ta kokarin tare Napep amma babu,kawai sai motoci na gani sun zagayeni,kafin kace me Sojoji sun zagayeni ba hanyar guduwa.
    Saurayin ne ya fito cike da jin kai ya kalleni da kyawawan idonsa,kwarjininsa da haibarsa sun cika min zuciya nayi kasa da kaina har gabana ya matso tabbas nice ya gane nice naje har gida na zagesu da Iyayensu,nan take yace a sa masa ni a mota ko ta wanne Hali,Kuka na fashe dashi me karfi ina rokonsa wayyo uwata wlh ni ba yar uwarku bace baka da dalilin hukuntani,yana jina ko kallona baiyi ba nan take suka jefani a mota suka figi motocinsu dani a ciki,Su kuma yan matan da kyar suka shiga mota daya me jarabar son girma ta jasu sannan tayi waya aka zo tare da daukan motar tata da ta bari gefen titi,Hospital ta wuce dasu aka yi musu Dressing tare da magani sannan suka tafi gida.

      Ina cikin bayan wata mota Sanyin Ac sai kadani yake na dunkule waje daya ina ta faman Rusa kuka cewar an saceni za a yanke min kai,ta window naga mun shigo wani katafaren Building na gasken gasken komai glass ne fadin tsaruwar wannan building bata baki ne ashe wai Office din wannan hadadden saurayin ne,harda su Lifter, ko ina Flowers kamar wani Hotel don a Hotel din ma sai shahararre,ina kallo suka sa Lock tare da kulleni ni kadai a motar tun 9am suka shige ciki ina ta sa ran zasu fito gashi motar taki budewa,na rasa yanda zanyi,11am shuru,12pm tuni nayi bacci a cikin motar,3pm dai dai na farka daga baccin daya saceni a cikin motar tun 12 na fara baccin,yunwa taci har ta cinye amma banga Alamar zasu fito ba Sam,tun ina kuka har na hakura gashi banyi ko Sallah ba ni da bana kauna na hada Sallah sabo da gaskiya Allah yasa min son Addini sosai,ganin basu da niyyar fitowa kawai na fara karatun Qurani a hankali sai da nayi ya kai izu biyu sannan na koma tasbihi da sauran Zikhri dana iya,ina ta yin abina bilhakki da gaskiya ina adduar Allah ya kawo silar samun kudin asibiti na Ammah kuma Allah yasa ta warke,yunwa ta addabeni da kishirwa,5pm naga hadadde ya fito cikin shigar 3qtr fari da riga Armless red kamar ka saceshi ka gudu sabo da haduwa ta ko ina,kallonsa nake tayi ina tasbihi ga yanda ya zubawa wannan Saurayi baiwar kyau,sura, ga iya daukan wanka,uwa uba ga nutsuwa Kwarjini da haiba,Securities suna take masa baya yana gaba da robar ruwa a hannunsa,da sauri suka bude masa mota ya shiga ga yan Jarida suna binsu da gudu suna jefa masa tambayoyi amma ko bude baki baiyi ba bare ya basu amsa haka aka bude masa mota ya shiga sannan Securities suka shiga nasu harda motar da nake ciki suka figa muka bar wajen,ina ta mamaki ko ya manta dani gashi nasan Ammah da yan uwana yanzu sun shiga wani a kan rashin dawowata,

     Wata katafariyar Unguwa ta masu Hanu da shuni muka nufa ina mamaki nan kuma kamar a turai wacce GRA ce wannan haka?domin nasan Ba Unguwarsu bace wannan,Harga Allah wannan Saurayi wato Aayan ya manta dani a cikin mota,direct Gidansa wanda babu wanda yasan dashi nan ya nufa,gidan fadin haduwarsa da tsaruwarsa bata baki ne ya wuce duk inda ake tunani,gidane na fada wanda kafin a sami irinsa sai dai ko a turai ko Abuja watakil,sunayin parking a compound duk suka firfito aka bude masa ya kallesu tare da basu Umarnin su kwashe motocin su kaisu main Family House tunda yana da motoci iri iri a cikin wannan gidan kalarsu daban masu shegen kyau jibga jibga,daya daga ciki ne ya sanar dashi yarinyar fa? Sai lokacin ya tuna da ina ciki,tsaki yaja sannan yace a fito masa dani su kuma su tafi Gida.
    Nan take aka yo waje dani suka figi motoci suka bar gidan daga ni sai wannan Matashi Aayan me cikar zati da kwarjini.

    Shuru nayi tare da sunkiyar da kaina kasa ina wasa da yatsun hannuna jikina yana bari kamar mazari,Kallo daya yayi min wani na mugun wulakanci tare da rainin hankali yana yatsina fuska kamar yaga kashi,nayi mugun raina kaina domin bani da maraba da Almajira mara galibu,juyawa yayi cike da takama hannunsa cikin aljihun wandonsa daya hannun kuma yana latsa waya yace let's go,bana jin turanci amma na gane go din kawai nabi bayan sa kamar Munafuka burina kawai ya kyaleni na tafi gida abina.

    Code number ya danna nan take kofar ta bude ya shiga nima haka,Wow ai ciki Aljannar duniyace kawai komai na Alfarma abin ba a cewa komai domin shagala nayi wajen kallo ina mamakin kudin wannan matashin komai Allah ya bashi.
    Steps ya hau na bene,har na taka zan bishi ya daga min hannu alamar na tsaya tare da zabga min uwar Harara yana tsaki,a tsorace na kame a wajen,tunda ya shiga ya mugun dadewa har ana shirin Magrib sannan ya fito sanye da farar jallabiya fara fitted a jikinsa yana sheka uban kamshi,ina tsaye kamar gunki yazo ya wuce ni kamar Allah bai halacci dan Adam ba haka ya wuce ya fita daga palon sai karar mota naji da alama ya fita Ashe Sallah ya tafi masallaci,nan take naga tsaiwa baza ta kaini ba kawai na fara duba dakuna gaba daya dake cikin palon kasa Allah ya taimakeni ina bude wata kofa na hango makeken daki dauke da lafiyayyan gado da mudubi tare da sip na Alfarma komai milk and Brown color ne a dakin,kofa na gani a cikin Bedroom din nan take na Murda Handle din toilet ce ta yan gayun gaske ban taba ganin irinsu ba dan Allah yasa a birni muke da bazan iya gwada yanda ake kunna tap din ba,ina shiga wajen sink na nufa abin mamaki ina mika hannuna sai ruwa ya fara zuba shaaa idan na janye hannuna sai ruwan ya dauke haka shower ma kai abin kamar Aljanu,ban San lokaci ya ja ba na shagala na manta da kowa ina ta tabe tabena har na gaji nayi fitsari da tsarki sannan na daura Alwala na fito Palo da sauri dan kar mugun ya dawo ya isheni na shigar masa wani waje,ina fitowa na duba gabas na shimfida dankwali na sai na fara jero salloli,Magrib na fara yi sai la'asar da Azahar ina zaune ina azkhar na Mike na gabatar da Sallar Isha da kyar kasancewar yunwa taci karfina gaba daya a kasa a zaune ina adduoina.

     Motarsa naji da Alamar ya dawo lokacin ina yanda nayi Sallah ina adduo ina wanda ban san ma a fili nakeyi ba ina fadawa Allah ciwon Ammah da halin da muke ciki Allah ya yaye mana,kamshinsa naji alamar ya shigo  da mamaki ya kalleni da alama Sallah nayi karfa ko Bedroom na shigar masa,wata mahaukaciyar tsawa ya buga min da tasa nan take na saki kuka,Keeeee a ina kika samu Ruwan Alwala? Jiki na rawa na nuna masa Bedroom din dana shiga da yatsa na, tsaki yaja tare da cewa Allah ya taimakeki wata leda ya wurgo min a jikina sannan ya haura Sama da nasa a hannu.

    30 mnt ya fito da lemon gwangwani a hannunsa yana korawa nan ya fada saman kujera tare da nutsewa a ciki ya dauki remote yana kunna Tv ya kamo tashar wakokin turawa na yan Iska kusan ma kamar tsirara ake nuna su su Nicki Minaj etc.
     Da kyar na Mike na karasa kusa da kafafunsa a hankali cikin ladabi da kwantar da murya nace Sir....Shuru ya min kamar bai San ina magana ba,Nace Sirr.....shuru,Sirrrrrr.....da wani mugun Bala'i ya juyo ba tare da yace komai ba,nan dai na daure da kyar sabo da kwarjininsa nace Dan girman Allah kayi Hakuri ka barni na tafi gida dan Allah,Ammah ta tana gida bata da lfy da kannena yanzu suna cikin damuwa dan Darajar Allah Sir,idan ma baza ka barni na tafi ba to ka kira min su a waya ka hadani dasu na kwantar musu da hankali kafin Lokacin da zaka barni na tafi.

     Shuru naji yayi kamar ma ba dashi nake magana ba,na daure ina hawaye nace Sirrrr....sai lokacin ya juyo ya kalleni tare da dauke kai can yace me kike so kice? Wato duk maganar da nayi ma bai ji ba,wani bacin rai ya kamani cike da fushi na hayayyako masa nace ka barni na tafi idan baza ka barni ba ka kira min sis dina na fada mu......wani gigitaccen Mari naji a kumatu na,kafin na bude Ido ya kara min wani marin me masifar Radadi nan ba shiri na barke da kuka,mikewa naga yayi sai gashi ya fito da dalleliyar wuka a hannunsa,a wuyana yasa ta yace will u close tht ur dirty mouth or...kafin yayi Magana na hadiye kuka na sai shesheka duk da bana jin turanci amma na gane Close da mouth tunda Su Meenat suna koya min.

      Dan kinga ban miki komai ba shine zaki raina min hankali am I ur mate or what?,baki da tarbiya na gama ganewa dama ina nemanki ke gaki marar kunya ke har kin isa ko kalleni ki zageni har gida,kin San ko ni waye who do u think u r? Murmushin takaici yayi tare da cewa dama bari nayi naga karshen rashin kunyarki,har kina min fada ni zaki kalla ki min maganar banza bayan kina hannuna ko yankaki nayi na yanka banza, shi dama Aayan haushin mata yake ji har jira yake mace ta masa abu yaga ya ci mata mutunci domin mata sun masa abinda bazai manta ba.

      Ina gefe nayi mukus fuskata tayi jajir sai yatsunsa kwance a fuskata,wancen abincin ubanwa zai ci miki?da sauri na rarrafa na dauka na bude ledar jiki na mazari na bude Fried rice tasha hadi tare da kaza sai lemo,ruwa da Yogourt a ciki nan take na bude na kai lauma da bismilla kamar mayunwaciya haka nake afka abinci 5mnt kamar waccen ta zubar har na lashe abincin na shanye yogourt tare da lemon sannan na daga ruwan na shanye du,yana zaune mamaki ya rufeshi yana kallon ikon Allah ci kamar jaka,ya tabbata ko da yunwa ya kwana bazai iya cinye abincin ba,na gefensa ya kara jefo min a jikina nufinsa na cinye,ni ko dama ji nake kamar banci ba domin ba laifi akwai ci,haka na dauke na kara budewa yana bude baki da mamaki yaga na kara cinye nasan ruwan ne kawai ban Sha ba amma har yogourt din na shanye ta,da hannu ya min Alama na mike,zumbur na Mike tsaye,yace naje can bangon na dawo haka da sauri naje na dawo,yace yi tsalle na gani nayi tsalle ba shiri sabo da tsoronsa da nakeji,shi tunaninsa bazan iya tashi ba wannan uban abinci dana cinye amma sai yaga ras dani,a zuciyarsa yace bari ya kara gwadawa ya gani,nan ya Mike ya shiga kitchen ya fito dauke da fura tasha hadi a katuwar roba tare da Fruits a wani bowl,nan take yawuna ya tsinke naga dadi ban saba cin irinsa ba amma da shinkafa da wake ce ko plate daya bazan iya cinyewa ba,ko tuwo bazan sauraresu ba amma wannan kayan dadi haka ina zan barsu ko cikina zai fashe bare wannan dan abinci na take away kamar an roko gaba daya bazai plate daya ba,
   
    Furar ya miko min ya tamke fuska yace shanyeta,da mamakinsa yaga na dauke da sauri har ina murmushi don ina son Fura a duniya,kawai na fara Sha cikin nishadi har lumshe ido nake ina addua ga Allah ina inama Ammah na kusa,ina Sha ina Santi a raina gata tayi sanyi a raina nace ah lallai wannan yana so aci a koshi Ashe ma bai cika mugu ba yo ni badan su Ammah ba ai da na rokeshi ya dauki rikona a gidansa,ina ta santina sai gashi na shanye harda lashe spoon din,wata nannauyar ajiyar zuciya ya sauke abinfa ya daure masa kai karfa ko Aljana ce,Nan ya mika min Bowl din Fruits dama su nake kallo cike da kwadayi nan ma na karba harda godiya na koma gefe na fara lunkuma su kankana a baki nace kai Allah me iko na yini banci ba Ashe tanadi Allah ya min harda kara'i yana kallo yaga na tashi Fruits tsaf,karkuce abubuwan masu yawa ne basu da wani yawa kun San dai Harkar yan gayu komai kadan kadan ba dole na cinye ba.

     Yau kuwa yace sai ya kure yarinyar nan mayya,ya Mike ya koma kitchen sai gashi dauke da kaza tasha hadi tana tiriri da Alama warming dinta yayi ya turo min gabana,kamar nayi kuka sabo da dadi yaushe rabon naga kaza guda a gashe sabo da murna ban san sanda na kalleshi ba nace Dan Allah ka daukeni aiki ko share share da goge ne a gidan nan,wata uwar Harara ya zabgo min ban san sanda nace yi hakuri na fara yagar kazata ba ina aikata cikina,gani yayi fa da gaske zan iya cinyewa kawai yace karta je ta barke min da Zawo a gida kawai ya taso ya fisge plate din tare da cewa Mayya.

     Yana dawowa ya mika min faskekiyar wayarsa nufinsa wai nasa Number na kira gida,ban iya ba amma gudun laifi na karba haka nan take nayi kamar zan iya na zuba yatsuna guda biyu na fara birkita screen din,naga Sam ban gane ba nasa yatsuna guda hudu na fara dirzawa a fuskar wayar,na juyata na juya na dukufa kamar Idona zai zazzago sabo da yanda na zarosu ni a dole me danna waya,shi kanshi da ya kalla yayi tunanin wannan yarinyar Aljanu gareta ko mahaukaciya ce bai San tsabar rashin zaman aji ne da rashin shiga mutane daga siye sai siyarwa, gani yayi zan masa barna ya fisge abarsa tare da cewa fada min Number cikin hasala kamar zai dakeni,to mu dai a gidanmu babu waya dama akwai wani Shehu me Kanti idan wani abu ya faru shi Muke kira a waya sai ya kai gidanmu ayi magana don Number dinsa na kaina,na iya da turanci amma wai dan kar nayi mistake ya dakeni sai naji tsoro nace gwara na fada da hausa nan na fara cewa

sifili takwas sifili...wait wait ths is bull shit ban san wannan abun ba,nan nace yi hakuri bari na Canja na firgita kawai maimakon na fada da turancin sai wai dan yafi ganewa sai nace..tayar mota.. takwas..tayar mota,wai gani nayi Zero (O) yana kama da tayar mota shine dan yafi ganewa nace haka,wani mugun dariya ce ta kamashi da ya gano me nake nufi da Zero ne Tayar mota lallai wannan yarinya dakikiyace amma sai ya daure fuska yace wlh zan kwada miki mari zan miki abinda baza ki manta ba,nan take nace 080 sannan na fada masa Numbers da turanci,yace amma ke dan Iskanci zaki raina min hankali kin iya fada dai dai nonsense tare da Jan tsaki yana dialing bugu daya aka daga ya mika min wayar nace Hello...Shehu Mufeeda ce,dan Allah dan kaiwa Ammah wayar mana minti daya,nan Shehu yace to Mufeeda ya fita da sauri yayi Sallama gidan tare da gaishe da su Ammah dasu Meenat suka gaisheshi suna cikin wani Hali sunyi jirim suna jimamin Ina Mufeeda ta shiga tun safe har dare hankalinsu ya tashi,Shehu yace gashi inji Mufeeda tace za kuyi magana ai da sauri Ammah ta karba jiki na bari,Mufeeda tace Ammahna kuna lfy? Ya jikin naki? Ammah tace ba ta wannan nake ba kina Ina Mufeeda lfy iceko,dariya ni Mufeeda na kakalo tare da cewa lfy lau Ammah kin ganni a gidan wannan kawar tawa wacce kika sani Naeema yar gidan me kudin nan kin San ai da sun tafi kasar waje to sun dawo shine muka hadu a kasuwa tace muje naga gidansu,
     shine ma mamanta take tambayata ke nake basu labarin cutarki da aikin da za ayi miki shine Maman tace mijinta yayi tafiya gobe ko jibi zai dawo na zauna kar na tafi na jira zai iya biya mana kudin aikin da za ayi miki,kinga ai bazan taho ba shine na zauna ina jira kuyi addua Allah sa a dace,nan take Ammah wani farin ciki ya lullubeta tace Mufeeda kin tabbatar haka zancen yake ba karya?nace tabbas Ammah ai kin San halina dai ko kin San kuma dalilin fita ta Allah watakil ya amshi adduar mu,Ammah kinga dadin da naci harda Kaza da Yogourt,kuyi addua amma yau Ni ina cikin daula ina su Meenat bani su,nan ma aka bawa Meenat suka Sha labari aka mikawa Maeeshah ma tana Anty jambaki pink ya kare ki siyo min wani,kuma takalmi na ya tsinke Sis nace to Maeeshah zan siyo bawa Ammah,nan nace Ammah aci gaba da kular min da Kasuwanci na dan Allah Meenat tayi komai,Ammah tace kin San basu iya kosan sosai ba,Nace Ammah suyi haka koma yane a tara min kudin in na dawo za muyi magana sai goben idan ya dawo me gidan zan sanar dake idan Bai dawo ba zan fada miki komai dai,Allah yasa a dace cewar Ammah ta mikawa Shehu wayarsa Mufeeda tayi masa godiya ta kashe shima ya musu sallama ya tafi,nan Ammah tace Meenat ta kulle musu gida ta rufe suka yi kwanciyarsu cikin farin ciki.

    Ni kuwa ina gamawa hankalina ya kwanta nan na saki ajiyar zuciya,shi kuwa da mamaki yake kallona yanda na iya fesa karya haka,lallai suna da matsala amma ina ruwansa,ni ko dama su Ammah nake ji kuma na gyara komai,idan na koma nasan karyar da zan kara shimfidawa, baki ya tabe nan take ya fisge wayarsa tare da wucewa samansa,ni kuwa yana tafiya na koma saman 3seater na kwanta a tsorace har bacci ya saceni, tunda ya shiga bedroom ya rasa wannan mugunta zai min wacce bazan manta ba ina cikin bacci naji ya harbo ni kasa daga saman sofa,a firgice na tashi, ba Imani yace sai nayi Kamun kunne,haka nayi na Dade ina yi har sai da na saki Kuka,sannan yace nayi kneel down sannan Hands up nan ma na fara ina tayi haka yayi tafiyarsa ya barni ina ta abinda ya sani har bacci ya kwasheni na bingire a wajen,ban farka ba sai da gari yayi haske na Mike a firgice tunawa da banyi Sallah ba yasa na Mike da sauri na fada bedroom din da nayi Alwala jiya,komai na kayan wanka da amfani a kwai a toilet din masu tsadar gaske,ba bata lokaci tube kayana na kai hannuna ruwa me dumi sosai yana zubowa gwanin dadi  ban san sanda na fara wanke kaina da shampoo me kamshi da tsada ba,ina gamawa na dauki liquid soap na sheka wanka sai kamshi ina ta washe baki,ina dubawa naga harda sababbin tooth brushes da toothpaste na dauka kuwa na wanke bakina tas abinka da abu me tsada hakorana suka kara haske da kyau Malam nayi wani Fresh dani,Towel nasa tare da goge jikina tas,sa nan na daura Towel na fito ina kara tsane gashina,mirror ba abinda babu na shafawa masu tsada,na dauki lotion na shafa a jikina,babu powder sai wata fara kawai na shafa abata na dauki lipgloss na shafa me kyau red,ban san jagirar waye ba na dauka na zizara a Idona sai gashi nayi kyau sosai.

    Gashi na wanda ya bushe na taje na shafe shi da Maya Mayan gashi yana sheki da kamshi dama gani Allah ya bani tsayin gashi,Daure abina nayi nan take nayi acuci da gashina sannan na shafa roll on tare da turaren jiki dana gani me arnen kamshi,kayana na kwaso na saka haka ina so na wanke pant dina amma ba dama kawai na maida abina sai lokacin na tuna banyi sallar Asuba ba da sauri nayi tare da Azkhar sannan na fito Palo cikin Jin dadi na zauna,ina jin motsi na sauka kasa tare da kneel down na daga hannu sama wai dan yace a haka na kwana inayi,kallo daya ya min yasan Lallai har wanka nayi,ko kallona baiyi ba ya fita,15mnt sai gashi ya dawo tare da take away leda hudu,ya zauna a saman Sofa tare da miko min leda uku da sauri na karba dama yunwa nake ji nan na zauna daram tare da bude ledar sai ga kwai da chips tare da gashashiyar Hantar rago, haba Malam nan na zaro harshe na lashe labbana na fara dagargazar Harka yi nake ba ji ba gani,nan na kau da Leda daya na bude daya na lashe na jawo ta Ukun na cinye komai tas tare da daukan ragowar ruwana na jiya na shanye tas nace Alhmdllh tare goge hannuna da tissue din dana gani ciki.

   Mamaki ya gama kashe Aayan har firgita yayi yana mamakin a ransa kuma cikinta baya lalacewa,yana kallon TV yace tashi ki gyara gidan nan kaf yayi maganar kamar bada ni yake ba,Zumbur na Mike na kayan aikin,kitchen ya nuna min da yatsa ina shiga na gansu a shirye na hado da kayan mopping,yace na biyo shi haka yasa na gyara samansa Kas Kas, ko ina yana kyalli har su toilet,abin ya bashi mamaki baiyi zaton zan iya gyara haka ba,muka dawo kasa ko ina na gyara har room din da nayi wanka da toilet,haka ya dinga nuna min wasu sashen har wajen motsa jikinsa sai da na gyara tsab,ta window na hango maza suna ta aikin gyaran compound flowers tare da goge windows ni kuma na gyara ciki, nayi matukar jigata nasha wahala,yace sai na shiga kitchen haka na shiga na wanke na goge na gyara komai neat har store,haka fridge ma ya fitar da abinda suka lalace yace na gyara ciki tare da bani wasu abin na gyaran Fridge haka na gyara fes na kara Mopping kitchen din na wanke komai na shanya su sannan na fito,ina fitowa yace naci gaba da Kamun kunne ba Hutu,inayi ina kuka,sai da na kai 1pm sannan yace naje nayi Sallah na bar masa gida,cike da Murna na Mike na gyara jikina tare da Alwala nayi Sallah ta saida na kara gyara fuskata gudun tuhuma wajen Ammah sannan na fito tare da yin hanyar waje,Keee naji muryarsa me sanyi,juyowa nayi a rude nan naga ya daga waya yana magana Hello Abbi ka tashi lfy,ta ciki naji Muryar Abbi yace zo ka bude min kofa ina son magana da kai gani a gidan ka wato ni zaka rainawa Hankali ko,nan take ya firgita amma dake namijin duniya ne sai ya maze bai kawo komai ba ya raba ta gefe na wani kamshi ya dakeni nan take jiki na ya mutu na lumshe ido,kofar ya bude kawai sai ga Abbi ya bayyana a gabana da sauri na tsorata tare da ja baya.

    Salati ya saki da salallalami yace dama nasan wlh ba abin kirki kake aikatawa a wannan gidan ba shi yasa nazo da kaina,ashe baka da kunya baka da mutunci ai jiya na tambaya ina ka kwana ance ba a sani ba nasan kana nan,ashe abinda kake aikatawa kenan munafiki ka nuna Sam kai baka kaunar mata Ashe abinda kake kenan,karuwai kake kawowa gidanka,ashe shi yasa baza ka iya zama da aure ba,wannan yaro kwai tsinanne in Allah ya yarda Cutar kanjamau ce ajalinka,baza ka jawo mana abin kunya ba wlh dole yau Hajja taji zancen nan kuma aure dole kayi zaka ga abinda zai biyo baya,nan Abbi ya min kallon Banza ya fice a fusace.

    Shi kuwa Aayan ko a jikinsa haka ya nuna amma yaji zafin sharrin da Abbi ya masa,ni kuwa tausayinsa naji sabo da na tuno maganganunsu farkon ganina dasu,Driver ya kira a waya sai gashi yazo  umarni ya bashi jeka wannan zata gwada maka gidansu ka,ka kaita can.Nace na gode wata uwar Harara ya balla min nan take nayi mukus tare da bin bayan Driver na shiga motar sai muka bar gidan ina jin dadi na rabu da jaraba.









AsmaBaffa
[1/1, 10:59 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

   KASUWANCI NA




          11-15




Official




By
AsmaBaffa





      Ths page is for u  MARCYCOOL.

    ina matukar Godiya da jinjina fans masu Sharhi aci gaba da gashi kuna birgeni.






       Allah ya taimakeni Driver na da kirki cikin mutunci ya kaini har kofar gidanmu wanda kaf mutanen unguwar mamaki sukeyi na wannan arniyar mota amma wai sai suka ga Ni Mufeeda yar Kasuwa yar talakawa fitik wai ni aka sauke a wannan mota, ai fa sai mutane suka fara guna guni ga zahiri ai karuwancina ya girmama ni kuwa Allah sarki ban san ma sunayi ba, wata kawata a makwaftan mu Nawwara itama dai Nawwara yar malam Shehu ce talakawa amma sun fimu rufin asiri ita kadai ce kawata sai kuma wata yar gidan masu kudi Na'eema amma ita yanzu sun koma Kasar waje da karatu har iyayenta suna kasar waje abinsu,

    A hanya Nawwara tace Mufeeda kece a wannan zundumemiyar mota haka duk da bana zarginki ki kiyaye ko sabo da sharrin yan Unguwa,Murmushi nayi tare da cewa Allah kadai nake tsoro ni,Allah yaga zuciyata.
    cike da farin ciki na shiga gida da Sallama dauke a bakina,da fara'a suna min Oyoyo sannan na wuce wajen Ammah tare da gaisar da ita,tace  Mufeeda kar ki kara yin irin wannan tafiyar kinji na fada miki,wannan ya Zama na karshe da zaki tafi wani gida ki kwana ba tare da Sanina ba sai dai ki bugo waya,bazan yarda da wannan shirmen ba,karki ga na yarda dake kice zakiyi abinda kika ga dama ko dan kina ci damu etc kice zaki juya ni baki isa ba,ni ba irin iyayen nan bace masu son abin duniya akan yara ne ke ci dasu sai su zauna yaran na juya su sai abinda suka ga dama zasu yi,ki nutsu wlh akan haka gwara mu daina karbar abin hannunki bana so neman Kudi ya kaiki ga halaka ko sabawa Allah,naji matukar ciwo da sai dare ma zaki bugo ki fada min ni har ga Allah ban yarda da zancenki ba kawai dan naji lafiya kike yasa na dan samu nutsuwa,nan Ammah ta dinga fada ba ji ba gani ina bata hakuri harda kuka na,nace bazan kara ba kiyi hakuri abinda na tsaya nema ma ba a dace ba domin me gidan yayi tafiya kasar waje nan ma na kara mako karya ta na fada,aiko nasha fada wajen Ammah,ni dai hakuri nake bayarwa har ta hakura.

     Bayan kwana biyu tsakani naga sana'ar tawa ta danyi kasa don haka na tattara ragowar kudin dake hannuna na siyo kajin Hausa da Akuya guda daya wai zan gwada yin kiwo ko za a samu suyi albarka,Kaji biyu yan budurwa na kawosu,akuya tana meee...mee na samu na daure ta can karshen gidanmu,lokacin wake beans yana araha kawai na auni kwano biyar na boye ina jira yayi tsada na siyar naci riba,sannan na dan siyowa su Meenat kayan kwalliya tare da kayan makaranta Uniform na dinka musu sabo idan an koma schl suma su sa sabo,haka na siyo mana Atamfa muka raba yadi biyu kala Uku akayi mana dinki me kyau na talauci domin rabi wasu yadi ne na adon Atamfa akayi mana kari dashi,sai suka ba da ma'ana,dama bamu da kudin dinka shadda daga atamfa sai materials sai kuma kayan gwanjo da muke sawa,suma dinkin atamfar na talauci duk bamu da riga da zani ko daya daga skert damamme sabo da yadinma bai isa ba bare tela ya maka mana dinki dole sai dan fitted,sai ko dogayen riguna baza ka gammu cikin Tsumma ba Sam sabo da ina yawan yi mana dinki tare da yan takalma na roba yan Dari hudu zuwa biyar muna dasu da yawa dasu muke too match,haka mayafai ma ina siya mana da hijabai zaka ga muna canja abinmu iri iri mata sai da gyara ai,bani da burin da ya wuce naga Ammah cikin farin ciki Tare da kannena duk kudin da nake nema sabo da su nake nema.
   
    Asalinmu
       Sunana Mufeeda Adam Fatima, Asalin Shuwa Arab ne Babanmu,a Borno state suke da Zama tare da Family dinsa gaba daya,Bashi da Ilmin Boko sosai sai kasuwanci da yake y,Babanmu Adam yana da dangi da yawan gaske wanda mu bamu San dasu ba Sam,Iyayensa sun Dade da rasuwa tun yana yaro domin shi kadai suka Haifa Allah ya musu rasuwa ya taso a maraya,shi yasa ma ya taso da neman Kudi har Allah ya kawoshi Kano state,yana shiga kauyuka saro kayan Noma ya kai kasuwa,Har ya shiga Kauyen Ammah wato Kauyen Rimin Gado can rigar Fulani,Nan yaga Ammah cikin halin rashin gata tana Shan wahala hannun matar uba sabo da bata da Uwa sai Uba,danginta kuma fulanin tashi ne basa Zama Sam kullum a yawon daji suke basa Zumunci,bayan Adam Abban mu ya auri Ammah  da shekara daya Allah ya dauki ran Baban Ammah wato Sulaiman,Haka Abba yaci gaba da kula da Ammah suna zamansu lfy a cikin birnin kano gwale,ko sunje kauyen ma ba wasu dangi sun tafi yawon Shanunsu har Ammah ta daina zuwa ma tunda duk yan Uwanta sai wanda suke uba daya kuma basa kulata sai ta kyalesu kawai amma duk da haka tana kaimu muna zuwa itama kafin lalura ta sameta tana zuwa musu.

     Mu kuwa ganin basa zuwa basu damu da mu ba ko tace muje sai muki zuwa idan munje ma basa ganinmu da daraja,Shekarar Ammah da Abba biyu da Aure ta Haifeni aka sa min suna Mufeeda kowa yana yabon kyauna,sai da na cika shekara biyu sannan aka kara haifar Meenat,itama After 3years sai aka Haifi Ma'eeshah,Lokacin Babanmu ya samu wadata sosai ya siyi gida kato cikin Rijiyar Zaki muka koma ciki yana Business sosai sannan ya zana waec da Neco ya koma makaranta yayi NCE ya gama,lokacin tuni ina zuwa Primary schl amma ta Gomnati sabo da ba masu kudi bane mu sai rufin asiri domin munfi karfin ci da Sha bare sutura,ina primary 3 aka saka Meenat da Ma'eesha suma muna zuwa nice Babba, Da yamma muje Islamiyya, ina kula dasu sosai domin tun ina yarinya Allah yasa min son iyayena da yan uwana fiye da kaina,mun taso cikin kulawa da tarbiya muna jin dadinmu har na kusa gama Primary

sai kuma muka ga Abbanmu sam ya daina kula Ammah sai wulakantata yakeyi,ba irin wulakancin da Ammah bata gani ba a hannun Abba,idan suna fada har Kuka mukeyi,amma duk lokacin bamu da wayo bamu San akan me suke fadan ba,muna dai ji yana cewa idan ya gaji korarta zaiyi,tun abin baya damun mu har muke damuwa muna bashi hakuri,bamu San dalili ba dai sabo da Ammah bata bari mu San halin da suke ciki,sai dai muga tana kuka watarana Abbah yace zai fita wata state dake Kudu Abia state neman Kudi tun da Allah yasa ya tafi bamu kara Jin labarin Inda yake ba ko a waya.

    Mun shiga damuwa me tsanani,Amma taje har garinsu wajen danginsa tare da mu amma sukace suma basu da labarinsa,haka abokanansa na business da sauransu duk an nemesu shuru suma basu sani ba,munyi kuka munyi bakin ciki har aka kwashe shekara guda lokacin na gama primary,anyi cigiyar Abbah har gidan Radio amma ba labari haka Ammah ta fara Sana'ar kosan siyarwa da Awara tare da sauran kanana nan sana'a gida dasu take mana komai na rayuwa,har na shiga Jss1 na gama na shiga jss 2,Katsam lalura ta samu Ammah haka kawai bata iya motsa kafafunta daga Hips zuwa toes,munci kuka gashi nice Babba ga karancin Shekaru haka makwafta suka taimaka mana muka kai Ammah asibiti mafi sauki,da yan kudin da Ammah ke Tarawa muka sai mata magunguna sannan suka ce dole akwai wani aiki da za ayi mata nan gaba,tun da muka dawo Ammah ta dan samu sauki ni kuma dama duk sana'oin nata na iya su sai naci gaba da yi na daina zuwa schl nake biyawa su Ma'eesha suna zuwa,ni ke kula da Ammah da gidan baki daya,akan sana'ar ma sai na kara wasu da yawa ina yi iri iri komai siyarwa nakeyi ba sauki,har Allah yasa  Meenat na Ss1 Maeeshah na jss2 ga Islamiyya suna zuwa ni kuwa komai ya tsaya min sai neman kudin jaraba kamar zanyi sata.

har yau munyi munyi da Ammah ta fada mana fadan dake tsakaninta da Abba kafin ya bace amma taki fada mana sabo da haka muka kyaleta sannan muka kara tsanar Abba da ya gudu ya barmu,dan ni ko zancen wani Abba bana yi sam bama na so a ambaci Sunansa shi yasa a makaranta ma Sunana Mufeeda Adam Fatima sabo da sunan Ammah Fatima kawai nace ai bazan sa Kakanmu ba Ammah ta zan sa,haka Meenat Adam Fatima tare da Maeeshah Adam Fatima haka duk muke Amfani dashi da ace da halima sai dai nasa Mufeeda Fatima Adam to kawai dan da uba ake ado shi yasa ba kyau dole nake Sa Adam.
    Za muji nan gaba Ina Abbah ya boye oho,ko da gaske ya bata,ko yana raye,ko yan Mafiya ne,mene ya hadasu da Ammah suke fada,wacce lalurace a jikin Ammah haka? Oho dai.

     Ci gaban labari

bayan kwanaki kadan na yanke hukuncin zan fara zuwa gidan yan siyasa tare da yan kasuwa da sauran masu kudi na fara neman taimako ko Allah zai sa a samu me Imani ya tallafa a biyawa Ammah kudin magani,bayan na gama kosan siyarwata tare da gyaran gidan haka nayi girkin rana na kwashe a cooler sannan na fara daka lallen da nake siyarwa ina daurawa a leda ina saidawa ashirin,lallen ma ban barshi ba sai dana yi masa Algus na hada da gayyen bishiyar sabara na daka ya kara yawa na daura na ajiye,idan mutum ya siya lalle sai yaga lallen yaki yi masa ja yadda yake so to anyi masa Algus da wasu gayyen,wanka nayi na shirya cikin skert dina dan gwanjo tare da T-shirt dita nayi kyau nasa Hijab dina me hannu sunsha wanki da guga,ban shafa ko Powder ba na yiwa Ammah Sallama nace na tafi kasuwa siyo kaya,tayi mun a dawo lfy,ban zarce ko ina ba sai gidan Chairman din local government dinmu,ban san gidan ba da tambaya aka nuna min ni da me Napep,bayan na sauka mutane damkam a kofar gidan har da yan Sanda masu gadi gida me kyan gaske,maza yan siyasa sai kallo na suke domin sunga baiwar kyau wajena,da gani kuma sun San ba yar siyasa bace ni kamilalliyace ni yar mutunci,salamu alaikum nayi musu sallama tare da gaishesu sannan nace Dan Allah yau Hon yana nan? Suka ce ae kinyi sa'a yana gida muma shi muke jira,amma tunda ke macece bari mu rokar miki masu gadi ki shiga kice wajen matar Hon kika zo,ai kuwa haka akayi nan take yan Sanda sunga kyau suka ce na shiga,

nayi godiya na fada gidan cikin nutsuwa,wata yar aiki ce ta nuna min kofar shiga ciki,nace tayi min jagora zuwa wajen Hajiya,har nan ta kaini sannan ta shiga tare da sanarwa Matar Hon,cikin Sa'a aka ce na shiga har ciki yar aiki tayi min iso,matar Hon yarinya baza ta wuce 24yrs da ganin irin kyau da Allah ya min yasa ta tsaneni kar na kwace mata miji,nan take naga ta canja fuska ta Mike tare da miko min Dubu biyu tace na tafi an sallameni,babu bakin magana jiki ba kwari na karba na dau hanyar fitowa kenan kicif sai ga Hon ya sakko daga sama da katon cikinsa yana shafa tumbinsa,ya kalleni nan take ya lashe bakinsa tare da yi min signa da Ido kamar kwarto,ni dai na fice da sauri daga palon.

    Matar Hon tana Alhaji ga abincinka amma tuni yace Hajiya na fita Office ana jirana ya fito da sauri yazo kusa dani a bakin gate,da sauri na durkusa na gaisar dashi sannan na fada masa abinda ya kawoni nan take yace ai karamar matsalace wannan ya bani card dinsa yace na samesa a guess house dinsa,na tsorata amma dai na karba nace sai nazo na fito daga gidan na tafi gida ina murna ta.

     Ban fadawa Ammah inda naje ba nasan fada zata min kawai nayi shuru,washe gari kuwa dama yace 5pm zanje gidan da yace,ba tsoro na shirya na tafi ba wahala na gane gidan na fita daga Napep,Naga gida rafkeke na kwankwasa sai ko ga me gadi ya bude yana ganin budurwa yasan irin matan da Hon ke Tarawa kullum ne da fara'a ya tarbeni yace shiga yana ciki,nan ya min iso har cikin palon Hon,sai lokacin tsoro ya kamani,lokacin na hango Hon daga shi sai Singlet da gajeren wando yana latsa waya,da fara'a yana washe baki yace zauna mana kyakyawa me kyan sura,Nace ba sai na zauna ba idan zaka taimakeni to ka bani dan Allah,dariya yayi yace zo mana ke ya kike abu kamar bagidajiya ina ganinki wayayya zo muji dadi mana sannan na baki kudin a wuce wajen kawai,tsorata na karayi na fara ja da baya nace ni ance ba kyau namiji ya rike ma mace  hannu nidai zan gudu,Hon yayi dariyar Kuruciyata yana lallabani yana hure min kunne amma naki matsawa ko kusa dashi,tasowa naga yayi ya taho jikina ya fara shafa min fuska yana kokarin cire min Hijab,yana sakin wani Gurnani ai da gudu na ja baya a rude na bude kofar na fice da gudin tsiya ko me gadi gani yayi kamar walkiya na bude kofa na fice wufff.

     Ina Haki na fito da matsiyacin gudu na cukwikwiye Hijab dina na tattara skert dina ba takalmi a kafata tuni na watsar dasu,Na samu gefen titi kawai na Mike na dinga tsinka uban gudu ka rantse yan Mafiya ko Zaki ne suke Bina,ga unguwar shuru irin ta masu kudi ba kowa ba a ganin ko mota a titin,can naji karar mota ta bayana tunanina Hon ne haba ai sai na kara karfin gudu na yi nake kamar numfashina zai fita,a hankali motar take tafiya a saitina sai lokaci ina gudu na dan kalli glass din window din an sauke glass din ana ta min magana ta ciki gudu nake iya karfina da karfi nace wlh bazan tsaya ba Hon tsinanne dan Iska ina ta zagin me motar ji nake Hon ne ashe Aayan ne yake ta Bina da motar yana sheka dariya yanda yaga ina uban gudu kamar na tashin kiyama,tsabar mugunta sai yaki yin magana kawai yake ta Bina da mota duk inda nasha kwana sai yasha da motar yana ta dariya har sai da karfina ya kare tas na fara kokarin tsayawa Ashe ban sani ba idan gudu ya cika yawa yakai wani limit mutum kasa tsayawa yake da kansa sai an rikeshi kawai zai ta gudu ne,ina so na tsaya ina kokarin tirjewa amma ina gudu kawai nake falfalawa na fashe da kuka kuma ina ta gudu na kamar masifa har dai da kyar na samu na rike wata bishiya sannan na zube a kasa wajen ina maida numfashi,Dai dai lokacin Saurayi Aayan yana ta dariya harda kwalla sannan ya take birki a inda nake Kuuuuu yana ta dariya yana rike ciki,sai da na Huta sosai da sosai sannan na tashi tsaye ina karkade jikina,sai lokacin na hangoshi cikin motarsa Ashe shine ba Hon ba,kawai nima abin ya bani dariya kamar sabuwar Kamu na dinga sheka dariya harda kwalla,a ransa yace lallai yarinyar nan da alama mahaukaciya ce ko Aljanu gareta,na kalleshi saitin window na daure fuska sannan na maka masa harara,ai ko ya fito a fusace na firgita ba damar guduwa dan na gaji ina ji ina gani ya fito ya zabga min Mari sannan ya jefar dani a kasa keee ya daka min tsawa ba a min ko kallon Banza mind ur fucking Business,bana jin turanci tunanina yasan Business dina dana keyi a gida kawai sai nace dama ai ni Kasuwanci na nakeyi ina ruwanka dani haka kawai sai ka dinga cin zalina dan kaga bamu da kudi,ai kudin naku bana tsoron Allah bane tunda ba a taimako sai yawo a mota ana zalinci,tsaki yaja me karfi cikin takama ya koma labebiyar motarsa fuuuuuuu ya figi abarsa.

   Ni kuwa na turo baki tare da cewa Allah ya isa wlh duk ranar daya mareni again Allah sai na rama za a gani ai,nan na gama Kuri na sannan na tafi gida abina.

     Washe gari ban tsorata ba na kara shiri na tafi gidan Vice Chairman neman taimako amma haka na yini ban samu ganinsa ba sai yaronsa,Nace dan Allah wajen Vice nazo idan baza ka damu ba ka min hanya na ganshi,cikin daure fuska kamar zai bigeni ya hayayyako min da masifa ke malama an fada miki ya tafi Umrah bazai dawo yanzu ba,irinku dama yan mata makaryata da Iyayenku sabo da son abin duniya sai ku fara karya kuna zuwa Maula daga nan a lalata Ku yan iskan yara,har nawa kike amma har kinsan yawon Maula,nan dai yaron Vice ya min tatas na baro kofar gidan da takaici.
    Ban dai kara hakura ba washe gari haka na kara shiryawa na nufi gidan wani Commissioner na Ilmi,a bakin gate kofar gidan na yini ina jira ko za bani dama na shiga ciki amma masu gadin ko kallona ba wanda yayi,har zan tafi sai ga wani ya taho da Jibgegiyar mota kida na tashi Malam nan take mukayi Ido hudu da wani Saurayi black Handsome dan gayu,sai kallona yake,ina tsaye aka bude masa gate,sai wani kallo yake Bina dashi kamar tsohon maye,nan take naga ya sauke glass yana murmushi tare da yafito ni da hannu wai naje,da sauri na karasa,sai kallo yake kare min tun daga sama har kasa yace yan mata wa kike nema?nace wajen Babanka nazo Commissioner na Ilmi da alama kai dansa ne ko?murmushi ya kara saki yana min kallon irin na yan duniya,yace ae dansa ne ni ya akayi?Nan na sanar masa taimakon da nake nema akan rashin lafiyar Ammah yace wannan ai karamar matsala ce Beauty,kawo na sa miki Number ta,nace ni bani da waya mu talakawa ne,baki ya tabe tare da dauke kai yana cewa ai kuna da amfani ta wani fannin,ban gane me yake nufi ba kawai naga ya miko min wata waya sabuwa dal a kwalinta amma karama ce Nokia me kyan gaske,yace kinci sa'a Baby na siyo wa yaron Mama waya karbi ki rike wannan ga sim card  sabo bari na sa miki zamu dinga magana ta waya kafin Abba ya dawo sai a kaita asibiti.

    Tunanina da gaske ne ba tunanin komai nace nidai ka bar wayarka amma ka bani Number dinka zan nemeka kaji,yace karbi karki damu kyauta na baki yan mata kamarki ba waya ai abin kunya ne,cike da tsoro dai na karba hannu na rawa garin zai miko min sai da ya shafi hannuna yana sani harda lumshe ido,da sauri na dauke hannuna ina godiya,da kansa ya hada min wayar da komai ya sa min Number dinsa ciki ya dauki number ta sannan ya miko min Dubu biyu wai na hau Napep,naki karba kawai sai ya zubar min da kudin a kasa yana shu'umin murmushi ya figi motarsa ya shimfida cikin wannan gida na alfarma,na dade a tsaye ina tunani kawai dai nace Allah gani gareka na kwashi kudin nayi gaba abina.

     Danaje gida Ammah dan kar ta hanani amfani da wayar sai nayi karya nace Ammah yau dai na karbi kudin adashina na gidan Haule kinga na siyo waya sabo da baza a ace a gidan nan bamu da waya ko daya ba,nan suka dinga murna da tsalle,Ammah harda sa albarka tana murna dama yaran Zamani badai zuba karya a kifar da iyaye a corner can.

     Next day ban hakura ba dai sabo da ina tsoro kar fa nazo ba a samu tallafi wajen Dan Commissioner ba kawai na shirya na Tafi gidan Dan Majalisa na tarayya da suke Zama Abuja,ni dai nasan ba lallai na sameshi da family dinsa ba domin wasu ma ba a Sanin inda gidansu yake buya suke su canja unguwa ko state dan kar a je musu Maula,ni kuwa tsabar jaraba sai da na kwakwulo gidan da tambaya tun daga unguwarmu nake bin gidajen manya ko wani ya sani,idan ance me zaki yi sai nace sako wasu zasu kai gidan da haka aka gwada min gidansa amma fa basu cika Zama a kano ba kawai dai zanje na gani ko me gadi na samu contact Dinsa ya min hanya, haka na fada Napep sai gidan Dan Majalisar tarayya Abuja,gidan kansa abin kallo ne sabo da ya hadu karshe.

     Securities ko ina a gidan harda mutane a kofar gidan Yan maula,haka na kutsa kai cikinsu tare da tambaya ko me gidan yana nan suka ce ai rabon da yazo kano ma yau Shekara biyu kenan.
   Baki na bude tare da mamaki wani ciki yace sai dansa Yarima Bobo da ake aikowa da sakon yan siyasa ana kawo musu,yanzu ma shi muke jira ya fito kin San shi a kwai gadara da wulakanci sai yaga dama yake fitowa ya bamu sakon Hon Rep,
    Nan take nace aiko sai na jira dan nasa dan Ubansa ko shi waye,ina nan tsaye na gaji da jira har 2pm a wajen nayi Sallah saman dankwalina wata me tallan Fura tana zaune a kusa nace ta dama min ta Hamsim,haka ta dama furar tasha Nono me kyau da sugar, nace juye min ita a leda ki kulle,haka ta bani katon Dauri a farar leda na Fura da nono na bata ,sannan na siyi yogourt yar hamsim a leda tayi kankara,ina fara sha sai ga wani dan sanda yace Yarima yace Ku shigo ya ganku zai wuce Flight dinsa ya kusa tashi,da sauri mazan suka fada gidan yuuuuu,ni kadai ce mace haka na danna kai ciki ina Shan furata a leda yanda nake zuka kamar jariri ya kama Nonon uwarsa haka na lumshe ido ina tsotsa Malam ba ruwana.

    Muna shiga ciki nan na hangame baki wajen kallon irin haduwa na gidan ba a magana,Saurayin muka hango chocolate dashi ya hadu sosai ga kyau ga iya wanka abin kallo yana kamshi yasha light blue shadda yana sheki ga motoci a gidan birjik,muka karasa gabansa yana zaune a wata farar kujera yana faman yanga da gadara,ido muka hada dashi yasha mamaki ganin harda yarinya haka,dan a wajensa bana Sahun yan mata
   Ya fara sauraron wasu kawai muka ga Securities sun wani gigice sun nutsu waje daya tare da bude gate jikinsu na rawa,sai ga wasu motoci dalla dalla sun shugo gidan sun kai biyar kamar nasan motocin,ashe kuwa shine domin Saurayi Aayan ne me tashen kyau da Naira.

     Gani mukayi Yarima ya fadada fara'arsa tare da mikewa ya tarbi Aayan da alama abokaine harda wani tafawa suna dariya,Yarima Bobo yace amma kai dan Iska ne Aayan tun safe kace zaka zo kasan yau zan koma Uk amma ka bata min time yanzu na daga flight dina sai 12am na dare,Murmushi Aayan ya saki cike da izza ya dage masa gira daya kana yace to ya akayi ne man sauri ka gama da mutanen nan naku kasan ban son jira,Yarima yace ai kai dan Iska ne ga sit can,kusa da mu ya zauna can nesa a wata kujera ta yan gayu,Juice aka kawo masa yana korawa,a raina nace Allah sarki talakawa mu ko ruwa babu me bamu.

    Yarima yana ta ganin mutane yana sallamarsu da kudi,sai yace pls Ku mazane kuyi hakuri na sallami yarinyar can tunda macece,a raina nace Ashe yana da kirki,nan yace ke zo naji na sallameki sai lokacin Aayan ya kalli inda nake muka hada Ido,da mamaki ya kalleni lallai yarinyar nan wato har maula take zuwa gidan masu kudi sabo da son kudi,ko dai bata da iyaye ne oho,yana gani na karaso gaban Yarima ba tsoro na durkusa gaban Yarima tare da cewa ina yini?yace lfy tashi tsaye ki fadi abinda ya kawoki sauri nake ina da bako,ina durkushe a gabansa kaina a kasa kuma ina ta zukar Fura ta kamar yarinyar yaye,idan nayi magana daya biyu na zuki furata,babu wanda baiyi dariyar abinda nake ba kowa yana ganin ai yarinya ce,shi kuwa Gogan Aayan a zuciyarsa yake Dariyar kwadayi na,kuma sabo da kuruciya a gaban kowa ina mace ko dai bani da hankali ne. na karanta masa ciwon Mahaifiya ta,yaji tausayina kuma lallai yaga mu abin taimako ne,sai yace jirani a gefe bari na sallami sauran,

  nan na Mike na koma gefe,Aayan ko kallona bai kara yi ba har Yarima ya gama da mutanen kaf suka tafi ya rage daga ni sai Aayan sai Yarima,yace zo ke,da sauri na karasa gabansu su biyu,yace ina babanki ko ya rasu? Bana so na fada a gaban Aayan wanda ke latsa waya,sai nace Sirri ne sai dai idan zamu koma gefe na fada ma,murmushi ya saki yace to ya Mike ya taso na kara kasa da murya da rada nace bacewa yayi ba a San inda yake ba,kawai ko guduwa yayi wa ya sani,dariya Yarima yayi yace to shike nan ki kawo takaddun asibitin naki mu gani,nace to ai naji ance zaka yi tafiya,no ki jira zamu fita da frnd dina sai mu saukeki ki dauko takardun,a tsorace nace tab wancan masifaffen ne zai yarda,kin sanshi ne?ya tambaya,nace ae na sanshi kullum sai ya mareni idan ya ganni,murmushi yayi yace to ki jira ai motata zaki shiga,murmushin da nayi shi ya tafi da Imaninsa ya tsaya yana kallona,sai can ya dawo hayyacinsa yace ina zuwa ya koma wajen Aayan dake ta faman cika yana batsewa,Yace kai Yarima kasan fa ban son jira wlh zan tafi ka tsaya kuyi hirar,ba class ba komai,Sorry let's go,Aayan da mamaki yaga na shiga Motar Yarima shima cike da takaici ya shiga nasa motar suka ja muka bar gidan cikin zugar motocinsu,sai da aka zo kusa da gidanmu suka tsaya,Yarima yace yarinya yisauri ki dakko mana na gani,ina fita na kwashe da gudu na karasa gida na fada daki na ebo kamar kiftawar Ido na fito da wani gudun kowa ya ganni sai ya tsorata ko wani abu ne ya biyoni,da gudu ina Haki na kawo masa takaddu ya sauke glass kasa ya karba ya gani tabbas da gaske nan ya miko min card dinsa yace ga Number ta na Nigeria dana waje ki kirani kiji,da sauri na daga kai sama,ya zaro Dubu goma ya bani yace gashi ki siyawa marar lfy ko ruwane,godiya nayi na karba, Yarima yace ki daina gudu kinji yarinya ba kyau mace tana gudu,da ladabi nace to na daina ai tsoro naji kar Ku tafi sannan na juya na dau hanyar shiga gidanmu,sai da naje bakin kofar gidanmu zan shiga na juyo baya sai naga Motar Yarima sunyi gaba sai Na Aayan yana kallon inda zan shiga kamar Munafuki muna hada Ido suka figi motarsu fiii suka kara gaba abinsu nima na shige gida.
   Still ban gamsu da taimakon Yarima ba sabo da yan siyasa basu da tabbas ayi maka karya ka dauka gaske ne kayi ta jira ana ja ma rai,don haka kwana nayi ina tunanin cewar wanne gida kuma zanje nan take na tuno da wani dan kasuwa Hamshakin me kudi a GRA unguwar su Aayan,har matsuwa nayi gari ya waye na tafi,ga kuma gidan wata Mata nan ma Naji ance tana taimakon Talakawa.
   Sannan Zan biya sakateriya ta unguwarmu wajen Kansila Adamu me tallafi ko Allah zai sa ya shigar da sunana cikin masu karbar tallafin Manoma na Gomnati.
    Kuma duk a gobe zanje wani Training shima ko zan samu a dauki sunana cikin masu koyon sana'a idan ka gama a baka jari.gaskiya gobe ina da tsare tsare da yawa,don haka kosai ma kadan na soya na barwa su Meenat komai tare da shiryawa yau ba Hijab nasa ba mayafi na yafa nayi kyau yau doguwar rigar material nasa red and green mayafinta green da takalmin robata baki,Ammah nayiwa Sallama ta zuba min addua sannan na fita da addua a bakina.






AsmaBaffa
[1/3, 9:47 AM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

   KASUWANCI NA




          16-20



Official



By
AsmaBaffa





        JIDDER ZARIA ina godiya kema ga page dinki.

    Masu Sharhi kuna kasheni da dadi Allah dai ya saka.





        Napep kawai na shiga 8am dai dai ina kofar gidan dan kasuwar nan me kudi dake Unguwar Su Aayan,abin takaici ba irin buga kofar da banyi ba amma ba wanda ya bude min hasalima me gadin ne yazo yace ai sun Dade da tafiya Kasar waje basa rayuwa a nan sai jefi jefi,haka na juya da Niyyar tafiya  katsam sai ga yan matan gidan su Aayan su uku sun fito a cikin mota da Alama schl ko wani waje zasu je sunsha wanka da kyau,suna Shan kida,da sauri suka fito daga motar suka zo ba bata lokaci suka fara dukana,ina ihu nima ina ramawa Amma sunfi Karfina,nan take daya ta cire takalminta me tsini ta kwala min a kaina a akasi nan take na zube a Sume wajen na fitar da jini,ba Imani suka koma cikin mota suna murna sun rama abinda nayi musu suka shige mota,ina yashe a kasa ban san inda kaina yake ba,sai 10am Aayan ya fito yau a mota daya zai fita shi ke Driving ma,kawai ya hangoni a kofar gidansu cikin mawuyacin Hali,mamaki ya lullubeshi me ya kawo ni nan da sassafe ko dai Aljana ce ni,a tsorace ya tsaya tare da bude motar ya fito da ruwan roba ya watsa min,nan take na ja numfashi na Mike zaune a firgice ina Dafe goshina wajen da jini ya fita,mikewa tsaye nayi ina Jiri kamar zan fadi na dauki gyalena da kudin Napep dina,na fara tafiya ina Kuka gwanin tausayi,amma marar Imanin ko a jikinsa sai ma tsawa daya buga min yace me ya kawoki nan again da safe,ko kulashi banyi ba naci gaba da kuka na ina tafiya,shuru yayi tare da cewa Yau sai naga inda zata kara zuwa,ya shiga mota.

    Yana gani na shiga Napep yana Bina a boye ban sani ba,tuna ninsa gida zanje amma ina sai yaga me Napep ya Parker a gate din wani makeken gida,na biya Napep ya tafi na shiga kwankwasa gida,Aayan dai yana mota yana Shan kallon ikon Allah mutum jini na zuba a jikinsa amma bata lafiyarsa yake ba ta neman Kudi yake.
    Security ne yazo yana turanci where are u From? To ni dai Na gane me yake nufi amma bazan iya juya yaren ba sai nace na kakalo karya nace ni yar gudun Hijirace  daga wajen Nijar nake,wajen Hajiya nazo a tallafa min Mahaifiyata bata da lfy,lokacin da nace haka Ashe Aayan yana bayana yaji komai harda yiwa Gate man signa yayi shuru,ni kuma ban san yana wajen ba sai nayi karya a akasi,abinda nacewa Frnd dinsa Yarima Bobo daban abinda na fada anan daban,sabo da bana so nayi ta tona sirrin gidanmu shi yasa ni a ganina idan nace yar gudun hijirace mahaifiyata ba lfy Zanfi samun tallafi kuma Ashe Munafuki yazo jin gulma.

     Tuni gate man yaja tsaki tare da banke kofa ya rufe,ina juyowa muka hada Ido da Aayan yana mun mugun kallon tsana alamar yaji komai,karya ba kyau yan Uwa mu guji karya kanayi watarana sai asiri ya tonu duk da akwai dalilina na karyar amma ya dace kayi gaskiya a komai idan za a baka a baka don Allah. bai ce komai ba yana gani goshi na yana jini amma yayi tafiyarsa ya shiga mota,nima na siyi pure water na wanke Raunin tare da fuskata sannan na sa gefen gyalena na danne gaban goshin nawa Ina duba agogon robar dake hannuna,
lokacin Training yayi nan na nufi sakateriya inda za ayi,mun taru da uban yawa amma sai me hanya da gata shi ake dauka mu da bamu da hanya sai muka koma yan kallo muna zare Ido,

    Ina duba lokaci na shiga wani part can cikin sakateriya nan na fara neman Kansila Adamu me tallafi aiko yana nan na sameshi a Office dinsu na kansiloli,masu son mata suna lashe baki ana kallona wanda kuma basu damu ba kallo ma ban ishesu ba haka na karasa wajen Adamu Kansila wanda yana daga cikin masu son mata,Adamu ko kudin Hotel zaka biya masa shi da mace to ba abinda bazai yi maka ba,kullum rayuwarsa a hotel take da mata,aikinsa kenan a kai mata hotel,ko so kake ka yaudari Adamu Kansila to ka biya masa Hotel ya kai mace ciki.

   Ni dai ban sani ba muna ta hira da Adamu ana kallona a karuwarsa har muka jero tare da ketowa ta cikin mutanen dake sakateriyar har bakin titi ya rakoni yana cewa ki kwantar da hankalinki ai tallafi kamar kin samu ki kyale wannan na sana'ar aikin banza ne zan sa ki a me tsoka,ina murna still hannuna yana kan goshina na danne ciwon,Adamu yace me ya sameki nace bigewa nayi wajen shiga mota,yace sannu muje na kaiki Chemist ayi miki dressing,muka jera tare da Adamu Kansila muna hira yana ta murna ya samu Damar hure min kunne,yana wani taku da iyayi shi a dole Kansila me kudi,haka muke tafiya muna ta murmushi kamar saurayi da budurwa ga Adamu akwai wankan shadda gashi matashi dan kyakyawa dashi ba laifi dai,sai kallonmu akeyi,abinda ban sani ba Aayan yana can side din da mota yana tafiya a hankali yana kallon komai nawa da nakeyi don yace sai ya kure karyata bai yarda dani ba.

    Yana kallo Adamu ya kaini chemist akayi min Dressing muka fito tare Adamu na kokarin rike min hannu na matsa gefe da sauri shi kuma yana borin kunya,amma duk da haka Adamu yace yaushe zamu hadu,nace ban gane ba,yace akwai maganganu da nake so muyi amma a Hotel zamu fi samun sirri ko? Nan take nace ban gane ba,yace au da nufin ki a banza zan saki a tallafin?ai ban gishiri na baka Manda,nan take bakin ciki ya mamayeni wato duniya baza a taimakeka don Allah ba,yan Iska sunyi yawa kowa sai ya nemi lalata ma rayuwa,ban san sanda naji haushin bata lokacina danayi a wajensa ba na fara masifa shi kanshi Adamu bai San bani da mutunci bani da kunya ba sai yau da nayi masa tatas daga karshe nace Algungumi a haka kamar mutum Ashe mata kake yiwa ciki to baka isa ba in dai hannu ne bazan bari ka taba ba bare kayi min ciki,ni tunanina ai kawai hannu ake rikewa ana yiwa mace ciki,nan na kara boye hannayena cikin mayafi tare da gallawa Adamu Kansila harara nayi gaba abina ina tafiyata a hankali,duk abinda nakeyi Aayan na kallona ban sani ba.Napep na shiga na koma gida nace na fawwalawa Allah na daina fita neman taimakon kowa Allah ya kawo min hhh naji wuya.

     Kasuwancina na rike bilhakki da gaskiya domin yanzu har funkaso da miya nakeyi da yamma,shima na kan danyi masa Algus yanda za aci riba me yawa nifa komai nawa sai anyi cuwa cuwa.
     Ammah kwana biyu da alama ciwonta kara karfi yakeyi sai addua muyi kuka mu gaji ina ta kiran wayar Yarima bata shiga idan kuma ta shiga ba a dagawa.
   Haka na kira dan gidan Commissioner da gudu ya dauka sabo da yayi saving number,dama kwadayinsa ya tashi yana ta neman Number ta amma bata shiga har yana masifa cewar yayi asarar kudinsa ya bani waya Bai Mori kudinsa ba,shima muna fara waya naji yana kawo min maganar iskanci,Hello Baby ya kike?nace lfy idan na kawo maganar maganin Ammah sai naji yace za ayi yan mata karki damu sai ya dauko maganar iskanci me kikeyi yanzu?wanne kaya ne a jikinki? Ai da zan aureki kullum sai na miki sucking sau biyar,ni ba wani ganewa nakeyi ba da na gaji na gano lallai dan iska ne kawai sai na kashe wayar tare da cire layinsa na ballashi sannan na siyi sabo na sa a wayar da ya bani nace naci banza yaro nasa mata kudi naci gaba da neman Yarima Bobo.hh

     Ina ta nema amma ba a dagawa sai na tuna abokinsa Aayan ne nan take na shirya da yamma wurin 5 lis na rubuta yar takarda na tafi har gidan su Aayan nasan ba lallai a barni na shiga ba kawai na mikawa wani security nace ya bawa Aayan,yace ai yana gida ma jira ya kai masa abinda yace sai na fada miki,nan ya tafi ciki ni kuma ina daga wajen gate ina faman jira cike da tsoro kar yan matan nan su dakeni ko Aayan ya wulakantani.
    15mnt sai gashi ya dawo yace wai ki shiga yan mata,yace ayi miki iso,a tsorace na bi bayan Mutumin mukayi tafiya me uban Nisan gaske kamar zamuje wata unguwar yan aiki kawai muke wucewa har muka isa wani part wanda ban san dashi a cikin gidan ba ya kai karshe wajen tsaruwa har Palo aka shigar dani sanyi da kamshi ya daki hancina har wani bacci nake ji.
    Daga shi sai dogon wando ya fito jikinsa ba riga wow...wow Innalillahi ko wace sai taso ta kwanta a kirjin Aayan sabo da tsananin kyansa wayyo,nidai nayi kasa da kai ina jin kunya,cike da Izza ga masifa yace karki kara zuwa gidan nan da zummar kina nemana wajensa kika je can da matsalarku,ni da kika ganni dana taimaka miki gwara na zubar da kudin,kuma sai na baki punishment na aiko min da takarda da kikayi wai na fadawa Yarima Number kaza ta kirasa ya kiraki back ni zaki aika? Look at u Nonsense yaja tsaki a gabana ya zura farar riga ko kunya babu yace follow me,haka na bishi kamar Rakuma,abin haushin duk kusan mutanen gidan kowa ya fito a wannan lokaci duk part in muka zo sai mun iske mutane mata da maza dattijai duk yan uwan Aayan,kowa baki bude yake kallonmu yana gaba ina baya,shi kuwa Gogan ko kallonsu baiyi ba bare su sa ran yasan da zamansu kayi masa magana bashi da mutunci dole sukayi shuru sai kallo da mamaki kucaka kusa da Aayan kuma a part dinsa to karuwa ce? Nan take yan matan da suka dakeni suka ce Mommy wlh akan wannan yarinyar ya dakemu rannan kamar zai kashe mu karuwarsa ce,Abbi dake fitowa shima yace haka zancenku yake yaran nan.
   Hajja kakarsu Tsohuwa me ji da kai da kudi tuni labari ya kai kunnenta cewar maganar Abbi gaskiyace cewar Aayan mata yake bi na banza don haka ya Zama dole a dauki mataki a kansa tsatsaura,ranta ya baci amma tace zata yi maganinsa.

     Ni dai a tsorace nake har muka karasa wajen mota yace get in the car,ba shiri na fada ciki sabo da na matsu na bar gidan a tsorace nake,Driver ne yaja ina baya,Aayan yana wata motar daban wannan gidan nasa muka shiga,da sauri ya fito nima na fito ina murna Allah yasa ya bani irin abincin ranar nan,ban San me yasa Bana Jin tsoron komai idan ina tare da wannan masifaffen Aayan ba.

    A baya na bishi har ciki yace Oya fara gyara gidan nan,da sauri na fara aikin sai da na gyara komai yana sheki duk da cewar dama ba wani dirty kawai mugunta ce,sai da na gama ya sani kneel down hands up na Sha wahala sannan ko ruwa bai bani ba ina kallo yana ta cin abun dadi da lemo haka yace na tashi na bar masa gida,ba shiri na Mike da sauri domin magrib ta kusa ina tsoron Ammah,har zan fita sai na dawo gabansa yana daukan wani abu kamar hanta yana ci yana kora lemo na faki idonsa na dauke ledar zan kwashe da gudu ya sa min kafa nayi muguwar faduwa a kasa,a fusace yayi kaina nasan duka zanci kawai na fara kuka amma ko tausayi yana huci zai mareni sai kuma ya fasa hannuna yaja tare da jefani waje ya banke kofarsa,sai da na ci kuka na sannan na Mike tare da karkabe jiki na,zan fita kenan wani cikin yan aiki yace kiyi hakuri kinji ki daina shiga sabgar Oga wlh baya kaunar mata ki kiyaye ba abinda bazai miki ba kuma bazai taba nadama ba,ke naga yana daga miki kafa ma wlh da wasu ne ko hanyar da yabi basu isa sun bi ta ba,amma ke har yana kyaleki ki shiga gidansa har ya saki aiki,a raina nace ni ina ruwana da zai taimakawa Ammah ai da na yarda ko kullum yankar naman jikina zaiyi ba matsala,haka na fita na bar gidan na koma gida, my
  Ammah sai fada take min ta gaji da yawon da nake ranar ta sa min doka tace bazan kara fita ba sai bayan sati biyu ko me za a siyo Meenat ta karba taje ta siyo.

   Tun daga Ranar ban kara fita ba ko kofar gida Ammah ta hana,ina zaune da wayata ina game Ma'eesha na kallo Meenat ta tafi cefane kawai sai ga kiran Yarima,jiki na rawa na daga muka gaisa yace gobe na kai Ammah Hospital din an gama biyan komai da komai,sabo da murna ban san sanda Hawaye suka kwararo min ba,na dinga godiya ina masa addua yace ba komai ko mene ake ciki na kirashi a waya,nan take na sanarwa dasu Ammah kowa murna haka ma Meenat da ta dawo harda Rawa,ranar har Nafeela mukayi na godiya ga Allah.
   Washe gari da wuri muka shirya tare da daukan Ammah a napep muka tafi asibitin Murtala.
    Ba bata lokaci akace Doctor mu yake jira an biya komai da komai yau za ayi wa Ammah gashin kashi tare da sauran aikin da za ayi mata,muna ta addua aka shiga da ita.
   Abin da ya bamu mamaki shine abinci lafiyayye na resturant take away tare da ruwan roba carton biyu,tare da lemuka iriri sai fruits da kayan hada tea duk aka dinga shigowa dasu wai inji Boss dinMufeeda,ni kuma  tunanina ya bani dama Yarima ne,kuma ina tunanin so na yake.
    Haka harda su flask na tea dana abinci da cups tare da spoons sai plates wai duk inji Yarima,abin ya bamu mamaki muka dinga murna,na koma gida domin kwaso kayan jinya,mota wata sabuwa naga tasha gaba na,Aayan na gani kawai sai na karasa jikin motar tare da cewa ina kwana?ko saurarata baiyi ba yace shiga mota,ban so ba amma ya zanyi haka na shiga gaba na zauna ina jira ya kaini inda zai kaini,sai naji muryarsa me sanyi da dadi kamar na suma haka naji,yace  karbi waya Yarima zaiyi magana dake,waya na karba a tsorace muka gaisa yace Mufeeda kike ko?

nace ae yace to gaskiya zan fada miki duk kudin aikin nan da komai bani na biya ba Aayan ne ya biya abokina,yanzu haka an fede Ummanki amma baza a dinke ta ba sai anyi deal dake akwai sharadi idan kin yarda sai a karasa mata aikinta ta tashi idan baki yarda ba kuma a barta haka ta mutu,a firgice tare da fara kuka nace mene sharadin?yace Aure za a daura muku da Aayan na kasuwanci domin shima a gida ance dole ya kawo mata ko a bashi wata akwai abinda yake so ya nunawa yan gidansu kin gane zai miki bayani idan kin yarda,nan take nace abu me sauki muje a daura indai Ammah ta zata tashi,yace Amma dole sai da danginki nace ba komai muje suna Borno da wasu a kauye nan kano,y ace za kuje a jirgi ai sharp sharp.

     Waya nayi da Meenat basu San halin da ake ciki ba nace su kula da komai sai gobe da safe zan dawo,Guess house din Aayan muka je dashi ba tare da ya ko kalleni ba nima haka ina mamakin duniya babu na Allah,muna zuwa ya mika min wasu kaya a kwali yace je kiyi wanka sosai ki sa,da sauri na fada bedroom dake palon nayi wanka da Sallah na shafa lotion da komai kwalliya ce kawai na kasa yi sabo da halin da nake ciki na sa kayan na shafa turaruka yanda nayi kyau abin ba a cewa komai kamar yasan size dina doguwar rigar Arab ce fitted me shegen kyau da ado kamar wata Amaryar Larabawa haka ba dawo da mayafinta,black da adon sky blue nasa takalmin da na gani sky, harda wata jaka itama sky,na fito sai dai kirjinsa babu Nonon kirki yan kana na ne dasu kowa yaganni yaga yarinya danya danma ina da tsayi kuma ba kiba ba ramammiya bace,normal nake yar cakwas dani. wayyo shi kanshi yasan na hadu amma sai ya dauke kai yana yatsina fuska,ya shirya cikin sky blue yard me shara shara kamar Amarya da Ango lallai zamu kwashi yan kallo,amma gaba daya zuciyoyinmu ba dadi,ni haushinsa ma nake ji,shima haka,

muje naji yace tare da cewa bani da lokacin yi miki bayanin dalilin aurenki da nace zanyi,amma ina da dalili,ki nutsu Rayuwar gidanmu da zaki shiga daban take,da kanki zaki gane me yasa na aureki idan kin shiga gidan,bazan cuceki ba karki sa rai ina sonki, ko zan faranta miki,ko zaki ji dadi no Kasuwanci ne deal ne,zan biya ki kudin da zaki kula da yan uwanki kuji dadin duniya tare da Ummanki zan biya mata kudin hospital da komai,ko mene kike so a duniya zan baki,ni kuma zaki aureni ki zauna cikin kunci dan baza ki so Zama dani ba baza kiji dadi ko da minti daya ba,sannan ga matsalar family na sai kinbi a sannu zaki gane matsalarsu ko kiyi Nasara a Kansu ko suyi a taki wannan ya rage naki,ko da ace ina Sonki na aureki to fa ni bana haihuwa, kuma an auna lafiya nake amma nayi aure har sau Uku ban taba yiwa wata ciki ba,ba asibitin da banje ba,sannan zaki ji ance ina da Hawan jini ina da Diabetes wannan karya ne lafiya kalau Alhmdllh kawai fada nayi dan na samu sauki wajen family ta wani ban garen,bance ki dagawa kowa kafa ba a dangina sabo da ni kike aure ba su ba,amma banda rashin kunya karki soma raina min yan Uwa thts all,idan kin kiyaye zaki samu kudi da jin dadi,sauran yaki ya rage naki,ni dai ina da manufata da burina na aurenki wanda a yau zaki fara ganin daya.lets go,bana bukatar kiyi wani abu dan ki faranta min rai sabo da na tsani mata kaf banda uwata yayi gaba abinsa.

   Ni ko a raina ban dauka serious ba tunda bani da wayo yarinya ce ni ga karancin ilmi,ai sai nace tunda zan samu kudin kula dasu Meenat da lafiyar Ammah kawai a daura banyi tunanin komai ba,duk na rude har na matsu a daura domin a mayar da Ammah a dinketa ta samu Lfy burina kenan,abinda ban sani ba tuni ma har anyi aikin an gama komai Ashe wayo suka yi mini dan ba yarda da wuri.
    Gidan make up ya kaini da kansa yace na shiga ina shiga naga ana ta karramani Ashe sun San da zuwana,nan fa aka gyara min gashi da kwalliya yar sama sama,na fito shi kanshi saida ya kalleni ya kara kallona,amma sai ya tabe baki na shiga yaja muka tafi sai gidansu dake GRA,a cikin motar yace karki tunanin auren zan sakeki da wuri tunda kema dan kudi kikayi ni aurena ba saki sai da dalili,ni kuwa kudi nake nema dama kawai nace karka damu ni ma dan kudi nayi ai kasuwanci ne kawai nima idan kudin sun isheni zan nemi saki  sabo da na auri wanda nake so ni insha'allah kamar yanda nake yar sunna sai nayi auren so da kauna na sunna.

   Baki ya tabe ba tare da yace komai ba har muka shiga cikin gidan kafin na fito yace kiyi kamar muna son juna a gaban iya Family na,kudi da Ammah kawai nake hangowa nace to an gama, fitowa yayi nima na fito muka jera kamar masoyann gaske abin birgewa muna tafiya can wani part sai ga yan matan nan da samari birjiki muna hangosu kowa da abinda yakeyi na nishadi,a hankali yace action nan take na tuno kudi da Ammah ta kawai na kakalo murmushi lafiyayye na saki ina masa wani kallo da kowa zai ce Masoyina ne mun shaku da juna.
    A hankali yace Good job Ashe lallai Yarima bincikensa yayi gaskiya kina son kudi,murmushi nayi nace na gaske ma kuwa ai na shaku da kudi a duniya bani da burin da ya wuce kudi,Muna tafiya muna magana tunanin mutane ai duk soyayya ce da kallo kawai ake binmu, muryarsa naji yace karki gaisar da kowa nasan ke village girl ce,nace an gama in dai da kudi baza ka samu matsala dani ba,wani kallo ya min yana yatsina fuska muna tafiya,yan matan nan suna ta mamaki yar iska nan Ya Aayan zai aura tab ai kuwa zata ci duka,nan take kishi ya turnike su zai auri wata ba su ba ga mata kyawawa a gidansu yan Uwa,nan take suka ci Alwashin ganin bayana,dan haka daya a ciki ta taso cike da kishi tace ya Aayan badai kazamar nan zaka aura ba,dama itace kace zaka kawota bayan gamu a gidan ka Zaba mana,kallo ma bata ishe mu ba harda ni ,aiko ta fusata tare da jawo gyalena ke yar matsiyata,na rigada na gama rainasu nan take na fisge mayafina tare da cewa kinci sa'a ina da muhimmin Uzuri banda lokacinku amma da kin San yau kin rike gyale me daraja nayi gaba abina,dan ta kara Jin haushi ma kawai nayi ta maza na rike hannun Aayan a karo na farko,yayi matukar mamaki nan take ya canja fuska,nace Business ne ka bari a gama lfy na fika Sanin dokokinsa muje kawai nima ina da dalilina na yin hakan a sannu zaka gane. mamaki
Ya cika shi a fili yace lallai Yarima yayi bincike me kyau,nace ba karya indai akan kudine shirka da kisa ne kawai bazanyi ba.
     Muna wuce wajen yan matan na saki hannunsa ya juyo tare da gasa min harara karki kuma taba min jiki,nace an gama sai da dalili duk cikin kudinka,har muka shiga part din tsohuwar nan wato Hajja,tana takama da isa na durkusa har kasa na gaisa ta tsabar tsufa bata gane nice nazo polio ba,cike da wulakanci ta amshe ni,sai ga wasu dattijawa yan gayu su Hudu mata sun shigo nan ma kaina kasa cike da ladabi har kasa na gaisar dasu suma dai a wulakancen suka amsa,sai ga maza manya su Uku sun shigo ciki har da Abbi duk suna kama da Alama brothers ne,suma haka na gaisa su Abbi ya gane ni murmushin mugunta ya saki ya kalli Aayan tare da cewa karuwar taka zaka aura kenan,lallai bariki tayi dadi,dayan cikin su yace ke bafa ya haihuwa ba lafiyayye bane amma kin bamu mamaki da zaki aureshi to mudai baza mu rufe miki cutarsa ba idan kudi kike nema ma ki shafawa kanki ruwa idan kuma tuna ninki aure na gaskiya to kece a wahale,mamaki ya kamani amma na tuno Ammah kawai nace ina sonsa haka sabo da Allah zan aureshi,Abbi yace a ina danginki suke? dangina na uba suna Maiduguri,na kalli Aayan cike da fara'a nace ai munje da kai rannan kasan ko ina ka basu address suje,ido na kifta masa,mamaki ya kamasu karfa da gaske soyayya muke da Aayan gashi ma yasan dangina.

     Yace muje na saukeki a gida ko,Abbi yace no Ku tsaya dole da ita za a tafi gaban iyayenta muka sani ko karya take,nace ba damuwa,muna zaune aka shirya tafiya maiduguri a jirgi abinka da Naira,Manyan mata su biyu su Abbi su Uku sai Aayan da ni kuma,ina kusa dashi babu wanda ke kula kowa,wai abinka da masu kudi sai gani a jirgi ina tsoro dai haka na maze,mintina kadan sai gamu a Maiduguri Allah yasa muna zuwa watarana,nasan ko ina,motoci aka kawo musu yan gaske nayi jagora har gidan su Abbanmu,nanfa yan uwansa Allah sarki suka dinga murna cewar Ammah dani mun girmamasu mun basu hakkinsu za ayi min aure amma su aka barwa komai a matsayin su na dangin uba,haba shi Kanshi Aayan yayi mamakin irin mutunci da karramawa da aka musu duk da cewa ba masu kudi bane amma an mutunta su matuka,matan ne kadai suke ta yatsina fuska suna tabe baki kun san dama mata sunfi maza kasa danne abu.

     Nan take abin mamaki sukace a daura Aure domin su Abbi su gama shirya mugunta a kaina.
   Dangin Abbana sai da suka tabbatar ina so da yarda ta sannan kawai suka tara mutane a masallaci shi kanshi Aayan baiyi tunanin Abbi zai ce yanzu za a daura ba,shi Sam bai ma kawo nan kusa za a daura auren ba,nan take dana sani da nadama suka lullubeshi.

    Nima haka har kuka a boye yar yarinya dani yanzu na shiga 17yrs ace za ayi min aure,tunowa nayi Ammah na can rai a hannun Allah,ina zaune naji ana guda kamar wasa wai an daura Sadaki Dubu Dari Uku,ina jin yanda nayi tsada a sadaki na sai gashi ina murna naji kudi domin ni in dai kudi ne an gama kawai,har wani yanga na fara yi daga jin sadakina Dubu Dari uku,Aayan kamar ance an masa mutuwa ya kasa boye fushinsa,nan na karbi Numbers na dangin mu na basu tawa muka musu Sallama zamu dawo Kano,har kudi na dan basu kadan cikin na sadakina da kyar ma suka karba domin Aayan ya basu kudi masu yawa.

    Bamu zarce ko ina ba sai kano a jirgi,muna sauka sai kauyen Rimin Gado dangin Ammah mun samu kadan daga ciki na nuna musu kaf dangina an karbemu a mutunce sai dai nace Ammah tace a gaishesu bata da lafiya ne,kamar yanda na fadawa Dangin Abba, sunji ba dadi har wasu sunce zasu zo dubata.
    Sharp sharp muka gama komai suma sunsha kudi wajen Aayan amma kowa yasan wannan Ango bashi da fara'a kamar ba auren so ba haka muke dashi sosai yake fushi a fili.

  Su Abbi sai kus kus sukeyi ana shirya mugunta.
      A ranar muka dawo cikin garin Kano bani da burin da ya wuce naje naga Ammah ta samu sauki,daga ni sai Aayan a mota,yana Driving, cike da zumudi nace kayi waya naji an gama aikin tunda na yarda an daura auren,kallo na yayi a matukar hasale yace an dade da Gama mata aiki tuni anyi komai je ki gani,a hospital din ya saukeni ya figi motarsa ya barni tsaye baki bude da jakata a rataye,nace oho dai ni tunda zan samu kudi shike nan,ya kaga Ammah ta samu Lfy?gashi nayi auren da take buri nayi,na cikawa Ammah burinta gashi nayi auren da takeso,da sauri na shiga dakin da su Ma'eesha ke ciki special room aka bamu sabo da Naira.

     Ina shiga gabana yaba da dum ganin su Meenat suna Rusa uban kuka,ga mutum nan a lullube da alama gawa ce,lokacin dare yayi jakata na jefar a kasa a tsorace na karasa tare da bude gawar Innalillahi na maimaita domin Ammah ce tabbas ta rasu.
    Zubewa nayi kasa sumammiyya,nan likita suka shigo aka mai Dani gadon tare da rufuwa a kaina da kyar na farfado ina uban gunjin kuka,sai hakuri ake bamu su Meenat suna rungume a jikina,kwana mukayi kuka ni tunanina laifin Aayan ne mugu su suka kashe min Ammah ta gashi ya zalunceni na yarda an daura min Aure dashi amma sunyi ganganci da Rayuwar Ammah ta rasu wayyo Allah,yau ina Algus da nakeyi sabo da maganin Ammah duk sabo da kar ta mutu tasha wahala nake tsoro,kullum yawon neman Kudi na tsallake risk da dama don kawai na samo kudin magani.

   Ba tare da Sanin uwata ba naje nayi auren kasuwanci don sabo da kar ta mutu ayi mata magani ta warke,nayi duk abinda zanyi amma kash baiyi amfani ba,sai ma gani nake ina zargin kaina cewar da hannuna na kashe Ammah domin nice na damu sai an mata aiki duk da cewa an fada mana cewar aiki biyu za ayi mata da na kafafu sai kuma wani a cikin Mahaifarta shine me matsalar ba lallai ta tashi ba,amma na dage sai anyi gani nake zata warke,dana sani da nadama nake ta faman yi,Ammah na zaune lfy na damu gashi ashe ta hanyar aikin da kudin da komai amma sai lokacin ta rasu,burina bai cika ba domin bani da burin da ya wuce nayi kudi Ammah taji dadin duniya tare da kannena sannan nayi aure Ammah taga mijina da jikokinta amma kash babu ko daya da ta gani domin wannan auren ma na Kasuwanci ne.
     Iya karfina na kwalla kara da ihu,kowa sai ya tausaya mana,kuka muke ba ji ba gani tare da tumami harda birgima tare da shure shure abin sai wanda ya gani,sai da muka kwana cir muna abu daya,gari ya waye ma muka daura. lokacin akace Muzo mu nemo yan uwanmu maza a dauki gawa.
    Nan take nayi waya dangin Ammah kaf da Dangin Abbah da sauran makwafta da abokan arziki tuni zancen ya watsu Ammah ta rasu,Allah ya taimakeni dangin uba na ne suka daura min Aure,haka dangin uwata da saninsu.h ar mamakin auren nakeyi sabo da kudi wai nan a rana daya anyi an gama komai gaskiya kudi sunyi a rayuwa.







AsmaBaffa
[1/3, 11:17 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

    KASUWANCI NA

  

           21-25




Official




By
AsmaBaffa




 
        CHOICE ths page is for u...😍❤

     ASYCOOL ina kika boye ne?

     Fans masu sharhi ta ko ina ina matukar Godiya da kulawa ina jin dadi yanda kuke kokarin yin Sharhi abin ba a cewa komai sai godiya Masoya ta ko ina,Allah ya bar zumunci ya biya muku bukatunku na alkhairi,tsakanina daku sai godiya,insha'Allah kowacce da page dinta masu sharhi,shine farin cikina da zan baku na yanda kuke sharhi.loves u all.😍😘😍😘❤❤







        Gaskiya duk Wanda ya San Ammah mutuniyar kirki ya girgiza da mutuwar nan,nan take asibitin ya samu halartar dangin Ammah maza da mata da yake mutuwa ce har sunzo mana.da taimakonsu aka bamu gawar muka tafi da ita dan  gidanmu na talauci,nan fa dangin Abba ma na Maiduguri sun samu Damar zuwa da yawa,ga yan unguwa harda kawata Nawwara,su Shehu me waya sune kan gaba,Adamu Kansila ma yazo haka aka hada gawa tare da sallatarta aka kaita gidanta na gaskiya,Kuka mukeyi sosai musamman ni da Meenat,Maeesha ba hankali sosai Sam bata ma damu ba sosai har ta daina kukan,mu kuwa sai nasiha ake mana da Wa'azi ana bamu hakuri, washe gari kuwa da safe ana ta kawo mana abinci daga makwafta,ga wani dangin Ammah sun dafa,

     Ma'eesha tasha baccinta ta tashi ba hankali ta fara bude abincin iri iri sai ta rufe ta dawo gefe na tare da nuna min da yatsanta tana Sis ni wancan nake so cike da shagwaba tace ni me tiririn  can nake so,saida ta bawa mutane dariya,da rana kuwa tana cin tuwon shinkafa tace Sis wai kamar ana biki? Muci tuwon mu musha Kokonmu Ammah ta tafi Rimin Gado kafin ta dawo. haka muke ta amsar gaisuwa,har akayi sadakar uku dangin nesa duk wasu sun tafi sai iya na Ammah mata da wasu mazan su uku wanda suke uba daya da Ammah,makwafta suna kawo mana abinci iri iri kullum,da kudin sadakina nake yin komai na kashe kudi sosai domin mutuwa yanzu kamar biki haka take,Meenat sunji ana ta ce min Amarya Allah sarki jiya aka daura mata aure sabo da har yan unguwar mu sun San anyi auren domin munzo da Aayan tare dasu Abbi sunga gidanmu na asali da muke rayuwa,haka kuma na hada su da wasu manyan dake makwaftan mu tunda mu bamu da yan Uwa a cikin kano sai abokan arziki,gashi Ammah na asibiti kuma Bai dace ace anyi aure ba wasu shedu ba babu Sanin mutane ai babu dadi a ganina bai dace ba,shi yasa nace dole Muzo sharp sharp su gani su San inda muke da zama duk da cewa dangin Aayan sun min kallon wulakanci ganin inda muke da zama har dariya suka yi masa dama sun San ai sai talaka ce zata iya aurensa.

    Ni dai ko a jikina tunda kudi zan samu gani nake kudi sune maganin komai,sai gashi tun ba aje ko ina ba an saukar min da Aya,Meenat ce ta jani gefe tace Sis ya naji ana ce miki Amarya?ki Bari baki su tafi zan sanar daku komai,da gaske kinyi aure? No ki Bari idan mun nutsu zaki ji.Bayan anyi sadakar Bakwai muna zaune Dangin Ammah suka samu a tsakiya cewar zasu dauki Meenat da Ma'eesha su tafi dasu kauye ni kuma tunda nayi aure na zauna dakin mijina duk da cewa abin ya daure musu kai rashin ganin angon nawa a wajen janaizar Ammah,amma sai nace dasu baya kasar yayi tafiya kasar waje,cikin ladabi nace Ni bance karku tafi dasu ba dama Ku ya dace Ku rike mu,amma sabo da karatunsu kuma kauye ba schl baya ga haka basu saba da rayuwa acan ba,kuma nima zan shiga damuwa na rashinsu ga rashin Ammah me zai hana a bar min su mijina zai rike su ba matsala zai musu komai sai mu zauna tare,Dangin Ammah dama kadan suke jira nan suka fara masifa to ai gaki gasu in dai rikon dadi gareshi,sannu yan Birni Ku yan boko ko to dama dan mu fita hakkinku mukace zamu tafi daku amma tunda haka kuka Zaba shike nan, a cikin matan ma daya tace a'a haba a bisu a hankali ai yara ne ga rashin Uwa sunyi amma har ita Mufeeda kanta nawa take kuruciya ce kawai,nayi mamaki a birni guda amma kamar Mufeeda wai Fatima ta yarda tayi aure tana yar Sha bakwai a shekaru,duba fa yan Birni da sai su kai shekara talatin yarinya na yawo a titi wai karatu take.
   Daya cikin maza kanin Ammah yace to Alhmdllh ai mijinta me kudi ne da alama zai iya rikesu da Amana na tabbata amma ya dace ace munje munga gidan mijin naki,gumi ne ya keto min nan take na rude.

   Karya na kakalo nace ai ba yanzu zan tare ba,dazu munyi waya dashi jibi zai dawo daga turai sannan zasu sa ranar da zan tare sai na fada muku a waya ko nazo har gida na kawo kati sai kuzo ayi komai da Ku,ganin mijin nawa me kudi ne tunda sun ganshi tare da danginsa ba karya gashi sunsha kyautar kudi kawai sai suka washe baki tare da cewa to Allah ya kaimu ki tabbatar kin yo mana waya,da sauri nace Insha'allah,to yanzu abinci fa da sauransu wa zai baku kuma Bai dace Ku zauna Ku kadai ba a wannan gidan ba,nace ai masu gadi zai kawo mana yace suna kan hanya ma sojoji ne,da mamaki sukace lallai kunyi dacen me kudi ke ko yar nan kin huta a duniya dan Allah a dinga tunawa damu dangi kar a samu a manta damu,nace haba dai ai daku za a ci komai,nan dai suka yi ta kauyancinsu na Fulani daga nan suka tattara gaba daya suka mana Sallama zasu tafi,har kudin mota na basu muka rakasu har tasha sabo da bamu saba dasu ba ko kuka bamuyi ba sabo da sun ishemu dama sai bata mana gida sukeyi suna samu aiki.
    Suna tafiya mu Ukun muka tsaya a wani gidan yan haya,gidan haya ne Babba,daki daki ake bada hayar kowa da dakinsa sunfi mutum ashirin a gidan kuma toilet daya garesu,Meenat tace me zamu yi a nan? Ko magana banyi ba nace suzo muje,muna shiga muka gaisa dasu suna ta mana ta'aziyya,dakin wata Dattijuwa Uwaliya na shiga tana zaune gefe tana Shan kunu,Uwaliya bata taba haihuwa a duniya ba,danginta duk suna kauye sana'ar aikatau wanke wanke da shara ce ta kawota birni,bata yi dacen gidan da take aiki ba kuma bata son zaman kauye sabo da babu sana'ar kirki a can,sai ta kama hayar daki a birni tana zuwa gidan aikin haka da safe ta dawo da yamma kullum,da fara'a ta tarbeni muna gaisawa nace  Uwaliya idan baza ki damu ba ki dawo gidanmu da zama mana kyauta na baki daki daya mu kuma sai mu dauki daki biyun,dama gidanmu daki Uku ne sai dan kitchen da toilet ammafa bashi da wani kyau gidan gidane na talaka amma nasan yafi wanda Uwaliya ke haya a ciki,da murna Uwaliya ta dinga godiya,haka mutane suka tayata murnar daina biyan kudin haya zata zauna kyauta a gidanmu,wasu suka dinga mamaki wai duniya ta juya min baya duk son kudin Mufeeda yarinyar da komai nata na kudi ne yau gashi taji uwar bari kar a hauro ayi musu fyade har roko take a zauna musu kyauta a gida lallai duniya tun ba a je ko ina ba kenan.

     Uwaliya ta kwaso kayanta kaf tare da sanarwa me gidanta ta dawo gidanmu sabo da gida ba Babban gida bane gashi mijin kasuwancin nawa ya kashe min Uwa ya gudu ban kara ganin sa ba,ya barni da igiyar aure mara amfani a kaina,idan bai nemeni ba ya zanyi wayyo neman kudi ya jawo min.

    Dare yayi Uwaliya tana dakinta ta gama cin abincin da na siyo mana har ita na bawa tana ta godiya sabo da Uwaliya mutuniyar kirki ce ba ruwanta da kowa ba gulma ba sa ido.
   Na tasa kannena a gaba Meenat da Ma'eesha nace dole suci abinci naga duk sun rame,duk da cewa na fisu ramewa sosai,Bani da karfin gwiwar da zan mana girki duk cikin kudin Sadakina nake cinyewa,Meenat tace sis kici mana idan baza kici ba mu taya zamu iya ci,duk kin rame dan Allah ki kara hakuri kullum fa sai kinyi kuka cikin dare muna jinki,Maeesha tace kuma ance ba kyau ana yiwa wanda ya mutu kuka yanzu Ammah kina kara mata azaba fa,wani hawayen tausayin kanmu ne ya zubo min na share ina kakalo Murmushin dole tare da sa hannuna a abincin muka fara ci badan muna so ba,kawai tunanin Ammah nake da kanmu tare da igiyar dake kaina,miji bai San me nake ciki ba,kaico na nikam na tafka kuskure dana sani nakeyi da nadama,ganin basa ci da yawa na shiga basu da kaina ina ciyar dasu suma suna bani abin haushin na fisu saurin kuka kawai hawaye nake ina ci har sai da na karya musu zuciya suma suka fara,Maeesha tace Wai Ammah baza ta dawo bane? Wai Sis ba a dawowa? Nace baza ta dawo ba ina shesheka na kara fashewa da kuka babu me lallashi,muna ta tuno Rayuwar da mukayi da Ammah me dadi tun tasowar mu,dan ma Allah yasa gaba daya kayan Ammah na sawa na kwashe na bawa Danginta dan kar ma na gansu bakin ciki na damuna da yawan kuka,sai pics Namu da nata amma komai nata na kwashe na bayar,masu amfani kawai na ajiye tunanina ko da kuwa Allah zai bayyana mana Abbanmu watarana.
    Uwaliyace ta shigo ta zauna kusa damu ta fara yi mana nasiha tana lallashi tare da kwantar mana da hankali har mukayi shuru,sai ta fara yi mana labaran tatsuniya na abin dariya muka dinga ta faman dariya kamar ba mune dazu muke kuka ba,mun dade sosai sannan nace muyi bacci ta tafi dakinta,nima na kulle mana daki,muna kwance mun cure waje daya,cike da nutsuwa nace Meenat Ku tashi muyi magana,da sauri suka Mike zaune a saman katifar domin ko arzikin gado bamu dashi.

     Rungumesu nayi a jikina sannan na kwantar da Ma'eesha saman cinyata ina shafa kanta,Meenat ma tana jikina ta jingina,nace Meenat nasan kinfi Ma'eesha hankali zan baku labari akan zancen da kuke ji nayi aure,ba wai bane tabbas da gaske Meenat nayi aure nan na kwashe labarin duk yanda akayi tun daga fitar da nake nemo kudin maganin Ammah har haduwata da Aayan,Yarima tare da Aurena kaf na basu Labari Ma'eesha nasan duk da ta fahimci komai amma baza ta kai Meenat fuskanta ba,gani nayi Meenat tana ta murna tana dariya,nace mene haka ke kuma? Sis wlh kin cikawa Ammah burinta shi yasa,kuma Alhmdllh kin samu me kudi Allah yasa na gari ne sis ya tallafa mana,kawai ni shawara mu dage da addua kamar yanda muka saba sai kiga Allah ya canja masa zuciya from bad to good,kuma am serious bashi ya kashe Ammah ba domin kina fita aka fito da Ammah lfy an mata aiki tuni kinga lokacin ma baki je wajensa ba bare yace miki baza a hada ta ba sai kin aureshi kawai wayo sukayi miki, naji dadin zancen Meenat sosai da ta ganar dani amma da haushin Aayan nakeji cewar shi ya kashe Ammah amma duk da hakan ban wani yarda ba kawai shi ya kashe min Uwa.

    Meenat tace lokacin da Ammah ta farfado Sis tana ta nemanki bakya nan,sai tace mana naji a jikina wani abin Alkhairi zai samu yata Abin alfaharina Mufeedata yau Alkhairi zata hadu dashi,naso ace zanga wannan lokaci da Idona amma kash,sai muka ga tayi shuru,ta kara rike hannuna tace Meenat kuyiwa yar uwarku biyayya idan kuka saba mata bazan yafe muku ba,ku hada kanku  karku taba rabuwa sai aure,Mufeeda zata rike min Ku da Amana kamar ina raye,ta Zama madadina,sai tayi tari taci gaba kuce ina son Mufeedata Allah ya bata miji na gari me kaunarta wanda zata huta taji dadi a hannunsa,sannan Ku fada mata nace duk Wanda ta aura ko waye tayi masa biyayya,ta kara hakuri sannan ta kula dashi da rayuwarsa tare da komai nasa da ya shafeshi,karta bari a take mata yanci duk Rintsi ta kwace yancinta,Mufeedata nasan ba me tsoro bace dan haka kar taji tsoron fadan gaskiya a duk inda take,taji tsoron Allah a duk inda take,tabi Allah,ta kula da ibada,ta tsare mutuncinta na ya mace,sannan tabi mijinta ta kula da iyayensa,ku rike addua, kuyi Zumunci dangina dana babanku baku da kamarsu, ba da iya Mufeeda nake ba,gaba dayanku yarana wannan shine abinda zan bar muku,shine a matsayin gadonku tunda ban bar muku komai ba,karshe Ku fadawa Mufeeda idan Allah ya bayyana babanku kuce masa duk abinda ya min na yafe masa baki daya,ni nasan ban zalinceshi ba amma shima ya yafe min,naso ace na aaaabaku labari akan zamana da babanku har zuwa sabanin da muka samu,da dalilin sabaninmu amma idan ya bayyana nasan zai sanar da......Nan mukaga Ammah tayi shuru Sis sai ga Doctor ya shigo yayi aune aune sai muka ga ya lullubeta suna magana da turanci da wasu nurses nan take mukaji ashe mutuwa Ammah tayi,gaba dayanmu kafin Meenat ta gama bamu labari mun jige rigarmu da hawaye..Nan Ma'eesha tace Sis Meenat kin manta tace mu fadawa Mufeeda wai tayi aure shine burinta sannan idan tayi aure ta fadawa mijinta Ammah na gaisheshi kuma ga Amana nan ta yarta Mufeeda abin sonta me share mata hawaye,ya daya tamkar da Dubu,mace me kamar maza ya riketa Amana ya bawa mufeedanta farin ciki shine bukatar Amman Mufeeda,nan take da jin zancen Ma'eesha sai muka koma muna dariya muna hawaye kamar Ammah ce ke maganar,dama Ma'eesha akwai iya bada labari gashi bata mantawa yanda ka fadi abu haka zata bada labari. Haka mukayi ta hirar Ammah har dai na sa Ma'eesha a tsakiyarmu muka kwanta abinmu har bacci me nauyi ya kwashe mu.

    Sati biyu da rasuwar Ammah cikin kudin Sadakina na kara jarin sana'oina,cikin Sadakin na canjawa su Meenat makarantar Kudi aka yi musu transfer a secondary schl me Saukin kudi sunfi na Gomnati karatu ni kuma bani da burin da ya wuce suyi karatu,Komai har su Uniform nayi musu har kala Hudu hudu su schl bags littatafai etc,haka nayi mana sababbin dunkuna masu dan kyau,na kara siya mana abincin gida domin tuni na cire rai da auren da nayi na gama tabbatarwa cutata Aayan yayi sabo da haka kawai nayi watsi da wani aure,na manta ma ina da igiyar aurensa sam duk da cewa abin na raina amma na hakura na rungumi rayuwarmu ace anfi sati biyu da daura aure amma kamar wanda ya auri karya ai idan da gaskiya sai yazo ya biya ni kudin kasuwancina dana yarda na aureshi bisa sharadi.

     Haka na kwashe wata guda da aure amma babu labarin Aayan abin takaicin kuma duk na karar da kudin sadakina,gashi kuma sana'ar tawa yanzu Sam bata tafiya ba kudi a hannun mutane,sai a yini guda ba a zo ance za a siyi ko Wake ba,duk na shiga damuwa ina tunani idan komai ya kare mana ya zamuyi ina zan sa kaina,abinda ya Dameni shine nayi Nadamar Halayena na Algus a sana'a ta tuni yanzu tsakani da Allah nake yinta bana kara komai marar kyau,kuma Istigifari nakeyi Allah ya yafe min,Amma Kuma dana gyara halina sai ma na daina ciniki,komai ya tabarbare,ba riba,lokacin kuma da bana yin ingantacciya komai tafiya yake min dai dai ina samun ciniki da riba,ikon Allah kenan yanzu Kusan duk sun karye ma,idan ya kare sai dai na iba a cikin Sadakina na kara dama duk kudin ma sun kare sabo da nayi mana abubuwa ciki da dama.
   Sai da nayi dana Sanin canjawa su Meenat makarantar Kudi yanzu da uban me zan biya musu idan shekara ta kare,nidai haka nake ta yawon saro kaya da siyarwa ina sana'ata tunda ba labarin angon,ni kuma bazan je gidansu ba,ga rasuwar Ammah kullum sabuwa ce a wajenmu ko yaushe muna kuka muna tunaninta.

   Yau juma'a na kai wata daya da sati daya da Aure kuma haka da rasuwar Ammah,tun safe na sallami su Meenat suka tafi schl,Uwaliya ma ta tafi gidan da take aiki,ni kadai ce a gidan sai da na gyara ko ina dake gidan fes fes tare da kunna turaren wuta,na kunna turaren wuta har Toilet sannan na dawo tsakar gida jikin Rijiyar gidanmu ina wanke mana kayan sawarmu ina shanyawa ga girki ina yi jullof din shinkafa taji kayan hadi harda kifi sabo da bamu da yawa shi yasa girkinmu ke dadi,sai dana cika igiya da kayanmu kana na shanya tare da kara wanke wajen,kwashe abincin nayi a wani foodflask me dan kyau sabo dana siya mana shi set biyu.

    Lokaci na kalla naga bani da abinda zanyi kawai na kwashe yan kudin da suka rage min na zuba cikin Aljihun tight wando na na ciki,sabo da ni duk tight din dana ke sawa cikin kaya to sai na kaiwa wata tela ta dinka min aljihu da zip a jikinsa sabo da ko ina zanje a duniya da kudi a jikina kaf nake tafiya tun Ammah Nada rai,bare yanzu da nake tsoro kar na barsu a gida wani cikin yan iskan gari su shiga su yashemu tas mu rasa inda za muyi shi yasa kamar me aikin Hajji kudina na jikina wanda zanyi amfani dasu kawai nake rikewa a hannuna,kulle gidan nayi tare da tafiya gidan kawata Nawwara sabo da tana ta zuwa ni bana zuwa,da Sallama na shiga muka gaisa da Ummanta tare da Yayanta Hammad,tunda na shiga Hammad yake ta kallo na har kunya naji,Umma tace shiga ciki mana Mufeeda mutuniyar taki yanzu zata dawo ai,ina Zaune sai ga Nawwara ta dawo dama Salat aka aiketa ta siyo,Da gudu ta fado palon tare da miko min hannu muka tafa,tace shegiyar gari sai yau zaki zo, nace ke dai bari ba lokaci wlh yanzu ma dan kar na karya alkawari nazo miki sauri nake na koma kafin su Meenat su dawo kin San yau Friday,Nawwara tace hakane uwar mata,Wlh ina tausaya muku musamman ke da kike komai it's not easy ace kamarki ke kula da gida just 17yrs,ni abinda ma ya Dameni Mufeeda auren nan naki kinji yanda ake gulmar a unguwa dan abin ya shafeku ne ba za ayi a gabanku ba,wasu sunce karya ne dama,wasu kuma sunce ai auren kudi kika yi sabo da son abin duniya gashi wai ya gudu yaki zuwa ko kallonki baya yi,wasu ma sunce bature kika aura,wasu kuwa wai ciki yayi miki shine aka zubar dan kar a gane shine akace ya aureki,wasu kuma sukace ai ana daurawa ya samu ya kwanta dake shine ya fece,ke kowa da abinda zaice,murmushin takaici nayi nasan ni na jawowa kaina sai nace can da matsalarsu zasu gani ai watarana gaskiya zatayi halinta,yanzu gulma ba kauye ba birni kowa yinta yake.

    Ita kanta Nawwara karya take tace tasan sirrina ni dama can ban damu da kawaye ba bare duk sirrina na kwaso na fada musu a dinga gulmata sabo da mutum mugun ice wani jira yake yaji sirrinka yaje yayi ta yadawa a duniya shi yasa ni bana so wata ta fada min sirrin rayuwarta kuma nima bazan fada miki nawa ba kawai ayi hirar duniya,duk inda mutum ya kai da gulmarsa bazaice ya San sirrin gidanmu ba,shi yasa ko ita Nawwara tayi tayi taji gaskiyar Aurena da halin da nake ciki amma naki yarda ma Sam ta sani daga ni sai yan uwana suma kuma haka Ammah ta tarbiyar damu,sirrinmu iya mu kawai family,share zancen Nawwara nayi na saki wata hirar can ta duniya daban,daga nan na Mike nace yan makaranta sun kusa dawowa ni zan wuce,Hammad yana  Jin haka ya mike tare da fitowa waje,saida ta rako ni har waje muka yi Sallama,ina cikin tafiya Sai ga Hammad yana cewa Mufeeda na amsa a mutunce,Yace wai da gaske kina da aure dan Allah? Nace ae,da gaske ko wasa ni fa ban yarda ba na dawo daga service naji labari,murmushi nayi nace wlh yaya Hammad da gaske ne, bata rai naga yayi tare da cewa to gaskiya wannan ba mijin kirki bane kisa ya sake ki kawai ai gwara ki zauna ba aure,nace to idan ya sakeni wa zan aura?Ni ina son mijina bazan iya rabuwa dashi ba,komai shi yake daukan nauyinmu,Hammad yayi wani dariya kamar Boss yace sannu yar karya da ba a San Asalin balbela ba da sai ace daga masar take,ance me kudi ne ya akayi kike sana'a?kina ci da kanki,wa ya taba ganinsa yazo wajenki?makaryaciya rufa miki asiri zanyi kisa ya sakeki na lallaba Na aureki Ku ba gata ba,ba yayan uban kowa ba sai shegen iyayi wai ku  kyan da kuke dashi ne yake rudarku ko?

Nima fa bani da hakuri watarana nace ina ganin mutuncinka Hammad karka bari na yaga ma mutunci a unguwar nan,ka gyara kalamanka,ni yanzu me daraja ce da tsada domin ina da aure kuma da ace kasan wa nake aure da sai ka raina kanka tare da yin nadamar kalamanka,ni nafi karfinka wlh ko ace bani da aure hankalinka da nutsuwarka sun min kadan a matsayin mijina,ina fadar haka na juya cike da Raunin zuciya ina son fara Kuka... dum gabana yayi mugun faduwa ganin motocin Aayan sun kai su Bakwai a jere kofar gidanmu,juyowa nayi na kalli Hammad kana nace ga dan Halak can, zo ga mijin nawa sai ka mutu na juya ina tafiya,na barshi nan tsaye,kusa da inda suka yi parking akwai me salat ba ruwana na tsaya na siya mana salat da tumatir sannan na rike ledar zan shiga gida,muryar su Meenat naji da fara'a suna sis mun dawo ina kika je?da sauri suka karaso tare da rungumeni ina musu Kiss a goshi domin mun saba da hakan ma,Ma'eesha ce ta karbi ledar salat dake hannuna ni kuma na karbi jakankunan makarantarsu muka nufi shiga gidanmu,ko kallon motocinsa banyi ba,yana ciki duk abinda mukeyi yana kallonmu,yasha mamakin ganin ko kallon motocin banyi ba kuma yasan na gane shine saima gida yaga mun shige,ni kuma cike da bakin ciki na banko kofarmu da karfi da niyyar na rufe dan Ubansa tunda baida mutunci nima zan nuna masa abin haushi da kunya kawai sai kofar ta balle baras ta fadi kasa rigijif ai ko har securities dinsa sai da suka barke da dariya yanda na shiga gidan cikin fushi da hasala tare da mako kofar kuma sai ta balle.

     Aayan ma sai da ya dara duk kuwa da kuncinsa,muna shiga na taimaka musu suka cire kayansu,nace suje suyi wanka muyi sallah sai muci abinci, shi kuwa Aayan ganin masallaci za a fara sallar Juma'a sai yace suje suyi sallah sai su dawo,a nan masallacin unguwarmu sukayi Sallar, kafin su fito na gyara salat na yanka mana,Bayan munyi sallah na zuba mana a tire kato kun San dai akwai ci ni kam,a tsakar gida saman tabarma na wani baje cinyoyina,sanye nake da Vest red,sai skert din atamfata yayi mugun Dameni gani da hips tare da da tudun Mazaune kamar babbar mace,haka nayi wani cas dani ga skin dina jajir da ita fara,ko dankwali ban daura ba sabo da ni dama a gida bai Dameni ba,jelar gashina har yaso wuce tsakiyar baya na,sajena da gashin gaban goshina sun kwanta luf,ina ta bawa su Meenat abinci a baki kamar wasu yara nima ina ci suma suna bani muna hira.

    Wani yaro ne ya shigo da Sallama wai Mufeeda tazo sauri yake zai tafi,nasan bazai wuce Aayan ba cike da masifa nace kace bata da lokacinsa,yaro ya je ya fada sai ga yaron ya dawo yace wai idan ya iskeki sai kin gwammace kida da karatu,Mufeeda tace kace nace yazo din koma mene yayi idan zai iya,yaro yace ni dai tsoro nake ji bazan iya fada masa ba,Mufeeda tace to dan uwarka nice sa'arka zaka zo ka fada min fice min a gida,yaro ya fice da sauri yana kuka Mufeeda ta zageshi,can sai ga Oga Aayan da kansa ya shigo gidan cike da bacin rai yana huci,kamar ance wani ya mutu yanda yake kunci,yanda ya hadu yau ba a cewa komai,yayi masifar kyan da ban taba gani ba,cikin kana nan kaya yake hadaddu duk gidanmu ya gauraye da kamshinsa.

    Wani Kwarjini ya min tsoronsa ya kamani na fara da na Sanin maganar dana fada masa,Ma'eesha sarkin Surutu tace sis gashi nan ya shugo ko shine mijin naki? Meenat ta kalleshi ta kalleni haka take yi sannan sukace ina yini? Da kyar ya iya bude baki yace am fine tare da kare min kallo ta kasan ido,

ni dai naci gaba da basu abinci a baki ina cewa kuci abinci akwai Islamiyya kun sani, ganin su Meenat a ransa yace har kanne gareta Ashe,muryarsa naji yace ina Mum naki,cike da zafin rai nace taje inda ka aiketa, ba wannan ne ya kawo ni ba ina da aikin yi,kizo muyi magana dake,Meenat tace Sis kije mana,sai da na ebi abinci a hannuna sannan na Mike da abina ina ci kamar mayya,ya kalleni yana mamakin jarabar ci na ko micijin ciki ne da ita oho,hannuna da shinkafa a ciki na dunkuleshi nace shigo wannan dakin,ya wani yatsina fuska yana tabe baki haka dai ya shiga yana wani makale jikinsa irin zai kwashi dirty,

     Ji nayi yace ba a gidanmu zaki zauna ba yanzu,wani gidan za a kaiki daban,kiyi fixing Date da kike so su Abbi sunce ba yanzu zaki shiga family house ba sai nan gaba,so gidan dana kaiki rannan kike gyarawa nan zaki shiga,ki sanarwa Mum naki,wani farin ciki ya kamani kamar na taka rawa wannan hadadden gida ga kayan dadi zanci na koshi, ban san sanda na fashe da murmushi ba tare da cewa wannan gidan me kayan dadi? sai kuma wani bakin ciki ya tsaya min wato bai ma San Ammah ta rasu ba,kuma ko irin yace min ya me jiki ko ta warke Sam,nace aiko ya me jiki kace min ko? Au bata warke ba?kamar na mareshi haka naji,nace ta rasu,Allah yaji kanta ya furta irin ko a jikinsa,nace daga ni sai kannena mu uku,yace then? kuma ni yanzu na fasa auren ka sakeni kawai yafi min bashi da amfani sam,murmushi yayi yana daga tsaye yace kin makaro kinci Sadaki,kuma na biya kudin Magani na cika alkawari dole ki cika min nawa,don haka sai ki biyani ko ki karbi aure zabi daya,Hawaye ya zubo min da muryar kuka nace mugu ka kashe mana Ammah zaka ce na biyaka kudi,ai kaine ya dace ka biyani kudin diyyar Ammah kai ka jawo ta rasu,da tuni muna nan da uwarmu,Kuma haka ake Business din idan banda sadaki me ka bani,bayan kai kace zamu ji dadin duniya da kudin,zaka yiwa kannena komai na rayuwa zanyi abinda nake so da kudi yanzu me kayi daga ciki,haka ake Deal din,ai sai na fara gani a kasa tukun,Oya na mika masa hannu nace miko kudin fara harkoki da jin dadi first mu fara murmurewa muma muji dadin duniya sai na yarda nima a kaini gidanka,kuma dole ka sai min injin Markade na dinga yiwa mutane ina samun kudi domin makociyar mu da kudin Markade taje Makkah, tare da keken saka kayan sanyi, bai sanda yayi dariya ba matar dake neman jin dadin duniya kuma wai itace da Markade a inji, ita nufinta duk cikin Jin dadi ne bata saba da dadin ba to,nace kuma sai ka sai min irin abin rannan me dadi,ka bani kudin kashewa,yace nawa zan baki?Na gama tunanina na shirya masa mugunta zanci kudinsa da yawa nan take na sosa kaina nace Dubu bakwai duk wata daya,kacal?yace, Na hangame baki nufinsa basu da yawa nace Dubu goma Sha daya to,ya juya tare da cewa get ready Next wk Driver zaizo ya daukeku.

  nace to haka za a kai maka Amaryar taka kai ba dangi?ba kwalliya?ba gyaran jiki?ko haka kaga anayi ko kuma son kudi da tsumulmula ce tayi ma yawa,mene Tsumulmula? Nace gashi nan haka wai ake kasuwancin zaka tafi ko sisi baza ka bani ba cikin kudina na business,abinci ya kare hakkinka ne,bani da Vaseline,ina so zan yi kitso ai sai ka kawo kudin ko? Ni tunanina ai nayi ne dan na tatseshi kudi na hada masa mugunta zan cinye masa kudi su kare,ya kalleni tare da daure fuska yana dariya a ransa yace nawa ne kudin?Na shirya karya na ninka kudin nace Dubu biyu,wata dariya ta kamashi amma ya maze ya zaro Dubu biyu sababbi kar yace gashi,na karba nace tsaya na irga domin kudi suna da doka tare da ka'ida,na dankwali yawu kamar me irga wasu milliyoyi na irga nace sun cika,yayi hanyar fita daga gidan, wai duk cikin Jin haushinsa dan na kona masa rai nace amma wlh girma ya fadi,an fadi kasa ba nauyi,ka bani kunya kuma ka bada guys ashe ma duk bogi ne da ake kurin ana da kudi sai dai a kwashi motoci ana yawo a gari,a tambayi Dubu biyu ba kari ba komai ina laifin ka bani Dubu uku ko ka kankaro girma da mutuncinka,amma yanda na fada haka ka bani a haka kamar gaske,ana tafiya kamar dan sarki aji tsoron Allah wlh azara'ilu ko yaushe zai iya zuwa, ficewa yayi da sauri sabo da dariya taci karfinsa bai so kuma taga hakorinsa yana dariya, haka ya shiga mota yana dariya,su Kansu escort din nasa mamaki sukeyi Aayan kamarsa duk jarabarsa wata na sashi dariya.





AsmaBaffa
[1/5, 5:03 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

    KASUWANCI NA




          26-30





Official




By
AsmaBaffa






       MAMAN MEENAT ina godiya da Sharhi,taku ta manya ce kunfi karfin kowa sai dai mu kwashi gaisuwa. page na yara ne😍HAFCYCY this page is for u Sweety.

    QUEENMERMU tamu dubun gaisuwa😘😘😘❤❤❤❤
MAMAN WALEEDA kin boye Allah yasa lfy.

Masu Sharhi yan albarka
ASMABAFFA FANS CLUB
TASKAR SURAYYARMS
TASKAR FIDDAUSI SODANGI
HAUSE OF HAUSA NOVEL tare da sauran Gps ina matukar jinjina muku da godewa.masu min magana ta Pc tare da masu kira ina rangado muku gaisuwa me yawa Allah ya kara kauna.





     Koda ya fita basu zarce ko ina ba sai gidan Yarima Bobo abokinsa wanda suke shirya komai tare,ni kuwa mamaki nakeyi kamarsa duk kudinsa wai yanda na tambayi kudin ba kara ba komai iya 2k din ya bani,nan nace bari ya dawo sai na gwadashi nace ya bani Naira Dari kacal na gani iya 100 zai bani,Meenat ce tace Sis mijinki me kyau dan gayu wlh kinyi sa'a wannan irin kyau amma dai dan kasar waje ne ko? Kyan banza ne dashi Meenat sai fadan masifa,Hmm to Allah yasa ya canja ya koma Sonki Sis ai idan munje gidansa kwalliya zaki dinga yi ta jan hankali ki sace masa zuciya da wuri,idan mun ganshi a gidan ko?ai ba gida daya zamu zauna dashi ba main gidansu daban inda za a kaini daban kuma ni ai ba sonsa nake ba ina ruwana da har zanyi kwalliya sabo dashi,sis ke har yau da sauranki Allah ana gabas kina yamma irin wannan ai abin a so ne,baki na tabe tare da cewa ke karki Dameni me zanyi dashi auren Kasuwanci nayi ba abinda ya Dameni ya dauki nauyin mu komai da komai muji dadi shike nan buri na,kallo na Meenat tayi tare da cewa Sis ke bakya sha'awar maza ne kamar wacce wanzami ya cirewa Budurci?ko dai ba a sani ba Ammah tasa wanzami ya yanke miki Belin ki? Dariya nayi domin Mufeeda ta fini Sanin duniya tana zuwa schl,nace baki da kunya Meenat ai ni bana son wani Namiji me zanci dashi tir Allah kiyaye,Meenat ta dinga dariya tare da cewa Sis yanzu ko yar Runguma kuyi bacci ba kya so ga dan Kiss ma? Baki na rike ina kallonta nace ke wanne kiss wanda nake gani a film? Wlh bai isa ba idan yace ma zai min za a kwashi Bala'i da yan kallo ke nifa duk irin harkar nan bata damuna gwara kudi kawai,Meenat tace ni kuwa da nice na Samu me kyau haka ga kamshi,kudi komai ya hada ai da anga kwasar duniya,ke Meenat yarinya dake kike irin wannan zance,da nawa kika girmeni wai ma ki zauna kamar ba yar cikin birni ba gaki a cikin Birni amma kamar kina kauye, ae naji tunda Ku zaku Zama yan birnin ba komai zan muku ko mene abinda nake so kawai na koma makaranta idan ya Amince amma ni me ya Dameni da wani love.

      Muna rayuwarmu bayan kwana uku su Meenat suna zaune suna ta faman game a wayata Nokia a tsakar gida,ni kuma sanye nake cikin wando tight 3qrt blue sai rigata iya rabin cinya me gajeren hannu pink kaina ba dankwali jelar na lilo  ina kusa da Rijiya na ebo wanki ina ta wanke mana kayan sawa kusan ko yaushe sai nayi wanki haka nake bana son kazanta.
    Sallamar mutum muka ji kawai a cikin gidanmu kamshinsa ya gauraye ko ina nan take muka gane Aayan ne yazo yaji lokacin da na Zaba a kaini gidansa matsayin matar Aure,mamakina shine rannan a waje ya ganni ina yawo amma Bai ko tambaya me yasa na fita bada saninsa ba,kaina na bawa amsa ai ba Sonki yake ba ina ruwansa ko ma ina zaki je.
     Ganin su Meenat suna wajen yasa na amsa Sallamarsa tare da mikewa ina goge hannu na,gabansa na karasa tare da cewa sannu da zuwa wani Kwarjini da tsoronsa yasa na dan duka nace Ina yini,ko amsawa baiyi ba,na Mike na kawo masa wata kujerar roba fara tare da kara goge masa kujerar da wata duster,sai lokacin ya zauna kamar wani sarki yasha kana nan kaya yau ma wandon kansa abin a kalla ne ya hadu pencil dashi,Meenat ga Uncle yazo nace sabo da shishigina shi kanshi sai da ya tabe baki wai Uncle,da sauri suka zo suma tare da durkusawa a gabansa suna gaisheshi to su dai sun fini samun matsayi sabo da ya amsa musu sau daya da lfy bai kara ko ce musu komai ba suka koma inda suke suna ta game dinsu,Yau wacce rana ya ganni bana cin komai, bai gama tunaninsa ba yana zaune yaga na shige dan kitchen dinmu na fito da pure water a plate guda biyu na ajiye masa,ko kallon plate din baiyi ba sai faman chat yake a waya yana wani murmushi,kara komawa kitchen nayi na dauko Ayaba guda wajen biyar na mikawa Meenat da Ma'eesha guda biyu,tuna ninsa shi zan bawa ragowar sai yaga na koma inda nake wankina na bare guda daya gutsira biyu na cinye gudan Ayaba,na dan ci gaba da wankina na kara bare guda itama gutsira biyu na cinye duk yana kallona ba tare da na gane hakan ba,guda daya na rage na koma wajensa tare da dora masa saman ruwan dana kawo nace gashi nan Kaci sabo da Ido guba ne shi yasa,komawa kitchen nayi tare da zubowa su Meenat tuwon shinkafa miyar ganye tun daga Ido zaka San akwai dadi,Nace kuzo Ku kara abincin yamma kar yunwa ta kama min Ku,dama indai ba schl to dole muna kara cin abinci da yamma,ni kuwa a rana sau hudu sau biyar nake cin abinci,shi yasa kannena ma haka nake dura musu ko basa so sai nace sai sunci kadan.

   Ma'eesha tace nidai sis na koshi har sau nawa za muci tuwon nan gashi da dare ma kice sai munci,Na bata rai tare da cewa kin san tunda na zuba sai an cinyeshi ko Amai zakuyi sai kunci,Meenat cike da shagwaba tace pls Sis mun koshi Allah,nace to Ku kuzo muci tare nima zanci na zauna wajensu na fara ci ina dura musu ta dole suna yatsina fuska sun koshi,sai da muka cinye dole sannan na wanke plate din na maida kitchen,nace Ku ajiye wayar nan kuzo Ku karasa wankin nan da sauri suka taho tare da karba sunayi,ni kuma na koma kusa da Angona Aayan na zauna saman tabarma na kalleshi tare da cewa Angon Business,ba tare da ya kalleni ba yace wacce rana kike so? Nace to wai dangina baza suzo a dauki Amarya ba? Ni bana son mutane a harkar nan Business ne mene amfanin sanin mutane,ba auren so ba mene sai an sani wani auren kirki ne wannan da har zan nemi mutane,Allah baka hakuri zabi date da kanka idan ma yau kake so muje,amma kuma da mun tafi tare da Uwaliya da take gidan nan ko? Wani kallo me cike da masifa ya wurgo min tare da cewa wannan gidanku ne ko na haya? Namu ne na kanmu cewa ta,yace to bana son kwashe kwashe ku din ma dole ce zata sa Ku shigar min gida bare wata Uwaliya ko me,ku Uku nan zan iya rikewa wannan gidan kusa yan haya ko Ku bar matar a ciki ko Ku siyar da gidan ni ba matsala ta bace.

     Burina kawai muje hadadden gidan nan ace yau gamu a ciki zamu zauna wayyooo dadi gashi nasan ma zai dinga siyo mana kayan dadi ai nan take nace azo gobe a dauke mu,mikewa yayi zai fita,wata dabara ta fado min na Mike da sauri tare da dauko Hijab na saka nabi bayansa da sauri sabo da so nake wasu yan unguwa masu sa ido su ganni tare dashi su tabbatar da gaske ne aure na a daina zagina a gari,sai da nayi sauri na jera dashi har waje,ya kalleni tare da cewa ina zaki je,nace uhmmm makwafta zanje tunanina zaice kar naje ai ina da aure sai naga ko a jikinsa,muka fita har waje tare ina ta faman Mannewa kusa dashi sabo da yan unguwa suga fa ae ga zahiri ga sheda,na rasa me zance nace wai ka tsaya mana banfa gama magana ba,ina jinki ai,sabo da na jashi da zance har mutane su ganmu da yawa nace haka ake Business din kuma ni me zansa idan anzo daukan Amarya? Banza ya min,nace sannan ina son Naira Dari zan sa kati a wayata na kira Family,da mamakina sai naga ya tsaya a jikin motarsa ya zaro Dubu guda sabuwa ya kira Almajiri ya mika masa tare da cewa dan Allah samo min canji ka ce a hada ma da yan 100.

    Muna tsaye mutanen Layinmu yan sa ido yau sunga zahiri da idonsu motoci sunfi 8 a kofar gidanmu,sunga da gaske ne me kudinma na gaske ga kyau,muna tsaye dan mutane suce auren soyayya ne sai wani murmushi nakeyi ina washe baki,shi kuwa tunani yake anya lafiya ta kalau kuwa ko dai ina da tabin kwakwalwa mutum shi kadai ya dinga dariya yana murmushi haka,wasu maza ne matasa duk na sansu mugayen yan sa ido ne a unguwarmu hango su nayi sun taho wajen mu da alama ball zasu je duk sunyi shigar Jersey ina ganin haka na kara matsawa jikinsa kamar zan shiga cikinsa,kamshinsa yana ratsani ba zato yaji na saka hannuna a cikin nasa na rike kam kam kamar za a kwace shi,dama tuni na gano ba ta rike hannu ake yin ciki ba Meenat ta fayyace min komai,hannunsa yaja yayi yayi ya fisge amma sai dai ya girgiza da jikina gaba daya na rike hannun kam,idonsa yayi ja sabo da bacin rai da ace ba mutane yau da naci ubana a hannunsa dan Zane ni zaiyi kawai,Sake min hannu mana are u mad? Cewarsa ina murmushi tare da tamke lips dina ina mamularsa nace uhm uhm ni bazan saki ba kawai ka tafi baka bani kudin ba,su kuma mutane na layin yan sa ido ana wlh da gaske ne yana sonta sosai kalli soyayya,matasa suna cewa tayi dace Allah ya bata,wasu matan da suka sanni cewa suke ina ma sune wayyo dadi suna sha'awata,haka Nawwara ma ta fito ta hango mu nan ta tabbatar da wannan soyayya ce me karfi rike juna har a bainan nasi,Haka almajirin ya kawo canji still ina rike dashi ya hakura ya kyaleni ya karba abin al'ajabi sai ya cire Naira Darin dana tambaya ya mika min yace jeka da sauran Dari taran na bar maka kyauta,yaro ya tafi yana ta tsalle da murna,ni kuma ya bani Naira Darin,Nace ka rike albarka bana so tunda Ka iya bawa Almajiri Dari tara ni ko Dari,hannunsa ya fisge tare da maida Naira Darin aljihunsa ya shiga mota escort suka ja motoci suka kara gaba,ni ma nace Alhmdllh an samu shedu a unguwa na koma cikin gida abina.

   Uwaliya tana dawowa na sanar mata cewar gobe Mijina zai turo a dauke mu zamu koma can da zama ita kuma ta nemi wata suci gaba da Zama a gidanmu suna gyara mana shi,ta dinga godiya sosai,nace danma mijina bai yarda bane da tare zamu tafi dake,Uwaliya tace hakan ma na gode ai kun gama min komai akwai wata kawata Kaltume zan nemota mu zauna tare,nace to ba matsala ga kayan kitchen da komai kuyi amfani dashi mu iya kayan sawarmu kawai zamu Eba. A daren muka hada kayanmu tas marasa kyau muka zubar domin babu wanda zamu bawa sun lalace da yawa.
Gidan mu kuma so nake na samu kudi na gyara shi na zuba yan haya a ciki shi yasa nace su Uwaliya su zauna kafin na samu kudi.

    Washe gari 5pm Driver da katuwar mota ya Parker yace mu fito inji Oga,muka zuba kayanmu a boot Uwaliya munyi Sallama tuni ta tafi wajen aiki,munsha kyau domin duk jaraba sai da na  dinka mana Atamfa me kyau ko wacce kalar tata daban,tasha dinki me masifar kyau riga da skert,da mayafi me kyau tare da takalmi me dan tudu me kyau,muka je saloon,sannan akayi mana lalle me arnen kyau har su Ma'eesha akayi komai.
    Bayan munyi wanka Meenat ta tsantsara kwalliya tare da dauri me kyau dama ta iya watarana Amare marasa kudi suna kiranta tayi musu kwalliya da daurin gogoro sabo da tana da basira a nan sai ka rantse make up kaje aka yi ma,Haka tayiwa Ma'eesha ma kamar ka sacesu haka suka koma.
      Amarya kizo na miki kwalliya kar mijinki ya raina ki yana kallonki a bagidajiya,da kyar na yarda Meenat ta zauna ta fara sheka min kwalliya tare da dauri me masifar kyau,ni kaina ji nayi kamar na lashe kaina sabo da tsananin kyan da nayi,kowa ya kalleni sai ya kara,sai kuwa ga Driver yace mu fito,Maeesha ce ta dinga kai kayanmu Driver ya zuba a boot dama ba wasu masu yawa bane,muka yafa gyalenmu kamar yan mata zamu party,Hips dina kamar zai fado tsabar tudu da fadinsa a skert, muna fitowa Driver sai wani girmamani yake,muka shiga mota nace Baba zaka kaimu makwafta muyi musu sallama,samun waje ga baki ga hanci amma haka nace Driver ya dinga kaimu gida gidan da muke mutunci sosai harda Nawwara mukayi musu Sallama cewar zamu dawo sai mu basu address na gidan mijina.sai kallo da gulma anga uwar motar da muke ciki makwafta ma sai an kaimu a mota,wasu suka ce Allah ne yasan manufar Jaki shi yasa bai Yoshi da kaho ba.
    Bayan mun gama nace wa Driver muje ya kaimu gidan mun gama,ya fige mu muna dan kamshinmu har gidan Aayan dama na rigada na San gidan,Driver na parking muka ga wasu sunzo sun dauki kayanmu tare da shigar mana dashi ciki suka fito tare da cewa Oga yana ciki Ku shiga yace.

   A raina nace ai ko bai ce ba zamu shiga kunji fa,muna zuwa kofa na danna Door bell ya bude muka shiga sanyi da kamshi ya ratsamu,yana jikin kofar ya bimu da kallon mamaki yanda yaga munsha kyau kamar yayan Larabawa zasu je Party musamman ni ba a magana,a ransa yace ashe dai suna da kyau,sai kuma a fili ya tabe baki yace kuje ciki mana kun zura min Ido,a hankali muka shiga tare da Zama a saman kujera,yana zuwa yace ba a Zama min a kujera,ya kalli Ma'eesha yace wannan ce kadai zata dinga Zama a kujera amma Ku banda Ku,shuru mukayi muka ji ya kuma cewa Bedroom guda daya gashi nan shi zaku dinga Zama bana so ana fitowa Palo ana takura min,bana son Surutu a gidana,akwai komai a kitchen na girki,dan ma bana so a bata min gida da hayaki ne amma da itace zan siyo muku yanda kuka saba kuyi girki dashi a Compound amma kunci Sa'a zaku iya amfani da Gas,wani dadi da murna ya kamani zan dinga dafa mana kayan dadi dama nasan gidan nan akwai harkar dadi.

    Je ki duba kitchen abinda babu ki dawo ki fada min,da sauri na Mike ko kunya irin zan ga harkar dadi,ina shiga na tsaya turus ganin buhun dawa,gero,masara,wake,shinkafa yar hausa harda ta tuwo fara, sai maggi kala biyu Rak fari ajino motor da star,harda kanwa,Flower,kukar miya etc duk dai wani abu na cimar talaka futuk shine cikin kitchen,haka kayan cin abinci ma komai ya siyo na roba kar mu taba masa nasa na glass,komai irin cimar mu ta talaka ya kawo,haka fridge ba komai a ciki ko ruwan roba wai musha na pampo alhalin ko a gida pure water muke Sha duk talaucinmi.

   Jiki a sanyaye na fito cike da jin haushinsa,nace Meenat kuje Bedroom,ba tare da nace komai ba na zauna a kasa tunda yace kar wacce ta hau masa Kujera,ko kallo na baiyi ba yana ta kallon News abinsa,nima ina kallo ne kawai don bana jin me suke cewa sai dai dai nake tsinta,sai satar kallonsa nake yana ta Shan juice lafiyayye da gani zaiyi dadi,yasha rabin kwalin sai naga ya ajiye glass cup din ya Mike tare da haurawa samansa,sai da na tabbatar ya shiga sannan na daga kwalin na kafa a baki na tare da shanyewa du na lashe bakina sai na fada kitchen na ebo ruwa a tap nazo na dura a cikin kwalin dai dai yanda ya bar lemonsa na maida cup din tare da dawowa kamar da na zauna na wani langabe kai irin Allah sarki din nan.

     Kamar jira yake sai gashi ya fito sanye da shadda yar gaske yana sheka kamshi da alama fita zaiyi,yana zuwa sai aka yi sa'a ya bude kwalin lemon da niyyar ya tsiyaya yasha Sam bai zata nice zan yi haka ba,yaga maimakon yaga lemo sai yaga ruwa na tsiyayowa da sauri ya jefar da kwalin tare da yin gefe ya firgita ko Aljanune,tunani ya shiga sai ko ya kalli bakin kwalin ya hango jambaki na a jikin abun,nan take ya gano nice na shanye na zuba masa ruwa,ni kuwa tuni na Mike tsaye cikina ya Duri ruwa jikina ya fara bari,yasan guduwa zanyi don yaga har na tattare skert sai naga kawai yayi hanyar fita waje,nan na sauke ajiyar zuciya,ashe Duk bedrooms da kitchen tare da sauran kofofi ya kulle ta yanda bazan iya guduwa ba, tuni Idona ya kawo Ruwa nasan yau sai dai gawata,saman 3 seater ya koma ya zauna tare da nutsewa a ciki yayi dai dai cike da isa yace zo,nace ni?yace no ni,da sauri na karasa tare da durkusawa a gabansa yace bude bakinki na gani,ba shiri na bude ya kuwa ganshi wani fes dashi,ruwan dana dura a kwalin ya dauko ya fara dure min shi a baki ina kwat kwat har ya kare  ,jefar da kwalin yayi tare da barin gidan gaba daya.

    Yana fita nace su Meenat su fito mu shiga kitchen,kayan abincinmu na talakawa muka shirya a store sannan na ebo dawa muka gyara ta na wanke na shanya ta a kwandon ta bushe,haka masara ma,na ebi gero cup 4 na jika shi zan kai markade sabo da kokon safe,waken da zan soya mana kosai ma haka na ebo komai dai muka gyara komai abinmu,Na fito wajen masu gadi nace dan Allah a ina za a kai min nika da Markade? Wani cikinsu yace Hajiya unguwar masu kudi irin wannan sai ansha tafiya me nisa,nace ni dai a gwada min,ai ko ya gwada min,nasa Meenat ta dauki Dawa a cikin Leda Viva,nima na dauki masara duk sun kai kwano uku uku,sai geron dana jika na Koko a cikin dan botiki dan kadan Ma'eesha ta dauka,muka fito tare da tafiya me uban nisa muna tambaya har sai da muka bar layin sannan muka samu gidan wata mata me Markade wani namiji kuma da injinan nika,na bada kudi nan take akayi mana komai da komai muka dawo gidan tare da tankade garin muka adana abinmu,Nasa hijab na kara fita yan su Curry da sauran abubuwan girki na bada kudi na siyo mana harda su kayan kamshi,kayan hada lemo,da zobo da sauransu,ina dawowa a gate na bawa gate man kudin pure water nace ya siyo mana manyan Leda biyar mu dinga Shan abinmu, na dawo su Kubewa bushashiya na bawa su Meenat dama akwai turmi dan karami a kitchen din suka daka mana muka tankade da yawa duk sai da muka shirya kayan abincinmu komai na marasa karfi na shirya kitchen tsaf muka gyara shi tas,pure water kuma na shirya wasu a fridge wasu kuma a can gefe na ajiye idan mun shanye sai mu dinga zubawa ciki,a hakan ma sai murna mukeyi abinci available zamu ci mu koshi a kan lokaci ba sauran wahala da babu kaza babu kaza,shi abinci ko garau garau ne kake ci in dai ba yankewa kuma akan lokaci to Shar za a ganka.
   Bare har da su shinkafa ga ta tuwo ma,mangyada manja ai shike nan mu,shi yasa dana fita ma sabo da yau jira nake Allah ya kawo Aayan da dare na nuna masa cewar ina da zuciya.
   Shi ko Aayan jira yake yazo gidanmu da wuri yaga wanne girki zamu kwaba tunda yasan ko kayan miya bai ce asiyo mana ba,ba nama bare kifi bai San na siyo mana kayan miya harda naman rago na Dari uku tare da danyar Kubewa zamu zabga girki.

       Meenat tace sis mu wlh ai indai zamu dinga samun wannan ai Alhmdllh a gida ina muke samun haka kullum sai dai fa muyi girki tazarce,Nace Ku canja kaya kuzo muyi sauri mu kara gyara gidan nan sabo da idan yaga dirty daya to jaraba zai mana,nan take muka kara gyara gidan ya dau kamshi,ni kuwa ina kitchen sai girki nakeyi kamshi na tashi,Magrib nayi mukayi Sallah lokacin na gama miya tuwon danyar shinkafar nake karasawa,ina gamawa mukayi wanka da Sallar Isha tare da canja kaya marasa nauyi, Ma'eesha tasha 3qtr dinta dan me kyau da nake siya musu tare da yar vest na sa mata, Meenat kuma riga da skert tasa suma English wears na gwanjo amma masu kyau kalar yan gayu, ni kuwa doguwar rigar material nasa fitted nayi kyau amma ba kwalliya a fuskata.

     A katon wani tire na roba na zubo mana miyar Kubewa danya da naman mu kowa yanka uku,Sai tuwon a leda har guda hudu manya,ga pure water shima na zubo a wata roba kalar ta Almajirai duk cikin kayan da Aayan yace a ciki zamu dinga cin abinci ne.
     Na dakko mana komai muka zauna tsakiyar center Carpet na tattare rigata zuwa wajen hips gaba daya cinyata a waje take fara sal da Ita mul mul da su,Meenat ta fara dariya wai Sis ke baza ki taba cin abinci a hankali ba kuma sai rufe dankwali kin wani kwaye cinya jiba ana hango short wandonki,to mu da waye a cikin gidan daga ni sai ku,zamu fara ci kenan muka ji karar bude kofa kamshinsa ne yasa muka san shine ya shigo,Sallama yayi muka amsa na fara basu abinci a baki,tsabar sa ido shine yazo ya wani baje saman 3seater yana kallonmu a nutse,yanda yaga na kwaye cinya dankwali yayi kasa duk sabo da abinci,Maeesha tace Sis ki san masa abincin mana nayi banza da ita muna cin abinmu,ni na manta ma yana wajen Sam ina ci har cinyata nake dana da duka sabo da dadin girkin,idan na ci Loma daya sai na sosa kunne sai soshe soshe nakeyi kamar me kwarkwata ko cutar karzuwa sabo da ni idan da abinci a gabana mantawa nake da uban kowa,Meenat su Kansu dariya sukeyi tace sis ya dai wai abincin nan ko yafi Nama dadi ne,Ina lashe hannu tare da tsotse yatsu na ina tande baki nace ke Wannan gonar da aka shuka kubewar nan daban ce maybe kasar kalarta daban kinji har zaki zaki haka,wajen mutumin nan zan dinga siyowa,suka sheke da dariya shi dai Na'im yana kallo ina ta side plate din,Maeesha tace Sis ki kyale kwanon haka mana nace baki San ba kyau cin abinci ba tare da an side kwano ba ai sai Abar albarkar abincin a kwanon.

  Aayan yana kwance yana ta faman kallon ikon Allah cike da alajabin abin nawa,muna gama nace muje a wanke hannu Muzo asha karatu,yana zaune yaga na Mike ina uban nishi tare da jansu muka je muka wanke hannu da baki sai ko muka kwaso jakan makarantarsu muka dawo palon kusa da shi yana kwance kai ka rantse nice shugaban masu ilmin boko na duniya yanda na faffake ina bude littatafai,Aayan yana jira yaji yanda zan fara koyawa kannena karatu.

      Ga mamakinsa sai yaji Meenat ta bude wani English book tace fada min words din jiya naji,Bai san sanda ya bude baki ba wanda bamu San ma yana yi ba,Na fara cewa Singular and plural,Abu me guda daya da abu me biyu,Examples like Mango-Mangoes,Orange-Oranges,Bag-Bags,Lady-Ladies ina fada ina rubutawa a littafi har na gama,Maimakon nasa Ladies sai nasa Ladys nan take Ma'eesha yar karama taci gyarana tare da kwace biro tace sau nawa za ace miki haka ake rubutawa ladies wai yau kusan wata daya kenan kullum sai kin manta,Meenat tace to Saura mu fara  present tense and past tense amma yanzu a koma baya muji,mene Noun? Nace Noun? Noun... to ....Noun.. dai shi sai na fada tunani tare da kallon sama kamar a nan zan samo amsa,nace to shi dai Noun... shine dai,nan take Aayan bai San sanda ya kwashe da dariya ba sai da muka kalle shi yanda dariya ke masa mugun kyau,Meenat tace Sis what is a Noun? Shine dai me? Na kara kallon sama tare da zura biro a bakina nace shi dai Noun is a name of....of.....yawwa shi dai Noun is a Name of Yawwa uhmmm....yes Animal dabbobi irin su Damusa, Kunkuru,zaki,kuma dai shi dai Noun is a  Name of place like harda yanga irin na gano gaskiya harda daga yatsa kamar malama na kwalla da karfi nace like capital city of Nageria Abuja,na kara karfin muryata nace also kasar Masar,na daga kai sama nace yes Habasha,idan muka dawo gida Nigeria zan iya ce muku Rimin Gado,Kura,Kasuwar Rimi,yan Kura and also kofar wambai  market,Aayan Dariya ta mugun kamashi duk uban labarin nan wai a Noun akeyinsa.

    Meenat tace yes muna jinki sis,Nace kuma dai shi Noun is a Name of person na saki murmushi irin shegiyar nan nace like ni Mufeeda,Ammah Allah yaji kanta duk da ta riga mu gidan gaskiya amma zan sa da sunanta Fatima,Abba wanda ya arce,Maeesha kema kina cikin Noun,Meenat ma ta shiga ciki,Aayan ma gashi nan a kwance,Maeesha suka sheke da dariya, nace ah to dana fadi wasu banza na waje ai gwara na gida.

     Na kara daga murya kamar me koyar wa a class nace Kai Noun shege ne wato shi ya hada komai harda Things kinga Bag,pencil,biro,spoon duk suna karkashin Noun.Meenat suka dinga dariya sosai suka ce kinyi dai dai amma labarin ai yayi yawa,nace wai me yasa Noun bai hado da abinci masu dadi a ciki ba aikin banza,ai kamata yayi ace akwai su Hen,su Ram,kabewar miya,Danwake,Taliya,Apple.
    Aayan yana ta boye dariyarsa,Ma'eesha tace Saura Verb, nace Verb gaskiya ita bata dadi is an action word or a doing work, ni Verb bata birgeni sam,kamar yanzu munyi aiki yawwa Cooking,jumping,running,washing,kuji wani iskanci wai harda kallo watching ace yana cikin aiki,eating ma ai ba aiki bane amma a ce harda shi ciki,haka dai suka dinga tambayata ina bada amsa amma sai nayi dogon bayani da Hausa na cinye lokaci.
   Ma'eesha tace daga yau an daina hausa sis duk bayanin da zakiyi sai dai kiyi mana da turanci kaf,na zaro Ido tare da cewa dan Allah kuyi hakuri ni dai me zance,Meenat tace wlh ba hausa gobe ki shirya naga Alama indai ba haka ba baza ki iya ba.
  
  Sabon karatu sukayi min present tense an past tense,sannan sukayi nasu na manyan kwari tare da assignment ina kallonsu,sai kuma muka koma Islamiyya,anan kuwa nasan komai Qur'ani suke kara min da wasu littafan amma duk na iya tunda na iya karanta larabci da rubutu kuma ni nafi kokari a fannin Arabic sosai ko Aayan ya sheda daga jin yanda nake karatu ina cin gyaran su Meenat.har muka gama abinmu sannan Ma'eesha ta mayar da komai Bedroom ta dawo still Aayan yana kwance abinsa yana danna waya, nace su tashi muje su kwanta bai kula mu ba muma haka,amma yayi mamakin ganin yanda muka yi girki lafiyayye haka gamu yara kuma yasan fita nayi na siyo wasu abun amma abincin ya birgeshi sabo da shi yafi son abincin zallan hausawa fiye dana turawa.

    Sai da ya dade sannan muka ji karar mota tare da bude gate wato mu kadai zamu dinga kwana a gidan,munyi addua na kara yi na tofa mana baki daya muka haye saman lafiyayyen bed din da bamu taba ganin irinsa ba muka fara bacci sosai,can cikin dare wurin 12:30 naji motoci sun shigowa gidan na farka tare da mikewa na daga labile na leka ta window Aayan na hango da ledojin take away dinsa a hannu ya dawo.A zuciyata nace dama yana kwana a nan? Na tabe baki tare da komawa na kwanta,shi kuwa yana shigowa sama ya haura yaci kayan dadinsa ya fesa wanka tare da shirin bacci yayi addua ya kwanta sai bacci.

   Washe gari na tashe su mukayi sallar asubah tare da azkhar sannan nayi wanka suma suka yi tare da shirin makaranta ni kuma nasa kaya Atamfa riga da skert me kyau harda shafa powder tare da lipgloss,wake na gyara da sauri na fice tun gari baiyi wani haske ba na taka har inda ake markade sabo da Blender bata yin laushi yanda ake so,dan markade kadan nayi na dawo da sauri na daura ruwan dama Koko,sai na fara soya kosai yasha kayan miya kamshi ka rantse wani nama ake soyawa,Aayan yana jin motsinmu tare da kamshi yana tunanin wai ina muke samun abun girki me kamshin dadi haka, ruwa na tafasa na dama Koko me dadi da lfy,na ebi nawa a cup ina cin kosai ina kora Koko Malam,Meenat ma suka shigo sanye da uniform dinsu na zuba musu suka ebi kosai a plate da sugar suka fito Palo suna Shan abinsu,sai ga Aayan ya fito sanye da Jallabiya fara,suka ce ina kwana ya amsa ba yabo ba fallasa da lfy Alhmdllh,Ya kalli abinda suke ta ci bilhakki da gaskiya ganin yana kallonsu Ma'eesha tace Yaya gashi in zaka ci,baki ya tabe tare da cewa ban iya ci ba,d a dadi fa,yace am Ok,Meenat a tsorace tace ka dandana,a ransa yace wannan jagwalgwalon zanci ganin bana wajen ya mikawa Ma'eeshah hannu wai ta bashi ya gwada,da Sauri ta mika masa kosai daya yaci yaji shegen dadi,dama kosai yana dadi haka? Abinda ya ayyana a ransa kenan,Meenat tace a karo? Ba tare da yace komai ba ya mika hannu a karo masa,ta dauki plate din suka koma gabansa gaba daya Yana sama suna kasa zaune,Yana Sa hannu ya dauka yaci suma suna ci suna shan kokonsu,Maeesha tace Yaya a kawo ma kokon da dadi fa,karon farko kenan da ya kalli Ma'eeshah ya gansu kyawawa gwanin sha'awa ga tsafta,yace sai dai ki bani naki nasha,ta mika masa ba kunya ya karba yana sha da kosan,dan rashin Imani bai ce tazo a kara mata wani ba dan shi sam bai iya kula da mutum ba,ba ruwansa da wani caring ko kina cikin yanayi na Kaza yace je kiyi Kaza sam bai san wannan ba,yaci ya sha abinsa ya mike bai ce ko a dawo lfy ba yana uban takama da gadara ya koma sama abinsa,a haka na fito suka bani lbr nayi mamaki da ya iya ci,na Sa Hijab na rakasu a kafa har Babban titi tare da sasu cikin Napep suka tafi schl nace idan an tashi kar su taho su jirani zanzo na daukesu a schl tunda baza su gane gidan ba.komawa nayi gida lokacin yayi shiri zai fita an kawo motoci wasu kalar,ni na manta ma ina da aure Sabo da ba abinda na fasa yi ko ina fita nake yi,shima bai ce min ina naje ba ko mene ma nayi ina ruwansa ko kallo ban isheshi ba haka ya shiga mota aka jashi nima nayi ciki tare da fara gyara gidan ko ina.






AsmaBaffa
[1/6, 11:20 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

    KASUWANCI NA




          31-35




Official







By
AsmaBaffa




       SAMEERAN GAYA yar ALBARKA ga page naki.

   HAFSAT KHAIRAN   Tare da MAMAN SAMHA ina gaisuwa.

JANNAT jinjina gareki me tarin yawa.




  Dan Allah masu Sharhi kuci gaba da yi ina gani,kwana biyu Net yana bani prob zaku ga reply baya zuwa da wuri ina matukar damuwa wlh,fans kun san dai AsmaBaffa ba haka take ba,ina kokarin Yiwa kowa reply sai daí idan ban gani ba,dan Allah ayi min uzuri ko da wata tayi magana taji ban mata reply ba to wlh ban gani ba ko matsalar networkc.sai masu yi min magana ta pc kuma indai anga ba reply da wuri to net ne kwana nan matsala yake yi,kuma ko wacce nayi reply back sai yaki Tafiya sai da kyar,dan Allah ina kara baku hakuri za a gyara kuma ayi min sharhi na ina gani Sabo da nayi typing me kyau.

   Sai kuma typing error ayi hakuri dashi,sai kuma kuskure na Dan Adam dole zaku ga abinda bai muku a ciki ba,har kullum ina so kusan cewa Sako ake isarwa,idan mutum shine star bazai yuwu ace baya kuskure a rayuwa ba,dole sai yayi abubuwa shima na kuskure tunda ana so a koyi darasi da shi ne,baza ace star shi ya Zama halaye 100% ba,so ayi hakuri aci gaba da karatu da Sharhi Insha'allah Novel zai tafi dai dai.
   I really love my fans wlh sosai Sabo da so nake na dage ko wacce Insha'allah masu Sharhi sai na baku page Insha'allah sai daí mantuwa,wadda bajintarta tayi yawa har 2 ko 3 page ma zan bata suna nan kuma ina ta ganinsu AUTA, FlOWER ma suna ciki etc Bazan fadi sauran ba yan kuri ne zasu cika min Gp🤣.








       Ko da na shiga gidan kawai aikina nayi ta faman yi sai da na gyara ko ina har Bedroom din Aayan ko ina sannan nayi mana miyar jajjage na siyo kifi na Sa mata,tayi dadi sosai,na dafa farar taliya na gama ,a gurguje nayi wanka na shirya tsaf sannan na maka Katon Hijab na tafi dakko su Ma'eeshah,ina zuwa suna fitowa da Sauri suka karaso inda nake tare da frnds dinsu wai zasu gaishe da Sis din frnd,harda gaisheni da turanci kawai na amsa tunda nima na dan iya a raina nace da kunyi hausarku Yara nafi karfi a nan wai su a dole yan private,shi kanshi me Napep yayi mamakin shegen gidan daya sauke mu,yace kamar wannan gidan ace za hau Napep ga yan mata zuka zuka haka,Me Napep tunaninsa ko yan aiki ne tunda yaga bamuyi kalar masu kudin ba,kawai sai ya fito daga Napep zai gwada sa'arsa a wajena ko zai dace da ya more ko yar masu kudi ce ai zaiyi auren jari.

    Yashe baki yayi tare da cewa yan mata ku bar kudinku ai kyauta na kawoku ni,kamarki Hajiya ai kin wuce a karbi kudinki,na daure fuska tare da cewa kaga Malam karbi kudin ka ban son kinibibi ina da aure ni koma meke Ranka ka Adana kalamanka,yace yar yarinya dake yana dariya yace sake magana yan mata ido ba mudu ba ai yasan kima,tsaki Naja nace karbi da Allah kar mijina ya ganni a nan,yaki karba yana kallo na,muna haka sai ga motar su Abbi ta shugo tare da mata ciki manya biyu da yan matan nan dai abokan fada na su Uku, tare da dattijai su Abbi su biyu suma.

   Cikina ne ya wani kulu kulu Sabo da tsoro nan take gumi ya keto min,na cillawa me Napep kudi Naja hannun su Meenat muka bi su ciki domin tuni sun shige da motocin su ciki,gashi basu san Code din kofar ba,nima ban sani ba Ma'eeshah ya rubutawa a paper jiya yace ta bani,dole suna jikin kofa suna jirana,a hankali na taho,suna bina da wani banzan kallo wanda saura kadan na fara Kuka,wata a Cikin manyan matan ta ja tsaki tare da cewa an kawo mana irin jaraba kuma dangin matsiyata sai abinda muka gani,Abbi yace taki yin Sauri ma kamar gidan ubanta,Yan mata a ciki daya tace zaku gaji da kallo indai wannan Villager din ce bata da kunya wlh zaku ce ni na fada muku,Dayan Babban yace wa zata Yiwa ai ko masa a saketa dan ubanta,cikin manyan matan wacce batayi magana ba tace dallah ki Sauri ki bude mana ko gidan uwarki ne wannan dole a maida ita Family house ko dan ta koyi Ladabi,nan take Abbi yace a'a ba yanzu ba tukun na gama planning idan lokaci yayi zakuji.

   Ni kuma jin matar nan tace ba gidan Uwata bane jin za a zagi Ammah ta yasa zuciya tazo min wuya,haushi ya kamani gani dama da saurin fushi ni ban fiye jure a fada min magana a gabana kuma ace na danne ba zai wahala,ana fada min nake tunzura nima sai idona ya rufe ko za a kasheni sai na rama.
   Ina zuwa gabansu na bata rai nasa hannu zan bude matar nan ta dungure min kai dan ubanki baza kiyi Sauri ba,a fusace na juyo tare da maka mata uwar harara ba ruwana ko uwar Aayance ni ban sani ba kawai kasa dannewa nayi,aiko yan matan nan da kadan suke jira suka fara salati suna zuga tare da cewa kun gani ko ai mun fada muku to wlh nan gaba ko marinta kukayi sai ta rama,Abbi yace Dan ban tan ubanki baza ki bude ba,aiko na kara harzuka kawai na fasa budewa Naja hannun su Meenat na juya inda na fito ina Tafiya a hankali cike da gadara ta nima,maganar duniya sukayi ko ehem basu ji muryata ba,ina ji suna lalalala lallai dole a dauki mataki ba karamar yar iska bace wannan magana ma tafi karfin tayi,shima dayan yace wannan tantagararriyar yar iskar tsagera ce,bata da kunya bata da mutunci kamar mu ta iya yi mana haka,ka duba Nafisa da Bilkisu babu abinda ba a musu ba Amma yaran nan basa iya daga mana ko yatsa,ka duba Shema'u zagi duka duk taci a gidan nan Amma ko daga ido bata taba yi mana ba sai wannan yar matsiyata,talakawa ma sauran kuwa daya aura daya ke yayan masu kudi ne dama su basu gaji tsiya ba,Abbi yace bar shegiya zata shigo gidan ne sai tafi kowa wahala da kanta zata bar gidan,nan take suka kira Aayan yayi Sauri yazo,minti 10 sai gashi a mota daya shike Driving,yana shigowa ya hango mu can gefe a zaune,gashi dama kuma Business din namu yace a gaban danginsa a nuna soyayya,ni kuwa na manta ma tunda ban gani a kasa ba,ba a biyani kudin ba,banci na ta da kai ba,nan take ya canja fuska ya koma nishadi da farin ciki ko kulasu baiyi ba sai wajena da ya taho yana wani murmushi muna hada ido sai ya maka min harara,yana zuwa kusa dani ji nayi kawai ya riko hannuna,na fisge hannuna yace  film za ayi gasu nan zasu gane, nace can da matsalarku abinda ba sanin darajar business kayi ba ina ruwana ni, zan mareki kin san Halina wlh idan kika bari suka gane sai na yagalgalaki na koreki kuma,ni kuwa nasan zai iya mun samu rufin asiri ai ba shiri na mike,ina murmushin yake ya dauki Ma'eeshah a kafadarsa kamar yarsa yana mata wasa wai dan ace ana soyewa da mata kannenta ma ai kamar kannensa,Meenat tace a ranta kaga makirin Namiji a fili kuwa ya jawota kusa dashi itama ni kuma hannuna na cikin nasa,Maeesha an samu sake har wasa take da gashinsa a ransa yana ta jin haushinta tana lalata masa gashinsa me kyau yasha gyara.

     Muna zuwa yace ur welcome, Abbi karami barka da yini,Aunty ya kuka tsaya a nan,My life bude musu mana,Abbi ya fara masifa wannan har kake kira da ur life yarinyar da ta zage mu taci mana mutunci yar Iska,Aayan ya bata rai a ransa fa Amma don yasan Halina ba tin yau ba bana iya hakura idan anmin abu,yasan tabbas zan rama indai sun min tunda yasan halin danginsa,a fili yace ko baki ganesu bane Dear,nayi shuru ya mintsini hannuna na saki murmushi tare da cewa ban ganesu ba naga suna fada ne tunanina kar suzo har gidan mijina suyi min sata,aiko nan take suka yo kaina ubanki zamu sata,yan matan nan sunfi kowa,Abbi yace Kafura da fuska kamar ta mage,na faki ido na Galla masa harara,yace wlh wlh sai nayi maganinki,na kara fakar ido na Galla masa harara tare da juya idona sannan na murguda baki,karaf a idon Aayan,a gabansu bai nuna ya gani ba,sai da muka shiga ciki na zame hannuna Meenat ta rada min ki kirashi da Babyna,nan nace Babyna kawo min Ma'eeshah taje ta huta nasan kasha nauyi,ya miko min ita tare da zama kusa da su Abbi,ni kuwa ko ta kansu banbi ba nayi Bedroom abina har suka gama fada da jaraba wa Aayan ina jinsu wai ya auro gadon rashin mutunci bani da tarbiya,shi kuma yana basu hakuri suka dai gama mitarsu suka bar gidan cikin bacin rai dama wai a haka ganin Amarya suka zo za ayi gulma.

     Suna Tafiya ya haura Samansa yayi wanka da komai tare da cin take Away dinsa har Bedroom dinmu ya leko yace zo ke,lokacin wayata kawai nake dannawa ina game,su Meenat sun Tafi Islamiyya.
    Na mike na bi bayansa har palo,yana zaune na durkusa a gabansa ya dauki dogon lokaci sannan yace ke baki da kunya ko? Ana tausayinki ba kya jin tausayin kanki,baki na turo gaba,yace ko nima zagina zakiyi,baki da hankali ai ko ba komai sun girmeki,kuma kina Matata ko darajata ai baza ki raina min dangi ba,nan gaba ke zaki sha wahala awajensu ni ba ruwana iya kaci idan sunce na rabu dake nayi musu abinda suka ce,kamar Abbi zaki kalla ki harara Kanin mahaifina ne fa kamar mahaifina ne.
   Bazan hanaki yi ba tunda ke zasuyi ma ba ni ba,kinga ba ruwana,baki na kara turowa Hawaye yana zuraro min sannan nace haka kawai shike nan ni bani da yanci,ni mene baka Yiwa Kannena ba ashe da dadi kenan yanzu nayiwa naka kaji Haushi,sannan su zagar min iyaye sai nayi shuru Sabo da bani da zuciya ina...... wlh zuciyata bata mutu ba,babu wanda zai zagar min Uwa na kyaleshi ko shi waye,kai ko ni wlh Bazan dauki zagi da Duka ba sam bazai yuwu ba,bari kaji ko kai da bana so aka zaga Bazan kyale ba tunda yanzu kaine kake ciyar damu ko dan darajar wannan idan naga me cima mutunci sai inda karfina ya kare,sannan da kake cewa ana tausaya mana ai dai banzo gidanku nace ka taimakamin da sisinka ba bare kace taimako nazo nema,hasalima ni kake zalinta,tunda duk Aure ai aure ne ba banbanci,da kudinka Allah ya hore ma ka hana iyalinka sai daí ka bawa na waje ina zaka ci gaba ai baza suyi albarka ba kuma baza kaga dai dai a komai naka ba,tunda kana da Halin siya min Nama ka makale kudinka,ko kwai dan kwai ma babu,bare su madara me kwakwa ba daya bare kanwar biyu,sabo da son kudinka ko tsire baka siyo ba dan ka kyautatawa iyalinka,sai kudina na ma da suke hannunka tunda har yau Banga an fara bani kudin auren Business ba,ai in kana so nayiwa danginka biyayya to ka tabbatar sai ka karbi aurenka kace ba na kasuwanci bane tunda kai kace ba aure bane to mene hadina da wasu danginka da zan girmamasu,dadinka nake ji da zan mutunta su? kuma ko ba komai suma ai basu mutuntamu ba ko mu ba mutane bane bamu da daraja sai ku Sabo da kuna da kudi,Deal ne tsakaninmu zancen mutunci bai taso ba,a fara biyana kudi ayi a gama auren,idan kuma ka soke kasuwanci ka zabi daya ciki sai ka min komai da Allah yace miji ya sauke a kan matarsa nima zan sauke nawa,amma sai kazo kwata kwata ana abu ba akan dokar Allah ba mun tsara tamu dokar kace zaka zo da wani zance wlh kama zo da da bidi'a ....kau.....nake jin maruka ta ko ina a fuskata inba a lokacin sai da na dena gani kaf bana jin magana, yayi niyyar ya dinga ball dani kawai ya kyaleni da iya marukan da ban san adadinsu ba,na mike kuwa ko Hawaye babu na karkade jikina irin na gama kangarewa din nan nace Bazan fasa fada ba idan kana so na bisu wlh sai daí ka soke kasuwanci muddin kasuwanci za ayi wlh basu Isa ba ko su waye a danginka in dai sun min sai na take su nima,ni so nake ma ka kaini can Sabo da mufi goge raini,,na tattare skert zan Arce ya biyoni na kwalla kara nayi saman Bene da gudu,ya biyo ni a ransa yace yau sai ya hallaka yarin nan yana magana tana yi,ya auri mata manya manya ma magana basa iya yi masa sai wannan yarinyar, Ina gudu ina hakki nace dan Allah kayi hakuri karya nakeyi Bazan iya ba zan bisu sau da kafa,wayar chager naga ya fisgo ai na koma kasa da gudu garin gudu na fadi yazo kuwa cike da bala'i ya juya daukan wayarsa data fadi na mike idan guduwa zanyi kamani zaiyi,kawai ya sunkuya zai dauki waya na Arce ,nasan ina tsayawa zai ci Ubana, ina shiga su Meenat suka firgita suma sun dauka wani abu ne, jikin kofar yazo yace zaki fito ne,nace ni dai na fada ko gobe suka zo sai nayi musu,kwanan nan zan fara taka kowa, zaki fito ne sai na yankaki,nace ae idan anyi zuciya a biyani kudina,yace ko ina bayarwa ma Bazan taba baki ba,da na baki gwara na zubar kuma ko ina Tafiya ina taka kudi Bazan baki ba,shuru nayi masa Sabo da ina tsoro kar ko yar dubu daya ya hanani da me zanyi Cefane ko kudin Napep na schl din su Meenat.

    Meenat ta kalli fuskata tare da cewa Sis dama ke ai akwai jure duka, shawara kawai mu daina fita ko palo sai in baya nan,Nace baki da hankali ai gwara ana damawa damu idan ya gano tsoronsa muke ji raina mana hankali zaiyi,ni yanzu da kike gani na Salo Salo zan dinga rikida ina canjawa tunda naga ba kudin nan za a samu ba bare idan na samu nace ya sakeni kinga gwara kawai mu samu na lallabashi mu samu kudin siyen kayan daukan wanka muci mu sha mu baza gayu,idan ya maidamu Family house a haka mun gama yawo kalli bamu da kayan sawa na kirki,

Meenat tace ni tsoro nake ji Sis bazan iya ko daga musu yatsa ba wannan uban kudi da suke dashi haka, tsoro ma nake ji kar a sakeki,nace ke ki daina min fatan saki yanzu gidan nan shine rufin asirinmu,ni ina son aurena wlh rike abina zanyi da daraja,gwara kawai nayi dan samun lada tunda kudin nan naga Alama ba sune komai ba, Meenat ta dinga dariya tace kowa ya tuba dan wuya ba lada Sis.

   Ke na hakura da kudin na koma kama mutuncina ni kam harkar auren nan zan dawo na gaskiya,Idan ma ya sakeni Allah yagani,Meenat tace Good yanzu za a fara zaman aure kenan? Nace ae,tace to ai kin batawa mijinki rai sai ki fara zuwa ki bashi hakuri,haka ne miko min Katon hijab din can na Ammah nafi daraja a idonsa,hhhh Meenat tace yo wacce daraja zakiyi kinje wajen miji da Hijab ai kamata yayi ki dau wankan sugar,baki da hankali Meenat cewa zaiyi sonsa nake,ni kuwa ba sonsa nake ba bautar aure zanyi,so kike ya rainani ba class yana kallon tsaraici na,kin manta jiya da kika bude cinya kina lashe lashe a gabansa fa,to ai ni mantawa nayi dashi kuma in Allah ya yarda daga yau na koma yar gayu nima,ko kayan dadi ne sai nayi yanga zanci,kuma bazai kara ganin jiki na ba,Meenat ma ba hankali tace kin san kuwa Maza ba kunya garesu ba zaneki zaiyi kuma ta kalle miki jiki,nima nace ai yanzu zan fara bawa jikina tsaro.

     Sadaf sadaf na fito da shirgegen Hijab dina,ba kowa a palo na tafi ina taku na  nutsuwa irin nayi hankali fa,baya palo nayi ta Maza na haura samansa,har hadadden Bedroom dinsa na kwankwasa tare da Sallama na leka kaina ciki,na hango abinci lafiyayye da abubuwan dadi iri iri a gefensa yana ci yana aiki a system,Na murda handle na shiga,da mamaki ya kalleni yanda yasan tsorona na iya fitowa yanzu duk rashin kunyar da na masa,Har gabansa naje na durkusa tare da cewa sannu Aayan dan ni ba ruwana da wani yaya ko waye waye kawai Aayan tunda ba Masoya bane akan me zan boye suna.nace dan Allah kayi hakuri kaji wlh wasa nakeyi zanyi musu biyayya Bazan kara ba ni dai mu zauna lfy,da mamaki naji yace kin kyautawa kanki idan ma baki ba ke zaki sha wahala,ki nutsu ki san me kike abinda Family dinmu sukeyi bana wasa bane,har yau baki san dalilin auren Ki da na yi ba,kiyi abinda nace zan biyaki kudinki ko wani kike so ki fada min muna gamawa sai na warware aurenmu na aura miki wancan a ranar tare da kudade,nace to Alhmdllh ai ta kwana gidan sauki,amma da ni nufina zanyi bautar aurena tsakani da Allah,no..no..no Need kawai kowa yayi rayuwarsa cewar Aayan,nifa ba wai nufina aure kayi min wani abu na mata da miji ba ai na rigada nasan baza ka iya Yin komai ba,baka da lfy, a firgice naga ya dago tare da cewa a ina kika sani?nace ranar dana fara ganinka tare da Abbi time din da ka fadi nazo taimako ka min duka duk naji me kuke cewa,oh shine kika zo ki fada min kenan? karki jawo na goge miki hadda yanzu ki gani zan iya ko Bazan iya ba,nace ni ba haka nake nufi ba ina magana hankalina baya jikina sam yana ledar dana ga kayan tande tande a ciki har dogon wuya nakeyi haka nake ni Allah ya zuba min kwadayi a rayuwata tun ina karama Ammah bata yawo dani Sabo da babu dama naga me talla sai na mika hannu a bani,ko kuma nayi ta kuka sai an siya min,ko gidan biki idan akaje dani to fa kowa sai yasan kwadayi na,Ammah watarana sai dai ta goyani a baya tasa Zani ta daure ni har hannaye tam,sai dai nayi ta kuka a baya ina kallon masu tallan kayan ciye ciye.

    Yana satar kallona yanda nake kallon abin ledar sai yace bari ya gwadani,Muryarsa naji yace ko zaki ci ne? Da Sauri nace a'a na gode ni bama na ci,murmushi yayi kana yace to shike nan dama na koshi zubarwa zanyi dasu,da Sauri nace kawo na zubar ma,a'a kyale idan zan fita zan zubar da kaina,Nace da dai ka kawo na hutar da kai kamarka dan gayu ka tsaya zubar da shara ai bai dace ba wannan sai irinmu,gaskiya ne dauki to kije dustbin kasa ki zubar,da Sauri na dauka tare da cewa sai da safe,yana ta jinjina kwadayi na don yasan ba zubarwa zanyi ba,kuma dama shi din yaga damar bani ne ganin yanda nake shi yasa yace na kallon abun shine tace a zubar,ni kuma tunanina wayo nayi masa na fita ina dariyar mugunta irin na cuceshi.

   Ina shiga Bedroom na bawa su Meenat labari suka ce lallai Sister kin iya wayo,muka sha ice cream,Nama,lemo da wani chips yasha hadi.
   Tun daga wannan Rana bamu kara ganin Aayan ba ko kamshinsa har muka kwashe sati biyu mu kadai muke rayuwa a gidan kuma sisi bai bar mana ba haka ya tafi,a bakin masu gadi naji wai yana Abuja,nima ban damu ba sam tunda Allah yasa ina dan boye kudi a hannuna kuma na saba da irin wannan ni dama tun ina yarinya a wahala na taso da tunanin ya zamu kare.

     Sati daya shuru,biyu shuru,kudina duk sun kare gobe ma su Meenat basu da na zuwa schl nayi Cefane dana hannuna,muna zaune a palo na gama gyarawa Ma'eeshah kai na fara Yiwa Meenat kitso itama, door Bell muka ji, nace Ma'eesha je ki bude ta mike da gudu tare da bude kofar gani mukayi an mako kofar tare da ture Ma'eesha ta fadi gefe bakinta ya fashe,ba kowa bane face yan matan nan na gidan su Aayan su Uku har yau ban san sunansu ba, da sauri na mike tare da daukan Ma'eeshah ina mata sannu tare da goge mata baki da tissue,saman kujera na kwantar da ita ko kallonsu banyi ba naci gaba da Yiwa Meenat kitso,muna kallonsu suna ta jan tsaki ana yanga tare da taku dai dai muna kallo suka haura saman Aayan,da Sauri na mike tare da bin bayansu suna yanga na sha gabansu kafin su karasa bedroom din na riga su shiga ciki tare da zaro key din dake jikin kofar na rufe kofar da key na zare key din zan bar wajen suka tareni a palo dole sai na basu key dakin dan uwansu ne dole suyi abinda suka ga dama.

Kallonsu nayi sama da kasa sannan nace Bazan baku ba,a saman nan 2 palo ne ga Bedrooms har Uku kasa ma haka ku shiga duk inda kuka ga dama Amma banda dakin mijina.
   Bazai yuwu ku dauki abu ya dawo yaga babu ba ni zai tambaya,hakki nane kula da kayan me gida tare da dukiyarsa,sannan dakin nan sirrinmu ne na ma'aurata bazai yuwu dan kuna danginsa ku shigar mana dakin bacci ba salon a ga gadon kwananmu, kaina sukayo gaba daya zasu dakeni na zame tare da guduwa muka shige Bedroom muka danna key suna nan tsaye cike da mamakin kalamai na tare da rashin kunya ta Amma ba komai zasu gyara ni Allah kawo ni Family house.

    Nan take suka kira Aayan wai sunzo na zagi iyayensu,Yace su jirashi gashi nan ya dawo daga Abuja yanzu flight nasa ya sauka yama kusa da gida, 15 mnt muka ji motoci lokacin na fito daga wanka daure da towel na Sa Katon Hijab dina har kasa na fito don tunanina matan nan sun tafi sai na gansu a palo suna ta faman kallon kida a TV, dariya suka kwashe min da ita tare da cewa kaga yar kauye wai miji ya dawo Amma jibeta yanda ta Fito suna ta faman yi,ni dai ban kulasu ba na bude kofar da naji kara,wow yanda ya wani mugun kyau ba a cewa komai kamshinsa na tashi,Kallonsa na tsaya yi sai da yace Madam ya akayi ne yana murmushi ganin idon danginsa a wajen Amma nasan da basa nan ko kallona bazai yi ba,sai kallonmu sukeyi ganin idonsu yace ko Hug babu ya miko hannu zai rungumeni da Sauri Naja baya tare da cewa nayi fushi ai ka bata min,nan kuwa kawai ban so ya taba min jiki a wani auren business,Baki ya tabe sannan yace ni ko?yanda ya dage girar ya masa kyau,muryarsu muka ji sunce ur wlcm ya Aayan, tnx kawai yace musu yayi sama abinsa na dauki jakar nabi bayansa sama,su kuma suna ta tabe baki,ni na mika masa key ya bude dakin,Yana shiga Bedroom na ajiye masa jakar zan juyo naji yace me ya hada ku? Bakya jin magana wato ke ko? Duk abinda zakuyi karki sake kuyi min kokawa a gida tunda nasan kun saba,nace ni hauka nake na hada jiki dasu ai yanzu na girma Antynsu ce ni ai yanzu,zuwa sukayi tare da make min Ma'eesha harda fasa mata baki daga ta bude musu kofa,suka shigo har sama zasu shigar ma daki ni kuma naga bai dace ba ai nice matar gidan in banda an raina ni taya za a wuce dakin mijin mace kawai wai zasu dauki abu shine na kulle kofar na fada musu bai dace ba,ko ba komai idan wani abu ya bata ai ni za ace,Murmushi ya saki tare da cewa ashe kina da hankali,ina dashi mana ai kaine dan baka sanni ba kake tuna nin yarinya ce ni,ko magana bai kara yi ba ya wani shige toilet abinsa nima nayi waje,suna jiransa ya fito ya dauki mataki a kaina,amma shuru yama manta dasu gaba daya yana bacci abinsa.
    Suna komawa gida suka fadi karya da gaskiya wurin kakarsu Hajja nan take tayi masa waya lallai ya dawo damu Family House a yau ba sai gobe ba.

    Kawai ji mukayi yace mu hado kayanmu Driver zai maida mu can gidansu zamu koma da zama, haka muka shirya har kuka nayi a boye dan nasan shike nan mu kuma,Har part din Aayan na gidan Driver ya kaimu,dama na taba zuwa sau daya lokacin dana kai masa takarda ya nemo min Yarima abokinsa akan Aikin Ammah,part din ya tsaru harda na masifa,sama da kasa kasa 2bedroom da palo sama ma haka sai kitchen da store ya hadu iya karshe don yafi gidan da muka bari kyau da komai a kasa still muka zabi daki daya abinmu mu Uku,na duba kitchen da store wayam ba komai sai Indomie,kayan tea dana Coffee sai kayan sha dana gwangwani shirye cikin Fridge.

   Yanzu za a fara rayuwar fa.







AsmaBaffa
[1/8, 1:24 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

    KASUWANCI NA




            36-40




Official




By AsmaBaffa




      ZAINAB ATIKU SALAMA and MRS Hamza wannan page din sadaukarwa ce gareku.

   Jinjina gareku
HEENDU
RAMCY MAKE UP
MOMMYN ZAHRA
HAJIYA ABOU
AUNTY SUMEE
HUMAIRA
ZULAIHAT
SAFEEYA AHMAD
   Ina muku fatan Alkhairi tare da godiya da Sharhi.

     Masu Sharhi na ko wanne Gp da wanda kuka min magana ta pc ina gani kuma zaku ganni Online wlh Simcard dina ne yake da matsala sai kun min Uzuri kafin na gyara,sako yana shigowa ina gani Amma ni Idan nayi reply baza su zo da wuri ba,kuyi min Sharhi ina gani kuma zan bawa ko wacce amsa Fatana kuyi min Afwa da Uzuri.






        Kamar an sanar a gidan Radio haka muka dinga ganin yan gidan suna shigowa mata da Maza wasu na taba ganin su wasu kuma ban sansu ba,Kowa da kallon wulakancin da suke mana,ni kuwa ko magana banyi ba ko ina wuni bance da kowa ba nima kuma na cewa su Meenat karsu kula kowa,kaf yan gidan nan sai da suka sheda bani da mutunci bare kunya Sabo da zaman kawai da nayi a kujera ya isheka amsa, manyan ne kawai suke min kallon Banza ina kyalesu Amma indai mutum matashi ne ko budurwa yaro ko yarinya indai suka min sai na mayar musu da matartani ina daga zaune abina nima kuma basu Isa na gaishesu ba bare su Sa rai da mutunci na shigo.
   Wasu manyan samari ne su Uku za suyi basu kai Aayan shekaru ba sunji labari ance musu Amaryar Aayan kyakyawace ta karshen gaske sai dai bata da kunya ko kadan,gata kuma kalar kauye ce duk iyayin Aayan ya kare a yarinya karama kamata kuma ba yar gayu ba,da sallama suka shigo bayan Sallar Isha Sabo da su Maza ne kuma suna da dan hankali,kallo daya na musu na dauke kai tare da amsawa a hankali,Ganin basuyi min kallon Banza ba yasa na saki fuska tare da cewa ina wuninku,suka ce lfy sannu Amarya ya gajiya nace Alhmdllh babu wanda ya kara magana,Sai kare min kallo sukeyi musamman wani a cikinsu kallo kamar maye hakan ma da Hijab dina,Sai ko naji yace Amarya ya kamata a mana girki muci mu ji,nace sai dai ku shiga kitchen da kanku ni yanzu sai na huta nasha gajiyar hanya daga wancan gidan zuwa wannan na jigata a Cikin mota Driver ya jijjigani da yawa a hanya na fada ina yatsina,mamaki ya kashe su abinda sun san gidan ba wani nisa da wannan unguwar Amma wannan yar rainin hankali ce wai mu shiga kitchen ma,

tasan ko mu su waye,kaji yar talakawa cewar daya a cikinsu ya fada a hankali bai san naji ba,daya kuma yace min kannen Aayan ne mu ni sunana Khaleel,ga Ameer sai wannan Mujaheed, nace good bari na shiga daga ciki,wanda ke yawan kallo na wato Ameer kenan yace a haba ko hira ba ayi ba,zama nayi kawai nayi shuru suma suna zaune sun dade sosai har wurin 8:30pm

   Sai ga Aayan ya shigo rai a bace kamar zai daki mutane kadan yake jira,suna ganinsa suka min sallama suka fita,ni kuma na kalleshi yanda ya wuce da Sauri yana bin steps,Saman bed ya fada tare da kwantawa ruf da ciki ko me yake tunani oho ko wani abu akayi masa ban sani ba ni dai,nasan dai bazai wuce matsalar yan gidansu bace ni kuma ban san mene dalili ba bare nayi wani abu a kai,shi baya kulani bare nasan matsalarsu,ban ma san ko tarihin gidansu ba sai wanda na tsinta ranar ganina dasu na farko sai kuma abinda na fara gani yanzu a gidan kamar dai shi Aayan kadai shi suke warewa basa so Amma dai ban san komai ba,duk da haka sai naji tausayinsa,naji ba dadi me ciyar da kai ace yana cikin wani Hali dole ai kaji ba dadi sai kawai na wuce kitchen,Sharp sharp na dafa Indomie da kwai kar ma yazo yasa a kwashe su ya kawo mana su garin danwake shi yasa nace bari muci rabonmu,na bawa su Meenat na zuba wata a plate na nufi dakinsa can sama a nan na sha kallon haduwa.

   Saman Bed na hangoshi a kwance ban san me yake yi ba bacci ko tunani,Aayan...Aayan na fada a hankali,a hankali ya bude idonsa tare da cewa Lfy? Abinci idan zakaci Indomie naga ka dawo daga Abuja baka ci komai ba,ko kaci? Kansa ya dago a hankali tare da kallo na ya dauke kai yace ni bana cin Indomie yanda ya fada kamar dan yaron goye a shagwabe,nace to me kake ci? Ai nasan baza ki dafa min ba bakya jin magana,fada zan dafa ma ai nayi hankali na daina, yaushe kikayi hankalin? Na daga kai ina tunani sannan nace an dade fa tun shekaran jiya, murmushin da bai shirya ba yayi kana yace Kosai nake so da kunun gyada sai danwake,nace to ai nan babu kayan yi a wancan gidan ne akwai,Waya naga ya dauka nan take naji yace a kwaso kayan dake kitchen da store na abinci a kawo masa part dinsa,wani bakin ciki ya dirar min shike nan mu baza muci abincin zamani ba,kamar yasan me nace sai naji yace shi kuka saba ci ai a gidanku idan na baku na yan gayu baza ku iya ci ba,nace mu dai zamu iya dan Allah,yace to ba yanzu ba sai watarana idan naga dama, cike da takaici nace shike nan ai,su Meenat basu da kudin Napep na zuwa schl,sannan nima dan Allah ka sani a schl,budar bakinsa sai yace ni bani da time idan kina da wani zan baki kudi ki zabi schl me araha private ya kaiki zan biya ni Bazan iya biya miki private me tsada ba,sabo da na raina basirarki, nace wai mene amfanin kudinka? Kallona yayi tare da Sa Headphone a kunnensa irin na takura masa haka na fita na kyaleshi cike da tunanin to wai me yasa ya aureni yana kallo ko kayan sawar kirki bamu da Amma ko Ya siya mana wasu to bai bamu abincin kirki ba ma sai wasu kayan sawa kawai dai raini ne ya jawo mana a danginsa.

    Ina zaune a palo sai gashi an kawo komai na girkinmu irin na can gidan su dawa gero masara etc,Kitchen na shiga na fara shirin hada gyada da danyar shinkafa tare da lemon tsami na kunun gyada,ina cikin aikina sai ga samarin nan Ameer me kallon tsiya,khaleel da Mujaheed har kitchen suka ce Amarya girki ake shirya mana nasan ganin kwakwaf suka zo kuma sun gani su masara dasu geron,dan masifa suka ki fita daga kitchen din sai suka ce wai sai sun taya ni,nace a'a bana so kannena zasu tayani,sai ga Meenat ta shigo kitchen cikin English wears riga da skert tayi kyau Sabo da wanka tayi tare da fesa kwalliyarta da ta saba,aiko suka bi ta da kallo sunga me kyau da diri,ni kuwa a hijab nake baza su gane komai ba sai fuskata da take da tsananin kyau,Meenat tace Sis kawo na hada waken muna ta aikinmu tare suna kallo don zama sukayi a kitchen din wai sai an fara girkin sunci sunji,Ina tsoron tambayarsu gidan da ake markade na hakura mukayi a blender sai suka ga kosai mukeyi da kunun gyada,basa cin kosai su Amma suna shan kunun gyada,Aayan ne ya fito daga dakinsa Ya taho kitchen da niyyar daukan ruwa abin ya daure masa kai ganinmu gaba daya da rida ridan kannensa a kitchen muna yar hira jefi jefi sai tambaye tambaye suke mana akan girkin nan,ina tunanin zanga ya bata rai ko yaji haushinsu ko Ya musu magana su fita Maza bai dace su dinga shigewa mace me aure ba Amma sai naga ko a jikinsa ruwansa ya dauka tare da ficewa.

  Muna gamawa naga sun zaro cups zasu fara eba,nace ku tsaya mijina fa? nasa ne dole sai na fara ebar masa,Ameer yayi murmushi tare da cewa Amarya ai ko nasan ne muna da yancin shigowa mu eba ko shi bai Isa yace kar mu eba ba,Kallonsa nayi nace to ni na Isa dan shi yasa ni nayi masa sai na ebar masa,Na gano ba so suke su sha ba takura min suka zo yi don kamar ma turo su akayi su Sa min ido.

    Sai da na dauki wani jug me kamar flask na zuba ma Aayan, meenat bata ce mana komai Sabo da na hanasu magana akan dangin Aayan kosanta take soyawa,naje na ebarwa Aayan na ebar mana namu tare da kai mana Bedroom,na dawo lokacin Meenat ta gama soya kosai muka gyara kitchen sannan nace to zaku iya eba dan bakar jaraba suna palo sai da suka shigo kowa ya eba a cup suna sha duk wanda nayi suka shanye ba ruwansu da tambaya,Khaleel ma da yafi su rashin kunya Na Aayan yazo wai zai kara a ciki ya masa dadi, nan take na dauke komai tare da jerawa a wani tire me kyau sannan nace bazai yuwu ba kunsha rabonku nayi gaba na Barsu a palon,sama Na haura tare da knocking sannan na shiga yana zaune saman Sallaya yana addua na ajiye masa zan fita naji yace wait,ina tsaye ina jiransa ya gama tare da shafawa sannan naji muryarsa yace Zauna,can gefe na durkusa yace me suka ce miki su Ameer? Na bashi labari har abinda nace musu,yace to daga yau ko me suka ce ki musu kiyi musu ko nawa ne ki basu,nace ni Allah Bazan basu ba,nasha wahala kace na basu,to ba nawa bane nace ki basu,to me ya hanasu suyi auren su ko su tafi wajen iyayensu ni na haifesu da zan dinga wahala suna raina min Hankali,ina matarka tunda kannenka ne ai kamata yayi su dinga girmamani kuma sai suzo kitchen su tsaya min a kai ai duk kai kake basu kofa,kamar wanda ke jin tsoronsu ni ban gane maka ba,kace rannan na dinga ramawa yanzu kace na daina na bari kenan su takani ko? Shuru yayi bai ce komai ba,sai can yace nima  kinga ban san me ke damuna ba ths month ina jin bani da lfy ni ban san ma meke damuna ba gaba daya,ina ke maka ciwo? Yace babu a jikina nake jin kawai da matsala bani da lfy ban san ya zan iya fada miki ba,tunanina mutuwa zaiyi sai na fara hawaye nace ni dai karka mutu dan Allah irin Ammah yanzu wa zai bamu abinci gashi muna ci muna koshi,kallona yayi da mamaki shi da yake bamu abincin talakawa Amma har dadi nake ji a haka ina fata kar ya mutu Sabo da wannan.

    Miko min abincin,mika masa nayi sannan na zuba masa da Sauri wai dan kar ciwo ya kamashi ya mutu,ya karba a hankali yana cije lips ni tunanina ko jikin ne yake jin bazai iya karba ba,sai nace tsaya tsaya na karbi cup din nasa spoon a ciki ina juya sugar din sannan na rike masa a hannuna nace to bari na rike ma a haka kai kuma sai ka dinga sha ko na baka yanda nake wa su Meenat tunda baka da lfy? Banza ya min tare da bata rai yana ta fushi kuma yanzu kamar yaron da aka Zane,Sai ji nayi yace rike abinki ki sha,na fasa, yi hakuri gashi rike abinka Allah Sarki sha abinka kaji,ni kar na baka? Yace ae bana son naki, nace to gashi nan ni na tafi ma,na mike tare da bar masa dakinsa,na rigada na saba da Yiwa su Ma'eesha irin abun Yara idan zan basu abinci ko ina basu sai na dinga ta lallabasu shi yasa,ko ina basu ta dole.

     10pm muna daki muna karatunmu ya shigo Bedroom dinmu tare da cewa zo,Maeesha tace Hi Uncle,murmushi ya mata tare da daga mata hannu,Meenat ma ta gaisheshi ya amsa da sakin fuska kadan,Hijab dina na Sa tare da binsa a baya har Bedroom dinsa yana Saman Bed ina kasa a tsugune yana ta faman cika yana batsewa ga jarabar takama,yace  gobe ki shirya 8am kuje ku gaisar da Hajja kakarmu ko me zata ce karki mayar mata da martani kiyi biyayya,nace to Insha'allah,yace muje yanzu wajen Abbana,nace au kana da Baba mahaifi? Yace of Course ai ni dan gata ne Umarninsa nake bi,murmushi nayi nace kuna kama? Yace mene kika tambaya? Idan kuna kama to nasan Babanka ma me kyau ne ko Ummanka ka biyo?ke dadina dake shirme,Ummanka ta rasu ita? Ya daga kai tare da cewa kuma nafi son Abbana ba tun farko,Nace tab ni kuwa nafi son Ammah,Abbanka yana Sonka kenan da yawa gani nayi yana ta farin ciki kawai akan nayi zancen Abbansa lallai yana sonshi,fuskarsa na leka nace Dan Abba zan dinga ce ma yanzu,muje na ganshi ma zan dinga kai masa abinci,yace ai ba komai yake iya ci ba,bashi da lfy ya fada kwalla kamar zata zubo masa,nace eyya ai Insha'allah zai warke ne,lets go kawai yace min,nabi bayansa falau falau da hijab muna ta sheka uban tafiya yana gaba ina bayansa har muka je wani building a Cikin gidan katafaren me kyau,ciki muka shiga kafin ma mu Isa inda zamu hau steps duniya ce guda ko ina kuma Securities ne masu tsaron Daddyn Aayan, sannan muka haura sama can wani Bedroom shima nan duk sune suke tsaro har cikin dakin,saman Bed na hango shi dattijo kyakyawa irin Aayan suna kama sosai sai daí Aayan ya fishi farar fata,sallama mukayi masa da mamakina naji ya amsa yana murmushi tare da cewa My Son kazo ke nan,Aayan ya karasa jikin Bed din tare da rike hannunsa yace Daddy ya jikin? Alhmdllh Son yanda kasan jikin kullum haka yake ina so na taka kamar kowa Amma bazai yuwu ba,kana gani komai sai dai ayi min haka nake ba inda ke motsi a jikina sai baki na,addua kawai itace Mafita tunda ba inda ba aje ba ciwo yaki ci yaki cinyewa,to hakanma mun godewa Allah.

   Ina mamaki yanda yake fes haka cikin koshin lfy ace wai baida lfy komai nasa baya motsi gashi shar dashi muryarsa ras haka,a hankali naga Aayan ya rada masa magana a kunne nan take ya fara murmushi tare da cewa Yata matso kusa ya kika tsaya nesa,Da Sauri na karasa gaban gadon tare da durkusawa har kasa nace Ina yini ya jikin?Yace Alhmdllh,nace Allah kara lfy,Ameen yata Gashi nan sai kinyi hakuri kin ganshi baya jin magana na dade da cewa ya kawo min ke sai ya dinga min hanya hanya,Murmushi nayi ina jin kunya nace ai yanzu ya kawoni kuma kullum zanzo ba sai ya kawo ni ba yanzu tunda na gane hanya,Murmushi yayi tare da cewa na gode Allah ya muku Albarka,ya albarkanci aurenku ya baku zuria ta gari,Ya sunan yar tawa nace Mufeeda,Alhmdllh naji ance da kannenki ko?nace ae yace to Allah rayasu ya musu Albarka nace Ameen,Allah yaji kan mahaifiyarku nace Ameen Daddy, ki kara hakuri kinji,zaman gidan nan sai hakuri,wannan dan nawa baya ji kin ganshi ina fama dashi sai kinyi da gaske saurin fushi gareshi ga zurfin ciki,ki rike min shi da Amana yata kinji,nace Daddy ai shine sai ya dinga fada yana fushi, Dariya yayi sannan yace to zan masa fada,nace to Daddy,Harara Aayan ya zabga min nayi shuru dani,Mun dan dade a dakin Aayan suna ta hira sannan yayiwa Daddy sallama muka dawo part dinmu,na wuce dakinmu shima yayi samansa.

    Cikin dare 2am na farka da ciwon Mara sosai naji kamar abu ya zubo min a pant,mikewa nayi da Sauri na shiga toilet,sai naga period nima na fara dan ban taba yi ba sai yanzu,Meenat kanwata kuwa ita tun tana Jss 2 ta fara dama ta fini kiba, fitowa nayi tare da tashin Meenat nace Meenat tashi ki bani pad nima na fara period,cikin magagin bacci tace Sis ta kare tun last month wacce kika siyo min na karar da ita,To fa yanzu ya zanyi kenan,ki Sa tsumma kafin gobe,ke da rushing na fara fa wlh tsumma bazai daukeni ba kinji yanda yake tsiyayowa kuwa,to yanzu ya za ayi kenan,nace bani dankwalin tsohuwar a tamfar nan taki na Sa naje Wajen Aayan ya san ya zaiyi dani,Meenat tace baki jin kunya? Kuma kin san bazai je ba sai dai yasa me gadi,a'a zai iya karbo min ko wajen yan matan gidan nan ne kema kin san Bazan iya kwanciya haka ba gashi dare yayi dole tunda lalura ce kuma yasan mata sunayi ai dole gunsa zan je.
   Haka ne kam jeki to muji,nan na karbi karamin dankwalin na koma toilet tare da gyara jikina don nasan kafin naje sama Na dawo na bata kayana ko ma ya dinga saukowa saman tiles.

   Cike da tsoro na masa knocking shuru har sai da nayi yafi sau goma sha sannan naji yace Am coming yana jan tsaki ya bude min kofar daga shi sai wani dan tight short karami ko riga babu a jikinsa,daki ya koma nabi bayansa Sabo da ya kunna light din haske ya gauraye dakin,lfy ciki dare? Na fara ina ina uhm...uhmm..na juya baya tare da tamke idona kawai na maze kamar bani na fada ba nace ehmmm wai..Wai,yace to fitar min tunda baki da abin fada,da Sauri nace period na fara kuma bamu da pad gashi dare yayi ko zaka karbo min wajen kannenka na karasa tare da matse idona kam na juya masa baya.

    Tsaki yaja tare da cewa sai ki bari sai gobe kya siya ni me ya shafeni a nan fitar min a daki na zata wani abu ne,Marairaicewa nayi ina rokonsa dan Allah Dan Abbansa ka amso min pls haba Na Daddy,kallona ya tsaya yi yanda nake shagwaba kamar yarinyar yaye, hannu ya daga min hey..hey Hold it thr ban son shirme see u ko kunya baki ji kina min shagwaba ya fice fuuu ya barni,murmushi nayi tare da cewa oho dai ni dai ka karbo min shike nan.
     Yana fita na fada saman Bed dinsa nace sai na more naji dadinsa yau dai na dinga birgima a kai ina tunanin zaman da zamuyi wanne Hali zan aro na daurawa kaina dan naga karshen yan iskan gidan nan,tsawa naji keee...Ban san sanda na fado kasa ba dan na manta a Bed dinsa nake,yace Iskancin naki har ya kai Bed dina nan take ya bude wardrop tare da dauko sabon bedsheet ya jefo min tare da cewa cire min wannan kazantar zaki shafa min a Bed shimfida min new, ban bata ma bafa kalla ba komai a kai fa,i wl slap u,ba shiri na cire wancan na shimfida masa wanda ya bani tare da dame masa yayi kyau,wani turare ya miko min ungo fesa a saman Bed din,haka na fesa,yace to jeki da wannan ki wanke min gobe ki dawo min da Abuna Kazama,nace haba Ranka ya dade ka rage irin wannan ni fa matarka ce Amma kwata kwata baka kyautata min,ko Auren business ai ka bari dai mu rabu lfy Amma ba komai bani abun na tafi,naje sunyi bacci ban samo ba,To su manyan matan su Abbi fa? Ko lokacinsu ya cika basa yi su? Baki ya tabe tare da cewa bama shiri taya zanje nace su bani sun san ke zan bawa baza su bani ba,kuma dare yayi bare a siyo,sun tsofe ma wanne period zasuyi ai sai yayansu, nace to ni yanzu ya zanyi na fada kamar zanyi kuka ina doka kafafu,tafi ki san me zaki Sa sai gobe,ni Bazan tafi ba ya kake so nayi dan Allah,tunda farko ne ai bazai miki da yawa ba kije kawai,nace to ni nawa ba haka yake ba kana ta sani ina fadar badala da rashin kunya a baki na,baka san yanda nake ji ba idan ina ambata irin wannan lafazi na Badala a gabanka, murmushin da bai shirya ba ya saki,oh nan kunyata kike ji kenan,wlh da kyar nake iya magana lalura ce ta kawo ni dan Allah a san yanda za ayi dani Na Daddy Allah dai yaji kan Mommynka  ya dauraka akan makiyanka,jin nayiwa iyayensa Addua sai naga ya saki ransa kamar wanda aka Yiwa Bushara da Aljanna yace to yanzu ya za ayi kenan? A raina nace na gano lagonka,nace babu 24hrs ne a Kano?Yace da dai Abuja ne sai a samu kuma kinga 2am ba kyau fita ko fitsari tsakar dare nace haka ne,amma muje mana wajen yan matan ka rakani ni zan san yanda dole ma su bani.yace to muje a Cikin wardrop ta jikin Bed suke ajiyewa,nace an gama muje.

   Tiryan tiryan muka je har kofar dakin daya,yace wannan dakin Hanifa ne,ai ko na dinga knocking kamar dakina ta bude sai ta ganni tare da Aayan da har zata min masifa ganinsa yasa tayi mukus don tsoronsa suke ji,ni kuma da tsokana kawai nayi ciki da ita tare da tureta na banka cikin dakin,direct na bude wardrop Aiko na gansu a jere na dauko sinki daya na bude na kwashi guda uku sannan na watsar da ragowar a kasa nazo zan wuce na bata rai,tace wlh baki Isa ba ni zakiyiwa wulakanci har Bedroom,na kalleta sama da kasa nayi irin gwanar nan nace How Dear u zaki na min magana any how duk wanda yaji zaice na gama kwarewa da Turanci,taki Sakina kuwa,na kira Aayan Babyna da Sauri ta sakeni tana hararata na fito  nace masa muje to,muna Tafiya a hanya nace nayi fashi da makami kaga abinda baza ka iya ba,kai kullum sai ka dinga zura musu ido kamar wanda suka Yiwa asiri danma suna jin tsoronka ai da tuni ina ga kowa ma taka ka zaiyi.

   Ki shirya gobe zasu zo daukan fansa wlh harda iyayensu,nace dan Allah ina son muyi magana da kai Na Daddy Allah ya karawa Daddy lfy da nisan kwana, ina binsa a baya da Katon Hijab dina har Bedroom dinsa,ya fada saman Bed dama yasa jallabiyarsa,a hankali na zauna a gefen Bed din ina jin tsoro,ina jiran naji tsawa sai naji shuru,ina zama ina cewa Fatana Allah ya bawa Daddy lfy wlh a gidan nan,da anga yanda zaifi kowa Sonka ai da kafi karfin kula mu ma Sabo da ka zama Gold,yanda  naga Daddy na Sonka abin sai wanda ya gani inama Abban mu haka yake irin naka na furta tare da kwanciya na mike sambal a gefensa,tunanina wayo zan masa shi kuwa tuni ya san me nake nufi Amma sai ya shareni ya gama ganin iya wayon nawa me nake nufi.

    Dan Daddy wai ya maganar schl din tawa,yace anzo wajen,nace dan Allah Oga kwata kwata ka kaini schl,yace hmm yana dariya a ransa wai shi yar wannan Jaririyar zata Yiwa wayo,yace dama Arabic da boko kika shiga a hade tunda naga kinfi kokari a Arabic sai ki hada biyu abinki,nace ah gaskiya a'a nima nafi son na zama yar boko sosai,to ki zabi wacce kike so sai na biya miki,Nace to, Amma ai sai dai wani ya kaiki,bani da time ki samu wani a yan uwanki ko frnds su kaiki zan baki kudin,nace to zanje Amma dan Allah kasa a kaini a mota kaga raina ni za ayi a gidan nan,yace an gama,duk tunanina da gaske yakeyi sai murna nake yi nayi masa wayo,nace saura kayan sawa zamuje shopping Sabo da goge raini,yace nawa ne zai Isa a goge rainin?nace ko dubu goma sun isa,ya kyalkyale da dariya ku Uku dubu goma to kaya kala nawa zaku dinka kenan nace kala Uku Uku ko hudu,yace lallai dasu zaku goge rainin kenan? Nace to ni ban san kaya ba tunda ai kasan ba siya muke sosai ba.kawai biye min yake yaga iya wayon nawa.

    Dan ya nuna min na masa wayon sai yace bude can,naje na bude wata Wardrop,nan take na kusa sumewa kudi ne a jere a jere bundles da yawa na Dubu dubu da dollers,yace ebi yanda zai isheku,nan take gumi ya keto min na rude na rasa yanda zanyi jikina yana rawa na ja baya tare da cewa ni dai sai dai ka bani da kanka, ba yanda baiyi dani ba kan na dauka Amma na kasa sai ma shagwabewa danayi zanyi Kuka kudin sun tsoratani,mikewa yayi tare da kwaso Bundles goma yan dubu dubu ya zube min a gabana yace jeki dasu ai sai na fashe da kuka nace bana so ni,kamar naga wani Dodo na dinga ja da baya,yana dariya a ransa a fili yace kefa kike son kudi,nace ni ba irin wannan nake so ba,tunda kace sai na Eba da yawa to bani dubu ashirin sun ishemu komai da Komai,yace naga ai an baki kudin Sadaki har dubu dari Uku ya kikayi dasu?lokacin ai bana cikin hankalina Sabo da rashin lfyar Ammah da rasuwarta duk a nan suka kare.

    Bundle guda ya bani na yan dubu da kyar na karba na tsaya ina tunani,kafaduna biyu ya rike tare da bude kofa ya jefa ni waje tare da rufe kofarsa,Bedroom dinmu naje da murna na nunawa Meenat tace gaskiya Sis tsakani da Allah kin damemu a wannan tsakiyar dare 3am ta wuce kinki bacci sai labarin mijinki kike mana ki kwanta mana ki huta,ni dama idan labari na Cina to komai dare sai na tashi mutum na fada masa,bayan na shirya kaina duk sun koma bacci har na kwanta nima na tuna ban fadawa Meenat labarin Daddy Baban Aayan ba.

    Tashinta na fara yi Meenat Meenat ku tashi kuji banza suka min nace wai ina magana kun rainani ko,muna ji ki fada mu wlh bacci muke ji ke bakiyi ba kin hana kowa yi,ina basu labari suna uhm..eh...to...har bacci ya kwashe mu,kafin asuba wayata tayi kara ta tasheni ban dauka ba Amma sai na tashi Meenat,kawai sai ta fashe da kuka  wai na hanata bacci,nace to yi shuru kwanta jaraba bakwa jin maganar Ammah tace kuyi min biyayya Amma bakwa yi,Maeesha ta farka itama tayo fitsari muka koma bacci,ni dai banyi wani baccin kirki ba sai na dinga tunanin   Mijin Kasuwanci na.
   
   Washe gari da Safe lafiyayye tea na hada mana Sai kwai na hadashi murtuk dashi naga banza ta fadi irin muci rabonmu kafin yasa a kwashe mu koma Koko,sun sha Uniform dinsu ni kuma doguwar riga da dan hijab karami,tun Safe yan gidan suke ta buga mana kofa ina ji naki budewa,bugun duniya naki budewa sai ma kara Sa lock da nayi,Ina jin Abbi yana zunduma mana ashar akan naki budewa yaransa kofa,wai nice ma zan musu breakfast kuma abinda suke so haka kowa zai fada na dafa musu,ai kuwa bugun duniya muka ki bude kofa gashi suna jin motsinmu,Abbi na gani ta jikin window ya leko yace sai kun bar gidan nan wlh tunda ba yar arziki bace ke,yar Iska,guntuwar shegiya haka ya dinga zagina ta window,na kalleshi ido da ido tare da Galla masa harara na murguda masa baki,yace zaki ci ubanki wlh sai naga waye ubanki a kasar nan,tafi nayi da hannuna na kara Harararsa ina gatsina masa goshi da gira,ni dai bance komai ba,yana ta zagina,ke yarinya ki shiga hankalinki,a nan nayi magana nace Yarinya tana bayan Uwarta ni dama haka nake idan naji haushi bani da mutunci ba kowa nake iya dagawa kafa ba ko za a kasheni,Meenat tana ta dariya Abbi ya kara kulewa,ya bar wajen a fusace yana baza babbar riga.

    Aayan ne yake saukowa yasha wankan gaske cikin kana nan kaya,kamshi na tashi,Meenat tace ina kwana suka gaisa,Maeesha ya rikewa hannu tare da cewa ba gaisuwa yau?tace ina kwana tana dariya,tace kayi kyau Yaya,tnx yace sannan ya kalleni tare da cewa Abincina fa? Ai ban san zaka ci ba bari na hada ma tea,yace a'a Kunun gyada nake so ko Koko ni,idan babu kuma sai ki bani Tea,ai dole nayi maka,yo Allah na tuba ko ba gasara ai dole a nemota kamar Dan Daddy guda yana so akanta ba sai ayi yaki ba a gidan nan,Dariya na bashi sosai yanda nake maganar cike da girmamawa kamar Ina gaban Sarki,kun san wasu mazan akwai son a yabesu ko a girmamasu,wasu kuma suna so a daraja musu iyaye ya dace mata su dinga fahimtar mazajensu.

    Shi Aayan a ransa yace zan gama kure wayonki yarinya har yaushe aka haifeki,Kitchen na shiga dama jiya na tace mana markaden koko,sharp sharp nayi masa tare da soya masa Chips tunda ba time din yi masa kosai,a Dining na ajiye masa sannan na dawo palo wajensa nace Ranka ya dade an gama,a ransa yace zanyi maganinki soon wai ke me wayo.

    Ni na zuba masa da kaina,yana shan abinsa yayi nisa nace da sha nace Dan Allah ina neman wata Alfarma idan da hali ba damuwa kuma ban takura maka ba,yace ina jinki,nace so nake ka bani Driver daya da mota za a kaini unguwa zanje shopping sannan zamu je schl din da zan shiga,waya naga ya dauka tare da danna kira Malam Garba shugo ina son ganinka,minti kadan sai ga Malam Garba Driver yazo,Key din mota ya miko min na karba,yace gasu nan daga yau in zasu je unguwa zasu dinga kiranka kana kaisu inda suke so,ga key din mota nan a hannunta idan zaku fita ka karba idan kun dawo ka bata key din a hannunta,har schl zaka na kaisu,Malam Garba yace an gama Alhaji,nace ga key din ka kaimin su Meenat schl da yamma kuma zamu fita na fada ina wani  mazewa irin matar Alhaji,Aayan yana kallona duk abinda nakeyi.
Yana gamawa ya mike tare da kara ajiye min Bundle guda na yan dubu yace gashi ki biya kudin schl din ragowar ku kara a shopping karki dawo da kwandala gidan nan duk ki tabbatar kin karar dasu a shopping,nace da gaske mu kashe duka zaka kara mana na cefane?Yace yes.

   Yana fita na dinga tsalle da ihu tare da su Meenat,nace ai na fada muku ni ba a ja dani duk jarabarka sai na ma wayo,gashi dai kwana biyu har na samu abinda nake so,Meenat tace to bari mu dawo muje shopping wlh za a buga damu har mota ya bayar ana kaimu unguwa fa,Meenat tace Sis yau sai munje tsohuwar Unguwarmu a motar munyi musu birga,nace ke banza ce ba yanzu ba sai mun siyi kaya masu tsada mun koma yan gayu sai muje a gaisa ayi zumunci
   Muje na rakaku mota daga nan mu ganta,gaba daya muka fita har inda Aayan ke ajiye Cars nasa,Malam Garba muka hango a wata shegiyar Benz yar gaske sabuwa dal wai itace zamu dinga hawa,su Meenat suka gaisheshi ya amsa yana me fara'a don gidan kaf babu wanda ke Saurarar dan aiki bare a gaisar dashi komai girmanka.

    Meenat suka kame a gidan Baya,sai ga yan matan nan sun fito zasu tafi schl suma ina ganinsu nace pls Baba Driver ka kular min da motata ,ido suka zaro yaushe na samu matsayi har Aayan ya bani mota.da Sauri naga Hanifa ta koma ciki tana zuwa ta zayyanewa kakarsu dasu Abbi.
   Ina ciki ina aiki naji bugun kofa na leka ta yar kafa na hango su Aiko naki budewa bugun duniya naki aikina kawai nakeyi.
   Aayan na gani ya dawo yace na bude ina budewa Hajja kakarsu ta wankeni da Mari,ga hannunta kamar jikin bishiya Sabo da fatar duk ta tsofe ta bushe.
  Zata kara min na goce,nayi niyyar magana haka nayi shuru ganin Aayan na kusa.

   Abbi da Maza da mata sun kai su goma kowa da kalar zagin da yake min,Aayan na gefe ya kalleni na kalleshi,matar Abbi tace ke har kin Isa matsiyaciya daga kawoki cin arziki,na kalleta idona a bushe nace yo ai bake kika auroni ba,kema ai ba gidanku bane aure ne ya kawoki,kuma wlh Bazan ragawa kowa ba tunda ba aurenku nakeyi ba,Hajja tace iyye au Iskancin naki ya girma haka ina magana kina magana kin san dawa kike magana,nima ai baku san wace ba,Aayan ta kalla tace kai saketa yanzu na bada Umarni,maza rubuta mata saki,nace ku kuke tsoron saki idan an sakeni sai me rayuwa zan fasa ko me,Kaka tsohuwa Hajja ta rike baki dan tunda take babu wanda ya taba mata ko musu Amma gashi ni tana fada ina fada,tace saketa nace,Aayan yace baku kuka Sa na aureta ba ni ne naga dama kuma da dalilina Bazan saketa ba ya juya yayi ficewarsa tare da cewa idan kin gama ki kira Malam Garba a waya na ajiye miki Number dinsa a Dining,nace to Ranka ya dade a dawo lfy Allah ya tsare min kai,yace Ameen,nace Million dayar daka bani sunyi kadan Yanlabai,yace kin san inda suke kije ki kara yanda zasuyi,na Gode Allah ya kara budi,yayi gaba na kalli Matar Abbi Hajiya Karima nace kiji dan Allah Baby bashi da dama wlh common shopping a baka yafi million ga kyautar gida ga mota yau da Safe,tsaki naji sunja Hajja tace a sannu zan shayar dake mamaki wlh sai na canja miki kamanni ba a takani da yarana a zauna lfy.

    Na kalleta nace aiki ya ganki ga tsufa ga shiga rayuwar wani Allah ya taimaka,wlh dan ina ganin girmanki ne ko ba komai zaki ci darajar tsufa da kuma matsayinki na Mahaifiyar surikina kakar Mijina idan da mutunci ke kakata ce Amma baku san haka ba,ku tambayi wace Mufeeda a Unguwarmu kowa yasan yarinyar kirki ce kuma ta wanni fannin bani da mutunci wlh da ace haka kawai ne da kun san wace ni Amma kunci darajar Mijina,ba tabani a zauna lfy dan ma ba akan kudi bane,bana yarda a taba lafiyar hanyar cin Abincina akan wannan bana dagawa kowa kafa.

    Matar Abbi ce ta fisgoni suka hadu da Sauran matan suka fara dukana,sai da suka fasa min gefen bakina kadan hakan ma dan na gudu ne da Allah yasan irin Illar da zasuyi min.

   Daki na fada na kulle nayi Kukana boye a fili nace wlh kun jawowa kanku dan ni indai ba lallabani akayi ba to kara lalacewa nakeyi, musamman akan kasuwancina dan yanzu auren nan ta hanyarsa muke ci muna sha shine kasuwancina kuma kowa yasanni akan Business ba mutunci zan iya ja da kowa.








AsmaBaffa
[1/9, 4:55 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

   KASUWANCI NA



           41-45




Official





By
AsmaBaffa





       MMN BASMA,SALMAT BASHEER,SUBYUSMAN ga page na baku Sabo da kauna ina Godiya.

     Gaisuwa cikin Trailer zuwa ga
HAFSAT KHAIRAN
OUM FAROUG
MUM SUHAIL
MAMAN HAIDAR
HAJIYA JAMILA
MAIMOUNA MATER ta NIGER.

    Kuna Raina
MEENAL SIDI
YA SALAM
DJU LUV
NANA KHADIJAH
OUM SALM@
  Ina jinjina muku da Sharhi na gode.


   

    Bayan na gama gyara gidan kaf ko ina yana sheki da kamshi,tuwon danyar shinkafa nayi tare da miyar egusi harda naman Kaza Sabo da a kwai a fridge,a dining na shirya mana komai cikin Food flask masu shegen kyau,wanka nayi na shirya cikin material cotton riga da skert nayi kyau sai ka rantse me tsada ne,dan Mayafi kawai na Sa a saman kaina wanda yasha gyara,1:30pm Sabo da a motar gida ne ba bata lokaci sai ga su Meenat sun dawo suna kwala min kira,Ku karaso mana ina ciki kuma sai kirana kukeyi,Sis yanzu muka ga Yaya Aayan a Compound su Abbi sun sashi a tsakiya tare da tsohuwar nan kakarsu sai masifa suke masa,ko saurararsu baiyi ba kawai jinsu yakeyi,Baki na tabe nace saji dashi can kuje kuyi shirin Islamiyya ga abinci nan a Dining,Bari na kira Malam Garba ya karbi abinci yaci sai muje unguwa, a waya na kirashi ya shugo na bashi abinci a flask dama na ware masa nasa daban Aiko yaji dadi sai murna da godiya yakeyi don ba a basu abincin gidan yan aiki suke burkuta musu ko wanne kwamacala ko dadi babu,fita yayi yaci ya koshi sannan ya kawo min flask din,nace in ba damuwa mu fita ka kaini unguwa,yace ai ba matsala,kudi na zuba a jakata na yafa gyale na me dan girma kalar kayana,can na hango dandazon Family ana meeting akaina irin yanda za a dauki mataki a kaina,Aayan yana zaune gefe yana latsa waya,kamar ance ya dago muka hada ido dashi, hannu kawai na daga masa irin na fita,baki ya tabe irin ina ruwansa,bayan tsadajjiyar motarmu na shiga na wani lafe a kujera ina game da yar Nokia ta wacce dan gidan Comissionar ya bani ,wata Aisha  College nace ya kaini kana na Yiwa Malam Garba bayanin ya Zama wakilina a matsayin Babana ya kawo ni schl nan na tsara masa komai,yace ba damuwa yata.

    Schl din 2 to 5 pm ce yare biyu akeyi Arabic da boko,Kafin ka gamata ka kware wajen Turanci da larabci tare da Sauran karatun addini dana boko,tana da kyau sosai,bayan munje wajen Pc mun masa bayani yace kinci Sa'a saura kwana Uku mu rufe daukan student na wannan shekarar,da kansa Yamin tambayoyi a lokacin na nutsu na Bada amsar wasu wasu na fadi,yace Ss1 zai sani nace to na gode,haka na biya 15k kudin schl fees,na Bada kudin Uniform har kala Hudu,sai kudin littatafai,nace Ina da aure ayi min Hijab me dan girma,haka aka gwada Size dina da komai na mikawa Malam Garba kudin ya biya a matsayin shine Ubana,aka Sa min sunana Mufeeda Adam Fatima yanda muke amfani dashi.

   Bamu zarce ko ina ba sai inda ake siyar da schl bags da su Sandals na siya kala Hudu hudu suma tare da Sauran kayan karatu da komai,komai me kyau me tsada na siya,muna Tafiya a mota naga masu saida Glass na fuska,nace ya tsaya na siya,haka na zabi maka makan glass na yan gayu na gwada sunmin masifar kyau,da baki,da Brown sai farare biyu wanda ake yayi na zamani latest,yanda suka min kyau ba a magana,tun a motar na kara gyara fuskata na sa bakin nan faskeke kowa ya kalleni sai ya kara ya min kyau gashi kuma No respect.

    Yanda na fita na barsu haka na dawo na samesu ana ta maganganu an hana kowa tafiya tsohuwar banza tana ta isa da Mulki ita ke magana har da wata jaka ta yan mata a gabanta wai itama fa bata tsufa ba,ganin suna wajen koda mukayi parking ban fito da wuri ba sai da na dauki lokaci yanda naga Aayan yana yi,sannan na zuro kafa daya da sabon cokeken takalmina me tsada dana siyo a wajen masu takalma na ganshi ya birgeni Dubu Bakwai na siya da jakarsa me kyau,irin zanen dake jikin material din Golden,ba wani iya tafiya nayi da me tsini ba amma karfin Hali yasa nace ai dole a je damu muma,ina fitowa sai da kowa ya Bini da kallon kurilla,yanda naci uban acuci da gashina kuma ba dankwali na daura ba kawai gyalen me dan girma da dan kaurinsa na mutunci na yafa a kaina sannan ga glass dina,Malam Garba ne ya kwaso min kayan a ledojin store din dana je,karba nayi nace na gode kaje kawai Baba sai zuwa bayan Magrib zamu fita again sabo da zamuje shopping da kannena na,yace ba matsala Allah ya kaimu,nace Ameen sannan na bashi Dubu Dubu biyu nace a saiwa iyali Alawa,ya dinga godiya nace No Need Baba Ai ba komai.
  
   Su kuma dangin Aayan tunaninsu wasu kudi Aayan ya fara sakar min yanzu,nan take bakin ciki ya rufe su,musamman yan matan nan yau daya sunga na fara komawa wata Baturiya, Aayan yana ganin irin tafiyar da nakeyi ni ga yan mata,kwas kwas na cuno lips gaba irin yar gayun nan,nazo ta gabansu na makale Murya tare da Sallama ba wanda ya amsa nima ban damu ba dama na sani,na matsa kusa da Aayan yana zaune na sunkuya tare da rada masa taso Kaci abinci tuwo ne nasan kana ci ko? Yace zanzo kije yanzu magana akeyi min na Family,nace wanne family? anan tashi mu tafi ni dan Allah wannan har wasu dangin kirki ne,Yana so ya Harareni ko ya min rashin mutunci amma ba Hali sabo da Idan ya min haka zasu gano gaskiya sannan zasu kara wulakanta mu.ganin yaki tashi still ina tsugunne a gabansa nace ko tsoro kakeji? Naga Alama wlh tsoronsu kakeji muje ni zan tare ma fadan ko me za suyi ma zan amshe ma,tsaki yaja kadan tare da mikewa yace muje naga kin fara rainani dan kinga ina sakar miki fuska,ko kallonsu baiyi ba suka ga na janyeshi munyi tafiyarmu,Hajja makirar Tsohuwa tace kar kowa ya masa magana Ku kyaleshi ai Ubansa ya isa dashi zan yi maganinsu,kowa yaje yasha sha'aninsa zan nemeku,

   Haneefa tace wannan kwai tsinanniyar Yarinya wlh,Allah ya dau ran shegiya a huta da yar Iska,Dayar a ciki tace shike nan na kasa cika burina sai da nace wa Abbi yasa Aayan ya Aureni yace baya so naje na fada sonsa na kasa cika masa burinsa,Sauran yan matan suka ce ke dai bari ai Allah ya yarda sai an saki yarinyar nan shegiya ko Nono bata dashi bata fi 16yrs ba fa,Ameer yace 17yrs take amma wlh ta iya girki dan baku jiba ne gata me kyau da tsafta inama ni na aureta,ai ni wannan ko Haihuwa nawa tayi burina Aayan ya saketa ko ta halin yaya sai na aureta,Dariya sukayi dukkansu suka tafa da yan matan,Khaleel yace mayen mata yaga kayan Dadi kana jin Aayan zai kyale yarinyar nan ko Sufi ne shi? Ameer yace ina ai wlh ko abarshi bata motsi indai bata motsa akan yarinyar nan ba to ina tabbatar ma har abada babu kuma macen da zata gani ta motsa a kanta,Dariya suka kara shekewa da ita su Haneefa harda shewa,Mujaheed yace ka manta Aayan din yanzu ne fa dan bashi da lfy ya rage amma sha'awarsa ta kai karshe,jarababbe ne na karshe kullum cikin chargi yake baya Free dan bura uba ai yanzu ya gama da wannan yarinyar fitsararriya sai shegen baki kamar gidan tsutsa,Ameer yace ai zaiyi dadi ne lips din,Haneefa tace Ameer da Alama ka kyasa fa,yace tuni ni wlh sabo da ita nake shiga part dinsa so nake ko hannunta ne watarana dole na shafa dole sai mun raba jikin nan nata da Aayan,Mujaheed ya jinjina kai to ka dai bi a hankali kasan halinsa wlh kana ganin kamar baya damuwa ana abu kasan ba a taba masa mata ko zai shekara dubu bai taba abarsa ba indai wani ya taba masa mata wlh yaki kawai za ayi gidan nan,dan kasan shegen akwai kare mutuncin iyali,za kaga kamar bai damu ba yana sani kai kasan yanda Khaleel sukayi akan matarsa Bilkisu wacce Daddynsa ya fara aura masa Sabo da karfin sha'awarsa aka masa aure da wuri tun bai gama Degree ba,kuma duk da haka bai ko taba jikin Amaryar ba ya gano cewar da yarinyarka ce tun tana waje kuma kun sheke da ita,ya akayi farko sanda kake zuwa har Bedroom dinta kuna shoshalewa ya sani Amma ya muku banza kalli dai irin yanda ya gasa mata aya a hannu ga na Family sannan kuma ya mata saki mafi muni,sai a lokacin muka san ko yatsanta bai taba rikewa ba,hmm kai dai bari ashe matsiyacin ya sani tuni,Ameer yace ai ni so nake ma na kulla mata sharrin da zai saketa ni kuma na koma wajenta,ina nan ina hada mission dina.

    Ni kuwa tare muka jera muka shiga ciki ba wanda yayiwa wani magana ya wuce Bedroom a matukar gajiye,nima na samu su Meenat basu dawo daga Islamiyya ba,a gurguje na cire mayafin da glass dina tare da takalmin,na dauki kayan gaba daya nayi saman Aayan dasu,sai da na shiga naji karar ruwa yana wanka,ajiye ledojin nayi na koma tare da kawo masa abincin na ajiye,ina Zaune ya fito daure da dan Towel yana goge jikinsa da wani karami a hannunsa,kaina na dukar kasa ina wasa da yatsuna ban dago ba,shi kuwa ko a jikinsa har ya gama shirinsa sai kamshi naji yana tashi,ina dagowa naganshi Sanye da 3qrt da t-shirt yasha kyau yana jikin Mirror yana gyara gashinsa,na kalli Namiji yanda yake ta shafa man gashi masu tsada kala kala yana tajewa, sabo da bana gani na kyale nace to ai ya isa haka wannan ai sai ka karar dashi da wuri kunfi so kuyi ta asarar kudi amma wannan shanana mayuka da kake haka ko Mace albarka,naga ya bude wani kala yana fesawa shuuuu,na Mike nace dan Allah ka barshi haka yanzu idan kasa kadan ka adana abinka gobe ma ai sai ka dauka ka sa amma rana daya ka kusa karar dasu a dinga tausayawa kudin mana.

   Kawo na karasa ma,ya fisge abinsa,nace nafa iya naka ma da yake na maza da wuri zan gyara ma shi kuma wlh ko fita kayi sai an San kana da mata,kasan shi gwauro idan ya fita tun daga shigarsa ake ganewa sabo da babu me nuna masa inda aka samu matsala,wani sai kaga gashi a wuyan rigarsa ya zuba,murmushi yayi Bai ce komai sai yace ai bakinki ne Gwauron gashi nan yi min naga iyawar taki kuma karki min da zafi,Ina murna nace ai nasan har kyauta yau sai kayi min,sunkuyawa yayi tare da miko min kan,nace zan gaji da wuri a haka,na zauna Saman Bed shi kuma na shimfida masa Sallaya  nace zauna ka gani ni da nake me kitso,Kamar bazai Zauna ba sai kuma ya zauna,na ware cinyoyi kamar zanwa wata kitso dai yace ke hade wannan cinyar taki kina period,nace sai na fasa ma dan zan maka shine zaka fada min magana.

    A hankali na dinga taje masa ina fesa masa abun gashin,sai wani lumshe ido yakeyi zaiyi bacci,nace kudi biyu zaka biya ga na gyaran gashi ga kuma na hannun mace yana taba ma kai kasan hannun mace daban ne sai an biya,wannan hannun naki kamar Dutse gwara na maza dashi,ni kaina ba wani yi nake ba kawai tajewa nakeyi ina wasa da gashin dama karya nake ban iya ba,bacci ne ya fara kwashe shi har na gama,nace na gama tashi ga abincin can,yana son yayi bacci na mika masa,yace Hannuna da Mai ban son tashi kisa spoon ki bani naci,ba da wani abu ya fada ba nima haka nasa spoon ina bashi har yaci ya koshi nace lemo zaka Sha?yace Ruwa ni ban fiye Shan lemo na kwali ba nafison fruits ko ruwa,ruwa na mika masa yasha,na kwashe komai na maida,su Meenat suna dawowa nace su shirya muje shopping,wanka muka Sha nasa doguwar rigar da Aayan ya bani nasa lokacin da ya kawoni wajen Family dinsa shiri mukayi sosai Meenat ce tayi mana kwalliya mun Sha kyau,mun fito nace suje jikin motar Driver yana can bari na fadawa Aayan.

   Knocking nayi masa sannan nayi Sallama na shiga yana zaune yau magazine yake karantawa,nace zamu fita Shopping,hannu kawai ya daga min irin muje kawai,katon store muka je munsha siyayya sosai da sosai,Cosmetics,shoes,bags,mayafai,jelweries,Night wears,sai atamfofi kala biyar biyar,shadda kala Uku uku,sai materials tare da laces suma,Ready made dogayen riguna da riga da skert,mayafai dasu Inner wears duka masu kyau yan tsakiya dan yan tsakiya za ace baza ace masu tsada na karshe ba kudin baza su kai ba,wajen telanmu muka wuce duk Wanda za a dinka muka bayar,lokacin har dare yayi kusan ma 8:30pm,nace yau ba girkin dare nace Baba Driver dan kaimu Yahooza suya sai murna su Meenat sukeyi,mukaje na fita na siya mana muka zauna inda aka tanada don Zama ga masu son ci a wajen,muka ci abinmu muka koshi tare da ice cream,na siyowa Aayan ma nasa harda kilishin da suke siyarwa, Malam Garba ma na bashi nasa harda shi na siyawa,ya dinga godiya da addua,

  Wasu sai kaga suna cin abu ma a gaban yan aikinsu wai baza a iya bashi yaci ba,bare aje dashi waje shima a dan siya masa ko kadan ne babu me kulasu Sabo da son kai su tunda talakawa ne suci irin nasu,
     sai 9pm muka dawo gidan,a gurguje nayi wanka nasa rigar baccina kamar T-shirt take amma yar doguwa iya rabin cinya tsayinta,powder na murza nasa lipgloss  sai dan turare na Amtek na shafa na dauki Take away na Aayan na wuce Samansa.

     Da Sallama na shiga Yau ma yana saman Sallaya Sanye da Jallabiya yana karatun Qurani,ina zaune gefen Bed dinsa ya gama adduoin nasa sai lokacin ya juyo ya kalleni tare da cewa ya akayi? Ko ka tambaya mun dawo lfy? Gashi to na mika masa take Away,ledar ya bi da kallo sannan ya kalleni da baki ya nuna ledar tare da cewa bude na gani,da sauri na sakko kasa yace to Ustaziyya gyara Hijab din kina samun a fuska,Dariya nayi  kawai na tsuguna tare da bude masa ledar duk kamshinsa ya cika min hanci me dadi ji nake kamar na fada jikinsa na shako kamshin da yawa,na  bude yaga package na kilishi,daya ledar kuma Kazace da yawa tasha hadi,sai Fura da ruwa harda yoghurt,son jin dadi na da kwadayi na ya jinjina a ransa duk wata hanyar cin dadi na Santa har na iya na siyo masa wannan.

   Muryarsa naji yace ina naku?nace ai mu a wajen muka zauna muka ci Namu kawai sabo da nafi so muna dawowa yaran nan suyi bacci su kyaleni na huta,Murmushin da bai shirya ba ya saki gaba daya ya tafi da Imanina don idan yayi murmushi wani masifar kyau yake karawa na musamman,ke ba yaranki ba amma feeling kikeyi kamar yaranki ne kika haifa sai son girma,

    Fari nayi da Ido wanda ban san nayi ba nace ai ko Ammah na da rai nice kamar uwarsu,rufe wannan ledar bari na gyara farce na,nace au baka zuwa a yanke ma farce?yace a'a basa min yanda nake so ne a Abuja nakeyi ko kuma lokacin dana zauna a London,amma nan garin Sam nasu bai min ba tsoro ma nakeji kar su samin cuta,na kalleshi nace iyye kaji Manya Ashe har a London ka zauna uhm lallai dole kayi yanga,kallo na kawai yayi ya mike tare da dakko abun da yake yanke farcensa kalarsu ma daban ne, kawo na yanke ma kaji na iya sosai,Ba musu ya mika min na gyara Zama a gabansa, nace to fa sai ka koya min yanda ake amfani da kalar Nail cutter en nan ban gane ta ba,

gwada min yayi tare da cewa indai kika lalata min Nails sai kin biyani farce na in dai bai min kyau ba,ae naji kawo kafar to, kafarsa na jawo wani mugun laushi ba duk mace ba, na daura saman cinyata da na rufe da hijab, na mika masa take Away din tare da cewa to ci mana, naman ya fara ci ni kuma na dukufa ina yanke masa Farce,yana ci yana latsa waya yana murmushi ko chat yakeyi oho, ji nayi yana dariya nace mu gani me kake gani na dariya haka,ba komai kawai yace, da na dan shigar da zafi zai ce karfa ki yanke min precious skin dina, wannan kayan da kika cike min Bedroom dasu fa,nace au na manta ne na schl ne na kawo ma ka gani na bashi Labarin komai gobe ma zan fara zuwa,ba sai na gani ba kawai ki kwashe abinki,nace to ba damuwa.

    Ina gama yanke masa na kafa ya gama cin abincin nasa,hannu ya goge da tissu ya miko min yatsun hannu masu shegen kyau dasu,na fara gyara masa farce ina cewa Dazu mun siyo kayan mun kai wasu dinki,du na karar da kudin Dubu  uku ce kawai ta rage.

    Ok yace ke kika bawa Malam Garba Abinci? Nace ae har ba dare ma,ya min waya yana ta godiya Ashe kina da hankali dai? Murmushi nayi nace Kai wai nufinka bani da hankali?to ba karamin Hankali da wayo ne dani ba,yace sai dai kiyi wa wani wayon na ki,harda kai ma zan mawa,Sau nawa nayi ma wayo kaine dai baza ka gane ba,a ransa yace lallai yarinya zan nuna miki baki da wayo soon,ina gama masa ya kalli yatsun tare da cewa uhm ba laifi,toilet ya fada yayi Brush dama yayi wanka kaya ya canja zuwa na bacci,yana fitowa yaga na kwashe kayan dana kawo du na tafi dasu,light ya kashe ya kwanta abinsa tare da Addua.

    Washe gari ina gama aikace aikace na shiri nayi cikin riga da skert English wear nayi kyau na yafa mayafi na fita na tafi har part din Daddyn Aayan,securities basu barni na shiga ba sai da suka sanar masa matar Aayan ce yace daga yau indai itace a barta ta shigo kawai.
    a saman Bed dinsa na ganshi an canja masa kaya yana kwance abinsa,cike da ladabi na durkusa har kasa na gaida shi ya amsa da fara'a,daga nan yace zauna ya ta,a gefen gadon na zauna,nace Daddy da har zan kawo ma abinci na tuna Ya Aayan yace ba komai kake ci ba,murmushi yayi tare da cewa ae ni abu me ruwa nake ci sai kuma vegetables sai ko snacks amma duk sauran abinci basu Dameni ba,tun farko haka nake ni dama abincinmu na Hausawa basu Dameni ba sai Fura da Kunu kawai amma na turawa nake ci,me girki na ma daban take yata,nace Daddy shi kuma Aayan ko yana  yaro amma na Hausawa gargajiya yafi so,yace ai wannan kyaleshi kawai Uwarsa ya gado ta nan.

   Kuna zaune lfy dai ko?ae Daddy lfy Alhmdllh,to idan ya miki wani abu kizo ki fada min kinji,nace to,idan kin samu lokaci kizo watarana zan baki labarin tarihin gidan nan namu kaf sabo da ki koyi Zama dasu,ranar da bani da schl zanzo,Allah ya kaimu,na mike nace na tafi zanje makaranta,yace na gode Mufeeda Allah ya taimaka,na fito a hanyar dawowa part dinmu na hadu da Ameer a hanya yana kallona zan wuce amma yaki matsawa sai ma hanyata da ya kara tarewa,na kasa gane masa kawai na matsa can na wuce abina tare da ja masa tsaki,a ransa yace zanyi maganinki.

    1:30pm ina bedroom na fara shirin zuwa schl ina cikin sa sabon Uniform dina sai naji knocking ba zato,da sauri na zura hijab dina na fito da tunanin ko Aayan ne ya dawo to in ba shi ba waye zai min knocking a Bedroom,ina fitowa naga Dan iskan nan Ameer, ina ina ya fara ahm...ahm...abinci zaki bani,harara na maka masa nace banyi da kai ba don ba auro ni akayi dan na dafa ma abinci ba,na koma Bedroom tare da sa key,abin nasa ya fara tsoratani tun daga irin kallon da yake Bina dashi.

    Cikin Uniform na fito ba karamin kyau nayi ba black and white komai nawa har jaka da takalmi kowa ya kalleni a uniform din sai ya kara nayi matukar kyau,Sallamar su Meenat naji Ma'eesha tana Faman Kuka,lfy Ma'eesha ina Meenat din na ganki ke daya,Sis wannan matan ne suka Mareni kuma ga Meenat can a Compound wai shoe  maker ya tareta wai sonta yakeyi,wanne kuma me wankin talkami, wannan su Haneefa yake wankewa takalmin schl baki ganshi ba cikinsa kato hannunsa da jikinsa siriri kamar tsinke cikinsa kuwa katon gaske kamar zai fashe,sunce wai Meenat sai ta kulashi dole.

    To shine kike mana kuka haka,to ai marina wannan Haneefa din tayi akan nace Meenat tazo mu tafi,ok wuce kiyi wanka ga abinci nan a Dining na tafi schl ni daga can zanga Meenat,maza Ku fara shirin Islamiyya,Bye Sis nace Bye, na fita rataye da jakata,saida nayi tafiya kadan sannan na Iske Meenat Tsaye tare da wannan mutumin me gyaran takalmi,ni tunda na ganshi ma dariya ta kamani don cikinsa girmansa ya isa ga jikinsa siriri kamar a bushe shi ya fadi,su Haneefa suna zaune suna faman latsa waya.

   A fusace na karasa wajensu nace Malam mene haka lfy kazo ka tare min yarinya anan ko kunya baka ji idan kudin magani kake nema ai sai kayi magana a baka kaje Hospital,Meenat tace ba ke bace Sis nace ki bamu dama amma kince kar mu kula su ko me zasuyi mana dole kece zakiyi kawai,Yan matan nan ne suka taso kanmu,ke wace da zamuce ayi abu kice zaki hana wannan ya gani yana so kuma dole ta kulashi in dai tana gidan nan,sabo da shine dai dai ita,Haneefa tace au Ku nan har kunfi karfin wannan kuna yayan talakawa,dama kadan nake jira Mari lafiyayye na zabgawa Haneefa dama kin Marar min kanwa wlh ba wanda ya isa ya taba mana lfy ya kwana lfy,nasan in suka hadu zaneni zasuyi Marin ma da kyar nayi ta maza na shammaceta na fesa mata shi, Cikinsu Sukace KWAJA jeka ka dawo gobe dole sai ka auri wannan suka nuna Meenat,Meenat tayi dariya tare da cewa au dama sunanka KWAJA? Lallai Kaci sunanka ta kara sakin dariya,nace wuce to ciki yar iska idan kika kara tsayawa dashi wlh zan miki rashin mutunci,to ba ke kikace kar na dau mataki Kansu ba,motocin Aayan ne suka shigo ya hango Su Haneefa sun rike min Hijab gashi nayi kyau, har gabanmu yazo yace sake min mata yana gyara wayar Usb da ya Ciro a motarsa,Haneefa ya damko ya dinga tsula mata wayar tana kuka da ihu,su kuwa sauran tuni sun Arce,wlh duk ranar da kuka kara taba jikin matana sai na kusa kasheku a gidan nan kuma kinsan ba abinda zai faru,nasan kin san da haka,kallona yayi tare da takowa wajena zai damko ni nima na kwashe da gudu,ya biyo ni taku biyu ya damko ni Ransa a bace ya kalleni ido da ido sai yayi murmushi matsoraciya yi mata dariya zance shine kika gudu,aiko Nace Haneefa tana Kallona  na kyalkyale da dariya nace wooo ayi mata gwalo,Aayan yace fara frog jump dan ubanki kafin nazo nan na halaka ki,da Sauri ta fara yi,yace yi mata dariya ke kuma Aiko na dinga yi ina wooo harda tsalle,muna Haka sai ga Hajja kakarsu ta fito kamar zata make mutane,Aayan yace jeki schl tana cewa tsaya dan ubanki Karuwa Amma ko kallonta banyi ba na shige mota abina Malam Garba yaja,ta glass tana Kallona ina kallonta na mata gwalo,Aayan ya daga min hannu bye,tana zuwa ta daga hannu da niyyar sharawa Aayan Mari ya rike hannun caraf tare da matsar da ita gefe ya wuce ya bata waje bai ce kala ba,Kuka da kara tare da ihu ta fara yi a gaban yan aiki,Sai ga Abbi yana huci an taba Uwarsa.

    Tunda na fara zuwa schl yau Sati guda kenan lfy nake zuwa ina dawowa abina cikin jin dadi,haka su Meenat ma,Aayan kuwa tun daga ranar da ya Zane Haneefa ban kara ganin Sa a gidan ba,ashe wai ya tafi Umrah Saudiya bamu sani ba sam,koda kudina suka kare Bedroom dinsa na shiga na duba inda yake ajiye kudi na ebi dubu biyar idan ya dawo sai na fada masa.
  A schl dinmu har kawa nayi yar gayu wayayya MARYAM ga hankali ga sanin ya kamata,kullim tunda taji ina da aure take fada min yanda ake Tafiya da Imanin me gida,nace ai ni kullum da Hijab nake zama a gida idan zanje unguwa ne nake Sa mayafi watarana,aiko ta dinga dariya tana wayar dani ni kuwa dan kar ma Aayan yace Dan shi nakeyi nace ko Ya dawo bazanyi ba.

    Yau da yamma su Meenat sun dawo kenan daga Islamiyya KWAJA me gyaran takalmi ya biyota tun daga wajen gate,dama su Haneefa sun fadawa Securities in dai Kwaja ne a barshi ya dinga shigowa yana da budurwa a gidan bayan haka ma yana goge musu takalmin schl.
    Direct Kwaja ya shigo yana wargaje baki da wata falkekiyar T-shirt,hannun rigar Sabo da ramarsa kamar skert hannu tsilili a ciki, kansa har wasu jijiyoyine ke tashi kamar me kwoshokwo, wuyansa kamar mirkin laima,dan kirjinsa kuwa kamar Allo,hakoransa guda biyu manya a waje na gaba,bakinsa yake dargajewa shi tunaninsa ai dole ma ya auri Meenat tunda yayyenta sunce sun bashi ita.
     ta window din sama Na hangosu yana tsaida Meenat yana Meenatu Meenatu yan mata dan Allah ki tsaya,haba Meenatu so kike sonki ya kashe ni? Meenat ta ja tsaki tare da hararsa Malam Kaja mituncinka mun san darajar Dan Adam shi yasa nake daga ma kafa Amma tunda kaki ji zaka ga abinda zanma.
    Kwaja yace ko me zaki min ni Bazan ji haushiba tunda ina sonki,da wlh ba da gaske nake ba Amma na yaba da hankalinki da nutsuwarki,gaki kyakyawa ni yanzu ba zancen yayyanki nake bi ba wannan da gaske ne daga makwallaton zuciyata a daina maganar wasa, to bana sonka kaja Life dinka ka kara gaba Malam cewar Meenat,Murmushi yayi yace yan mata bani da Lifan ni bana karya dan a soni,karki kiyi tunanin Ina da Lifan kice Naja Lifan dina na tafi wlh Allah ko Keke bani dashi idan zaki soni ki soni dan Allah nasan ku manya ne kun wuce ayi muku karya,Takaici ya kama Meenat tace ina ruwana da karyarka ka ja rayuwarka kayi Out a gidan nan,Haushi KWAJA yaji yace na fuskanci Ku kunfi son dan karya azo ana muku birga da mota kullum idan nazo zance na baki Dubu daya ko Dubu daya da Dari biyar koma fiye da haka,to ni ba haka nake ba gaskiya da gaskiya nakeyi wlh da zaki aureni kullum sai na dinga siyo miki kifin gona kina soya mana,watarana ma Miyar zabo zaki dinga yi mana,Taliyarmu  guda da macaroni da wake gongoni guda ya ishemu na na kwana hudu zuwa biyar, tsaki Meenat taja tayi gaba ta barshi nan,ina jikin Window  ta sama ina ta dariya gaskiya Su Haneefa yan Iska ne,Meenat ta shigo na dinga mata dariya,nace Allah sarki kanwata duk iya kwalliyar nan kuma taki sai ki kare a KWAJA tumburarre,Dariya tayi itama tare da cewa ai Allah ya tsinewa su Haneefa yanzu idan nayi wani Saurayin yazo ya ganni da wannan ai wlh rainani kawai zaiyi ya daina zuwa,ina ta dariya harda kwalla Meenat tace dan Allah ki daina,har dare muka kwanta ko farkawa nayi sai nace ta KWAJA tashi na baku lbr,banza tayi min tace wlh sai na fadawa mijinki idan ya dawo tunda haka kike min.

     Yau nayi shiri tsab ba schl zanje wurin Daddyn Aayan ya bani labarin gidan nan da yace zai bani,koda naje  Sallah ya idar daga kwancen,yana murmushi muka gaisa,nace Daddy yau na shirya a bani Tarihin naku. Yace to yata bude kunnuwanki kiji.

     
     Next page is very Important readers ku tsaya ku karanta da kyau shine zamu san waye Aayan.
Raffa

Asma Baffa
[1/10, 10:37 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

   KASUWANCI NA




          46-50




Official




By
AsmaBaffa






    Page naku ne MADINA ALEEYU
MAMAN SAMHA
NAJA'ATU ALIYU

Jinjina gareku na wajena
MOMMY ARFAT
AYFA
MARYERM MUHD
HAJARANCY
HAULATU KAMBA
QUEEN KK




    Zaune nake na nutsu Daddy ya fara bani labari,
    Mu yan Asalin Kasar Algeria ne sabo Dama kasar suna da yawan farare duk kusan larabawa jar fata,har yau muna da ragowar dangi acan kawai zumunci ne da yayi karanci yanzu bama yi dasu suma haka,Babana Mahaifi kakan  Aayan shine Jabeer Muhd Jabeer tunda suke dama su masu kudi ne sun gaji dukiya me tarin yawa,a tarihinsa kaf  ba aji talaka a jininsu ba tun zamani me tsawo,komai sun hada ilmin boko da kasuwanci,Jabeer Muhd Jabeer Allah ya Yoshi me son yawon zaga duniya har Allah ya kawoshi Nigeria can cikin wani dajin Fulani dake Taraba sunje yawon bude ido a rugar fulanin Allah ya hada shi da Mahaifiyarmu Hajja kenan wacce kike gani a gidan nan tana zuba mulki sunanta Karimatu,Karimatu Hajja basu gaji arziki ba don a rugar ma su talakawa na karshe,Allah yayo su da son kai tare da son abin duniya ga tsafi da bin Malamai,Sau daya suka hadu da Jabeer taga yana da dukiya dama bata da burin da ya wuce ta auri me kudi wanda zai kaita kasar waje su zauna,tun daga tambayarta ina ne gidan me gari shike nan ta koma gida ta sanarwa Babarta cewa taga wani tana so Bature ne,sunansa Jabeer,nan Babarta Larai ta shirya sai gidan bokanta,Lokacin Jabeer ya bar kasar nan ma Nigeria yana Ghana,yaji son Karimatu ya shigeshi babu bata lokaci ya dawo a gigice sabo da tsafin da suka masa,yana zuwa da maganar Aure Larai da mijinta Usmanu Baban Hajja suka amince sabo da son abin duniya.

    Ko dangin Jabeer babu sai wakili aka yi masa a kauyen aka daura Auren Karimatu Hajja da Jabeer,sabo da aikin bokanci ya tafi da ita Algeria sunyi shekara daya ya dauketa suka koma London inda a nan aka samu Cikina ta Haifeni naci sunan kakana Muhd,ana kirana Muhd Jabeer Jabeer, a London na taso cikin Jin dadi gata tare da kwanciyar hankali,ga ilmi sosai na zamani dana Islama,sabo da Babana akwai son Musulunci,y anda ta mallake Babana yasa take masa abinda taga dama,wulakanci iri iri da cin mutunci,tana ta sace masa dukiya da kadarori amma duk da haka arzikinsa karuwa yake,ita kuma tana ta sace wasu tana adanawa.

    Bayan na kwashe shekaru biyar a duniya asirin da Babata Karimatu Hajja tayiwa Jabeer Babana ya karye,nan fa Jabeer yace Bai San zance ba baya son Hajja,ya dinga wulakantata,gashi sabo da kudi bata so su rabu tana kasar waje tana cin daula,haka take jure wulakancinsa sabo da kudi har ya kara Aure ya auri Masoyiyarsa Hafsat Balarabiyar kasar Jordan,mata ta gari suna zamansu lfy tana sonsa tsakani da Allah ba irin mahaifiyata ba da son kudine kawai,a haka take zaune har ma abin yaci tura ya saketa saki har uku,sabo da ta Saci kudi da yawa yasa ta san yanda zata yi dan kar ma a gano ta sai tattara ta gudo Nigeria da dunbin dukiya a wancan zamanin.

       Ni kuma ina wajen Babana hannun Hafsat Balarabiyar matarsa ta Jordan tana rikeni Amana da gaskiya,tun kuma daga kaina Babana bai sake haihuwa ba har aure ya kara amma Bai kuma haihuwa ba a duniya,bayan shekara Uku da sakin Karimatu ta samu wani mutum da take matukar Kauna da gaske amma bashi da ko sisi can cikin wani kauye yake shima a Taraba state Fulani ne sosai,sabo da tana sonsa ta gina katafaren gida na more rayuwa a cikin birnin Taraba,ta aure shi suke zaune tare da shi.

       Dama ni bata son Babana sai don kudinsa,bare da asiri ya karye ya wulakantata sai ta kara tsanarsa bata da makiyi sama dashi sabo da kudin basu isheta ba tafi so ta yashe shi tas, sabo da wannan har ni da ta Haifa ta tsaneni kiyayyar Mahaifi ce ta shafeni nima bata kaunata da abinda ya shafeni, shekara biyu da auren Yusuf ta Haifi danta dashi Namiji Mustapha shine da kike ji ana ce Masa Abbi a gidan nan, bayan 2yrs ta kara Haifar kaninsa Sani shine zaki ji ana ce Masa Abbin Ameer, sai dan Autanta Awwal  shine Abbin Khaleel  tare da kannensu. tana ta juya dukiyarta amma basa wani karuwa sosai sai rufin asiri,Katsam Mijinta sai ya rasu Baban su Abbi kenan,ita ta Sha wahala dasu ta dauki nauyin karatunsu har iya Secondary da komai sabo da tana masifar sonsu kamar ranta sabo da yanda take kaunar Mahaifinsu,ni kuwa Abbin London kenan ko waiwayenmu bata kara yi ba,har dai iyayenta suka rasu sai dangi,haka Iyayen Babana ma sai dangi ana ta karewa.
     Na gama Degree da Masters dina duk muna London,Babana yana ji dani sabo ni kadai gareshi,Har ya hadani Aure da wata budurwa Balarabiya yar Jordan cikin yan uwan matarsa Hafsat lokacin ya Damka min dukiyarsa baki daya da komai ga kuma aikina ina yi,na zama hamshakin me kudin da nayi suna a duniya kaf a wancan lokaci,Muna zaune lfy da Matata Asiya Wacce ta Haifar min Dan Albarka na Da daya tamkar da dubu Aayan kenan,dukkanmu a london muke rayuwa,har Aayan ya gama Primary lokacin kuma Su Abbi su Uku suma da matansu sun Haifi yaransu Maza,Abbi Mustapha mijin Hajiya Saratu Mami shine Baban Mujaheed,Haneefa,Sajeeda,da kuma Minal karamar yarinya,Awwal mijin Hajiya Zarah Ummi suna da Yara su kuma Biyar Khaleel,Farida mate din su Haneefa shegu Uku,Maryam,Nura sai dan Auta yaro mate din Minal wato Ahmad. Sani mijin Hajiya Haleema Anty yaransu uku Ameer fitinanne, Zahraddeen dan Wiwi,sai Yusrah.

     Yanda iyayensu suke da hadin kai haka suma yaransu suke da hadin kai ba a jin kansu, Sabo da Hajja ko yaro taga yana bijire mata sai ta tafi gidan boka ta kai sunansa cewar Danta wane baya jin maganarta ayi masa magani ya koma sai yanda tayi dashi,haka Matan yayanta ta gama dasu sai abinda tace,jikokinta ma haka, ni ne kadai da Dana muka gagareta, kuma a halin yanzu hausawa haka suka koma,wai ko dane sai iyaye suyi masa asiri su mallake abinsu sai abinda suka ce,sai kaji ana in ka zauna yanzu zaki haifawa wata ta gaje miki da,ko shaye shaye,ko dai wani banza idan yana yi maimakon ayi masa addua wai sai a tafi gidan malam,dana wane ko Ya ta na rasa yanda zanyi tana Kaza a canja mata ra'ayi,ko miji ne bata son auren sai iyaye su kai sunanta kaga kawai ta koma sonsa,yana karyewa kuma shike nan Allah kyauta.

kin san yaro tarbiyyar daka dorashi da ita zai tashi,ni da Dana da basa sonmu har yayansu basa sonmu,shi yasa ko yaro yana ma kallon Banza maybe sunji iyayen su sunce wani abu a kanka,wasu ma in kaga suna daraja ka to iyayensu ke yabonka gabansu a kula iyaye,daga kun samu matsala da yan uwanki ki kwashe ki fadawa Yara wane dan uwana ko yar uwata tayi min Kaza sai kiga har abada baza su sota ba,ko kin dawo kin gyara bazai gyaru ba,a guji gulma da zagin yan Uwa da mutane gaban Yara.har Matan su Abbi basa kaunarmu kuma nine nake musu komai na rayuwa har daukan Nauyin karatun yaransu da komai na duniya har yau har gobe har yanzu da aka kawoki gidan nan yata.
    Lokacin da Aayan yana secondary ya gama lokacin Allah ya karbi rayuwar Jabeer Babana tare da matarsa Hafsat sunyi Hatsari a jirgin sama.

    Muna zamanmu da Dana har ya shiga University lokacin Nazo Nigeria neman Mahaifiyata Hajja don Babana ya bani Address kafin ya rasu,bata yi wani farin ciki ba Amma ganin nine yanzu me kudin sai ta saki kuka tace dole sai mun dawo Nigeria da iyalina ko ta tsine min nabi duniya,ba yanda zanyi da dukiyata da komai nawa na dawo Nigeria tare da Gina katafaren gidaje har Biyu a  Abuja nace daya na dana Aayan daya nawa,ga motoci na Alfarma,har karatun Sojoji nayi shi yasa kike ganinmu da Securities a gidan nan harda jiniya in ta kama Sabo da nayi aikin soja na shekara Uku a kasar nan da Babban matsayi Sabo da tun ina yaro soja nake so shi yasa nayi aikin.

     Ni da Matata Asiya mun dawo Nigeria dasu Hajja tare da kannena su Abbi duk na kwashe mu muka koma katafaren gidana dake Abuja,kudin Hajja data sata sun kare dama,ni na dauki nauyin su Abbi duk da sun girma suma da iyalansu sai da na Sa su sukayi Degree,na basu aiki a Company na nake biyansu albashi me tsoka,na siya musu motoci still ban fasa daukan nauyin iyalansu ba,amma sam ko me nayi musu basa taba Cemin ko an gode hasali ma sai daí su nuna bana musu komai a duniya,ko yaushe burinsu suga na tsiyace na talauce,burinsu ace a cikinsu ne daya yake da wannan arziki,haka Hajja ma komai nine me laifi su basa taba yin laifi Sabo su take so,abu kadan in nayi zata fara zagina,tana min baki,amma su ko me zasuyi baza ta musu Fada ba,kullum burinsu su ganni cikin halin bala'i, ba irin asirin da basuyi min ba Sabo da na talauce su gaje dukiyata Amma Sabo da karfin addua tare da tsoron Allah da kyakyawar zuciya,bana nufin kowa da sharri,bana shirka sai Allah ya kareni duk abinda zasuyi a banza,tunda na gane halinsu na dage da addua,ita kanta Hajja bata so ace nine me kudi ba cikin yaranta ta fi so ace Awwal,Sani ko Mustapha sune masu kudin ba ni ba,sabo da dama bata so na da ubana kuma bugu da kari ba ita ta raineni ba, sam babu wannan shakuwar ta raino tsakanin Uwa da Danta,nima ban damu da ita ba nafi son matar Babana Hafsat data rasu nafi Jinta a raina Sabo da mun shaku ta rikeni da Amana.

    Makirci kulla tsiya ba wacce basa min,har Hajja ke Goya musu baya ana bin malamai akan dukiyata ta koma wajensu,kawai dai Hajja bata yarda ayi min asiri na cutar da lfy ta ba,tace duk da haka ni Danta ne na cikinta ko bayan ranta idan suka cutar da lfy ta ko raina bata yafe ba,duk abinda zasuyi na karbe dukiyata sunyi Amma ba abinda ya faru,su kuma Sabo da ita tasha wahalarsu suna jin maganarta amma shedan yafi karfin zuciyarsu don  ko taya ma so suke suga bayana,hassada suke min ta gaske,ni kuma da yake dama a goge nake na waye nasan me nakeyi bana kulasu duk wata hanya na tosheta wacce zasu iya samun dukiyar tawa ko kadan ne sai daí in ni na basu da kaina, Aayan yaro ne me hakuri da kawaici tare da danne bacin rai Amma ta wani fannin yana da zafin zuciya,tun yana secondary na fuskanci yana da karfin sha'awa har cuta yake kwanciya a asibiti Sabo da sha'awa.

    Saura shekara daya ya gama Degree a London mu muna Nigeria lokacin Hajja su Abbi sun zugata dole tace sai na dawo da Aayan Nigeria nayi masa aure mun zauna gaba daya Sabo da suna bakin ciki shi yana waje yaransu basa kasar waje bayan har saudiya da Dubai na kai yaransu sosai baki daya,da kudinsu ma suna fita kasashe suke duk ta silar arzikina, Asiya Matata kullum cikin kuntata mata suke tana ta hakuri har Mari tasha a wajen Su Abbi ban taba ce musu komai ba,wahala ba wacce bata gani ba,duk aikin gidan nan na abinci ita ke dafawa shi yasa ta iya girkin hausawa sosai,Hajja ta wahalar da ita sosai  tare da matan su Abbi suka hade mata kai kamar zasu kasheta kullum kalar abinda zasuyi mata daban.

    Ganin matsalar Aayan ta sha'awa gashi kyakyawan gaske kuma tana turai ina tsoro kar ya lalace sai na yarda nace ya fito da mata zan aura masa idan ya karasa Degree ya dawo Nigeria,ya kawo min wata musluma yar turkysh yana so,Amma Sai Hajja tace ban isa ba idan har na aura masa ita bata yafe min ba,nayi masa bayani ban boye ba,da yake Aayan akwai biyayya sai yace ya hakura to kar mamana tayi fushi da ubansa.

   Su Abbi ne suka zuga idan Aayan ya auri Jar fata zamu kara yin kudi mufi haka arziki,dan danan suka nemo wata budurwa kyakyawa Bilkisu yar gidan Minister itama budurwar Khaleel ce,suka hada baki dasu Abbi domin a aurawa Aayan sai ta san yanda zatayi ta yashe mu tas,koda suka ce ga mata sun samowa Aayan sai da na bincinka na tabbatar ba yarinyar kirki bace Amma Hajja tace sai an aura masa ko ta tsine min,haka na hakura aka daura auren Bilkisu da Aayan yana London nace Hajja tayi hakuri Bilkisu tabi mijinta ya gama karatu sai su dawo tare,kafin Bilkisu ta tafi sai da suka gama tsafeta a gidan boka yanda zata mallake Aayan ta samo musu kudi,to na rigada na sani ina Yiwa dana addua shima kuma akwai addini yana yi na kara ja masa kunne kan rike addua,koda Bilkisu taje baiji yana sonta ba,ya kasa kusantarta,har ya gama Degree lokacin ya dawo Nigeria kullum da sha'awarsa muna hanyar asibiti ga na Hausa muna yi,kuma ya kasa kusantarta,har ya gano cewar tana fasikanci tare da khaleel,bai sake ta da wuri ba sai da ya tabbatar da ita ta gane kurenta,su kuma su Abbi ganin bata samo kudin ba ta kasa komai sai suka tsaneta suka koma azabtar da ita,duka zagi ba abinda basuyi mata ba har Aayan yaga zalunci yayi yawa ya bata hakuri tare da kudi me yawa suka rabu,yanzu haka ta dade da aure harda yaranta biyu.

   Lokacin kuma Asiya Matata bakin ciki yayi mata yawa,lokacin kuma Hajja da kanta taje gidan boka ta samu nasara wajen Yiwa Asiya asiri tace dole sai na saketa,naki yarda don ina sonta,rigima mukeyi sosai,ta daina kula Aayan sam ta tsani Danta,tace indai ban saketa ba sai ta kasheni haka Aayan na rokarta tayi hakuri yana kuka nima haka na saketa saki daya ta ta koma kasarsu,bayan asirin ya karye na maida ita ba tare da kowa ya sani ba har Aayan,Shine ma dalilin da yasa yake jin haushin mahaifiyarsa har yau,na fada masa gaskiya Amma yaki fahimta yata,muna tare shekara daya da dawowarta  ta samu ciki wajen haihuwa ta rasu Allah ya karbi abarsa,munyi kuka ni da Aayan sosai haka muka hakura.

    Daga nan Hajja da kanta tace ta samowa Aayan matar aure Nafisa ita kuma yar talakawa ce Amma bata da tarbiya ni kaina tasha zagina a gabana,lokacin Aayan ya hakura bai sonta Amma dole ya bata hakkinta na matarsa,a lokacin kuma su Abbi sun masa asiri kwata kwata ya daina sha'awar mata ko kadan dan kar ma ya haihu a duniya zuriarmu ta yadu mu kara arziki,ba asibitin da bamuje ba,akace lfy yake,har na Hausa da addua anyi Amma sam,ganin haka yasa Nafisa ta bude bakin rashin mutunci wanda akan Aayan take saukeshi ya kasa Control dinta zagi da komai ba wanda bata yi,su Abbi na zugata dan a bangarensu take,lokacin Hajja ta matsa min ita Kano take so mu koma da zama Abuja ba dadi,haka na zabi unguwa mafi kyau na tsantsara mana wannan gidan da muke ciki wanda duk shekara sai an canja masa fasali, Sabo da bacin Rai Aayan ya tafi yin karatun masters dinsa na Electrical engeneering,Nafisa tana nan tana sheka rashin mutunci har da ni,yana gama Masters a london ya dawo ya mata mugun duka ya saketa sakamakon zagina da yaji tayi.

    Suka kara nemo masa mata wata Rukayya ana ce mata Ruky lokacin Aayan bai warke ba na dage masa da addua Allah ya taimake mu ya warke don baya boye min komai nima bana boye masa yace min yanzu yana jin Sha'awa, Ruky da Farko tazo da mutunci tasha wahala hannun Hajja duk cikin Matan da suka aurawa Aayan Hajja bata son Ruky Sabo da taga kamar tana Son Aayan,shi kuma Aayan bai son Ruky ya dade da ganowa Ruky Makaryaciya ce gata kawai sha'awarsa takeyi dama tuni tasan Maza tun a waje,amma duk da haka nace yayi hakuri ya bata hakkinta,yaje mata da niyya kawai sai kuma ya kasa aikata komai gashi yana sha'awa Normal Amma ya kasa aikata komai,Ruky dai taga no way itama tace a saketa,wannan da yake Hajja bata sonta sai da tasa wasu suka Zane Ruky tas wai ta ci kudinsu a banza bata yi zaman aure ba,Da kanta Ruky tace a saketa,na bata hakuri Amma tace ina sam Allah ya karta baza ta zauna ba,Aayan yace taje itama,daga sannan kawai yace wa su Abbi bashi da lfy bazai taba haihuwa ba,an gwada shi hasali ma bazai iya Yiwa mace komai ba,sannnan ya kara daurawa kansa cuta yace ai ciwon sugar da Hawan jini ne dashi wai duk dan su kyaleshi haka ya huta don ya rantse bazai kara auren matar da zasu zabo masa ba ko me za ayi.
    
   Muna rayuwa haka kullum kiyayyarsu Karuwa takeyi akanmu musamman Aayan sunfi takura masa har Hajja cikin jikokinta bata son Aayan,Shi kuma baya shiga harkarsu baiyi rayuwa dasu bama bai taso dasu ba sam basu saba da juna ba,Sabo da basa sona da Dana nace Abbi ko kannensa su bawa Aayan auren Yarsu daya ayi yar gida sukace sam basu yarda ba Sabo da a zuciyarsu suna da manufa a kanmu.
   Muna ta rayuwa kwatsam Aayan ya birkice min shi Barin kasar zaiyi bai son gidan nan,aikinsa ma Shi bari zaiyi ya daina komai,na rude muna ta addua watarana ya fita shike nan bai dawo ba,Kowa har Securities basu ganshi ba,sati daya,biyu,uku,wata daya har wata Uku,babu nema cigiya har kasashe ba a ganshi ba,addua sosai har masallatai na raba,ana ta yi sai aka ganshi can wani kauye a gindin bishiya ya dawo hayyacinsa,ashe su Abbi ne suka masa kucciya,ganin haka nace dole mu Barsu,ai kuwa Hajja tace idan na tafi bata yafe ba ta tsine min,Aayan yace mu zauna kawai Amma shi zai koma Abuja da zama shine Aayan ya koma rayuwa a Abuja lafiya yana min aikace aikace na Business tare da fita kasashe,yana yawan zuwa Umrah Sabo da addua ko yaushe zaki ji ya tafi idan ya Zama less busy.

    To Daddy wannan cutar taka fa? Ai yau kimanin shekara daya da rabi kenan ina haka har na saba ma,shima sati daya ina dan jin jikina ba dadi nazo wucewa Naji yan uwana su Abbi suna shawarar yanda zasu kashe Aayan mijinki Sabo da su gaji dukiyata su da yaransu,har yanzu a wannan kudirin suke,kuma duk yaransu sun san da wannan,dalilin haka na yanke jiki na fadi shike nan komai ya daina motsi shima ba kasar da ba aje ba har na gargajiya da addini anyi,masu irin cutata da yawa suna tashi suna warkewa Amma ni tun muna yi har mun gaji ma na hakura na barwa Allah.
  Aayan yace bai hakura ba na hanashi har haushina yake ji yaki zuwa gaisheni Sabo da naki yarda mu ci gaba da neman magani,kin san mijin naki ba dama.
   To Daddy ni kuma me yasa ya aureni? Nine nasa aka auroki yata ke zabina ce,watarana kafin kuyi aure yazo nan yana ta fushi da masifa wai daga ya kwanta a kasa wata tazo ta haye masa jiki Kazama,watarana ya kara zuwa yana fushi wai wannan ce ta zageshi wlh sai ya halakata,da kyar na lallashe shi,watarana kuma yazo yana dariya yace min kece dai ya kara ganin ki son kudi ya kaiki wani gida ko wani ya biyoki ko me kina dai ta sheka gudu kika kasa tsayawa da kanki sai da kika bigi bishiya,wata rana kuma yazo nan yace min Daddy naga mayyar nan nace wace mayya yace me son kudi taje Maula gidan Yarima tana ta shan fura a leda a gaban Maza.
    Shine na bashi Umarni nace lallai lallai dole ne yaje ya aureki,sabo da ina so ko Allah zai sa yayi dacen mata ko ma ya samu haihuwa ya tara zuri'a.idona na rufe gaban Daddy sabo da kunya,yace min ke yarinya ce,nace ae a hakan,ba fushin da baiyi ba shi baya Sonki bazai aureki ba nace dole ya aureki duk yanda zaiyi ma ya aureki amma nace zai iya aurenki na Kasuwanci zuwa dan wani lokaci sai ku rabu idan zaman bai yuwu ba,bana son a cuci wani,lokacin yace indai dan na wani lokaci ne ya yarda zai biyaki kudi ya aureki tunda ina son yayi aure,ko yaushe kike so kasuwancinku ya kare ki fada masa zai rabu dake yata baza a cuceki ba,bazan miki dole ba,nasan aure a haka bazai yuwu ba,shima na fada masa.

  Ya akayi su Abbi suka yarda? Sai da muka biyasu kudi me yawa sannan suka sa Hajja ta yarda suma suka yarda suka Zama maneman aurenki,kudi aka biyasu in ba haka ba sai sun zuga Hajja tazo tace bata yarda ba, ko auren da basu zuga Hajja tayi masa ba shima Contract sukayi Deal aka biyasu kudi suka kyale zancen,sun san kuma zamu iya kwace kudinmu tunda a tafin hannunmu suke,sabo da sun San baza su iya sawa a sakeki ba an rigada an biya shi yasa suka zuga Hajja tace ki dawo gidan nan da Zama,wannan securities din ma duk Aayan ne yasa suke tsaro na sabo da makircinsu,to Daddy dukiyar taka fa? Tana hannun dana Aayan na bar masa komai tuntuni shine me kudin shi yake komai kawai taimaka masa nake da shawara,mijinki young millonier ne da an San abinda yake dashi a duniya to da duk duniya sun San da zamansa,amma duk da haka da dama sun sani kasashe nayi suna shima haka.

   Yarima Bobo fa Daddy?shi kadai ne abokinsa dan Nigeria da sukayi karatu tare kuma ya yarda dashi sun aminta da juna,ranar danaga ya Zane su Haneefa fa? Waya tayiwa Abbi kuma yasan ba mai iya taka musu birki sai shi shi yasa yace yaje ya Zane masa su.babu wanda suka tsana yanzu sama da mijinki da kuma wanda suke tare da shi,suna nan akan bakansu karki ga suna miki dariya ko sunyi luf kice sun shiryu wlh wani kullin suke kullawa,da bana raye da tuni Aayan ya bar kasar nan tunda ko tayi masa baki bazai bishi ba to amma ina raye ni zata yiwa kinga akwai matsala,ki nutsu yata shi yasa na baki labari ki san yanda zaki zauna dasu da basira tare da gogewa,fada da zage zage ko duka ba shi bane use ur Upper ki kwaci yancinki da na mijinki, idan kuma Kun shirya rabuwa baku da matsala Ku kuke zaune sa juna ba ni ba,yanda kukayi dai dai ne,a takaice na baki labari dan na yaba da tarbiyarki,nasan Aayan bazai fada miki ba shi yasa na sanar dake,idan kin zabi business za a biyaki ko nawa ne karki damu tashi kije a sannu kuma zaki ci gaba da gano halayensu daya bayan daya,abinda da ma ban sanar dake ba duk zaki gane nan gaba,a takaice na sanar dake.

   a raina naji tausayinsu sosai har kwalla nayi sannan sai naji tausayin kaina da yan uwana,garin neman gira zan rasa ido,haka kawai son kudin jaraba ya kawoni inda za a ruguza mana rayuwa,yanzu ya zanyi?Me zanyi,lallai fada da masifa ba shine kadai zai kwace mu ba,ashe Aayan yana da gaskiya da baya saurarsu yake cewa na sharesu kawai,irin wannan kiyayya haka wacce zuciya ce dasu,ba a saduda ba dana sani tun tuni kayi ta abu daya akan wani,har Aayan suka batar dashi lallai,to tunda suka Yiwa yan Uwa haka ai nasan ma wajen Kudus zasu cilla ni shike nan zan bace ko a halakani,a raina nace ni na fasa auren na hakura da Kasuwancin kawai bari ya dawo ya sake ni kawai mu tafi,bazan iya wannan rayuwa ba wannan gidan ai sai su ni kam yafi karfi na.

   Muryar Daddy naji yace tunanin Me kikeyi yata?nace ba komai kawai mamaki nake yanda kuka iya Hausa haka bayan ba anan kuke ba,yace lokacin Hajja bata wani jin turanci da Hausa muke magana har na kai 5yrs daga nan ina son yaren akwai wani bahaushe abokinsa yaci gaba da koyamin na iya sosai,Aayan ma na koyawa Mamansa duk da bata wani iya ba haka muke masa Hausa ya tashi da yare biyu,da ya dawo nan kuma sai ya kara gogewa da yaren.
  
    Me kike so kiyi da kudi yata idan kin samu da har kika amince da wannan aure ba tare da bincike ba duk da cewa Aayan ya min bayanin halin da kuke ciki? Daddy Sabo da muyi Karatu Meenat ta zama Likita,Maeesha ta zama lauya,sannan nayi mana gida me kyau,mu dinga cin kayan dadi,sannan idan munyi aure mu dankara kayan daki masu kyau shike nan,Murmushi yayi yace to wannan tunanine me kyau,me yasa kike son Kanwarki tayi likitanci ke kuma fa? Nace ni abinda yake birgeni da Likita Daddy naga sun gwalewa mutum ido sai ayi zuruuu ana kallo sai ace yana da cuta Kaza hhhh na karashe ina dariya shi kanshi Daddy yaji kuruciyar tayi yawa sai dariya yakeyi.

   Yace Allah me iko to Lauya fa? Shi Lauya Daddy Allah hular nan da suke sawa wata tum tum kamar gashin tinkiya itace take bani dariya,kuma da glass dinsu yana birgeni,sannan idan suka tsaya suna zuba karya gaban alkali sai ka rantse gaske ne,shine suke birgeni sun iya sheko ta,Daddy yayi dariya to ai ba kowa ke yin karyar ba a cikinsu,amma dai sunayi ga shedar zuuur a karbi kudin mutum,Yace Allah ya shirya su,ke kuma fa me kike so ki zama ?nace  ai ni nawa yafi nasu dadi malamar Makarantar primary na dinga shiga aji gaba daya a mike ace Good morning Aunty,nace morning student How are u,suce we are fine thnk u Ma,sannnan ni kuma ina bata rai ina yanga tare da tsawa nace Sit down,kuma na dinga koya musu A babba a karama,Baba ya tafi Gona,malam yana karatu,Inna tana Girki.Daddy ya dinga dariya yace ah lallai naki yafi dadi,tashi ki tafi Yata gashi 4pm tayi Sallah zanyi, 8pm Aayan zai dawo yau daga Umrah,cikin Kasuwancin naku da kukeyi ki dafa masa abincin gargajiya yana son wainar shinkafa da miya.

   Na mike nayi masa sallama zan tafi yace Yata yau kin sani nishadin da na dade ban samu ba shekarunki nawa ne haka? Tunda kaine Daddy na gaskiya zan fada ma 16 nake saura wata biyu na shiga 17yrs Amma karka fadawa kowa Sabo da har Aayan 17 nace masa bana so a dinga min kallon yar yarinya.
   To Bazan fada ba sai kin sake zuwa yata nace to Daddy Allah kara lfy na fito  na dawo part dinmu.

   Sallah nayi na fada kitchen na fara  hadin wainar shinkafa da Miya,Su Meenat sun tafi karbo mana dinkunan da muka kai wurin tela, bani na gama Wainar ba sai wurin 7:30, ina kitchen su Meenat sun dawo tare da Driver duk na zuba musu sunci har Driver,Ni kuwa ina kitchen a kaskon ma naci na koshi da naga na soya wata tayi min kyau sai nace wannan tawa ce ni zan cinye ta,saai na jefata a plate na zuba Miyar taushen na cinye ina yarfe hannu,ga zafi ga Dadi,miyar tayi dadi harda naman Rago,ina gamawa na masa kunun gyada,na yanka masa Fruits a wani glass Bowl me kyan gaske nasa a fridge,Meenat da Ma'eesha ne suka wanke abubuwan dana bata tare da gyara kitchen fes bayan sun gyara ko ina na gidan sosai yana kyalli ko ina kamshi ke tashi,Dakin Aayan na kara gyarawa duk da cewa sun gyara sai da na kara tisawa na kunna Ac ga sanyi ga kamshi,na kulle,nayi Sauri na shiga wanka,na fito yau Salo zan canja a gidan nan.

   Meenat ce ta gyara min gashi da mayuka,na shafa lotion me kyau da kamshi,dama gashi na kara haske abinka da fara dama ta samu waje, yar kiba da kyau nayi Sabo da ina ci ina koshi a kan lokaci,Cikin dinkunan na zabi wani Lace me kyau pupple and Brown riga da skert nasa,yanda na fito a dinkin ba a cewa komai,mazaune sun cika fam dinkin das a jikina,Meenat ta shafa min powder sama sama ban son kwalliyar nan me yawa ni,maroon jambaki ta sa min sai kwalli tare da samin eyeliner a saman ido harda nayi tsananin kyau,gira kuwa na hana tayi min da brush na taje na gyarata ba tare da na kara komai ba Sabo da girarta baka ga yawa,tace saura sarka aka Sa min wata yar karama pupple da dankunnenta,nasa agogo na wani me kyau na yan gayu da muka siyo Brown,Meenat tace sai na Sa zobe ma yana kara kyau a hannu,haka nasa wani me kyau,ta zauna ta tsantsara min dauri tare da sakin gashina ta baya kyau ba a magana ni kaina sai yanzu na kara son kaina,naji kamar na lashe kaina Sabo da yanda na hadu,nace kai ashe nakai haka kyau,Meenat tace bakya fito da kyan naki ne ai ke kullum ke kike maida kanki baya.

    Nace a haka dai duk kwalliyar taki aka hadu da Kwaja kuma,Dukana tayi a baya da wasa muna dariya,tace Allah sai na kai kararki,nace yawwa gobe zan kaiku ku gaisar da Baban Aayan,Allah ya kaimu.
    Nace bari nasa takalmi ko?tace ae kisa me tsini ki Bada mamaki yau,ai ko na dakko cikin sabbabinmi wani Brown me tsini wow wow na gama birgewa yau ko uban waye ya ganni yau sai yawunsa ya tsinke indai Namiji ne.

    Ina cikin gwada yanda zanyi Tafiya Meenat tana gyara mana dakin muka ji Karar motoci,nan take na zaro Hijab Meenat ta fisge ke wai mene haka bayan kin gama kwaye cinya ya gani dan Allah muje palo,duk sunyi kwalliya Meenat cikin Doguwar rigar arab,Maeesha English wear tasa riga da Wando suma sababbi sun sha kyau,mun baza turaruka,ni kuwa kamshin nawa daban ne da nasu.
    Knocking muka ji nace wayyo kunya nakeji gashi nan zai ce sonsa nake,Meenat taja tsaki tace tonawa kanki asiri ki huta,Maeesha ce ta bude kofa ni kuma na hakimce a kujera na maze ina danna yar nokia ta ka rantse wata shegiyar waya ce nake chat ko wani abu.
   
    Wow wani Balarabe ne ya shigo Aayan sanye da farar fitted jallabiya yasha kyau kamar me don ya canja style din gyaran gashi na ala tsine uwar me karya.

    Kamshi ya cika gidan,cikin Securities wani ya taho zai shigo masa da akwatuna sai muka ga ya juya da Sauri ya bude kofar yace jeka daga nan ma is ok,da kansa ya shigo da akwatuna har Uku masu kyau na gaske.
    Sallama muka amsa Meenat ta kifta min ido na mike jin karar takalmina ya kalleni muka hada ido,na tafi da shi Amma sai muka ga ya tamke fuska,naje har gabansa na makale murya can kasa nace sannu da zuwa Aayan.

    Bina yayi da kallo yanda na sheka kyau ba a cewa komai,akwati daya na karba,Meenat ma tazo tace Sannu da zuwa yaya,da fara'a ya amsawa Meenat yace ya gida ya schl,tace lfy,Maeesha kuwa hannu ya bata suka tafa har suna dariya,tace yaya dama tuntuni Meenat take nemanka zata kawo ma karar Sis Mufee wani me Katon ciki ne  cikinsa kamar Randar Ammah yake zuwa wajen Meenat wuyansa Allah kamar bulalar malaminmu,shine Sis take ta tsokanarta tana mata dariya.da gaske ya tambaya yana kallon Meenat da yake duk yarane da Sauri Meenat tace ae wlh tun rannan kullum sai ta min dariya har da dare dan Allah yaya ka koreshi in yazo,ba damuwa in yazo ki fada min yace tare da Haurawa Sama,daya bayan daya na dinga kai masa akwatunan har Bedroom,ya shiga wanka lokacin na sakko kasa naji ana buga mana kofa nasan bazai wuce jarabar yan gidan ba,ina lekawa na hangosu kuwa mata da maza manya da yara na bude tare da cewa lfy? Basu gane ni ba sabo da kyau,Ke dalla matsa gidan ubanki ne? Juyawa nayi dan su kara ganin yanda na hadu,gaba dayansu da kyar suka gane ai nice, da mamaki sukace wajen dan Uwanmu muka zo ko kina da gado ne a gidan nan? Na yatsina fuska nace ku koma sai gobe da Safe a halin yanzu Bazan iya Barin me gidana yaga kowa ba dan karma a bata mana Mood, yanzu na boye abina na Adana mijina,na killaceshi baza kuzo ku Sa masa tention ba aikin banza sai roko da san abin duniya duk abinda ake muku bakwa gani sai kun shiga hakkin iyali ba dama mu gabatar da Sunna cikin kwanciyar hankali Naja tsaki kafin suce komai na banke kofa na kulle nasa lock nayi tafiyata.







AsmaBaffa
[1/13, 12:33 AM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

   KASUWANCI NA




          51-55




Official




By
AsmaBaffa






       Ina matukar baku hakuri fans na rashin posting dina jiya ayi min Afwa bana nan unguwa naje,yau kuma baki nayi shi yasa ban samu dama ba.



   
         Wannan page dina ne AsmaBaffa🤣🤣🤣nima na bawa kaina da kaina.







     Meenat suna ta karatunsu na wucesu na shiga kitchen tare da shiryo abincin Aayan na kai har Bedroom dinsa yana wanka bai fito ba dama wankansa dade wa yake sosai,ina zaune Saman Bed dinsa sai gashi ya fito daga shi sai dan gutun towel a kugu karami a wuyansa,jikinsa abin kallo ne ya hadu da yawa ko kai waye sai ka kalleshi sabo da kyau,dan kar yace ina kallonsa kawai sai na sa yatsana na tsakiya a baki ina ta tsotseshi na sadda kaina kasa,har ga Allah ban san ma na sa Yatsan a bakina ba, ina ta yi ya juya baya yana ta shirinsa don bazai iya kallon tsotsar yatsan nan da nake ba bilhakki abin so childish.

    Tunawa nayi da salona na wayo da zan masa tunda na Canja taku na,sai na Mike a hankali na taka har gabansa dama na cire takalmin dana sa Already,kunya da tsoro suka taso min sai na dake na matso lotion din da yake tsafawa na murza a hannuna cikin wata murya da ban san na iya ba nace kawo na tayaka baka iya bama sam kawai ban jira amsar sa ba na daura hannuna a kirjinsa tare da cewa mutum kato bai iya kula da kansa ba,suman tsaye yayi amma kuma sai naga yaja baya da sauri ya matsa tare da cewa kee mene haka,na nuna ban gane ba nace da akayi me? Ka tsaya mana na kara matsawa da sauri yaja baya again kamar yaga dodo, na bishi zan kara damkoshi sai naga ya ja da baya da gudu,na fara dariya ina binsa yana guduwa,na bishi muka fara zaga dakin da gudu dan sosai yake guduna kamar kamar yaga wani zaki ko Damusa,ina ta binsa ina dariya shi kanshi dariyarsa yake kunshewa yana yin kadan yana ke wai mene haka bana so, nace Allah sai na shafa ma,muka zaga ta bayan sofa ya daga kafa zai haura ta saman Sofa lokacin na kamo Damtsensa da hannu biyu sai ya fada saman Sofa  nima na bishi muka fada kai gaba daya ba shiri ya saki dariyarsa,nima haka na cikwikwiyeshi yana so ya cireni a jikinsa amma na rikeshi kam gaba daya a jikinsa na Dafe,da kyar dai ya kwace ya Mike ya gudu Saman Bed gaba daya ya shige blanket,sai kansa a waje,nace dan Allah ka tsaya mana wai mene? Yace ke tsaya a nan karki matso nan,Na tsaya a hankali nace shike nan tunda baka so bari na zauna a gefen Bed din naka,yace no sai dai in baza ki taba min jiki ba to ki zauna,ai nace na fasa Zama kawai zanyi.

    Ka tashi ka karasa shirinka Kaci abinci sai kayi baccinka,kaje wurin Daddy? Harara ya mako min ke wai nan nufinki wata mace ce har wani sani abu kikeyi kina tambayata abu kanki tsaye,ni da Daddy na me ya shafeki a ciki ki daina min shishigi tam.

    Allah ya baka hakuri dama tuna ma nayi,sakkowa yayi daga saman Bed din ya karasa shirinsa cikin kayan bacci masu kyau na maza ruwan toka,s aman carpet ya zaune dake dan gefen bed din,yana bude flask din yaga Waina da miya nan take ya dinga zuba murmushi maimakon ya min godiya kawai sai yace dan sunkuyo zatona wani abu zai ce kawai sai na ji rankwashi a kaina kwasss Gift ne wa ya fada miki ina son wannan? Anyway tnx da sauri na Dafe wajen nace ouchhhh ina turo baki cike da shagwaba nace da zafi Allah yanzu da kai na yiwa haka da tuni ka fara fada,abincinsa ya fara ci bai ce min komai ba,har ya gama yayi Brush ya fito tare da yin Nafeela raka'a biyu,lokacin na kwashe kwanikan na maida tare da gyara wajen,lokacin yana shafa addua ya idar.

    Saman Bed ya haura bai ce min komai ba dan ni Jarida nake ta buduwa ina kallon hotunan labarai,tunawa nayi ban fadi me ya kawoni ba,nace dazu mun dade da Daddy Muna ta hira,gaskiya Daddy yana da kirki sosai,kayi sa'ar uba Allah yaja kwana ya kara masa lfy me amfani,sabo da na yabi Daddy tare da masa addua sai naji yace dawo nan ki bani labari me yace miki ya furta yana nuna min gefensa da Hannu,naso naki zuwa amma kwarjininsa baza su bari na masa musu ba Sam,haka na Mike naje tare da hawa saman Bed din sosai har tsakiya kusa da jikinsa,kawai naji yanayina yana canjawa sai na tsinci kaina da son kwanciya a jikinsa musamman da naji laushin fatarsa dazu ga kamshi,du sai na diririce abinda nazo da niyyar na fada cewar a sakeni na fasa auren sai na kasa na manta ma da zancen Sam,sai naji kuma shagwaba ta motsa ba abinda nake so irin nayi abata na samu me biye min amma ba dama,a raina nace ke kina yar yarinya haka,muryarsa ce ta katsemin tunani da cewa ina jinki, kawai sai na susuce na rude abinda ya rambayeni daban abinda nake bashi amsa daban na riga da na zauce sabo da ya hadu da yawa.
    Na jingina da jikin Bed din nace hmm dama Ashe Umrah kaje bamu sani ba? Yace ae mana,me kika yi wa Daddy? Nace kudina ya kare nazo nan na dauki 5k ciki ka irga abinka kar kaga babu kace nice shima ba yanda zanyi su Meenat zasu je schl,yace Ok  Daddy yace miki wani abu? Ni dai ko jinsa bana yi wani iri nake jin jikina nace uhm...uhm...turarenka ma jiya nazo na fesa maka,amma kadan na fesa kar kaga ya kare kace nice, kalau kike kuwa ko aljanun sun motsa, kamshinsa ya gama gigita min rayuwata sam na kasa gane kaina,duk Ac da ke wajem gumi na fara yi,a hankali jiki ba karfi na zame dankwalina gashina me uban tsayi ya watsu ya kara wani kyau, bai kawo komai a ransa ba tunda yasan shirmena kuma kallon yarinya yake min har na Isa ma wani feeling,a hankali ya juyo kamar me rada yace ko baki da lfy?, Nace ni ina zan sani  lfy nake ko kalau bazan iya ganewa wanne yanayi ake ba,sanyi ne ko Zafi,zamewa nayi tare da kwanciya a saman bed din tare da lumshe ido nayi shuru ban kara magana ba nayi shuru,tasar min a bed ki tafi to tunda ke ba a abin hankali da ke,shuru bance komai ba,ya matsa na bar masa bed ni kuwa tuni jikina yayi weak da yawa bana son ko nayi motsi ina daga kwance nace kawai labarin gidan nan fa Daddy ya bani, to shine kike min shirme abinda na tambayeki daban amsarki daban? Banza nayi dashi,shima bai sake magana ba ya juya min baya tare da kashe light ina jinsa yace tunda baza ki tashi ba sai ki shekara a bed din,shuru na masa har ban san bacci ya kwasheni ba shima haka.

    Karfe daya na dare na farka na tuna maganar da zan fada masa ni ko dama komai dare idan na tuna zan fadi magana ban fada ba indai mutum na kusa dani sai na tashe shi,ba bata lokaci na kai hannu saman gashinsa na ja da dan karfi firgit ya tashi da masifa,hannu na kai  da niyyar nace Aayan zan dan bigeshi,caraf ya rike min hannu tare da juyowa daf dani muna facing din juna har muna jin numfashin juna,a hankali yayi magana ki daina taba min jiki,kinzo kin dameni menene,sai na kara mantawa da maganar da zan fada ta a sakeni,yanda naji hannunsa cikin nawa me laushi ga kamshinsa dake kashe min jiki sai nace ruwa zan sha,Ke haka kike dama kamar yar 4yrs ki hana mutum sakewa kuma haka kike kwanciya da kayan jikinki ke? Nace a'a yaune kawai,haka kawai kizo ki takura min ya Mike tare da kunna light ya miko min robar ruwa daya,ba shiri na bude na Sha ta dole,akwatin da yazo dasu daga Saudiyya ya bude tare da Zaro min wata sabuwar rigar bacci hadaddiya amma fa tayi tsaraici  gata fara wata silk ce yar guntuwa me hannun bra,in kasa komai sai an gani duk wani tudu da gangare,ina gani nace zan tafi Dakinmu ni,Murmushi yayi tare da komawa jikin kofa na dauka bude min zaiyi na tafi sai naga yasa lock ya dawo yace ungo tashi maza ki cire kayan nan,a ransa yace zaki takura min gwara nayi maganinki.

    Hade rai yayi kamar baya dariya ba yanda na sanshi tun farko,na tsorata yace get up ko yanzu nazo na fara ball dake tunowa nayi da yanda ya taba min farkon ganina dashi,da sauri na Mike na karba na kasa cire kayan na tsaya kawai,a hankali ya matso tare da rungumoni na kwanta a jikinsa ina ta salati a raina don wani zirrrr nakeji tun daga kaina zuwa kafa ta,zip din rigata ya zuge na kwace jikina da sauri na ja da baya zan tsere da zafin nama ya biyo ni tare da jawo rigita na dawo baya ina dariya shima haka,har mamaki nake dama yana dariya,ido muka hada sai naga idonsa kamar ruwa a ciki yayi dan red,ganin ina kallonsa kawai sai ya dauke kai tare da juya min baya yace na baki 2mnt ki canja idan kika sake na juyo wlh sai na miki sintir.

    Da sauri na cire kayana daga ni sai pant nace kar juyo na kusa da sauri na zura rigar a jikina dukiyar Fulani na yan matasa ana kallonsu da adadin girmansu,Na ninke kayan dana cire harda bude Sip side daya na adana abina kun San ni akwai tattali sabo da an saba da babu don wata tsaftar ma akwai babu a cikinta.

    Juyowa yayi yaga yanda nayi mugun kyau a ciki yace cire min a bata na fasa dama lefen wacce nake so zan aura na fara hadawa shine na baki daya sai naga ma bata miki kyau ba Ciro min a bata ba size naki bane nata ne, wani bakin ciki ya kamani tun ba ayi nisa da business ba za a ce aure za a kara,sai na tuno dama fa yayi aure ba sau daya ba yana saki,a raina nace me auri saki ne nima Sakina za ayi,da kyar na daure bacin raina na kakalo murmushi nace Allah ya sanya alkhairi kace zamu Sha biki ai ranar za a ga yanda zan kwashi rawa,kai amma naji dadi sosai kaga an samu me Kula da kai wacce rake sonka kake sonta haba ai Alhmdllh naji dadin wannan magana ka kuma birgeni da sauri da sauri nake maganar ina murmushi harda yar dariya kamar na zare, muryarsa naji yace tnx lallai kina da hankali na yaba da hankalinki kwarai ba ruwanki baki dauki duniya da zafi ba,sai ki dinga min abin cin gargajiya tunda nan kika kware ita kuma dama tafi iya na bature,cikin bacin rai da fusata na hayayyako masa da masifa dake ni tsinanniyace ko? Sama na zaga ko me? Kanwa na kawo? Wlh bazan kara kulaka ba bare har nama girki,auren Kasuwanci mukayi dan haka duk kudina ka tattarosu ka biyani gaba daya na kara gaba,kawai ka sakeni na gaji dama sai kawai na fashe da kuka sosai,da mamaki ya kalleni,cikin kuka nace bani takadda ta,wannan gidan naku bakin gida du ba na gari a ciki sai Daddy kawai gaba daya bakin Uwa ne a gidan banda Daddy,dariya ce ta kamashi ya dinga yi ni kuwa ina ta jin haushinsa,yace to kwanta gobe Insha'allah zan baki komai da kike so har sabon gida sai ku koma can da zama sannan na baki takarda abinda kike bukata yanzu,k karki damu kwantar da hankalinki indai wannan ne baki da damuwa,tunowa nayi da maganar Daddy cewar duk Wanda ke son rabuwa ba matsala za a rabu,naji wani mugun bacin rai ni rabuwar bata Dameni ba sai da naji yace wai aure zaiyi.

    Hannuna ya jawo zuwa saman Bed tare da cewa kwanta ki huta kiyi baccin karshe a gidan nan gobe zaku tafi,bazan huta din ba nace cikin fushi, kwanciya yayi a gefe na tare da kwantowa a samana yace tsaya kiji ina da nauyi? Nan take naji wani shock na gaske a dukkan jikina,nayi luf ya kwanta flat a samana kirjinsa saman nawa,wasu tsutsotsi naji yam yam a jikina ko nauyin nasa banji ba duk da cewa Bai sakar min nauyinsa ba, hannayena na zuro ta bayansa tare da sakalesu na rungumeshi nace baka da nauyi wai wayo nayi kar ma yace dadi naji gaskiya kuma abinda nakeji ne yasa na kasa daurewa sai da na dangana da rungumeshi.
    Gashina ya kalla me kyau da kamshi ya shafa a hankali yace ba laushi ma kamar ganyen bishiyar Dabino,murmushi nayi nasan ba gaskiya bane,na nutsa hannuna a cikin gashinsa me matukar santsi da laushi na kalleshi nace ina Sam taka Sumar kamar ta gyartai me gyaran tukunya da karfe,ni a raina dama so nake na taba Sumar shine na samu hanyar nayi masa wayo, hancinki yayi fadi da yawa duk bana ganewa me yake nufi ai nice kawai nake masa wayo,naja dogon hancinsa nace ai nawa yafi naka,yana karewa Lips dina kallo yace ke a tsorace na kalleshi yace ai bakinki yayi girma da yawa sai kace kofar gari,lips dina na turo tare da shegiyar Shagwabar da na zuke masa jini nace ai gwara nawa Allah,kalla na bude masa ka gani dan karamine wa zai ce spoon zai shiga nan? Ba wani nan cewarsa,ido na juya masa yana kallo na idonsa kamar ruwa ruwa ciki,ido muka hada da sauri yayi sama da kansa dan kar na gane yanayin da yake ciki,Aayan mene?na tambaya a hankali,murmushi yayi da saurin yana goge idonsa yace nothing me kika gani? ba komai I just ask never mind ok na furta irin naje schl fa,murmushi yayi tare da cewa kin san me yasa kike bani mamaki? Nace a'a duk wannan abun da muke yana samana a kwance,yace karfin halinki ne yake bani mamaki yana maganar yana kallon lips dina,a hankali ya gangare gefe daban yana cewa Good night ga key nan ki bude idan zaki tafi.

   Ban so ya koma ya kwanta ba sabo da ina jin dadin hakan banki mu dawwama a haka ba, munyi shuru kowa da abinda yake tunani,muka ji ruwa me karfi ya tsuge kamar da bakin kwarya,mikewa yayi tare da bude duka windows din nan take sanyin ruwan da ake da iska ya ka dakin gaba daya,Ac ya kashe da light,walkiyya fal fal tare da tsawa taratsatsa ake ta yi ba tsayawa,na tsorata dan ban son walkiya da tsawa ga window a bude muna hango komai,blanket ya jawo ya rufa mana gaba daya harda ni,ina ji ana tamfatsa tsawa,da aka saki wata ban san sanda nayi sauri na matsa kusa da jikinsa ba daf  dashi kamar zan shige masa amma sai ban ko taba jikinsa ba,bai san na matso ba ya juyo zai tatsileni duk girmana yar karama nake tashi a gabansa,kaina ya koma sam kirjinsa,kamashinsa ya bigeni, tsawa aka kara rankatawa me karfi na shige jikinsa sosai tare da kankameshi,duk dauriyarsa kasawa. Yayi sai da yayi hugging dina back,fuskata a saitin tasa a hankali na tsinci muryarsa yace tsoro?nace yeah wai ni baturiya,kina so ki daina Ji? Kai kawai na daga dan yanayin da nake ci bazan iya magana ba.

    Tafin kafarsa yasa a nawa kafar yana gogawa a hankali,cinyarsa ma tana gugar tawa,laushi da laushi sun hadu sai wani lumus kake ji,gashin jikinsa me santsi yana min wasu rubutu me lankwasar dadi😄 dadin ma Kun San har da me Lankwasa
     Ni ba gane me yake nakeyi ba dan nauka tsoron da nake ji na tsawa yake min maganinsa har ga Allah na manta ana wani abu idan anyi aure,kuma bayan haka ma ai nasan shi ance bashi da lafiyar da zaiwa mace wani abu,shi yasa na kara samun nutsuwa bana tunanin komai, fuskarsa ya daura saman tawa yana goga hancinsa a nawa,da kyar naji yace baki da hanci Ashe, kasa magana nayi sai da kyar nima na kara goga masa nawa back nace wannan kaine gashi me tsayi,bakinsa naji kawai cikin nawa sai da numfashina ya dauke yanda naji abinda yake min me tafiya da nutsuwar dan Adam,tuni ni na manta ma ana wani tsawa da ruwa tana ta rugiginta ni kuma muna rugurguzar juna,bakina yake tsotsa kamar zai cinyeshi,gaba daya na susuce shima haka,a hankali yace a barshi haka kin daina Jin tsoron? Nima naji dadi bana so a daina sai na shirya masa wayona shine da shagwaba nace ni dai tsoro nake ji zan iya suma gaskiya kuma har yanzu ina ji, dariya kawai yayi a ransa tare da Hamdala yace kai duk wannan abun amma kike jin tsoro gani a kusa,ni har na ma gaji amma dai shike nan bani tongue dinki, like how? Na tambaya,Ya ake mikawa mutum hannu ko wani abu,zaro tongue din kadan nace uhmm,Hhh dariya yayi yace sai kace miciji ya zaro harshe, karba yayi yaci gaba da gudanar da kiss dinsa sosai har lumshe ido nake ban san sanda na fara taimaka masa ba, wuyana yake shafawa tare da Sakkowa saman kirjina,nan take ya birkice ya koma wani iri,Nima haka nayi mukus dani ina ji yana murzasu ba da yawa ba naji kwakwalwata baza ta dauka ba sai na janye jikina da sauri nace na daina Jin tsoron,dake Ya kai karshe a duniyanci sai yayi murmushi tare da cewa har kin daina Jin tsoron? mace ae ni dai bacci zanyi,bai kara ce min komai ba ya juya ya fara addua ban san sanda bacci ya kwashe mu ba.

    Washe gari muna yin Sallar Asuba na tuna akwai schl yana Azkhar nima nayi nawa na Mike tare da maida kayana da sauri ina ka tashi ,yace Alhmdllh nayi waje abina Kitchen na shiga,sharp sharp na soya mana chips da egg sai ruwan tea na shirya komai a Dining,sai ga su Meenat sun fito cikin shirin schl dinsu,Sis ina kwana? Cewar Meenat kun tashi lfy? Sukace lfy Alhmdllh.
   Ma'eesha tace a Palo kika kwana sis jiya bamu ganki ba,Kunya ce ta kamani nace ae a Palo bacci ya kwasheni,Meenat tace a fadi gaskiya dai sis a kunne ta rada min ya akayi ne daga cewa kin canja salo sai ki dawowa har palo na  fito bakya nan,Dariya nayi nace hmm ai ke dai bari Meenat ai na fada miki so nake mu bar gidan nan,zuwa nayi na takura masa kwana nayi ina masifa sai ya bani takarda ta, fada mukayi sosai,Meenat ta dauka da gaske ne tunda tasan Mufeeda bata musu karya,nan take gabanta ya fadi kamar zatayi kuka tace haba dan Allah Mufee kamar baki da ilmi wannan ai tsarin addini bane bai dace ba,dan Allah karki tozarta mu muna rufin asiri samun miji kamar Aayan sai an tona,ki tuna da shawarar Ammah sis,Maeesha ma tace dan Allah sister karki bari mu bar gidan nan,ni kuwa bata rai nayi kamar gaske nace karku dameni na gaji duk ma yanda za ayi ni bazan zauna dashi ba,shi yasa jiya ban bari mun kwana lfy ba
    Meenat ce ta fara hawaye tace bakiyi halacci ba wlh.kuyi sauri Kuci Ku tafi schl,sai suka ce mun koshi su wai sunyi fushi baza suci ba,ku zauna to bari na fito,zama sukayi ni kuma na shiga wanka da sauri na shirya kaina cikin doguwar riga ta Atamfa dama na iya dauri yanzu wajen Meenat na kafa shi na zuba kyau,ina fitowa kamar mun hada baki sai gashi shima ya fito cikin shadda milk color ya Sha kyau kyau kamar a saceshi,agogon dake hannunsa ya kalla yana sakkowa daga steps,Dining ya nufo kamar bai sanni ba,kallona bai yi ba,abin ya bani mamaki mutumin da jiya muka kwana lfy,Su Meenat kawai yake kulawa suna magana yana cin abincinsa,Meenat ganin hakan da yayi y nuna sai ta tabbatar da gaske jiya rashin  mutunci nayi masa,nan take taji tausayinsa tare da jin haushina, ina lallashinsa suci abinci amma suka ce baza suci ba har haushinsu ya kamani nace Ku tafi ai cikinku ne kuma sai dai ku tafi a motar haya yau ko napep hukincinku kenan na bijirewa maganata,Hararata Meenat tayi ina kallonta Shima Aayan ya gani yasan suna min biyayya suna da tarbiya tunaninsa ko wani abu nayi musu, nace Meenat me kikayi ba dai ni kika harara ba? Kunkuni tayi,nace I saw u now zaki san ni kika yiwa rashin kunya ke kina ganin kin girma ko nawa kike har ina miki magana kice zaki harareni sabo da ina wasa daku,nifa ba hararki nayi ba,tsawa na daka mata ni irin Babba din nan dalla jeki stupid Girl,Maeesha tace amma kin San munyi late zamu makara da yawa,shi dai yana Shan tea yana jinmu, baiyi nisa da fara sha ba ya Mike shima tare da cewa ga tea dinki nan nima bana sha muje na saukeku a schl Meenat.

    Ina tsaye suka tafi ni kuwa dadi naji yana kula yan uwana ko bai kulani ba in dai ya kula yan uwana Alhmdllh,akan ya wulakanta min yan Uwa gwara ni yayi min ko mene,sabo da wasu kai kadai suke so duk Wanda ya shafeka basa saurarsu bare su taimaka musu sai iya matarsu ko budurwarsu,Meenat suna fita suka hango Kwaja yana wankewa su Sajida takalmin schl,da Sauri Meenat tace Yaya Aayan ka ganshi to dan iskan da suke hadani dashi shegen ciki kamar an kifa kwarya.

   Koda Aayan ya kalli Kwaja bai San sanda ya saki dariya ba tare da cewa lallai an cuceki am so sorry su Hanifa yan iska ne,kamar ya sani sai ga Kwaja ya dago kansa wanda ke dauke da keya me shegen tsini goshi rafkeke ya bude baki hakoran gaba cako yana sakin murmushi yasha uban askin kwal kwal jijiyoyi a kansa rada rada ya dago sirisiri hannunsa saitin Meenat yana kifta mata Ido kamar na Kwado, Kuka Meenat tasa sabo da takaici,Aayan da kansa ya kira Kwaja ya masa warning kar ya kara ganinsa ya kalli ko fuskar Meenat,kuma ko gidansu ya daina shigowa ya dinga tsayawa bakin gate,a gigice Kwaja ya dinga bada hakuri kan ba zai sake ba.

    Bayan na gama komai nawa dana saba na gida shirin schl nayi 1:30pm Driver ya kaini schl tare da kawata muka hadu Sayyah,Muna hira Sayyah tace tunda kina da aure ki dinga zuwa gidanmu ana miki gyaran jiki,Maman Mu tanayi har shagon gyaran jiki ne da ita,idan kika je a gida ma zata miki naki,kuma gaki best frnd dina naga ke yarinya ce baki ma san auren ba,zata koya miki komai ta dinga tsumaki Oganki yaji zam zam,yanda kike me kyau fara idan ta gyara miki jiki sai Oga ya zauce wlh.

   Baki na tabe tare da cewa ke ni bazan yi ba Natural wanda Allah min ya isheni yanzun ma a haka kinga yanda yake bani wahala ina ga na kara wani abu,Karya nayiwa Sayyah dan karma taji sirrin aurena amma sai ta dage wai dole na samu time a dinga yi min ko duk wata sau daya ne,sannan a bani na tsumi nasha,a raina nace hauka nake na Sha tsumi me gida baya ko kallona kuma ko yaushe zai iya Sakina mu rabu,jiya ne ma kadai muka taba hada makwancin shima hakan nice na je tsautsayi yasa kuma ban fadi maganar data kaini ba na bige da kwana a can,a fili nace Sayyah kenan zanzo to amma sai na sanar  masa,kirashi a waya ki fada masa yanzu muji,sai yanzu na tuna bani da Number sa shima baida tawa amma sai nace yana Office yanzu he is busy sai na koma gida,tace to shike nan zan fadawa Umma ,nace ba matsala Insha'allah.

   Muna cikin class 4pm Saura 1hr a tashemu sai naji wani malami ya leko ta window wace Mufeeda Adam Fatima?nace Sir tare da daka yatsa sama,yace zo kinyi bako,Mamaki ya kamani bako kuma ni to wa na sani,Haka dai na daure muka Mike ni da kawata Sayyah cike da tsoro na fito motocin Aayan na hango mamaki da tsoro ya kamani ina ta Addua a raina nace Allah yasa lfy dai,Sayyah tace waye wannan haka wani hamshaki? Mijina ne,Sayyah tace kut dama kece matar Aayan Muhd Jabeer ta yanzu? Nace ae mana kin sanshi ne? Tace a labarai muke ganinsa a TV kuma akwai wata yar kawar Umma yar gidan Minister of finance ta Dade tana binsa tana sonsa sosai ta dinga kiransa duk inda yake sai ta nemeshi amma Sam ya dinga Wulakantata baya sonta,har yanzu bata hakura ba wlh sonsa takeyi,akwai ke yan mata da yawan gaske da na sani suna bibiyarsa don kawai ya kulasu amma ko sauraransu baya yi,nan take gabana ya fadi, bakin ciki ya taso min na fara masifa wlh idan ma kin Santa ki fada mata kar ta kara kiran wani da namiji a waya,aikin banza amma wannan kwai jaka, dabba, Akuya, tinkinya inba tsinanniya ba mene na bin mijin wasu a waya asararriya wacce ta rako mata duniya.

   Sayyah shuru tayi tana kallon yanda na dage nake ta zazzaga masifa da zage zage,tace lallai kishinki yayi yawa,nace ai ba kishi nake ba kawai haushi ta bani mace na bin maza tana zubar da ajinta,Dariya kawai Sayyah tayi tace to nidai na koma class tunda mijinki ne bye ta juya abinta,a hankali naci gaba da tafiya kafin na karasa motarsa kawai ya fito ya tako har inda nake tare da kamo hannuna ya jani ya sani cikin mota ya shiga Suka ja motoci muka bar schl din gaba daya.

     Nace lfy?bafa mu tashi ba,yace ae ni na tashi daga Office yau kuma abinci nake so kiyi min 5pm Yarima Bobo zaizo, shuru nayi ina gefensa a baya nayi shuru har muka karasa gida muka fito da sauri ya rike hannuna yana Jana fiiii,har cikin part dinmu,Hijab ya zare min ya kaini har kitchen yace fara masa Abinci me kyau yana son Founded yam da miyar kwai,nace to da sauri na fara aikin shi kuma ya fita,nan danan na shirya lafiyayyan Sakwara da miyar kwai tasha nama da alayyahu tayi dadi sosai,na hada lemuka kala biyu na zallan fruits me dadi yayi Sanyi,na shirya komai a Dining sannan na gyara kitchen din tare da kara gyara part din sosai.

   Bedroom na koma tare da fesa wanka na shirya cikin wata Atamfa cotton Orange riga da skert na Sha kyau sosai nayi kyau na gasken gaske,ina kamshi na hau Saman bed dinmu na kwanta ina hutawa 15mnt sai gashi ya shigo sanye cikin jallabiya fara yace muje Ku gaisa,na Mike haka nayi hanyar fita,
    Ya riko hannuna tare da juyo dani baya yace haka zaki fita? Nace mene to a nan?nayi waje abina a haka,da sauri ya jawo ni tare da cewa ki canja kaya bakiyi kyau ba kisa doguwar riga,banyi musu ba nasa Arabian Gown tare da mayafin kamar Balarabiya na fita har Palon da suke.






AsmaBaffa
[1/14, 4:32 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

   KASUWANCI NA



             56-60





Official




By
AsmaBaffa




    SEEYAH IBRAHIM and UMMU SOPHIE ths page is for u tnx.






        A kunyace na Zauna a daya daga cikin kujerun palon nima sannan nace Ina yini kazo lfy,cike da fara'a ya amsa lafiya Alhmdllh Madam, daga mari kuma sai kuka koma Ma'aurata, murmushi nayi tare da cewa ai ka fini Sanin komai,dariya yayi yace gaskiya dai ai nasan watarana in kika ji labarin yanda na tsara sai kin bani gift ma,ya dai baka gift tunda Ku kuka San me kuka tsara,Aayan dai yana jinmu bai ce komai ba na Mike ina cewa ga abinci Fa yana Dining ko na kawo ma nan? Yace ai dole naci girkin Amarya guda kamar ma kin San yunwa nake ji,kai tashi Malam naje naci abinci.
   Mikewa sukayi har Dining suka zauna nayi Serving dinsu, Yarima sai murna yake yi abin cin da yake so ne,suka fara ci Lauma daya Yarima ya fara Santi uhmm kaga yar yarinya da iya girki shi yasa naga mutumin sai kiba yake yi da kyau, Dariya nayi wace tasa nayi wani mugun kyau.

    Tsaki muka ji ya ja tare da gasa min harara,shuru nayi tare da sadda kaina kasa,kallona yayi tare da cewa je bedroom ki dauko min wata paper saman Bed,ok nace tare da mikewa zan tashi kawai na bige flask din miya ta dan zubo min a hannu ga Zafi sosai,hannuna na yarfe tare da cije lips dina,da sauri ya Mike tsaye tare da rike hannun nawa yana min sannu ya tsotse min yatsun da miyar ta zuba yana hura min da bakinsa kuma fuskarsa ba alamar rahma Sam sai ma fushi da yakeyi,ni dai kallonsa kawai nakeyi har ya gama ya kalleni tare da cewa ba Zafi? Kai na daga tare da cewa yeah,jeki to ki kawo min.
   Ina tafiya Yarima ya dura masa ashar yana cewa amma kace min wani fada ma kukeyi munafuki,to me nayi na wani soyayya a nan? Ku fa bakwa ganewa Hausawa ba dama aga mace da namiji sunyi ko magana sai ace wani love ni zan iya kwana da mace same Bed naked ma ba abinda zai faru.

   Dariya Yarima ya dinga yi yace Allah ya taimakeka ba kyau ganin sirrin wani da sai an gwada na gani a gabana,kai har kana da bakin magana dan Iska da ban sanka bane sai ka fadawa wani abinda har wani Fyarfadiya kakeyi idan ta ciwo ka shine zaka zo kana min kuri,Dariya  Aayan yayi tare da lashe lips din kasa kamar an tuno masa wani dadi daya taba ji yace lfy ce yaro,Kai aka bawa wahala wlh tunda kana iya sha'awa amma baza ka iya aikata komai ba akwai wahala abin har tausayinka nake ji frnd,Aayan yace kama daina tausayina yaro ni ba abinda nake ji,suna ganin na fito sukayi shuru tare da canja hira basu San naji komai ba,mika masa nayi na zauna kusa dashi a Dining din nima harda leka cikin paper daya bude nace mu gani,miko min yayi sai da ya bari na karba yace to ki rike du tunda Sa'idon naki ya kai haka,Murmushi nayi  tare da mika masa nace amma da niyyar karantawa nayi tun a dakin zan tsaya na duba yanzu ma izininka nake nema,yace bazai karba ba Sam yayi fushi na masa shishigi, mikewa nayi da paper zan tafi ya jawo hannuna ta bayan kujerarsa na zagayo  tare da zuro kaina a hankali ta saitin kansa fuskata na daura a wuyansa nasa hannayena tare rungumesu ta kirjinsa sannan na rada masa a kunne ina dariya ga paper dinka Dan Daddy mene na fushi na daura saman table din na juya tare da barin wajen na shige Bedroom.

    Yarima yana ta dariya yanda yaga Aayan yana jin kunyarsa,yace ah to yarinyar nan naga Alama wise ce kai a boye kake yi kana mana karya gashi ita wlh ta birgeni baka taba auren ma irin wannan kalar ba sauran tsoronka suke ji magana basa iya yi maka,haka idan munzo basa iya zama a kusa da kai tare da bakinka lallai kana kwasar Harka wlh ga shawara ka fara tunanin fara Sex da wannan maybe ma ka warke kake batawa kanka lokaci, Allah kiyaye da wannan yarinyar karama ai sai na balla mata Hips cewar Aayan,  nan dai suke ta faman zancensu ban san me suke shiryawa ba sai tafawa suke suna dariya.

    Bayan kwana Uku muka shirya dasu Meenat mukaje tsohuwar unguwarmu tare da gaisawa da abokan arziki a dalleliyar mota,kowa mamaki yake,Nawwara ma yanda taga mun canja mun koma yan gayu ga hutu ya nuna a jikinmu ta dade tana mamaki, na bata Address na gidan mijina,Haka Uwaliya still suna zaune a gidanmu nace su zauna sai nan gaba zan gyara gidan.
    Mun shirya dasu Meenat idan anyi Hutu zasu je Maiduguri dangin babanmu tare da Rimin Gado dangin Ammah can zasuyi Hutu sabo da zumunci kuma muna kiransu a waya muna gaisawa.
   Tun daga Ranar da Aayan yayiwa Kwaja magana bai kara yiwa Meenat magana ba sai dai idan ya ganta a gefen gate ya fara lashe lips yana mata signa da ido ita kuwa sai tayi kamar bata gani ba.

    Ana haka wataranar Asabar sun dawo daga Islamiyya sai ga wani ya Parker a motar eban kaya wacce ake cewa yar Kurkura ya fito ya taresu a hanyar gida,wani dan Gajere daf da kasa kamar a kifeshi da kwando me kwalelen kai sai ka rantse baza a samu Hula size din kansa ba,harda sa wata barmemiyar suit tsohuwa tasha duniya,Handkerchief ya zaro tare da goge wani kwafjejen takalminsa ya kalli Meenat yace Hajiya Meenat ko? lfy Malam idan tambaya kakeyi kayi sauri muke,murmushi yayi tare da cewa yan mata kenan wato Allah ya zuba baiwa a nan wajen yana maganar yana watsa hannayensa kafta kafta yan gajeru dasu kutuf ,ya kara cewa Allah yayi Kudirarsa anan,baki ya rike yace kai Kudirar Allah kenan,harara Meenat ta maka masa,Maeesha ma taja tsaki yace ahh harda ke yar ficika? kema kin hadu har kinfi babbar ma naga kinji haushina ke ban yabeki ba mata akwai kishi to kema kina da kyau ai baki sani ba kinfi ma babbar kyau shike nan ko?

    Saura kadan Meenat tayi dariya kawai taja hannun Ma'eesha sukayi gaba,da gudu ya datse gabansu,in kina kaunar Allah ki saurareni in dai akan nace kanwarki ma me kyau ce to na janye dama dan kar ranta ya baci ne ace kamata bata ji yabo daga gareni ba naga tana kumbura shi yasa amma ai kin fita komai,kinga gaki fara,gaki doguwa yar tsakiya,ga sura,ga idanu,ga kamshi gaki me ilmi wayyo sai naji dama munyi aure,Meenat ta kara hade rai tace bamu hanya mu wuce,ya wani shagwabe fuska tare da canja murya kamar dan iska zan miki shagwaba Allah wayyo Baby,ai basu San sanda suka sheke da dariya ba,shi kuwa gani yake ai yaci gari ya birgesu,yace kin gani tun ba a je ko ina ba,ina me tabbatar miki zaki san Allah ya baki miji na gari,zan miki soyayya,zaki ji dadi,zan baki kulawa,zan miki duk wani abu wanda mace take so take nema a duniya komai,kawai ki bani dama,ki kula dani ki yarda dani zaki ji dadi,sai kinyi alfahari da wannan rana ta Asabar da muka hadu,da ace ana harba namiji sama ina tabbatar miki idan muka yi aure nasan sai kin harbani sabo da yanda zaki koma sona da ganin mutunci na,

   Bari kar na dameku da surutu sunana Nasuru ko kuma ki kirani da OPERA,amma a unguwarmu anfi kirana da Nasuru me Hali, yayi dariya ya kara goge rigarsa yace Business man ne ni ina da yara dasu ke ci a karkashina sanadiyar wannan motar da kika ganni da ita domin daya a yarana shike Jan wannan motar,mutum biyu kuma sune masu tayashi lodi da saukewa,ba inda basa kai kayan miya da fruits,irin su tomatoes,Kankana,ke in baki a takaice har yalo suke daukowa daga Sumaila zuwa Lagos Agege, da sauransu,Meenat taji baza ta iya ji ba ta figi hannun Ma'eesha suka barshi nan tsaye bakin gate,suna shiga suka hango Haneefa da Sajeeda sun labe ta jikin gate suna ta dariya da alama Nasuru Opera ma su suka turowa Meenat shi tunda sunga an kori Kwaja.
    Meenat ta hararesu su, sai kuma suka sheke da dariya Sajeeda tace a haka zaki kare in Allah yarda sai dai ki auri irin wannan wai ku masu kyau,anzo gidan daula za a ce sai me kudi zaku gani wlh nan gaba da kafarku zaku bar mana gida.

   Meenat tayi murmushi sannan tace masu gida manya gidan wasu dai har iyayen naku basu da gado a nan bare Ku,a haka zaku kare banzaye marasa class,tass Meenat taji saukar mari tana dagowa taga Mujaheed ne ya mareta gasu Ameer nan a tsaye suna huci,Ma'eesha tace Allah ya isar mana,aiko Mujaheed ba imani kato dashi ya zage ya dinga Marin Ma'eesha yar yarinya karama ya Ciro takalmi ya fara kwada mata ta ko ina tana ihu,Meenat bakin ciki yasa ta dauki wani dutse kato ta buga masa a kai nan take jini yayi tsartuwa a kansa ya fashe,ya Dafe wajen yayi baya Su Ameer sukayi kansa suka rikeshi,Kafin kace me gida ya dau Alert sai kowa ya fito harda Hajja,Su Meenat tuni sun arce part dinsu da gudu,lokacin Mufeeda ta fita shopping,Hajja Bala'i take zubarwa kawai a tsakar gida an kashe mata jika,haka Ma su Abbi sai gasu duk sun dawo da motocinsu gida,haka ma iyayen su Mujaheed mata har da kuka,aka daukeshi sai asibiti don tuni ya Sume,sabo da hauka gaba daya suka bisu asibiti kamar wani Gomna haka dukkan yan gidan,Matar Abbi da Hajja sai Haneefa su kadai ne a Compound suna jimami tare da shirin daukan fansa,suna cikin wannan Hali sai kicif ga Driver na mun dawo daga shopping tun daga yanayin da na gansu gabana ya fadi haka na daure na fito ban fito da kayan dana siyo ba sabo da nima cikin shirin ko ta kwana na fito,ina taku dai dai nasha wanka sosai,

Ban san me ya faru ba,ba zato naji sun rufeni da duka,sunfi karfina ma'aikata si hakuri suke basu amma suka ki ji musamman Hajja kamar mahaukaciya ta dinga dunkule hannu tana dukana,Haneefa da takalmi me tudu,Matar Abbi ma ta ko ina,har sai da Hanci na ya fara jini ina habo, ana haka matar Abbi ta kara dauko Wayar charger tace duk kowa ya kyaleta dani sai ta ramawa Danta haka ta dinga tsula min wayar nan  sai da suka min lilis,da kyar nake iya numfashi,sai lokacin hankalinsu ya kwanta suka koma can part dinsu suna murna.

    Ina kwance a wajen hancina na fitar da jini sai ga Aayan ya dawo ya iskeni haka,da sauri ya daukeni kamar Jaririya don shi yasan yan gidan ne suka min haka,kawai ya sani a bayan mota shima ya shiga gefena Driver yaja da sauri sai Hospital,a motar ya kwantar dani saman cinyarsa yana min sannu duk ya damu ya rude,Hadadden asibiti ya kaini,suka min allurai da karin ruwa sannan suka bamu magunguna ya siya,na danji sauki da karfin jikina,ina tsaye zamu tafi ina cije lips ya tsuguna a kasa yace hau baya na, na kaiki cikin mota,bayansa na hau na lumshe ido sakamakon wani dadi da sanyin Ni'ima naji ya ratsani shima bangarensa hakane,haka ya dinga taka Steps ana ta kallonmu har mota ya kawo ni ya sani ciki a hankali shima ya zaga ya shiga Driver yaja muka tafi,a hankali ya min magana ko zaki kwanta cike da shagwaba ina Hawaye nace ae zan kwanta da muryar Kuka,saman kirjinsa ya kwantar dani kaina yana kirjinsa ina shakar kamshinsa ina Kukana wanda ba iya na ciwo bane harda shagwaba ma ta samun waje, hannunsa naji a fuskata yana share min Hawaye tare da lallashina to kiyi shuru haka ya Isa Ok, kai na daga Amma ban daina Kukan ba,yasa harshensa cikin kunnena nan take na dauke wuta wani mugun azabar dadin da ban taba ji ba shi naji,da Sauri na kankameshi tare da cewa wayyo ka bari yanda nayi maganar kamar me rada,nan take jikinsa ya wani amsa yarr, a hankali na daura lips dina saman wuyansa ina ta shagwaba, yana lallashina kiyi shuru kinji zan rama miki,nace to ka rama min ka samu Haneefa ka zaneta a gabana, yace zanyi miki sai nan gaba idan ta manta tayi miki haka,dole zan rama miki kinji, nace to sosa min gashina, ba musu ya fara sosa min gashina ina lumshe ido. Muna karasawa gida nan ma ya goyani suna kallonmu don lokacin sun dawo daga asibiti suma,ba damar yi mana magana suna tsoron Aayan haka muka wucesu, muna shiga yace ebo kayanki tare da su Meenat kowa akwati daya daya Sauri ku fito,gabana ya fadi ko korarmu zaiyi Amma sai na shiga muna hada kaya suna bani labarin abinda ya faru tun farko nima na fada musu abinda suka yi min.

  Muna fitowa da akwatunanmu Uku shima muka ganshi ya sha wanka da trolley ya fito,duk muka kashe kayan wuta da komai sannan ya kira wasu ma'aikata suka zuba kayanmu a mota,yace muje wajen Daddy, muna zuwa muka gaishe da Daddy yana ta murna ya amsa yana tsokanar su Meenat,yace sai kun dawo Allah kiyaye hanya,ban san inda zamuje ba nace Ameen kawai na janye hannun su Meenat muka fito Sabo da mu basu waje suyi sirrinsu na yaro da Mahaifi.

    Muna palon kasa ya dan dade sannan ya fito yace muje,ni da shi muna mota daya,Meenat da Ma'eesha ma suna mota daya can wata unguwa muka nufa me shegen nisa gata ba wasu gidajen kirki,kalar gidajen kamar na yan mafiya ban taba sanin da irin wannan unguwa ba sai dai ta hadu karshe.
    Wani rantsatsen gida muka shiga idan na tsaya fada muku yanda tsaruwarsa take zaku sha mamaki ina kuma mamakin yanda Aayan zai dawo damu nan tunda Daddy yace Hajja baza ta bari ba zata iya tsine masa,ashe kuma Hajja ce da kanta ta sanarwa Daddy ta gaji da jarabata ta gaji da ganina a dauke mata mu daga gidanta zuwa wani dan lokacin da zata bukaci a dawo damu Family House Amma yanzu mun gallabi rayuwarsu a gidan,wanda ba kowa bane yayi wannan zugar Sai Ameer Sabo da yana wasu shirye shirye a kaina.

     Gidan da ma'aikata masu kula da komai babu wani gyara da zamuyi komai Neat,Daki daya na sama muka dauka shi kuma Aayan yana hawa na biyu,Meenat tace Sis shawarata anan dayace ki koma ku dinga kwana room daya da Mijinki ki rungumi abinki ki fara auren nan da gaske,kisan damuwarsa yasan taki,ki kula da abinki,tunda yana da lalura baki sani ba ko zai warke,amma wannan abinda kikeyi ba mafita bane,meenat ance miki so na yake? So kike na kai kaina ya wulakantani watarana,wlh bazai miki ba Sis ki duba yanda ba so tsakaninku Amma kalli yanda yake mana Gashi mutimin kirki karki bari wata ta kwace miki miji ki dage ki koya masa sonki Sis.

    Harara na watsa mata nace Allah ya kiyaye na zubar da class dina zan dai dinga zuwa ina tayashi hira iya abinda zan iya kenan 11pm na dawo muyi bacci tare daku,Meenat ta dinga rokona nace Bazan iya ba ni iya kacina tayashi hira idan baya bukata itama na ki zuwa,haka ta kyaleni.

    Da ruwan zafi nayi wanka Allah yasa habo kawai nayi basu fasa min jiki ba banyi rauni a jikina ba,kamar ma basu dakeni ba tunda Habo nayi sai ciwon jiki,Meenat kuwa sun fita kallon gida suna zagawa,na fito daga wanka Daure da guntun towel ya shigo tare da ajiye min ledojin take away har guda biyar yayi gaba ba tare da ya kalleni ba, sai da muka ci muka koshi sannan nayi brush na shirya cikin riga ta dan wuce gwiwa kadan,karatu mukayi sosai Amma Meenat ta dameni sai naje dakin Aayan wai ko hira na tayashi,Maeesha ma ce min kije pls Sis,na zura hijab zan fita ina cika ina batsewa,Meenat tace haba Mufeen Ammah kamar baki waye ba me yasa kike abu kamar yar wajen gari ne wai? Shi yasa akace akwai dan birni a kauye a birni akwai dan kauye, ai sai ya dinga raina ki yana ganinki a baki waye ba,ni kuma sai nace ae haka ne to ya zanyi kenan? Meenat ta mike tare da dauko wata yar Ficikar riga da wando wanda da kadan ya rufe mazaunai rigar ma iya mazaunai take me hannun siririn hannu ba sai da bra ba domin an mata abinta,ba karamin kyau nayi ba dama gasu green dasu, Meenat ta kara gyara min gashi tare da fuskata, kamar wata Baturiya haka na fito,dan girgiza Mazaunan naki mu gani,hararar wasa na balla mata sannan na shafa turaruka na sa Hijab dina har kasa na musu sai da safe Meenat tasa key a kofar su ni kuma nayi samansa.
    Koda na je ban san wanne Bedroom ne nasa ba haka nayi ta duba dakuna sai can na bude wani naga Hadadden Palo na gaske yasha kayan alatu kida na tashi sosai har tsakiyar kai da alama speaker ce a palon,a 3seater na hango shi kwance yayi wani dai dai dashi yana karanta Magazine,sallama nayi kusa dashi ya amsa ba tare da ya kalleni ba naji yace ya jikin? Nace da sauki,shiga kitchen gashi nan ki hado min Ginger tea,dama ban zauna ba na shiga kayataccen kitchen nasa na daura tukunya, wata waka ta Yan Nija ta ratsani sabo da shegen dadinta na cire Hijab din na ajiye gefe ba wata rawa na iya ba amma kidan wakar yaci ace ko kaine an girgiza mata,nan take na fara rawata nace in dai hakane zan koyi rawa kwanan nan, can na manta da wani tea saman gas ina ta shagalina a jikin fridge,har ya gaji da jirana ya nufo kitchen din da kansa sabo da so yake ya Sha ya kwanta bacci,yana zuwa yayi arba da shegiyar shigar dake jikina sai girgiza jiki nake ni dole sai na iya rawa,dariya abin ya bashi har wakar nake bi da bakina dan abinda naji suna cewa,saida ya gaji da kallo na kawai ya tako lokacin ina jikin gas din amma rawa ta nake,hannun mutum na gani ta gefe na yasa tare da kashe gas din ya dauke Pot din dake kai ba tare da yace min komai ba,ni kuwa kunya ce me tsanani ta kamani da sauri na maida Hijab dina ina kame kame kamar nayi karya,A kitchen din ya zuba sugar sannan ya dauki abinsa yayi waje ya barni a nan tsaye cike da kunya sai da na Dade sannan na fito Palo baya palon da alama yana Bedroom,Na dade a Palon daga karshe na Mike na kashe komai na nufi Bedroom dinsa,lokacin tuni yayi shirin baccinsa yana saman Bed amma ba bacci yake ba System ya kunna yana aiki, a jikin kofa na tsaya ya kalleni yace shugo mana ki kwanta ko ba a nan zaki kwana ba? Kunya ta rufeni na daure dai na karasa Saman Bed din tare da haurawa can sama,muryarsa naji yace ba a sa Hijab a saman Bed dina,a kunyace na cire tare da linkewa na Mike na saka cikin Sip sai kallona yake yanda kayan suka min tsantsan kyau.

     Dawowa nayi ta gabansa na koma saman Bed din kansa ya sosa ya dan tsaya da danna system din sai kuma naga yaci gaba abinsa, zo ki gani naji muryarsa a hankali na zauna a bayansa tare da leka kaina cikin System din wasu zanen gidaje guda uku yace wanne yafi kyau a nan na kalla nace wancan Blue din yafi,ashe kin iya Zabe yace,ina bayansa bai San na zo daf da shi ba ya juyo da niyyar yi min magana ai ko ya gogi kirjina da gadon bayansa,ban san sanda numfashi na yayi sama ya dawo ba,shima wani shock yaji kamar electricity da Sauri ya kashe Laptop din ya ajiyeta gefe, duf naga ya kashe light duhu dundum ya gauraye dakin sai kamshi da karar Ac ke tashi,gaba daya jikina ya mutu ji nake kamar na shige jikinsa ina wannan tunani naji shi kusa dani ya kwanta tare da cewa kwanta mana me kike tunani,nace ba komai na kwanta nima gaba daya rabinsa a jikina ya kwanta tare da daura kansa saman Boobs dina,ban san sanda na daura hannuna saman sumar Sa ba me uban yawa da laushi,a hankali nake wasa da ita,kara makaleni yayi sannan a hankali yace yau me kika yiwa su Hajja haka? Cin Zaline kawai na bashi labari har abinda ya hadasu dasu Meenat tare da dukan Ma'eesha da sukayi.
   Ransa ya baci yace Ok zanyi maganinsu so sorry for tht ya furta kamar me rada tsigar jikina ta tashi yarrrrrr nace ba komai ya wuce, yanda ya haye min jiki da Alama son jiki ne dashi kamar mage maimakon ni  ya daurani saman jikinsa sai dai shi ya hau nawa ya wani lafe yana narkewa.

       Gefen fuskarsa ya fara gogawa a tawa yana kara kankameni yana shidewa,ban san sanda na lalubi lips dinsa ba yana jin nawa saman lips dinsa da Sauri ya amshe ya fara tsotsar bakina kamar zai tauneshi ya huta,Wuyansa nake murzawa a hankali da hannuna,hannu yasa tare da zame rigata kasa,na
Tsorata Amma na tuna bashi da lfy bazai iya min komai ba sai Romancing shi yasa ban damu ba na saki jiki,Hannunsa naji a kirjina yana shafasu cike da Salo na kwarewa,na gama fita daga hayaccina dan ban san abin haka yake ba sai yau,taimaka masa na farayi sosai nima ina masa abubuwan da ban san a ina na koyesu ba,kokonto na fara yi anya kuwa wannan bashi da lfy? Gashi gaba daya gawurtaccen lafiyayye komai yana matsawa ace bashi da lfy,kai ban yarda ba,jikina na zame daga nasa ya kara shigar dani jikinsa gaba daya ya haukace kalaman da yake fada sun zarta hankalina ni nasan na karya ne dan kawai yana cikin mayen dadi ne,
   Ganin da gaske bana so sai ya hakura ya kyaleni Amma yana jikina ya hanani maida rigata daga mu sai dan wando wasa kawai yake da kirjina Salo daban daban wanda karfin hali kawai nakeyi ina daurewa Amma na kai karshe da zan kasa Control,a hankali murya na rawa yace Ki bari a gwada ko na warke pls,na fashe da kuka ni ban yarda ba, to mene abin kuka tunda bakya so Bazan miki dole ba,shuru nayi sai ya bani tausayi yanda ya dade yana shan wahalar mata data rayuwa kawai sai nace na yarda ka gwada tunda hakkinka ne, da zafi zafi yake sarrafani nima Sabo da abinda yake mun na kasa Control nima biye masa nayi bare nayi Control din kaina,tunda ya fara sucking mini Down na zauce na susuce na fara yabon halayensa, ina Common Baby u r so Sweet, ina kukan dadi iri iri wanda na kara birkita masa lissafi har nan take ya fara neman hanyarsa,amma gaba daya nan take ya dawo normal ya daina sha'awar ba tare da ya biya bukatarsa ba,naji ya kwanta a gefena kawai,nace lfy?Yace kawai i can't, wani tausayinsa ya kamani,nace dama haka kake? Yace hmm kin gani da idonki,shi yasa ban son aure Sabo da zan zalunci mace,amma Daddy yace na aureki,kiyi hakuri kar ki soni ni dama Bazan so wata ba Sabo da bata lokacina zanyi kawai wace zata zauna a haka dani,yana ta Surutai da gani cikin bacin rai yake,na koma jikinsa tare da shigewa kasansa nace kwanta ina lallabashi kamar kwai ya kuwa kwantar da kansa a kirjina yana tunani,ina shafa bayansa na Lallashi  nace zan zauna da kai haka,in dai akan wannan ne ni ban damu ba iya wannan romancing ya isheni,yarinya ce ke shi yasa kike ganin iya wannan ya isheki,kirjina na hada da nasa nace Allah zan iya kawai ka daina damuwa Insha'allah watarana sai lbr zaka warke yace Ameen tare da kara nutsar dani a jikinsa, yanzu me kike so na kara miki irin na dazu?, Nace ae amma Idan kaima kana so sai nayi maka cike da kunya nake maganar,shi kuwa murmushi yayi tare da cewa alright.
    Wannan ba ance sai ana son mutum ake masa ba? Yace me? Nace abunda mukayi dazu kuma ai mu ba soyayya muke ba,au haka ne fa? ya fada yana shafa wuyana zuwa kirjina, kwanciya yayi tare da kwantar dani a kirjinsa,a hankali nace a Sa min riga ta pls,Yace to ya dauko kuwa ya saka min a jikina,kina so mu rabu kika ce ko? Gaba na ya fadi sai naji bana son rabuwa dashi sam,dan kar ya gano ni sai nace taya zaka ce haka bayan ka gane min Tsaraici ka tabani,Murmushi ya saki tare da cewa ni fa da kika tabani? Nace tunda Business mukeyi sai ka biya kudi shike nan,nawa zan baki? Na tsaya na gama tunani nace tunda ka biya Sadaki an yafe maka wannan,dariya ya dinga yi tare da cewa Na taba na alakoro,No Sadaka na maka iya yau banda gobe,ni kuma wanne na baki? Ai ni banji komai ba,uhm karya ko kinga me kike min kuwa ko na fada kiji ya bude baki zai gwada yanda nayi masa da Sauri na Sa baki na saman nasa, murmushi yake tare da cewa yaushe kika iya abubuwan nan a ina kika koyi wannan abun bayan ke yar yarinya dake ba wayo ba? Dariya nayi tare da cewa ka bar ganina haka wannan ai ba sai an koyawa mutum ba kawai ji ake an iya,na iya da yawa ma da ace shiri mukeyi da kai ko Love to da sai na kwance ma kwakwalwa,Dariya yayi tare da cewa to mu fara shirin mana daga yau,ko love din ne sai ayi na kudi kullum zan biya mu fara Drama kamar film a gaban kowa kuma,amma a zuciyarmu mun san Business ne ko? Sabo da naki dadin abin sai na wayance irin zan masa wayo mu dinga shan dadi ,sai na karbi maganar nace to na yarda yanzu soyayyar wasa zamu dinga yi kuma itama cikin kudina na kasuwanci,a ransa yana tuna rashin wayona yana dariya yace lallai zaki sha kudi karfa ki karar min da kudi,dadi ya kamani zan masa wayo da yawa na dinga shan dadi na,nace karka damu kadan zan dinga amsa,yace to cikin kudinki gobe zamu fita shopping da kaina zan kaiki.

   Ai kuwa farin ciki ya kamani nace Allah ya kara budi Ranka ya dade,a hankali nace Yanlabai a Sa nayi bacci cikin kudina ka zame dubu Uku tunda na saka aiki nima,dariya abin ya bashi yace to shike nan cikin kudinki na Kasuwanci zan cire kudina tunda yanzu ke kika nema,nan ya fara min wasu Salo a kunne na yana lallabani kamar masoyan gaskiya,na kara yin wata mika yace har naci dubu biyu,nace a'a ai banyi bacci ba dubu daya da dari biyar kaci dai,Dariya yake ta min ni ko lokacin hankalina baya tare dani ban san sanda nayi bacci ba.

     Washe gari da Safe Hajja tayi shiri sosai ta je wajen Daddy yana kwance ta dinga zuba masa masifa da zage zage karshe tace wlh wannan yarinyar da kasa ya auro mana Sabo da mugun halinka Sabo da baka kaunar yan uwanka to wlh sai nayi fata fata dasu,ka fadawa Danka tunda ka Isa dashi tun wuri ya fara shirin sakin wannan matsiyaciyar ko kuma kai ka fuskanci fushina,kar ma kasa ya saketa kyaleshi da kaina zanyi maganin abin ka sanni kuma ba a taka ni a zauna lfy,haka Hajja tayi ta sambatu har da na mahaukata ma kamar sabon kamu,ficewa tayi a fusace sai wajen Matar Abbi nan ma tana takama da gadara tace Karimatu jiya wanne yan iskan ma'aikata ne suka dafa min cabbage soup dinn nan me bauri Maggi har saman kaina,ke kuma da yake shashasha ce kika bari suka kawo min Sabo da kun rainani,nice na Haifa muku Mazajen da kuke aure dai baku Isa kun canja musu Uwa ba yan iskan surukan Zamani mutum da yayansa ace za ayi maka iko dasu,matar Abbi da yake Hajja ta shanyeta haka ta durkusa tana ta bata hakuri,tsaki taja ta figi Jakarta tare da fadawa kitchen ta dinga cin uban yan aiki kamar zata yage bakinta sai da ta gaji tace ta canja dokar gidan taga cewar yan aiki suna nema a hada baki dasu a kasheta jiya an mata girki da farin Maggi me hawa kai dan ta kusa suma.
  Tana gama masifarta ta hau mota Driver ya kaita har Airport sai Taraba state can kauyensu zata je wajen bokayenta wanda take ganin kamar malamai ne na Allah ka h.

 
   



Bakwa Sharhi fans






AsmaBaffa
[1/15, 8:41 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

   KASUWANCI NA




          61-65




Official





By
AsmaBaffa







      Page nakine Zainabsanusi78 Allah ya bar kauna.

    Godiya da jinjina me tarin yawa TASKAR SURAYYARHMS na gode da Sharhi kuna kokari, haka ake son gp.





        Bata zarce ko ina ba sai wani kungurmin kauye wanda mota bata shiga sai dai ka sauka ka hau machine a karasa da kai wata hanyar ma sai dai ka karasa a kafa,wata yar bukkar kara ce kamar ta Fulani, daga kofa Hajja ta tsaya tare da cewa Gafara dai Malam,yace Allah ee Mana Hajiya kece tafe yau? Hajja tace ae Wlh Malam ta furta tare da shiga dan karamin dakin,gefe ta zauna suka gaisa yana ta faman washe baki,tsoho gashi wani mugun kazami bakinsa duk goro yana yauki,hakora Yellow dasu shar in banda wari ba abinda yakeyi, farcensa zako zako kamar na kanti duk dirty a ciki,suma duguzum da wani lalatattun kayansa,yace Hajiya da Alama wata rigima ta taso ko,Hajja tace kwarai kuwa abinda ya kawoni kenan da waya zan maka Amma zuwa da kai yafi Sako, ko ina a dakin wasu litattafan ne na  sunayen taurari da Alama taurari yake bautawa dasu yake aikin shirkarsa.

    Hajja tace Malam kasan idan aiki babba ne bana bukatar a duba min,bana bukatar a hango min meke akwai dan kar ma naji wata matsala,kawai aiki na kawo cikin Uku ayi daya,wannan takadarin jikan nawa Aayan,kasan yayi aure to matarsa naga tafi karfina irinsa ce bata da kirki,nan take yace ba sai kin karasa ba na san komai, tace to aikin da nake so shine ko Ya saketa har abada kar ta dawo hannunsa,idan bai yuwu ba ya kara aure ta koma baiwa,idan bai yuwu ba ya tsaneta inda take kar ya raba ko ita ta tsaneshi da kanta,Malam ya dago yace me sauki kenan Amma bari muji abinda su zasu ce ayi wato aljanun da yake aiki dasu kenan,littafin taurarinsa ya bude da carbi sai wata kwalabar turare yayi shuru yana kallon littafin sai daí kaga bakinsa na motsi yana magana shi kadai yana to..to...ae...yawwa...ae...uhum...uhum..suna bashi Umarni kenan.

  Sai da ya gama sannan ya dago yace Hajiya baki taba kawo aiki me wahalar wannan ba,da farko dai sunce jikanki kullum cikin addua yake baza su iya shiga jikinsa ba ko sun shiga wahala zasu sha,na biyu kafin ma su shiga jikin nasa zasu kwashe shekaru suna fakonsa sai ranar da ya shagala da duniya sannan su shiga,ko sun shiga din dole fita zasuyi da kansu, aikin kuma bazai yuwu ba sai dole an shiga jikinsa,sannan ita yarinyar idan an Sa ta bar gidan Jikanku shi zai sha wahala ta dalilinta zai iya rasa ransa ita kanta yarinyar ba a zaune take ba kullum Azkhar take ba fashi,kuma kin san asiri ma yana tadda hali wannan taurin zuciya ce dasu gaba daya idan ma anyi suna da karfin zuciya,amma abu daya za ayi shine a hanasu kwanciyar hankali da zaman lfy idan kin yarda idan kuma kina ganin bai miki ba to fa a wannan lokaci sai daí kije wajen wasu duk rashin Imani na wannan yaron yasha kaina,dama kuma nasha fada miki,Hajja ta nisa tace ita yarinyar a batar da ita ko a haukatata mana gaba daya in yaso Shi ya kashe kansa dan ubansa,Malam yayi dariya yace Hajiya har yau kina nan da Halin nan naki na mugunta Amma kije zamuyi iya kokarinmu,ni kuma har India zan kira manyana dole ko ta yaya ne sai an miki abinda kika ce kina so,tunda kin yarda ko mutuwa ma jikan naki yayi baki da damuwa, Nan Hajja tace da dai yafi a dage sosai ta zube masa makudan kudi ta bar wajen,tayi waya da malamai da dama duk akan aikin sannan taje wajen wasu ma sunfi biyar Sabo da a hada karfi da karfe kuma sun bata tabbacin ba matsala.

     Makara mukayi don har rana ta fito bamu sani ba muna manne da juna muna bacci,lokacin Meenat har ta hada Breakfast da komai,Maeesha kuwa gyaran gidan ta fara kasancewar yau Ba schl,ni na fara bude ido na da kyar na iya zare jikina cikin nasa sabo da gaba daya ya makalkaleni ta ko ina ko juyi bazan iya ba,wannan ne ya tashe shi daga bacci,muna hada Ido na runtse ido, kawai sabo da kunya,Murmushi ya saki har ina jin sautinsa da sauri na sauka daga Bed din na shige hadaddiyar toilet dinsa nayi Brush da wanka kana na dauro Alwala na fito dan guntun Towel dinsa na daura na fito ina goge gashina,yana Saman Bed ya tsaya sai kallo na yake sannan ya mike shima ya shiga wanka,kafin ya fito na idar da Sallah na shafa Lotion dinsa tare da turarukansa har gashina na gyara shi sosai ina haka naji muryarsa yace kawo min Towel dina ko ki bude Wardrop ki miko min new, wai dan kar a bata kaya da yawa nayi Sauri na dauko Jallabiyarsa fara nasa dan tight short dinsa na Sa Jallabiya ba karamin kyau nayi ba duk da tayi min yawa kowa ya kalleni yasan nayi kyau.

   Toilet din na nufa na manta kawai na murda Handle na shige gaba daya da Sauri ya juya min baya yana ta masifa ban kalleshi ko daya ba na fito da gudu nace kayi hakuri mantawa nayi wlh na kara dan tura kofar na dan tura hannu na tare da  mika masa ya karba ya zuba su a washing machine sannan yace miko min wasu ki bude part din karshe,da Sauri na bude na dauko tare da kara miko masa ya amsa ya daura sannan ya fito ina dariya nace na gani dai abin tsoro ma, murmushi yayi yace ke kika sani kuma,Wajensa na karasa kawo na tayaka Allah na iya ni nake shirya su Meenat ma fa, na zuba Lotion a hannuna nace to juyo mana ni ko dama wayo zan masa dan na taba masa jiki ne Sabo da yana birgeni,shafa to kiyi kuma Sauri sallah zanyi na fara murza masa Lotion ina ta murmushi dan fatarsa sai laushi kawai,nazo waist dinsa na tsokaneshi Sabo da naga baya so a kalle masa tsaraici nace kwance towel din nayi Sauri mana dariya yayi yace a'a ki kwance da kanki kai.

   Ina gamawa yace saura kaya to ya dauko wani Yadi shara shara fari me shegen kyau karamin dinki fitted na Maza yan gayu,da Singlet sai short ya miko min karasa aikinki, na karba kuwa ya dauka zan wani kasa sai ya karbe yasa Boxers dinsa,nasa masa singlet yasa wandon kayan na Sa masa rigar, da Sauri ya gyara sumarsa tare da fesa turaruka ya tayar da Sallah,ni kuma na fita tare da sauka kasa na duba na ga me su Meenat suka dafa idan basuyi ba nayi,tea suka sha da Doya da kwai kawai,sai farfesun kaji,na dinga masifa kun san dai bazan fito da wuri ba dan Iskanci sai kuyi wani Doya kawai da tea mijina yana ci ne? Ba sosai yake ci ba,Meenat tace au bamu birgeki ba a hakan? Ke da kika ce hira zaki je kuyi kawai ki dawo sai yanzu zaki fito duk hirar ce tun jiya? Shike nan bacci bazai kwasheni ba nama kwana din ina ruwanki ke zaki tsara min abinda ya dace nayi kece gaba dani ko nice gaba dake? Daga yau ma acan zan dinga kwana sai me kuma? Dariya Meenat tayi kawai tace ah mun gane, to gyaran gidan fa? Ya kika gani ya miki ko shima mijinki bazai masa kyau ba? Dubawa nayi nace wannan ai nasan kun iya dama kuma na gani kunyi kokari,bari to zo ki tayani muyi masa Kunun Gyada,da su muka shiga kitchen din suka taimaka min Dan danan muka shirya lafiyayyen kunun gyada,na fara soya dankali suka ce sun gaji su nace to kuje ku huta,suna fita sai ga Aayan ya shugo kitchen din a bayana ya tsaya kamar zai shige jikina ina jin kamshinsa a saitin kunne na yayi magana a hankali yunwa nake ji fa ki danyi Sauri,yana fadan haka ya fita ya barni nan ina jin jikina wani iri.

    Tunowa nayi da zan fara yanga ta na daina cin abinci a gabansa da yawa Sabo da kar ya rainani gashi kuma bana koshi da wuri sai na shirya dabarata yanzu duk girki sai na samu na zuba a kitchen din in ci abina na koshi sai na rage space kadan idan anzo ci a dining sai aga ina ta yanga naki cin abincin da yawa sai dai na dan ci kadan,
    Cikin rashin Sa'a yau nace zan fara tunda tare zamu ci a dining,na zauna na ebi chips din na zuba kunun gyada ta,farfesun kajin dasu Meenat sukayi nan ma na zuba Naja gefe ina cin abina a nutse,Kawai Aayan yazo zai shigo kitchen yaganni kicif ina cin abina,nan take ya gane me zanyi don Allah ya zuba masa basirar gane abu,dariyace ta kamashi me karfi ya danneta,ya juya palo dan kar na ganshi naji kunya.
   Saida na koshi sannan na sha ruwa na gyara lips dina na fito na shirya Dining na gyara kitchen din na fito,Aayan yana Dining yana jirana nazo na zuba masa ni kuma na zuba komai dan kadan kamar dan yaro ne zaici irin yar gayun nan, yaga ina ta wani juya cokali a ciki ina tsakura,shiko yana ta cin abinsa har farfesun,ya kalleni yace kici mana wannan dan abincin nufinki zaki ci? So kike ace bana baki abinci ko so kike ki rame? Baki na tabe ina yatsina fuska na ce ya isheni haka,ya kalleni tare da danne dariyarsa yace me yasa kika daina cin abinci ko baki da lfy? Na shagwabe fuska nace ni...yanzu bana son wani ciye ciye da yawa,yace to kiyi hakuri kici kinji yanda ya zage yana ta lallabani sai naci abinci ni kuma ina botsewa haba sai naji wani dadi nace lallai Aayan ya fara sona sosai ji yanda yake ta kula dani yana damuwa sai naci abinci,ni kuwa sai yanga nake wai ni a dole na masa wayo ban san shike min wayon ba.
  
   Kusa dani ya dawo yace Dole sai ya bani da kansa nafi ci na koshi yaga wasa nake da cikina so nake cuta ta kamani,nan take na Tsorata Sabo da na koshi taf cikina ya cika,ina ji ina gani ya zauna ya dinga dura min abinci da kansa,kamar zanyi amai Amma yaki saurara min,Dankali da Kunun gyada ya dinga danna min,ya dawo kan farfesu,tun ina dannewa nace dan Allah na koshi Amma dama Sabo da mugunta ya shirya min yace sai na cinye ya san ina da ci,Idona ya kawo Hawaye na fara kuka ina bashi hakuri Amma yaki yarda sai cusa min yake,sai da naci me uban yawa wanda kwakwaran motsi nayi sai nayi Amai,ya miko min yatsun Sa da ya bani farfesu dasu yace tsotse abinki,haka na tsotse yatsun tas shi kuma yanda nake tsotsar yatsun ne ya tayar masa da hankali nan take ya birkice,Sha'awarsa ta motsa da kyar ya dan danne yace ku shirya da yamma zamu fita zan dawo na daukeku,hararsa nayi nace to ina turo baki akan dura da yayi min.

    Ameer dasu Mujaheed ne zaune a katafaren Palonsu suna game suna hira,Mujaheed yace ni fa guys wlh ina son beb din nan kanwar matar Aayan Meenat take ko wa? Khaleel yace ai yarinyar tayi ne  ina fada ma gaba dayansu Allah ya zuba baiwa Barin ma matar Aayan gaskiya Ameer Banga laifinka ba,Ameer yayi dariya irin ta yan duniya sannan yace baza ma ku gane ba sai nan gaba,ni na hango abinda na hango,kullum da ita nake kwana nake tashi,Sajeeda dake gefensu taji haushi dan ita Ameer take so yanzu, rai bace tace haba Ya Ameer mene haka wannan cin fuska ne ina wajen fa wlh zan fadawa Abbi kasan dai yace Aure zai mana,Ameer ya kalleta shekeke ke dalla rufe min baki me zaki kaimin gidan nawa? Har daki kike bina muna aikata abubuwa zaki zo kice wani na aureki,Amma kasan dai ai kaine kace ba komai zaka aureni tunda kaine ka lalata ni,Mujaheed yace ko kunya bakwa ji ku rufe mana baki Hajja in ta dawo ku fada mata mana a fasa can da matsalarku,Cousins kenan dama haka akeyi ko mai ace cousin dina ne Kaza Kaza kullum kayi tunanin yan uwan ashe ana nan ana aikata masha'a tare,Mata har gidan kani ko wan babansu zaka ga sun tafi hutu an samu Cousin mace ko namiji ana ta shekewa,su kuma iyaye tunaninsu zumunci akeyi sai suyi ta jin dadi Allah kyauta.

    Hajja ce sanye da glass dinta na ido ta zauna a Cikin jikokinta nan Fa Sajeeda tana kuka tace Hajja kinji wai Ameer bazai aureni ba, Hajja ta gyara zama fatarta duk tayi yaushi tace shi din banza,ya Isa ma,shi waye shi wlh wlh Allah daya sai anyi wannan aure kwanan nan ma kuwa ko sama da kasa zata hade,waye kai? Ka Isa nayi magana nasa doka da hukunci ka tsallake ko Ubanka Mustapha bai Isa ba bare kai karamin shege,nan Hajja tayi masa tatas yayi shuru yana ji Amma ya rantse indai Sajeeda ta shiga gidansa sai ya kusa hallakata da muguntarsa ita kuwa Sajeeda murna takeyi don tun da ta taso a duniya take son Ameer sosai Sabo da ya hadu shima ba laifi.

     5:30 muka gama shirinmu tsaf mun hadu karshe yau kamar wata Sallah haka muka dau wanka,Aayan kuwa bamu san a inda ya shirya ba haka muka ganshi ya shigo cikin dakakkiyar shadda sea blue yanda yayi kyau ya zarta hankali ma,Maeesha ya kalla yana zuba kamshi yace kinfi kowa kyau yau,nan take naji haushi ni bai yabeni ba ai ni ya dace yace nayi kyau ba su ba,Meenat kuwa yace Yau kamar Queen haka kika koma nan take Meenat ta fara dariya tana tnx Yaya,Ma'eesha kuwa ta makale a jikinsa,ni da yau nafi kowa haduwa yanda nayi kyau har ya wuce misali Amma bai ce nayi kyau ba sai su Meenat,kasa danne fushina nayi sai kumbura nakeyi haka na karasa Sa sarka ta na dauki mayafi na da jaka nace muje Meenat da Ma'eesha suka yi waje ni kuma zan fito yana Bedroom din namu ya jawo hannuna na fisge abina,ya kara jawoni na fado jikinsa gaba daya,na sadda kaina kasa a saitin kirjinsa,hannaye biyu yasa ya dago da fuskata yana kallon lips dina tare da cewa wa kika sawa jambaki kuma? Nace masu sona na cikin gari idan mun fita nake Sa ran zasu kalla suji dadi, bakin ciki ne ya ziyarce shi me tsanani Amma sai ya danne ya hade bakina da nashi ya dinga sha,sai da ya shanye jambakin tas sannan ya dauki wipes a saman mudubi na dinga tsalle ina son guduwa amma ya rikeni tam da kansa ya goge min fuska tas ba abinda ya bari na kwalliya ta,hakan ma yaga baiyi ba sai ya jani toilet fuska ba walwala ya danna kaina a saman sink yasa soap ya wanke min fuskar tas ya goge min da towel nayi wani mugun Fresh jajayan lips dina suka fito natural sai na kara wani kyau kowa yasan Natural kyau na gaske nayi,ga kayan sun hau jikina,dankwalin dana kafa kamar gogoro ya zame ya jefa shi saman Bed ya dauki Hijab ya sa min duk da haka nayi kyau sosai sai ya cire Hijab din ma tare da cewa baki da kyau sam sam Bazan iya fita dake ba bari muje da kyawawana su Meenat,dama haushinshi nakeji ya bata min kwalliya kuma baice ina da kyau ba yanzu kuma wai ya fasa zuwa dani,ban san sanda na fashe da kuka ba me karfi, ba shiri yace taso taso mene haka wannan uban kuka zaki fasa min kunne,gyalena na dauka ina share Hawaye yace Sa Hijab na kara sakin kuka yace to yafa gyalen haka muje wannan masifa haka,ina dariya na yafa haka nabi bayansa,sai da na kara tsayawa a bayansa na zaro Powder a jakata muna tafiya bai San ina ta shafawa ba,na gama nasa jambakina red,kafin mu karasa mota har na gyara ribbom din gashina nayi acuci sosai na gyara mayafin aiko na dau kyau kowa ya ganni yaga yar gayu,nasa glass dina dan Brown nayi kyau ba a magana,yana juyowa sai da ya firgita kamar aljana kafin aje mota har na sake kwalliya yace zanyi maganinki a ransa tunda bakya jin magana dai dai  nake dake.

     Gaba na shiga Meenat da Ma'eesha suna baya  shike Driving yau,katafaren store muka tsaya Meenat sai jin dadi muke muma mun Zama yan gayu,sabo da neman suna sai da na karasa tare da rike Hannunsa muka jera sabo da naga Yan mata sai shige da fice suke a wajen ko wacce ta Sha wanka, hannuna ya rike yana murzasu muna tafiya duk inda muka keta sai an kallemu,Kayan sawa iri iri yace mu zaba,dana tashi sabo da tausayin kudi abinka da ba a saba ba kawai sai na zabo atamfofi dasu laces materials dasu Ready made duk ba na sama da Dubu biyar daka biyar sai kasa,gani nake na gama kure karyar kudi, yana duba kudin yace a maida su wannan ai wanke kudinka ne Hajiya,da kansa ya dinga jidar mana kaya masu matukar tsadar gaske komai latest,haka takalma  ma,bags ma ba a magana,har su cosmetics yana zabo me tsada muma muna daukan wanda muke so,har jewelries, muka je bangaren Inner wears yace su Meenat su zabi nasu aiko suka jida masu kyau iri iri,ya jani wani bangaren can daban na inner wears yace zabi size naki naga ko Bra kuwa kina sawa? kullum daga an dage miki riga direct ake tafiya can,Kunya naji na rufe ido nace Ina sawa mana amma a boye nake sawa na wanke a boye bana so ace kamata ina sa Bra,to mene a ciki dan kinsa yaja tsaki tare da cewa anya kuwa jinin birni ce ke? Nace a'a daga garinku nazo murmushi ya saki sannan yace mu bamu da dangi a Rimin Gado mu gaba da baya dan birni ne ni,muna ta Zaba iri iri masu kyau ya dauko min wata yar karama yace ga wata me kyau,Hararar wasa na masa nace kaima kasan sunfi haka wuce nan sai kace yarinya,muna dariya sai ga wata yar gayu tana kwas kwas da takalmi ga kamshi tana zubawa muryarta muka ji tace Aayan  kaine a nan we finally meet here ohh,Dagowa yayi tare da zuba mata idonsa me matukar kyau ya danyi murmushi kadan sannan yace Sameera kece How u?longest time,tace am great ina ta so mu hadu wlh amma ba dama tun aurenka na farko fa gaskiya mun dade.

     Wani kishi da bacin rai ya taso min na bata rai nayi kicin kicin na tashi hankalina gaba daya ina Harare harare,itace second wife din naka? Ina Yarima yana dariya yace yana lfy yar duniya kin buya amma dai kin sake aure yanzu ko? a'a aure ai sai na huta ina aiki ina samun kudina matsalar maza ta isheni baku da kirki Sam ni sai na huta zan yi Insha'allah,Jin bata da aure yasa na kara fusata na daure fuska na dawo gaban Aayan na juya bayana tare da kwantar da jikina a jikinsa muna facing juna da Sameera sai kallon Banza nake mata,Hannunsa na jawo guda biyun na sakalosu ta kafaduna ina wasa da yatsunsa,Murmushi Sameera tayi tare da cewa am sorry to say Aayan kasan bana boye abinda ke raina amma wannan tayi maka yarinya da yawa Aayan kamarka da auren kamar wannan da gani ma baza ta wuce 15yrs ba,ga mata a gari zunduma zunduma da ka fada mana ai da mun zabo maka manyan yara amma irin wannan ai kuruciya zaka sha baza kaji dadinsu ba.

   Dariya sukayi gaba daya tare da wani tafawa abinda ya bani haushi kenan ya kara kuleni mene nasa na tafawa da mace,nan take naga fa ta fada min baka zata barni da takaici  ban san sanda nace uhm Allah sarki kuma a hakan bashi da kamata dan ina masa abinda Babba bata isa tayi masa ba,tunda tsab nake daukeshi wanda nasan ko uwarki yafi karfin.....kafin na karasa yasa tafin hannunsa ya rufe min baki da karfi dan yasan sai na karasa ko za a mutu sai na rama,ina so na kwace baki na amma yaki Sakina ya toshe min da tafin hannunsa yana fada min a kunne kina magana wlh yau na lahira sai ya fiki jin dadi bakya jin magana ko ke ba a isa an miki abu kin hakura ba sai kice sai kin rama wannan wacce magana ce ta marasa kunya uwarta fa kika ce,Sameera ta kalleni sosai tace da Sameera kike zance yarinya zaki san kin zagi uwata,wlh sai kin San wa kika cewa haka,Allah ya taimakeki yanzu Kinci darajar Mijinki amma a sannu zan goge miki abinda ke kanki,Bakina na kwace nace Ba Sameera ba Allah yasa kece Sameeran Gaya🤣 wlh nafi karfinki kina magana kina cijewa ke ga yar daba karewar Daba munga Amana ta Alim ma😍 Sameera dama irin Masu takama da yan daba ne har yara ne da ita yan daba,bata da kunya duk abinda taga dama haka zata fadawa mutum shi yasa ko zaman aure bata iya yi,sabo da ko yaushe a shirin daba take kana mata zata sa yara yan daba suyi ma kaca kaca tana takama da kudi sabo da ubanta ita kadai ya haifa ya rasu ya bar mata dukiya me tarin yawa,Tun kafin ya mutu ya raba gado yaba yan uwansa ya barwa yarsa komai,shi yasa take abinda taga dama,kuma bata San mutunci ba duk inda take da kai zata iya ci ma mutunci ta ko wanne hanya,Aayan kuwa Business ne ya hadasu tsakanin Company nata da nasa tun da dadewa.

    Ni kuwa nace komai dabancinki baza ki bude min ido ba kiyi duk abinda zakiyi nima baki San ko ni wace ba shi yasa har kike magana dani haka ina kyaleki,ki Bari watarana Business ya hadamu anan zaki gane true color dina,Tsaki taja ta bar wajen a fusace,Aayan yana ta kallon yanda nake tsiwa yar ficika dani gaban sangamemiya irin Sameera ko tsoro bana ji,na kalleshi nace girma ya fadi wlh ka ba dani ina ma kallon Ustaz har wani hannu kake hadawa da yan tasha,da gani wannan yar tasha ce gaka da fyallelliyar budurwa me zaka ji a hannun wannan me suffar mazan, kayi dacen mata amma baka godewa Allah kana wani rikewa wata hannu bayan ga hannun da zaka samu lada Allah kyauta ka daina irin wannan a gabana dan wlh ni bazan dauki a wulakantani ba dan baka darajani ba Sam,ka zubar min da mutunci ace Namiji yana da kamata yana rike hannun wata banza,wannan babban matsalace dole na tuntubi kaina Ashe ma ban kai mace ba.

    Yana jina ina ta masifa kamar uwarsa yana dariya a ransa,yace to yi hakuri masifaffiya tunda bakya so na daina,wai nice budurwa shi baya daukana a budurwa Sam,yace wai ke nan budurwa ce? Bacin rai ya kamani sai na danne a fili  nace a'a kwaila ce,a na dinga masa masifa ina zan rama zaka San ba budurwa bace ni daga yau na Canja salo again na fasa wannan Business din da mukace za muyi wani zanyi daban sai na sa kayi nadama har ni za a wulakanta dan anga ina biyayya ina cusa kaina ina kokari naga an zauna lfy shike nan za a gani,dariya yayi yace a'a dan Allah tsokanarki nakeyi fa muyi Business dinmu zan biya kudin,nace anki din sai na rama nima.

    Mun gama siyayyar komai yasa aka kai boot din mota ya biya muka fito kenan sai ga Ameer da Khaleel tare da wasu yan mata masu suffar karuwai sai chewgum suke taunawa su a dole manyan yara,na kalli Aayan na bata rai nace kalli Meenat a gabanmu tsaya kaga abinda sukeyi kalli,ya kuwa kalla sosai ni kuwa wai dan kar ya kalli yan mata nayi masa wayo,Muna zuwa Ameer sai kallona yakeyi zasu shiga mu kuma zamu fito na bi ta tsakiyar yan matan nan a hankali yanda zasu ji nace yan iska sun dauko yan iska su a dole yan mata ana yaye baki a titi na wuce fit na koma kusa da Aayan,Khaleel ya fusata kwarai da maganata haka yan matan ma,Ameer kuwa so yasa baya ganin laifina sai dai ma birgeshi da nakeyi aransa ma cewa yayi wannan gaskiya kika fada Mufeedata tabbas yan iska ne suka dauko yan iska Allah ya baki basira tare da saurin ganewa🤣

    Yan matan zasu zageni Ameer yace wlh duk wacce ta fadi ko bakar magana a kaina sai ya mata illa har fada suka so yi da Khaleel..
   Muna shiga mota na tuna zanyi girki kuma kayan miyarmu ya kare nace Aayan kayan miya na manta,Yace to mu koma store din nace a'a danyi gaba wajen yar kasuwar can zamu samu.
    Muna zuwa yayi parking nace sai ya fito munje tare,yace a'a nifa ban taba siyan abu a kasuwa ko gefen hanya ba a store nake siya,Na fara rokonsa dole haka ya fito muka karasa wajensu,sabo da tattalina da son kudi nace Malam kwano nawa nawa? Aayan yace nidai a zuba kawai mu tafi,nace a'a so kake ayi mana tsada bazai yuwu ba yo ni akan barkono kwano daya idan nazo sarowa Basai na yini a wajen ba ana ciniki ba kuma karshe kaga na siya arahar banza,Dariya Aayan yayi yace yini guda fa? Nace Cass ma kuwa, Agogon Dubu biyu ina siyoshi a Dari biyu da hamsim ni highest Dari biyar zan siyi shege,ka dinga zuwa dani siyayya kaga araha,Aayan kallona kawai yake yana dariya,Nace kai me kayan miya kwanon tattasan ne dari biyar a garin gaba gaba muke da zan siya haka,yace gaskiyar magana Dari hudu da hamsim baya tsada bana nawa kike so a siyar miki,Nace to ka rage,nafa San kan kasuwar nan,Aayan yace Haba Ke kuwa har kwano guda Dari hudu da hamsim kacal a kasa siya mene na tsada a nan? Harara na watsa masa tare da dan zungurinsa nayi masa magana a hankali bana son haka ba a yiwa yan kasuwa haka,zaka kashe min ciniki idan kasan haka zaka min ka koma mota yanzu duk ragi ai ragi ne,Aayan yace Malam zuba mana kwano biyar ga kudin ya zaro kudi ya mika,na fara rigima na cumimiye a jikinsa baza a biya ba kwano har Dari biyar gwara Ku tafi gida ni Ku barni a nan nayi cinikin ko Dari hudu na siya sai na samu Dari Dari ta Zama tawa,na dawo a taxi, ko kulani baiyi ba yace to tumatir fa,nace a tsaya ni zan Zaba da kaina,me kayan miya yana ta dariya yace kudi kudi ne ga gwalagwaje wanda ya gama lugwiguwicewa daf yake da rubewa kudinsa daban,ga masu kyau manya da kanana,nayi layin  marar kyau gwalagwajen nace duk tumatir tumatir ne tunda dafashi za ayi mu sharbe miya Malam ga me sauki ba sai anyi asarar kudin ba a bamu wannan,Aayan dariya ta kamashi ta gaske ya dinga yi yace wlh baki isa ba gwara da Allah ya kawoni na gani dama abinda kike sawa muna ci kenan? Nace to sau nawa ka shanye miyar sa kana Santi ai ni in kaga lafiyayyan tumatir a fridge to na cin salat ne,ai ko harda kwalla Aayan yake dariya ni kuwa ko a jikina,yace Allah na gode ma da na gani da Ido na shi yasa Ashe ba kya yarda a bawa kowa yayi cefane sai ke Ashe Guba kike bamu muna ci.

    Aayan yace Malam me kyau wanda yafi kowanne tsada zaka zuba, na hangame baki ina jimami shike nan za a ci kudinmu a banza,akan dan tumatir har yan Dubu Dubu na fitowa naji kamar na fisge kudin,na bata rai ina ta fushi nace ai gwara ni ka bani na dinga tara ma kudin watarana sai mu dakko a siyi abu me amfani dasu amma wlh wannan Almubazzaranci ne, mukaje layin Albasa nan ma dan yaga yanda zanyi yace zabi da hannunki one by one ki dinga zubawa a ledar mu gani,me Albasa yace ai kwano kwano muke saida wa,Aayan yace bari ta Zaba sai a auna zan biya ko nawa ne,aiko na fara Zaba sai na duba wacce ta tsage ko ta kusa lalacewa ko marar kyau sai na dauka na nunawa me kayan miya nace kaga dai wannan araha zata yi ehe,wannan ma ba me tsada bace,Aayan yana murmushi yace pick the nice one mana,na kai hannuna kan me kyau sai na koma na faki idonsa na jefa marar kyan a leda yana kallona yana dariya har na gama sannan yace to Malam juye wacce ta bari bata Zaba ba su zamu siya,haka aka auna ina gani kamar na fashe sabo da ni kudin da aka kashe kawai nake jin haushi da an tattala su ai sai a moresu watarana Rayuwar Manage na iya a haka na taso da ita na saba.

   Na dauko shima ya dauki wasu muka zuba a mota ina ta harararsa yana kallona ta gefen Ido yace daga yau tsinke baza ki kara siyowa da kanki ba da kaina zan siyo ko na bayar a siyo,nace girkin ma ba sai kayi abinka ba,wlh ya kamata ka koyi adani sabo da rayuwa ni gaskiya nake fada ma.Maeesha dama suna gani sun San halina sun San yanda nakeyi a kasuwa dariya suma sukeyi Meenat tace Yaya Aayan ya kaga mutuniyar taka ta iya Zabe ko?

   Dama kadan yake jira ya dinga dariya yace ai naga Zahiri yau Meenat,haka takeyi ko a gida Ammah ta dinga ta mata fada amma baza ta ji ba cewar Ma'eesha.
   Meenat tace ai baka San abin haushi bama shi yasa bama Rakata kasuwa watarana akan egusi da zamu siya wlh sai da muka yini a table din me egusi har fada sukayi ya koremu gaba daya,kai ai kadan ka sani, turmi ma ba a cin arziki a gidanmu ko daka wasu sukayi a ciki sai ka biya ashirin, haka gugan Rijiya ma ko kurar Ciro guga duk na haya ne hhhhh Aayan ya dinga dariya Meenat suna ta bashi labari suna min dariya,sai da na saki Kuka sannan sukayi shuru.
    Haka ma Ya Aayan watarana ta siyo min jakar makaranta me kyau ina ta murna wata kawarta Nawwara tace gaskiya jakar tayi kyau nima zan siyo aiko Mufee na jin haka tace Dari uku na siyo ta bani Uku da hamsim na siyar miki,ina kuka haka ta siyar da jakar nan taci ribar Hamsim,Aayan yana driving yana dariya.

     Malamin Hajja ya hado mata muggunan da za a sa min tare da Aayan a abinci,da sauran wasu iri iri na wajen Malamai shi yasa yanzu ta saka rigima wai Daddy ya fadawa Aayan a dawo damu ai muma jikokinta ne taga abinda tayi bai dace ba bata kyauta ba
   Daddy yasan ba gaskiya bane amma yasan Allah na nan ba matsala ya Sanarwa Aayan.







AsmaBaffa
[1/16, 5:51 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

     KASUWANCI NA





            66-70




Official





By
AsmaBaffa





                JANNAT wannan page naki ne.

    Godiya gareku House of Hausa Noveld kun iya Sharhi.


















Bayan yayi parking a cikin gidan fitowa mukayi tare da jidar kayan muna kaiwa muna dawowa har muka kwashe komai ya rufe motar  take away na abinci da ya siya mana na karba ina ta masa godiya da addua ya wuce abinsa nima na shiga Bedroom dinmu, Bayan munci mun koshi wanka nayi na shirya cikin sabuwar Nighty dina iya cinya me siririn hannu peach color na fito fes ina kamshi Meent ce ta shigo Sis kije inji Ya Aayan amma fa yana compound jikin motarsa da alama fita zaiyi,Hijab nasa har kasa kamar zai ja kasa na fita lokacin tuni munyi sallar Isha,saman Motar na ganshi a zaune cikin kana nan kaya ba karamin kyau yayi ba,wani abu ya tsirga min na tsinci kaina cikin wani yanayi na shauki wanda bazai misaltu ba wani dadi yana ratsani, kallona yake cike da tsantsan nishadi kwance a fuskarsa zuciyarsa cike take da farin ciki wani Sanyi na ratsashi.

     Ina murmushi na karasa tare da cewa au akace fita zakayi kuma naga ka zauna saman bayan mota,yana murmushi yace zance fa nazo kinyi sabon saurayi kuma kina wani cewa fita dariya nayi nace kaima dai baka rabo da tsokana a haka zubin mugaye gareka, am serious ni fa zance nazo dama gori kike min kece kullum kike zuwa zance,Dariya nayi nace to nan gaba idan zaka zo ka dinga bugo waya sabo da ai banyi kwalliyar zuwa wajen saurayi ba na fada kamar gaske, muryarsa naji yace duk fa cikin business ne ki daina tunanin da gaske ne kudi za a biya ki wannan fitowar ma da kikayi kin ci kudade masu yawa,dadi ya kamani nace an gama ko kalma daya ce duk kudi ne? Yace of course, murmushi nayi tare da gyara tsaiwata yana sama na matsa jikin kafafunsa, yace yan mata suna na Aayan duk da cewa baki tambaya ba,ban san lokacin dana fara dariya ba ni abin ma kunya ya bani amma na daure nace ai yanzu gashi ka fada, yaci gaba da tunda na ganki kika shiga raina naji bazan iya bari ki wuce ba batare da na miko Kokon Barata ba gareki, uhmm nace tare da tunani sannan nace kasan me ni ban iya so farar daya ba dole sai mun zauna da mutum idan naga halayensa sun min sai na yarda amma yanzu bazan amince ba, sama naji yayi dani ya daudarani saman motar nima kusa dashi jikinmu na gugan juna,baki na bude tare da cewa wannan saurayine ko dan Shan minti ne kawai,dariya yayi ai an daura mana aure da Budurwar kawai bata sona ne shine nake zuwa zance sabo da na lallabata.
   Murmushi nayi nace to naji game din tayi kyau back to our business nawa na samu? Yace ai Dari biyar kika samu sabo da kin kasa magana baki fadi kalamai masu sanyi ba taya zaki samu kudi.

   Masu Zafi zan fada yanzu ma kuwa na irin fuske ba wasa nace look in to my eye aiko ya kalla da mayun idonsa I was kidding u  but u I knew I love u,i wish I can show u how much I love u,i care for u,my heart is full wth ur love my Prince, yana murmushi yace proof what u have just said, nan take da gaske nakeyin kalamai na ni, bana karya bane amma a boye a raina nace na samu Damar jin dadi na sai na fake da kudin,a fili kuwa sai na ce ka tabbata  zan samu kudin nan da yawa,kai ya daga min tare da kara matsowa jikina sosai yatsunsa ya sarke da nawa tare da jawo ni jikinsa, hannayena na sakalo ta wuyansa a hankali na rungumeshi a jikina sannan na dago kaina tare da shigar da bakina cikin nasa ya fara tsotsa kamar ba gobe, tunawa nayi ko yan aiki na zirga zirga a wurin nace yan aiki fa?yace ai basa kwana a nan gidan da safe suke zuwa nemi kudinki na Business yarinya,dariya nayi a raina nace Ina ta masa wayo ya kasa ganewa,nace ni dai mu koma bedroom,lallai kudi zaki nemo da yawa karfa ki karar min da dukiyata,ina dariya nace hau dani baya wannan ni zan baka kudin cikin nawa ka cire Dubu guda,baki isa ba sai dai na daukeki,nace ni dai baya nake son hawa,ko baka da karfi ne? Hannu yasa ya daga ni sama sosai kamar ya dauki tsinke ya dauri a kafadarsa naga ya mai Dani bayansa kamar yar jaririya,nace kai karfinka yayi yawa amma a haka dan Lange Lange da kai, murmushi yake har bedroom dinsa karki cire Hijab din, why? Zaki gani ya furta yana dorani saman bed sannan yazo ya daga hijab din tare da shigewa ciki,dariya nayi yanda yake min abubuwa a ciki don tuni ya zare min rigata tare da kashe light, gaba daya ya gama haukatani ni kaina abinda nake masa ba a cikin hankalina nakeyi ba, ba komai a jikinmu haka muke murzar juna, kalamai yake sabo da sucking na fara masa ko gidan ubanwa na koya oho wannan abu kamar da Aljanu sai kaji ka iya kaima🤣
    Kukan dadi yakeyi yana zazzagar da kalamai amma ni bana yarda kawai dama na karya ne tunda nasan Business yace ayi,nice nakeyi da gaske a raina, boobs dina yake murzawa har shidewa nakeyi,kiss kuwa yau ina jin sai lips da tongue dina sun kumbura maybe dan sun tsotse a wajensa,yau wani abin mamaki sai ga Aayan yayi releasing sosai abinda Bai taba yi ba tunda yayi aure sai dai a mafarki, bai taba tunanin zaiyi ba Sam shi yasa ma bai yi tunanin sexing dina ba Sam, ya dinga bakin ciki yana jin haushi yace ya zubar da yaransa a banza,za a wankesu a ruwa,na dinga dariya nace yanzu haka ma yan biyu ne ko yan uku ma,ya kara Jin haushi yana kwance gefe,na ce yanzu haka akwai me Sunan Mommynka a ciki ko me Sunan Daddy, dariya yayi tare da cewa wlh ba a wanke Daddyna ba ai Me sunan Daddy yana nan zuwa nan gaba bakiyi abinda zai fito ba,sai Abbansa yaji dadi da yawan gaske sannan me Sunan Daddy zai yo waje,haka kace ko? Ya jawoni jikinsa tare da cewa tnx Baby kinci kudi me yawa yau mota sabuwa dal da dalleliyar waya me tsada kika samu,ni haushi ma ya bani maimakon murna bai San dadin dana ke ji ba na faranta masa burina na ganshi cikin Jin dadi amma shi tunani yake ma dan kudi nayi ni Sam yanzu ba kudin bane a gaba na ba so nake ya so ni kawai.
   Shuru yaga nayi bana murna kamar baya can,ko sunyi kadan a kara miki? Nace a'a na gode hakanma sun isa,murmushi yayi yana kallon yanayi na,nayi miki kema kiji dadi? Jin dadine yasa nayi murmushi nace ae,ya fara gwangwajeni da salonsa nima saida na ji zam zam,garin kuma sani naji dadi shima ya sake dawowa ruwa nan na kara masa abubuwan da kawai ya kara kawowa,kamar yayi kuka sabo da takaici yace next time kawai Sex zaiyi shi kam,ina ta tsokanarsa har bacci ya kwashe mu,tun daga Ranar kuma ko me zamu yi bai kara kawowa ba,dama kuma baice ma zaiyi xxx din ba.

    Ameer kullum shi yana wajen Hajja sabo da sun shaku sosai duk wani plan din ta ya sani,duk bai damu ba dadi ma yakeji shi za a sa Aayan ya sakeni,kawai sai yaji Hajja tana cewa za a sa min ciwon hauka ko kuma wata cuta ko wacce za a rabani da gidan su Aayan gaba daya,nan hankalin Ameer ya tashi ya za ayi a haukata masa Mufeedansa,shi da yake so ya Aureni yana kauna ta baya kaunar abinda zai cutar dani ko ya ganni cikin wani Hali,nan take yace dole na dau mataki kan Hajja na hanata aikata abinda take niyya,nan ya dinga sawa Hajja ido har ya gano magungun nan data ajiye tana jira na dawo ta aikata abinda bokayen suka ce mata,Ameer murna ta kamashi ya kwashesu gaba daya harda wata yar tukunya da wani ruwa a ciki,ya zubar da ruwan a tsorace,ya fasa tukunyar,garin maganin da ruwan rubutu duk ya samu jikin katangar gidan ya haka rami me zurfi jikin flowers yanda baza a gane ba ya zuba rubutun ciki garin maganin ya juye su daga ledar a cikin rami sannan ya maida kasar ya binne su sosai yanda ba za a gane ba ya kwashe ledojin ya zuba cikin Dustbin.

    Bayan kwana biyu Hajja ta duba taga ba komai,kamar me ciwon hauka haka ta fito tana ihu da masifa,ta tambayi kowa amma ba wanda yace ya gani,Ameer kuwa dama tasan na wajenta ne bazai ma dauka ba sai dai ya goya mata baya shi yasa dashi ake tambayar yan gidan yana masifa kamar gaske,Hajja ana sa masa albarka ga wanda ya gajeta,haka a gaban Ameer ta kara buga waya wasu malaman sunce baza su sake samun irinsa ba bare su bata,wasu kuma sunce ta koma ta karba,Ameer ya makale mata tace ai shi zai kaita ma su karbo,kafin su tafi ya tara yan iska ya biya su kudi kan a tare motarsu su kwace jakar Hajja kudin dake ciki nasu ne masu aiki sauran maganin da suka samu kuma su bashi a hannunsa zai nemesu,haka suka tafi gari gari har wanda a jirgi sukaje daga nan suka je na kauyukan kano duk suna jakar Hajja tana murna,Ameer yana Driving tana gaban mota suna ta hira tana fada masa tsare tsarenta wanda zata shiryawa Mufeeda,suna tafiya hanyar daji daji ba kowa sai ga yaran Ameer sun tare motarsu kamar gaske suka kwantar da Ameer a kasa Hajja kuma suka kwace jakarta tana rokonsu suna ganin makudan kudin da suke ciki suka dinga murna suna godewa Ameer a Ransu,suka kwashe kudin tas,magungunan kuma sukace wato gidan bokaye kuke zuwa ko? Kune masu hana mutane Zama lfy a duniya Allah ya tonaki tsohuwar banza ke da jikanki yau karshenku yazo,Hajja ta fara magiya tana rokon kar a taba mata jika sabo da tana son Ameer sosai ita tun asali tafi kaunar Ameer da kowa,Ameer ya kifta musu ido su kyaleta haka su kwashe komai su tafi,ai kuwa suka kwashe komai suka jefawa Hajja jakarta,Ameer ya tuna da rubutu jarka har biyu a gaban mota yana sani yace Hajja maganin sun kwashe Allah yasa muna da biyu a gaban mota,kamar gaske suka take mishi wuya sukace au harda wasu a mota kuka boye Allah ya Toni asirinka dauko mana su ko mu fedeka,Ameer ya tashi yana kunshe dariyarsa ya ebo yana kuyi hakuri gashi kuje dan Allah,sai dai suka kaiwa Hajja masga daya sannan suka kara gaba.

    Hajja jiki na rawa tana kyarma a firgice tace Allah ya isanmu kaga shegun yara wannan turosu akayi,Ameer yace sannu Sannu Hajja ta Allah ya saka mana muje muyi mu bar nan kar su dawo ko wasu kalar suzo su harbemu,Hajja tace iceko baka ji rauni ba Ameer dina naga sun take ma wuya,ai munyi arziki da basu taba min kai ba,yana Driving Hajja tace yanzu me zan cewa malaman nan? da wanne baki zance an kara sacewa? Ameer a ransa yace kai Allah yayi muguwa a nan wajen sai son kai amma bata son Mufeedata,a fili yace shawara ta ki Bari sai an kwashe kamar wata daya ko biyu ki koma muce mun aikata baiyi aiki ba Sam bamu ga canjin komai ba sai su bamu wasu kalar kinga me zafin ma zasuyi mana tunda sunji wannan baiyi ba,Hajja taji dadi tana dariya ta balli goronta tace hakane Jikana shi yasa nake sonka akwai dabara amma idan suka ce sun San karya ne fa?,kasan fa duba sukeyi sun San komai,Murmushi Ameer yayi yace karya ne Hajja ba wanda yasan gaibu duk raina muku hankali sukeyi idan kina so ki san karya ne kije da jakarki ba komai a ciki kice ya duba miki mene a ciki idan ya fada ki bude wlh bazai San mene ciki ba wani abin ma da zaki ji sun fada Aljanu ke fada musu wani karya wani gaskiya amma sai ku dinga yarda,ai kamar Hajja zata daki Ameer ya karyata malamanta tace Wannan sabo kakeyi Ameer malamai magada Annabawa kake fadawa suna karya,Ameer ya dinga dariyar Jahilci n Hajja dan sunyi Islamiyya sun San komai,amma ganin baza ta gane ba kawai ya canja zancen ya kyaleta,ita ko sai masifa take masa,har ya gaji yace Hajja ke dai baza ki gane karyar mutanen ba a hadisi  aka rawaitosu ko a Alqurani?, Salati Hajja ta saki tace yau naji dan iskan yaro to yi min Wa'azi Allah ya taimakeka kaine da Mujaheed ne ko Khaleel wlh yau da basu kwana a gidan mu ba,ka kiyayeni rakani kayi ba Wa'azi nace kazo ka min ba,kai din abin arziki kake aikatawa? Wanne iskanci ne baka yi,ai ni nasan wlh ba dan iska bane tunda ni bana bin mata duk a baki kike ji ina surutuna ko kin ganni da mata wlh ni ba zina nake ba,ban taba yi ba,ko kinji nace Ina son mace wlh da aure nake sonta ni bada iskanci ba,bana fata na ajiye mace don kawai naji dadi da ita sai dan na aureta gaba daya har karshen rayuwata,Hajja tace Sajeeda fa ai tace ba abinda bakayi da ita ba? Wlh sharri ta min don na aureta amma ni ban lalata mata rayuwa ba kuje asibiti a dubata,idan ma an ganta a lalace to wlh Allah wani ne ba ni ba,ke kin San ni ba irin Khaleel bane ko Mujaheed wanda basa fada sai dai aga sun aikata sune masu son ayi fasikanci da mata, Hajja tace uhm naga Alama ai nasan halinka Ameer kai dai a barka da masifa ga kawo shawara wajen iya hada tuggu,to amma mene hadinka da mata tunda gashi duk inda za a ganku da mata kuma Sajeeda nima ai ina ganinta a dakinka,Hajja kenan kina son Gulma,zan ci ubanka wlh karka kawo min raini,ayi hakuri Hajja mata da kika gani Allah daya dan rage Zafi nake dasu ina dan tabe tabe a jikinsu idan na danji sai na kyalesu,Sajeeda kuwa har room take Bina na kwanta da ita naki yarda,tace na aureta naki shine take talla da kanta ganinta hakan ne zai sa na sota ni kuwa kara tsanarta ma nayi wlh ba wacce na tsana sama da ita,kuma ban aikata komai da ita ba sharri take min,Hajja dan Allah kar a aura min ita wlh zan iya mutuwa,banza Hajja tayi dashi sai daga baya tace amma kasan tana sonka,ae amma ai badan Allah take so na ba cewa fa tayi don duk gidan nan ni kadai nake kama da Yaya Aayan daga Aayan sai ni a kyau na yan gidan nan shine fa dalilinta dama nasan Aayan take so ba ni ba,ba sai ku aurawa Aayan ya kara ta biyu da ita ba,Hajja tace halina da kai basira haka za ayi aure za a kara masa ta nan zamu samu Damar wulakanta Mufeeda,Ameer najin haka yace ai kuwa bazan bari a aura masa Sajeedar ba tunda za a taba min lafiyar Mufeedansa ta nan za a dinga kai maganin bokaye,wa ya sani ma ko Sajeeda ta dinga dukan Mufee dinsa kullum ina Sam da sake bazai yuwu ba dole ya canjawa Hajja shawara amma sai ya nutsu ya samo dabara.

    Washe gari naje schl na dawo wanka nayi na shirya cikin wando pencil brown  riga Maroon na gyara gashina kamar wata Baturiya ba karamin kyau nayi ba, zaune nake a kujerar dake kitchen ina yanka cabbage, kamshin Aayan naji kafin na juyo naji ya tsaya a bayana tare da dafa kafaduna da hannu biyu a hankali yayi Sallama na amsa tare da mikewa tsaye nace sannu da zuwa, na kwanta a jikinsa ba tare da na tallabeshi da hannayena ba sabo da akwai cabbage a jiki,kallona yakeyi sosai yanda nayi kyau amma Bai ce nayi kyau ba,lemon Fruits dana hada  yayi Sanyi na tsiyaya masa a glass cup na mika masa ya karba ya shanye na karbi Cup din shi kuma ya bar kitchen din ya haura samansa,na dan Dade a tsaye ina tunanin ko lfy? Dan naga kamar yana cikin bacin rai amma ya zan masa tunda baya iya fada min matsalarsa sabo da ba sona yake ba nice dai nake wahalar da kaina a raina nace wlh bazan iya ba kaje kayi ta fushinka da kaina kuma nayi wa kaina fada ni da nake so ya soni back kuma in Zama jigon rayuwarsa na tsaya wasa gwara idan na sace masa zuciya sai na shareshi yanda zaita wahala a kaina yessss na fada da karfi wlh haka za ayi yanzu bari na kwantar da kaina first yanda Meenat tace nan ma da karfi nace shegiya Meenat yarinya da fusaha,da sauri na ajiye aikin da nake na wanke hannuna na bishi samansa sabo da irin su Aayan son girma garesu suna bukatar biyayya sosai.

    Ina shiga na iske wanka yake sabo da na sanshi ya sanni don ba kaya ma muna romancing juna me yayi Saura kuma kawai Toilet din na Murda handle din sannan nace na shigo,shigo mana kinga na huta ma,Shiga nayi da towel a jikinsa ya shafa shaving cream a kirjinsa zai fara aski, na karbi a bar askin na jawo masa wata doguwar kujera ya zauna nace aske gashin kirjin zakayi harda shi gaba daya? yana kallon shiga ta wacce tayi matukar yi masa kyau yace kinyi kyau idonsa har ya canja nace tnx amma yanzu har kirjin zan aske? Kina so ne? Hmm in ina so ma ai baza ka barshi ba tunda baya cikin Business dinmu, murmushi ya saki yace sai a zame wasu kudin cikin naki tunda ke kike so kece zaki biyani kudin ajiye miki shi,kuma yana da tsada kin sani,nace a'a karka taba min kudi aske abinka na hakura,in kina so zan bar miki kyauta,to ina so a bar min,hanci ya lakace min Hajiyar kudi kenan,dariya nayi nace to an fasa askin ai sai kazo ayi wankan,jansa nayi yace ai baki isa ba yarinya sai dai ki tube muyi tare amma baza ki min wanka ki kalleni ba bazan yarda ba sai dai ayi 50-50,Dariya nayi nace a'a to mene na jin kunyata abinda nasan komai na kai hannu zan janye Towel din ya ja gefe da sauri tare da Jana ya tura ni bedroom ya kulle kofar yace je ki kawo min abinci kafin na fito,lallai Aayan yana da kunya wasu mazan kuwa ba ruwansu amma shi ya sanni na sanshi amma kunyar na kalleshi yake.

   Kafin ya fito na shirya masa komai a dakinsa ina zaman jiransa dama wankan sa dadewa yakeyi sosai yafi mata ma,yana fitowa nace nazo? Yana dariya yace a'a dan Allah zauna abinki zan yi da kaina nasan halinki kice zaki cire min towel,ina zaune ya gama shirinsa tsab cikin kaya marasa nauyi,nace Ohh kayi kyau shi kuma ya dawo inda nake zaune a kasan Carpet dake dan gefen bed na sa abinci gaba,ya wara kafafuna tare da Zama a gabana ya jingina bayansa a fuskata,kayi kato ai Sai kace wani yaro zaka zauna min a gabana kalli fa ta ya zan baka abincin kato da kai a gaban  karama haka ka fiye son jiki,ni a Sanina mace tafi Namiji son jiki sai gashi kai kafi macen ma,sauri ki bani abincin wajen Daddy zan je yanzu,nace da dare nan haka? Ae mana dan Allah kaje Dani pls kaji,Su Meenat fa? sai mu tafi dasu ko a barsu a gida,hmm ina tunanin ma fa Family House zamu koma again tunda naji abinda Daddy ke nufi kenan,Nan take hankalina ya tashi,raina ya baci,muna jin dadinmu shike nan amma ya za muyi ko dan sabo da Daddy sai mu koma,a fili kuwa ban nuna damuwata ba sai ma nace ah kace mu shirya kayanmu amma an gyara mana part ko tunda har almost 1wk bama ciki,yace an gyara komai neat amma ban san me yasa ba ban son komawa amma Kin San Hajja zata takurawa Daddy ne ta fara fushi dashi a kaina,abincin na fara bashi me shegen dadi fried rice tasha hadi da kaji sai fruits da sauran kayan ciye ciye,nace ba matsala karka damu zamu koma ko dan Daddy ba abinda zai faru,kin san ma mene? Nace sai ka fada yace Ameer shike zuga Hajja akan komai na tabbata ma yanzu shine yace sai an dawo daku gidan,nan take na kara Jin tsanar Ameer a raina,Aayan yace Ameer shi ya gaji Hajja a mugunta komai shike tsara mata da Alama ya tsaneki kamar haka nake gani,baki na tabe ta Allah ba tasa ba,ya zaiyi dani ai ni Duwawu ce dole a zauna dani,shegen dan iska,jaraba annamimi da fuska kamar yalo, dariya Aayan dinga yi yanda yaga sai zagin Ameer nakeyi ba ji ba gani yace zagin ma harda Raps Baby ba a tsayawa a huta,dariya nayi nima nace Allah dan iskan yaro sai iyayin jaraba yana gadara da takama sai kace shine Aayan,to ko shine Aayan ma ya isa ya min na kyaleshi,Dariya Aayan yake au nine ma me gadara da iyayi? Nace a'a misali nayi hhh,Allah mutuncinsa daya da yasa nake dan raga masa yanda kuke dan kama dashi kadai kuke kama a gidan nan ni ban san ma ya akayi yayi kyau ba matsiyaci,Nan take naga Aayan ya hade girar sama data kasa kamar zai dakeni,lfy? Allah Baka hakuri in dai akan na zagi dan uwanka ne,Allah dan kuna kama....Tsawa ya buga min rabon da naji irinta har na manta tun farkon haduwarmu dashi,masifa ya fara ni bama kama zaki ce yana da wani kyau baki da hankali idan sonshi kike ba sai kin fada min haka ba ya ja tsaki ya haura saman Bed abinsa.

   Firgita nayi kaina ya daure daga ana labari sai fushi kuma ni mene hadina da wani Ameer kuma,mikewa nayi nace kayi hakuri ba haka nake nufi ba ni,da sauri ya Zabura ya Mike hado kayanku a kaiku can sai ki dinga ganin Ameer me kyau,Ka fahimceni bafa nufina kenan ba wlh,mene abin fushi a nan ana lbr to kayi hakuri na furta cikin sanyi na,shekeke ya kalleni yace na rantse yau sai kun koma Family House Hajja bata isa tasa na Canja muku gida ba ra'ayina ne ganin damata ne dan kawai hankalinku ya kwanta muje kawai na rigada na rantse,gani nayi ina lallabashi yana wani kara hawa nace fine mu koma mana mene to, na fice na bar masa Bedroom din naga cikin fushi yake gaba daya yau. 

    Su Meenat suna shigowa na sanar musu su Kansu basu ji dadi ba,nace su hada mana kaf kayanmu,Meenat tace sis dazu naga wani wlh kamar Abbanmu a mota wani me kama dashi tsaki Naja tare da cewa sai me to dan kin ganshi tunda bai neme mu ba me zamuyi masa,Sis kamar fushi kikeyi lfy? Ko fada kukayi da mijinki? Nan take na fara hawaye ina sanarwa Meenat,Meenat tayi dariya tace Sonki yakeyi kishinki ne,ke komai kiyi fushi ai ba haka akeyi ba,ki daina cewa zaki rama abu ko dole sai kin maida martani kinji mene abin Kuka ai zaku shirya ne,idona na goge muka shirya,Sai ga Aayan ya leko fuska a tamke yace let's go,muka bishi har mota da kayanmu,Driver ne yaja mu har gidan sai da ya tsaya a inda ake siyar da wayoyi ya siyo guda biyu masu kyau da shegiyar tsada ya bani daya ya bawa Meenat daya,sai Meenat ce kadai tayi masa godia ni shuru nayi masa muka je har gidan,Ameer yana so zai fita da mota kawai ya hangoni wani farin ciki ya kamashi Bai San sanda ya tsaya ba ya fake da gaisawa da Aayan,Bro ya kk? Aayan yana fushi kamar zai tsage yace am ok,ya kalleni kawai yace Sis barka da zuwa ko kulashi banyi ba Meenat ce ta amsa,sai da ya kara yi min magana sannan na amsa da kyar ina fitowa da kayanmu,yace Bari na tayaku kaiwa ciki,Aayan yace no need jeka abinka,murmushi ya saki a ransa yana ko banza zan dinga kallonta ina jin dadi na.

   Hajja tana sama tana kallonmu sai murna takeyi burinta zai cika,Abbi bakin mugu yana kusa da ita yana tsara mata muggun nufi,matarsa ma haka tare da sauran  kannen Abbi,Ameer kuwa ganin na dawo sai ya fasa fita kawai ya koma part dinsu.

    Aayan sai fushi yakeyi nima haka aka shigar mana da kayanmu, komai Neat a gidan yasha gyara sai kamshi,muna Hutawa muka wuce bangaren Daddy har Meenat muka kwashi gaisuwa sai murna yake yana jin dadi tare da sa mana albarka,bamu zauna ba muka dawo part dinmu tare dasu muka fada kitchen kamshi ya fara tashi a bargarenmu,sai ga jaraba sun fara shigowa,Sajeeda da Haneefa sunzo harda lekowa kitchen suna tabe baki Sajeeda tace yara ana ta jagwalgwalon ne? kamshi na tashi kamar gaske a baki ba dadi bari yau zamu dan dana muji,Aayan yana jinsu basu San yazo sakkowa kasa ba,yace kafin nazo nan waje Ku tabbatar kun bace min a part Nonsense ya furta yana Jan tsaki,da sauri suka fice Sumi Sumi sai suka tafi wajen Hajja,tana ganinsu tace to fa Allah kawo mu jaraba ta dawo na shiga uku da kawo kara me tayi muku,nan suka shirya karya wai nice nasa Aayan ya zagesu kuma nace ya koresu,Hajja da kanta tace muje wajen nata na daina saurara mata.
    Suka taho Aayan ne ya bude musu kofa Hajja ta fara ta kansa kamar zata cire bakinta tana zagin Aayan,Haneefa tace daga munce idan ta gama girki ta sanmana sai zagi,Hajja da karfi tace ina makirar take tana shigowa kitchen tace gidan ubanki ne ko kayan abincin uwarki ce ta zuba mana,to dole suci idan naga dama ma part dinsu zaki je ki dafa musu abinda suke so,Aayan yace wlh basu isa ba ai ba baiwarsu bace ni na biya sadaki na aureta ba wanda zai sata ko ya hanata sai ni,Hajja ta fashe da kuka Wlh sai na fadawa ubanka yiiiiiiii,muna jinsu a kitchen tace ke dan uwarki wlh sai jikokina sunyi abinda suke so baza ki raba min kan zuria ba,matsiyatan bayi a gama a zuba musu suci,Meenat tace ga danye nan shine naku shi kuka siyo da kudinku wannan kuwa mun rigada mun dafa,kuma hakki ne a kan miji ya ci da matarsa muma tunda ba mutunci baza mu basu ba basu kai matsayin da zamu dafa musu abinci suci ba,Hajja tace iyeeeeee kana ji da girma na suke fada min haka? Yace ai Hajja kin dade da zubar da girmanki shi yasa suka take amma matata me tarbiya ce,Haneefa Hajja ta kiftawa ido tare da cewa Ku zubar da abincin uban kowa ya rasa,Aayan yace wlh duk wacce ta zubar sai gaba daya kun bar gidan nan yau ba gobe ba ai ba gidan ubanku bane,akan Mufee ba abinda bazan iya ba dama darajar Daddy kuke ci gaba daya zaku bar min gida wlh kunji na rantse,haba wani dadi ya kamani a kitchen mijina ya tare min fada ya nuna yana sona a gaban kowa,Muna haka sai ga Ameer da zureriyar wayar wuta,yace ke Sajeeda dan uwarku abin naku har ya kai kuzo kuna zagin matar Aayan,a ransa kuma matarsa yake nufi tunda sona yasa baya so ko sauro ya cijeni,Sajeeda zata masa rashin kunya ya fara tafkarsu son ransa sai da ya Zane musu jiki Hajja na tsine masa tana kuka.

   Gaba daya fadan ya koma kan Ameer Hajja ta sanarwa Abbi,nan fa Ameer aka hadu a kansa suka masa tatas,a ransa kuwa yace babu wanda zai taba Mufee na kyaleshi,ta nan bangaren soyayyar Ameer a gareni rahma ce sabo da shi ke Tsarawa Hajja komai baya bata me kyau a kanmu yanda zata ci mana mutunci,shi kadai ya samu Hajja ya lallasheta ta hakura yace Hajja Ku baku iya mugunta ba ai ba a nunawa mutum a fili ba a sonsa ta kasa zamu bullo musu ki daina bari ana musu a gabansu sai su dauki mataki suma fa suna zuwa gidan malamai nan Ameer yasa Hajja farin ciki ya gama tsarata tsab,yace Asiri muka yiwa Aayan yanzu abinda zasuyi a karya asirin dake jikinsa sai a dora sabon aiki,Hajja ta fara kiran malamai tana so a karya asirin dake jikin Aayan ko wanne iri ne,maganin tsari take so ayiwa Aayan sannan ta sake sabon kalar nata.
   Hajja ta manta Sam anyiwa Aayan asirin da bazai Haihu ba bazai iya komai ba,Kuma tace a karya komai dake jikin sa ko zai karye din oho?

  Abbi Kansu suna mamakin Ameer bai fiye shiga harkar su ta makircin da suke aikatawa ba sai jefi jefi amma kuma yanzu yafi kowa bawa Hajja shawara a kanmu,sai sukayi tunanin Ameer ya tsane mu ne da yawa shi yasa,suma murna sukayi za ayi maganinmu sunga muna nema mu canjawa Aayan zuciya kamarma ya fara sona tunda sunga yana bin umarnina sabanin wancan matan nasa na baya,amma Abbi yace shima dole ya shiga harkar nan dan ganin ya raba ni da Aayan.












AsmaBaffa
[1/17, 9:08 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

   KASUWANCI NA





          71-75









Official






By
AsmaBaffa








   Ina matukar Godiya ga masu Sharhi Allah ya bar Kauna,kuma Insha'allah daya bayan daya sai kunga sunanku a Novel din nan na Kasuwanci na,sai dai ko Halin mantuwa,ina ganin sharhin ko wacce kuma kuna cikin list dina,sai dai duk wacce taga kamar na manta da ita ta tuna min pls love u all❤❤

   Sai masu Sharhi wanda zasuyi watarana ban kula ba suga banyi musu reply ba kuma nayiwa wasu to ayi min Afwa ban kula bane, wacce taji ban kyauta mata ba kar tayi shuru tazo taci kwalata sannan ta tsige min dankwali ta wankeni tasssss🤣🤣🤣na baku dama.

   Ga page dinki ta gidana,Al albarka, masoyiya ta gaske me Sharhi kamar ruwa,kina birgeni KHADIJA A HAMZA

  Gaisuwa ta zuwa ga babbar me kaunata HANAN ta Gp na gata nan na Cillo ta ki cafketa.😍







    Abbi cikin takaici ya ja Hajja bedroom dinta yana cewa Hajja munyi sake,wlh munyi sakaki,taya zamu bari mu rasa dukiya muna ji muna gani,kin san yaron nan ya fara son yarinyar nan shike nan wlh sai abinda tace dashi talaucewa zamuyi dan naga Alama yarinyar nan bata da imani ko kadan, nan Hajja ta fada masa tsarinsu da suka shirya ita da Ameer,Nan take Abbi ya Dafe kai,yace shike nan kun kashemu iceko baku aikata ba? Ya zaki biye wani Ameer ai Rusa mana aiki ne wannan kin San mene a jikin yaron?dama da kyar muka samu wannan ya zauna a jikinsa,Hajja tace mene abin yi? Abbi da yan uwansa sukace ki bar komai a hannunmu,Ameer yazo shigowa wajen Hajja ya dau wanka so yake yazo part dinmu na ga kwalliyarsa.

   Yana jin me su Hajja suke yi hankalinsa ya tashi tabbas yasan sai sunga bayan Mufee amma yace ina Sam ba a isa ba baza a Rusa masa farin ciki ba,Shiga Bedroom din yayi tare da Zama gefe yana jinsu suna ta tsare tsare dan kar su gano shi sai ya dinga kiftawa Hajja ido yana mata signa da ido,ko idan Abbi yace ga abinda za ayi sai Ameer ya makewa Hajja kafada wai kar ta yarda,Hajja kadai ke gane me yake nufi,su kuwa su Abbi basu sani ba,sai ji sukayi Hajja tace me kuka sani,me kuka iya,har nawa kuke a duniyar,ni na tsuguna na haifeku zaku zo kuce ni zaku canjawa tunani,to baku isa ba iyyeee wato Ku ga wayayu wayonku yafi nawa?Ni wato bani da tunani ban san me nake ba ko? Abbi cike da ladabi ya Dafe kai yana Oh Hajja ki saurara kiji,Ameer ya kara makale mata kafada yana mata signa,Sani Kanin Abbi yace kai dan ubanka me ya sameka ne ko kafadarka ke ciwo ko tabin hankali ka hadu dashi,Abbi yace Lfy? Yace gashi nan Ameer sai wani makale kafada yake yana wani farfari da Ido ko dan daudu ka dawo bamu sani ba,kaga dan iskan yaro to uban me kake yi, pink lips dinsa ya turo yace to ni me nayi daga abu ya cijeni sai ace bazan sosa ba,Abbi yace to zaka bar dakin nan dan uwarka,Hajja tayi gazal tace kar Ku Zagar min shi ba ruwanku yaron kirki irin Ameeru dan albarka,Abbi ya tabe baki yaci gaba Hajja ki Bari muyi tsarinmu,Hajja tace sam bazai yuwu ba ni zanyi haka kawai na zauna jiranku wankin hula ya kaimu dare komai naku na yan boko sai anyi lissafi an tace an rairaye sannan a aikata,mu kuwa sha yanzu magani yanzu,Abbi suna matukar yin biyayya ga Hajja basa tsallake maganarta haka suka kyaleta cewa tayi nata suma za suyi nasu,Ameer ya kara kallon Hajja ya makale mata kafada Hajja tace a'a  ban yarda ba Ku bari idan na gama kalar nawa Bai yi aiki ba sai na baku dama kuyi naku mu gani,a haka suka tsaya amma Abbi yace karta je a karya asirin jikin Aayan pls sabo da akwai shirinsu a jikinsa,A nan kawai Hajja ta yarda cewar ta fasa karyawa kawai zasu ci gaba da nasu,a nan Ameer bai hana ba tunda ya hana abubuwa da dama kar Hajja ta ganeshi ne kawai ya hakura.

    Direct part dinmu Ameer ya zarce irin dole fa naga wankansa wanda ni ban san me yake nufi ba, ya kuwa yi dace muna zaune tare da Aayan a Palo yana fushi dani tun kan maganar Ameer dan nace yana da kyau,yaki cin abinci yau fushi yakeyi,har yamma 5pm yazo ya zauna a Palo,kuma nasan yunwa yake ji sai chat yake a waya,har sabon girki na masa kala biyu yaki ci,Yanzu haka ma Kunun gyada na masa na Dade banyi masa ba sai kosai naga yana sonsa,wanka na fesa Malam kamar a London cikin Wando tight iya rabin cinya Maroon,sai rigata fara me arnen kyau gashi yasha gyara na sakeshi na danyi masa style a gaban goshi kadan,Allah tsine wanda zai ce ban hadu ba yau ko mutum dutse ne yau ya kalleni sai jini ya fara gudana a jikinsa.

    Sabo da haka ma na kalli Meenat da suka dawo daga Islamiyya nace to ku zauna a Bedroom kar naga yar iskar da fito palo Dariya Sukayi Meenat tace to kin manta zamuje birthday party din kawata yau ni da Ma'eesha zamu wuce ta palon, wanne which kind party ba inda zakuje kun San dai ko Ammah na da rai bata bari muje wani party,bafa wani party bane na kirki sis,Driver baya nan kun sani schl ma yau banje ba kun  sani dai wa zai kaiku,zamuje a napep,fine amma kafin Ku fita kuje Ku fadawa Aayan shine ke rike mu yanzu kamar yayanku ne ko ma uba idan ya yarda kuje idan yace no shike nan.
   Meenat tace uhm lallai Sis yanzu mun koma hannun mijinki ma? To kici da kanki kiwa kanki Sutura sannan ki zauna a gidanki Meenat,duk wannan shike mana ai ko dole baza muyi gaban kanmu ba,ni macece Allah ya rufa mana asiri mun samu me Kula damu shike nan kuma komai sai muyi ba saninsa?

    To fa wasu idan ana rikesu a gida ganin wanda ke rikesu ba shine ya haifesu ba,kuma suna tunanin in ya tsine musu ko ya musu baki baza ta kamasu ba,kana gani zaka ciyar da mutum,ka shayar dashi,tufatarwa ka bashi ilmi da sauran abubuwa wasu ma ko yayansu basa yiwa rikon da sukewa dan riko sabo da su kyautata sai kaga kuma wanda ake rikewa yafi ma dan gidan iko,gadara,da rashin mutunci a gida,ayi ta ganin laifin masu rikon da ka zauna a gidan zaka ga yaron Ashe kwallon shege ne,ba wanda ya isa ya fada masa yaji,abinda yaga dama shi yakeyi baka isa dashi ba,da ka takura ace ka zaluncesu,kana gani zaita abinda yaga dama karshe ma wasu kaji a gari suna zaginka suna kala ma sharri cewar baka musu kaza kaza gari ayi ta tsine ma,karshe ma wasu su dinga cewa marikan nasu iyayen banza,ko a gidan suyi ta shirya ma mugunta iri iri suna zalintarka baka sani ba,more especially ace matar me gidan ce ta dauko wani ko wata take rikewa,suna ganin kamar itace da gidan ma ko saurarar mijin nata basa yi bayan komai shike yi a gidan suna cin arziki,kawai matar zasu fadawa itace take rikesu itace yar uwarsu mijin nata ko gaisuwa sai sunga dama,itama kuma tana kallo gani take ma ita ke musu komai ba mijin ba,bayan da dama zaka ga komai shi za a fadawa yayi musu amma Bai isa dasu ba,wani ko aikene sai dai ya aiki nasa ko na waje,da yawa ana magana kan azzalumai masu rikon yara ko yayan kishiya ko na yan Uwa ba a fadar laifin yaran,duk da cewa akwai masu zalincin Amma ya kamata mata masu dauko rikon Yara ko mijin ya kawo miki a daure a nuna musu muhimmancin me rikon nasu.ba kawai ayi ta yin abinda aka dama ba ana ganin ba iyayen da suka Haifa bane me zasuyi ya bika.

    Fita nayi ina sheka uban Kamshi Aayan zaune a palo yana danna waya na karasa dauke da hadadden tire jere da abinci iri iri,gaba daya bana jin dadin fushinsa yau,duk sai naji duniyar tayi min zafi,tun kafin na karaso ya zuba min ido yana kallona kamar ya hadiyeni naji dadi a raina ko bai fada ba nasan ya yaba kuma nayi kyau,kafin na gama tunanina ya juya min baya a saman 3seater tafkekiya,ni dariya ma ya bani kamar yaro na fushi,
  Ranka ya dade ga abinci ka daure kaci kaji,dama ni na saba da lallashin mutum kan dole yaci abinci ji nakeyi kamar nice banci komai ba shi yasa nake nacin sai anci abinci,Muna haka muka ji bugun kofar Ameer,na manta shigar dake jikina nayi hanyar Door zan bude, muryar Aayan naji a hankali yace kuma a haka zaki fita again? Da sauri na koma daki na saka Katon Hijab sannan na fito na bude kofar,Ameer yasha wanka gaskiya ba karya yayi kyau cikin kana nan kaya,Murmushi yayi min na bashi hanya ya shugo,Aayan tunda yaga shine ya kara hade rai da kyar ya amsa masa gaisuwar tasa,Yau Ameer harda ce min Aunty ya gida,ganin da mutunci yazo da fara'a na amsa masa nima sannan na koma kusa da kafafun Aayan inda yake kwance na fara masa tafiyar tsutsa a kafafu ina wasa da yatsunsa,Ameer yana satar kallonmu ransa ya baci sai kishi yake taso masa Amma ya danne, Aayan yana kallon yanayin Ameer shi bai yarda dashi ba sam yayi kicin kicin.

    Cike da shagwaba nace Yanlabai Abincin pls,wani shock yaji a jikinsa yanda nayi maganar shi kanshi Ameer sai da yasha mamakina a haka yar yarinya dani sai iya shege fal ciki,Ameer a ransa cewa yake ina ma nine Aayan gaskiya ya dace wlh irin wannan kulawa haka ga shagwaba kai da sake,a fili kuwa kamar baya jinmu danna wayarsa yake ya hakimce a kujera,Damun Aayan nayi da pls kajiii har sai da ya gaji ya mike zaune tare da ajiye wayar gefe can yace Bani zanci,da murna na zuba masa tare da mika masa,kin karba yayi yace hannunki aikin me yake? Da Sauri na gyara zama kusa dashi,yace ba fa a dining bane bazanji dadin ci ba,Nace ya zanyi to? Ke kika damu naci ai sai kiyi yanda kika ga dama ya fada cike da gadara, cinyarsa kawai na zauna samanta sosai bai ce komai ba sai lumshe ido da yayi ma,

na fara bashi a baki da hannuna idan na bashi bazai ko hadiye ko taunawa ba sai nace to ka ci mana sannan zai fara taunawa yana yanga yana kumbura wai fushi yakeyi shi fa,Ameer Kamar Tv yake kallonmu ya wuce gaban a share abin,yanzu ma waya Aayan yake dannawa yaki dago kansa bare na bashi abinci nayi nayi lallashin ya dago yakiya,sai ma ya kara yin can gefe da kansa ina binsa da kyar na rike kan da hannu na biyu na saitashi nan kuma ya tsaya Kikam a haka yaki bude bakin,Sai da nasa daya hannuna na bude masa lips sai ya datse hakoran nasa kuma suma,Yatsu nasa na ware su da kyar ya hangame dan mitsilin bakin nasa ya barshi haka,Ai Ameer tagumi ya rafka tare da Sa mu gaba kamar Tv yana ta dariya, na Sa masa abincin yaki kulle bakin bare ya hadiye nan ma Hannu nasa na rufe na matse bakin sannan ya cinye, haka yake ta bani wahala idan nayi wannan sai nayi wancan duk ya gajiyar dani ni kuma kamar dole sai yaci.
   Ameer ganin gatan Aayan yayi yawa ma haushi da kishi ya dameshi gashi wani abin yana sashi dariya ma watarana Amma kishi ji yake kamar ya mutu ko Ya batar da Aayan ace yau shine ake masa haka ai da yafi.

    Muna zaune na zubawa Ameer nace gashi Ameer kana shan kunun Gyada na sani ko? Ga abinci ma ka zuba ai ko ba ya sha sai ya sha yau tunda ni nayi girkin kuma daga hannuna ya fito, ya karba yana sha ko kallon Aayan baya yi Sabo da haushinsa yake ji ya aure masa Mufee Amma ta wani fannin yana godewa Aayan dan ta silarsa ya sanni kuma zai kwace ni nan gaba.

       Muna zaune sai ga Meenat da Ma'eesha sun dau wankan Material dinsu na ankon Birthday da zasu je yanda suka sha kyau ba a magana,Kamar yanda nace haka suka zo gaban Aayan tare da durkusawa suka gaisheshi cike da Ladabi sannan sukace Yaya Zamuje Birthday din kawarmu ta schl a gidansu akeyi idan ka Amince,mamaki yayi sannan kuma yaji dadi ga Sis dinsu basu nemi izininta ba sai shi gaskiya suna da tarbiya sun san me sukeyi,da murmushi dauke a fuskarsa yace shine kuka sha kyau haka salon a dinga kalkemin matana gaskiya am gealous dariya mukayi gaba daya har Ameer,Ameer yace Wannan Ma'eesha ai tafi kyau ma wannan Meenat ta fiye iyayin tsiya wai ita me kwalliya shi yasa bana kulata ni,Dariya nayi nace Wannan ai tsokanace Ameer kana ganin Yan mata an hadu,Ameer ya tabe baki tare da cewa masifaffiya dai ta fasawa Khaleel kai rannan wannan ai Dukan mijinta zata yi watarana, shi yasa ma bata da saurayin kirki sai irin su Kwaja da Nasuru Opera,Aayan ya sheke da dariya Kai Ameer wanne Nasuru Ópera din kake nufi? Ameer yana dariya yace Opera daka sani wanda su Haneefa suke aikensa Sa ido wajen wanda suke fada ai Camera suke bawa Opera Sabo da shige shigensa ake ce masa Opera kaga ko ina ka shiga ta Opera kayi Searching,Dariya muka dinga yi banda Meenat da take son yin Kuka.

   Ma'eesha tace wlh mantawa nayi Sis ban fada muku ba rannan ma a hanyar schl wani ya dinga bin Meenat yace sunansa FELA me GALA wai shi dan rawar gala ne  a kasuwannin kauye baku ganshi ba kafafunsa kamar na sauro yasha wandonsa Fela kato sai uwar Kafada kamar ansa riga a hanger ,Ameer yana dariya yace baki da sa'a Meenat Allah yayi a cikinsu zaki samu miji wai ya akayi ke duk wankan naki da iyayinki kike karewa a yaran su Sajeeda,Nima nace dama Yaran su Haneefa ne? Ameer yace sosai ma ai Fela Gala shike sanar musu duk wani wajen chasu idan za ayi show Saturday sunday irin su Haneefa ai duk basa muamula da manyan Yara,ki kula ki gani duk wata yar duniya me ji da kanta zaki ga mace har mace ga kudi ga kyau Amma indai lalatacciya ce bata taba kula mazan kirki sai daí ki gansu da maza kazamai,garori,munana, tabbas zancen Ameer hakane na fada a raina duk haka yan bariki suke kuma mace na ji da kanta Amma in kaga wanda take kulawa suna harka sai ka kusa kuka.

   Aayan yana dariya ya kalli Meenat da ta hade kamar yar Minister ya kasa rike dariyarsa duk ya san yaran nasu Sajeeda,karku damar min mata Kunji na fada muku kai Ameer tashi ka kai min su Driver dinsu dama baya nan kaga kaima kaci wanka kuje ko zaka samu wata Operiya a can kaima, wannan yarinyar da bata da kunya zaka ce na kaisu,Magana nayi nace haba Ameer ka kaisu mana kuje ku dawo yanzu ko dan ni ka taimaka,Ameer yace  a ransa dole na kai tunda Umarninki ne Queen Mufee ta,Tunda zan faranta miki ai zan kaisu dole,A fili yace Sunci darajar Ya Aayan da ke  kuzo mu tafi kuma ku tabbatar takalminku fes yake kar a bata min mota,Meenat sai Harara take zuba masa har suka fita tare gaba daya,da Sauri ya wuce wajen Hajja yace ku je jikin mota ina zuwa,

yana Zuwa wajen Hajja tana ta faman kurbar kunu yace Hajja Albishirinki na samo babbar hanyar maganin matsiyatan nan,Hajja tace mene abinda ka samo fada min Dan Albarka, yace yanzu zan shiga jikinsu sosai zaku ga muna mutunci dasu sosai,zan kwantar da kaina a wajensu yanda zasu yarda dani kinga kafin mu karbo maganin da zamu Sa musu na kulla alaka dasu me karfi ni sai na shige na aikata komai da Komai ko Ya kika ce,amma in ba haka ba za a samu matsala wajen aikata abinda malamai suke so a kansu tunda basu yarda damu ba,don haka yanzu zan fara kullum zaki dinga ganina a part dinsu zamu dinga mu'amula har su yarda dani cikin kankanin lokaci sai kawai mu gama dasu,Wani farin ciki ya kama Hajja,tace haka za ayi yanzu ka kawo magana me kyau,amma da ubanka yazo min da maganar banza ba basira ba wayo a ciki,to Amma kana ganin zasu yarda ka shige musu jiki har su yarda dakai? Ameer yace har nayi nisa ma yanzu ma sun yarda dani gashi nan sunce na kai mata kannenta wani party na dawo dasu,Hajja ta mike tsaye da murna dan Manzon Allah fa? Ko wasa kake?Yace da gaske leka ta window zaki gansu shi yasa nazo na sanar miki kar a kawo miki gulmata ki yarda kin san muna tare ke nakewa aiki,Hajja tace yo wa Isa ya kawo min gulmarka dan Albarka ai kasan bana yarda da maganar su a kanka,dariya Ameer yayi a ransa yace tsohuwa kenan nima kaina nake gyarawa hanyar samun Mufeeda na aureta ina ruwana da wani kudirinku ke dasu Abbi can da yawarku,a fili yace Hajja me zan siyo miki? Hajja tace abinda ka saba siyo min kullum dan Albarka,Ameer yace ai yau ba Hantar Rago kadai zaki ci ba harda yan shila idan ma dawisu kike so shi zan kawo,Dariya Hajja ta saki tace Ko mene ma duk ina so tunda kaine dan Aljanna.Ameer ya fito ransa fes ya tsara Hajja Sabo da yasan ana ganinsa tare da Su Meenat za a kai gulmarsa wajen Hajja ta daina yarda dashi,yanzu kuwa ya kashe bakin tsanya.

    Yana fitowa ya harari Meenat ke zaki shiga baya Ma'eesha ta ce zata shiga gaba tafi kyau baza a ganni da mummana a gaban mota ba,Meenat tayi banza dashi ta shiga bayan felleliyar motar Ameer, Ma'eesha a gaba,Ameer shi irin yan Tsabtar nan ne da shegen iyayi shi a dole Saurayi wankan ma da yake irin na mawakan turai matasa irin su Justin Bieber etc kowa yaga Ameer zaiyi tunanin kwallon dan iska ne ko ta askinsa kawai ba sai an tambaya ba,wandunansa kansu na zamani samari masu ji da kansu,Duk da cewa duk matasan yan wanka ne a gidan su Ameer Amma Ameer shi mata ma rubibinsa suke gashi da wanka Tsabta ga kamshi kuma yana da kyau wanda ke jan yan mata Uwa Uba ga diri me kyau.

    Aayan ne kadai bazai já dashi ba dan Aayan shi halittarsa ce ba kakalowa yayi ba haka yake komai in yayi me kyau ne,shiga kuwa dama shi a turai yake kana gani komai a jikinsa yake ba wasu yan dabaru akayi ba zallar baiwa ce,Shi kuwa Ameer tsabar kakale kakale ne da jarabar son iyayi ace Babban yaro sai da ya tsatso kyansa ya fito fili,Su Mujaheed ma haka suke shegun duniya ne wajen gayu,Suna Tafiya a hanya Ameer ya daga waya wata cikin yan matansa ta kirashi yanda ya kanannade murya kamar Sardaunan Ramlat yana Rapping English kamar wani Dj khaleed,Baki Meenat ta tabe tana jin iyayin da yake faman Digawa,aranta tace wannan wlh irin mijin Sis ne har kusan Halinsu ma sai daí Aayan karshe ne a komai,bayan ya gama wayar ya wani rare kidan Nija kawai tashi yake kamar zai fasa mana kunne,Maeesha ce mayyar rawa har ta fara yi a motar tana ihu uhhhh tare da dage hannaye sama,Shi kuwa idan kida yayi kida sai daí kaga ya bugu sitiyarin yana juya kan mota komar ma motar yakewa rawar,yanayi da kansa gashi duk Baiti ya iya abinda suke cewa kamar shi ya rerata, dama ga motar tasha tint ta samarin zamani,Maeesha yin abinta take wata tana shigowa me dadi tace ohhh yeee taci gaba da yi tana bi itama shi kanshi Ameer ta bashi dariya,ya kalleta yace ashe dai ke yar gari ce kin waye,duk kin san wakokin nan haka Amma kin iya rawa? Ma'eesha tace sosai ma ai  wayar Sis Mufee nake sacewa naje schl da ita na turo latest a wayoyin classmate dina,duk wacce ta shigo bata wuceni har rawar,Ameer ya mika mata hannu suka tafa yace kin birgeni ta gidana,ai kawai a Shana,tace tunin ma ai Baza a barmu a baya ba ina jss3 fa going to ss1 ai dole aje damu,Ameer yace yessooooo Baby,

Meenat tana jinsu suna tayi sun cika motar ga kida ga surutu suna ta yi da baki gashi ana jin wakar ana bi kuma da baki ga rawa anayi a zaune gaba daya sun gigita motar.
     Meenat kuwa wayarta take latsawa wacce Aayan ya siya mana tare katuwar gaske.
    a wani karamin hole akeyi Amma ya tsaru sosai wajen sabo da yarinyar dangin masu kudi ne shi yasa aka tsara abin,ashe yarinyar Cousin din Sameera me yan daba ce,itama Sameera tana wajen itace ma ta hada mata Birthday party din,Yan mata irin su Meenat duk sune a wajen ansha wanka da samari na schl Yara tare da wasu kuma manya sai yan Uwa,Yarinyar  Husna tasha wanka ana ta pics wasu na rawa,su Meenat ma suka Parker a wajen,Ameer yace ki bari yarinya na kankaro miki girma yanzu,Harara Meenat ta watsa masa,yace ni da zan taimaka miki nayi featuring dinki a wajen,Maeesha tace muje tare Yaya Ameer ni kayi ft dina ko a pics din da za muyi,kina ja Baby kanki na kawo light muje,ya rikewa Ma'eeshah hannu Meenat na gabansu duk inda suka wuce sai an kallesu,abinda Meenat bata sani ba an san Ameer sosai shima yanda yake nuna kudi da kalar Naira yana karyar arziki,kusan dama Daddy na Aayan ya makalewa lokacin Aayan bai dawo Nigeria ba,Ameer yake likewa Daddy sai da yayi suna sosai,ko a Tv za a nuna Daddy zai bude Abu sai kaga Ameer a wajen tun yana karami yake son ace shi wani ne yayi suna duniya ta sanshi shi yasa da farko bashi da Kamar Daddy shi yake masa labadi,ganin haka su Abbi suka juyawa Ameer hankali da ya girma sosai sai ya daina Saurarar Daddy gaba daya yake bin iyayensa.

     Ai kuwa Meenat tasha mamaki yanda taga ana ta kallon Ameer ana girmamashi ,mata na rubibinsa,Har uwar gayya Sameera tazo wajensa suka gaisa tace Ina Aayan?Yace yana gida,ka gaisa min shi,wannan yaran fa?ta furta tana mana wani kallon Banza,tana ta kallonmu tace Amma wannan sunyi min kama da wata sosai,yawwa yarinyar da Aayan ke aure,Ameer yace kannenta ne,Sameera tace kai Amma yarinyar bata da kunya ko kadan ina nan zan gyarata soon,nan take Ameer ya canja fuska yace ban gane ba? Tace kwarai tayi min laifi wanda ni kuma sai na nuna mata duniya ba kowa ake tabawa a kwana lfy ba,Ameer ya fusata yace lallai kema kuwa da kin tabbata wani in ya tabaka ya taba banza kuma ba kowa ake tabawa ace za a iya ramawa ba,wani in ya taba har abada ba a iya daukan fansa a kansa,Sameera tayi murmushi tace ba irinmu ba wlh,Meenat ma tace to ke har wace da baza a miki ki hakura ba wata tsohuwa ma dake,Sameera tace duk sai kun maimaita abinda kuka ce,Ameer yace Sameera kin san Halina ke a yan daban naki kanana ne kawai kallonki ake ana tunanin kin wuce haka Amma baki kai ba,wlh wlh kika sake wani abu ya samu Mufeeda ki fara irga kanki cikin wanda suka sheka lahira kin san mu kin san Halina try me.Dariya Sameera tayi tace Ameer kenan ko Aayan da take matarsa bai ce min komai ba sai kai? Husna ce tazo ta janye su gaba daya tana kuzo muyi pics nan fa suka dinga daukan hotuna Har Ameer dan shishigi cewar Meenat,yan mata kuwa jikin Ameer suke faman mannewa ana daukansu,anyiwa Ameer  ma haka inaga Aayan uban kyawawa da daukan wanka Meenat ta fada a ranta.

    Tunda su Meenat suka tafi naci gaba da bawa Aayan abinci yana min yanga,Yana karba da kyar har na gaji na mike na barshi a nan yana fushinsa,Kwashe komai nayi na gyara ko ina aiki yana kallona har Magrib tayi na shiga kitchen zan mana Dinner,Ban san sanda yaje masallaci ba kuma bai dawo ba har bayan Isha sosai,

     Su Meenat Suna gamawa Ameer ya dawo dasu gida sai da ya tsaya ya siyo musu ice cream sai yace banda Meenat bata da biyayya nawa dana Ma'eesha ne,Meenat tace sanda zansha ma ka sani ne,kuma sai na sha sai dai ka mutu.
    Ina gama girkin na gyara komai na gidan nayi wanka nasa rigar bacci ta da turare na kaiwa Aayan abincinsa yana dakinsa ya dawo ina ajiyewa na juya na bar dakin,Bedroom naje tare muka ci abincin  mu dasu Meenat muka koshi bayan ina dafawa naci wani kitchen Sabo da tsaro ko Aayan zai ce muci tare sai yaga ina cin kadan irin yar gayu ni.
    Muna gamawa mukayi Brush muka kwanta tare dasu kamar yanda mukeyi da,Meenat tace to yau kuma baza aje hirar ba?Nace ina ruwanki Sa ido,Meenat tana dariya tace a'a maida wukar bani na kar zomon ba,Sis yau ba jin dadi?Dan Allah da zafi ko dadi ne dashi nasan yanzu an gama kwashe ki,Dukan wasa na kai mata ina dariya nace zan ci uwarki wlh uban kwasheni akayi ki bari idan kinyi auren kyaji naki kalar, kwana nan zan fara zuwa gyaran jiki idan munyi hutun schl zan karbi kudi wajen Aayan Amma bazance gyaran jiki zanyi ba kar ma yayi tunanin shi zanwa ko sonsa nake,Meenat ta dinga dariya tace Sis wa zakiwa gyaran jikin to? Kyaji dashi can sai kizo nan ki tamana zancen da bashi kenan Ba can kuma da kinje ki zage ku sha love,oh karya nake miki kenan? Meenat tace to mu dai kiyi bacci dan Allah mun gaji da labarinki ke Sis sai za ayi bacci kice zaki bamu labari,ko tsakar dare ki tashe mu,

Nace Meenat kinfa rainani wlh tam,ai kuwa sunyi Baccinsu wurin 12 na kasa bacci sabo da tunanin Aayan Yamin yawa sai juyi nake ina tunano yanda muke murza juna ina murmushi ni kadai, na tuna da abinda nake so muyi shawara da Meenat Aiko ba bata lokaci na juya jikin Meenat dake shakar bacci nace Meenat ina girgizata tsaki ta ja  tana sosa gefen kunne,nace Meenat ki tashi mana na daka mata duka ta mike a firgice, nace mantawa nayi ban fada miki ba wai don Allah rannan kika ce kinga alamar Aayan kamar yana so na?

    Wani takaici ya kashe Meenat tace yanzu akan wannan zaki tasheni kusan karfe dayan dare?Nace ae gwara na kara jin gaskiya,cikin magagin bacci Meenat tace baya Sonki ko kadan,yaaaa tsaneki ne Sis kin kasa ganewa bakya birgeshi ko kadan ta koma ta kwanta sai baccinta takeyi,ni kuwa gaba daya naji duniyar ta kife min.

    Nan danan zazzabi ya fara kamani me zafi ga bakin ciki Meenat ta gano Aayan baya sona bana birgeshi,nan nayi tunanin yes gaskiya ne tunda ko yabo na ba yayi bai cewa ina da kyau na hadu,wannan ya nuna ya tsaneni sosai ne kawai sai na fashe da kuka na dinga yi da karfi a saman Bed cikin bargo,duk na hana Ma'eesha da Meenat bacci da Kukana sai ma kara karfinsa da nayi,sai tsaki sukeyi suna juyi su fa sam basa kaunar bacci tare dani dama tun Asali tun Ammah na da rai Sabo da tashinsu nake na hanasu bacci,lokacin ina Sana'a a gida tare da da Ammah cikin dare zan tashe su nace sai munyi lissafin kudi ko na fara basu labarin ya za ayi a tara kudi,ko tattali,idan kuwa nayi Sana'a banci riba ba ko jarin ya karye to fa sunga ta kansu kwana zanyi ina kuka a kan gadon mu,Ammah watarana sai ta jawo sandarta ta kwandala min sannan nake shuru dan ni bacci bai dameni da yawa ba,na riga na saba da jarabar neman kudi ban fiye bacci me yawan gaske ba.

   Suna jina kalar Kukan da nake harda me jiniyar motar yan kwana kwana,Meenat tasa Hijab ta fice har saman Aayan dan ita ta manta ma tace Aayan bai sona,cikin magagi ta fada min,knocking tayiwa Aayan ya zata nice sai yaji muryar Meenat,a firgice ya bude tunaninsa wani abu ne ya sameni tace wlh Yaya mudai kazo ka tafi da ita ta damemu wlh sai kuka take ta hana mu bacci,ko ka canja mata dakinta ita kadai mu takura mana takeyi,me ya sameta? Ba komai mu bamu sani ba dama haka takeyi ko a gida idan ta fadi a Business ko jarinta ya karye to sai ta kwana tana uban kuka har sai tayi Zazzabi,Aayan yace akan kudin? Meenat tace sosai ma watarana akan Naira darinta ta fadi a kasuwa sai da ta kwana tana kuka karshe sai da aka mata Allurar zazzabi Sabo da kuka,Duk daren nan sai da Aayan ya dinga dariya,Meenat tace ranar da jarin Awarar ta ya karye aka rasa dubu daya mun zata wlh ta samu tabin kwakwalwa,ni dai kaje dan Allah ka daukota a can ta damemu mu,maeesha ma tana zaune ba bacci kuma gobe muna da Test a schl.

   Meenat na gaba Aayan yana bayanta suka je har Bedroom din yanda nake haka nake ta barka kuka na,muryar Aayan dana ji ce tasa na kara ci gaba da kuka na yafi na da karfi ma,na cukwikwiye kaina a bargo ga uban gumi na hada,yace ke mene haka? Amma anyi girman banza babba dake to wa zai wa wani fada kenan? Na dauka ma lallashina yazo ya lallabani mu tafi dakinsa sai kawai naji ya rufe ni da bala'i, Kamar me Aljanu na dinga shure shure a Cikin bargon na kara ci gaba da kuka na,ina wayyo Marainiya ni,Zan mutu, Meenat tace baza fa tayi shuru ba wlh sai a kwana a haka da ita gwara ka dauketa kuje can in yaso ko zaneta ma kayi mu muyi baccin mu,Maeesha tace wai me akayi mata ne tana dariya tace wlh sis Mufee baza ta girma ba ko ni na fita wannan kuka dama ta saba abinta,Aayan yace Dan kune kawai zata hanaku bacci Amma da Bazan kalleta ba ta shekara tanayi,Meenat tace dan Allah ka rufa mana asiri ka dauketa muyi bacci,Aayan ya fara kokarin janye bargon dana ke ciki yana tsaki nace wlh tunda yayi tsaki Bazan je ba a barni nayi Kuka na,da karfi ya fisge bargon ya hau saman Bed din yanda nake kwacewa ina burburwa hannayena ya rike biyu na kasa motsi sai Kukana nake harda hawaye kwara kwara,ya samu bakina yasa yatsun hannunsa dan mugunta ya dinga dalla masa yatsansa kamar Harbin kunama ba shiri nayi shuru,tashi mu tafi yace, nace Bazan je ba,ai kuwa ya make min baki naji zafi ba shiri nace zanje wlh kayi hakuri,meenat sai dariya suke ya figeni yana jana fii yace kusha baccinku yau zata gane kurenta,Meenat ta rufe kofa tace wanne zata gane kurenta wai mu za awa wayo kuje dai ku sha iskancinku kuyi luf abinda shi kanshi kasa bacci yayi dama hakan yake so na ganeku.

   Ai kuwa kamar Meenat ta sani yana kaini Bedroom ya fara masifa yana min fada ke baki san kina shiga hakkinsu ba? Ba kyau takura rayuwar wani Yara suna so suyi bacci kuma a gabansu kannenki kike musu kuka,ai ba su akewa ba matan aure me gida sukewa kuka ba wani ba,idan shagwabarki kikeji kizo kiyi min ni zan dauketa ba su ba,nace to ni me nayi abinda fushi kake dani, yace ba dole nayi fushi ba muna Business dinmu kinzo kince Ameer yana da kyau ke yanzu zaki ji dadi nace Meenat ce me kyau ba ke ba,to ai nima sau nawa kace Meenat ta fini,wannan ai cin fuska ne,to ki kiyaye yanzu duk kinsa ma na fasa baki kudin Business sai an sake sabo,nima dadi naji zan masa wayo naji dadina nace to a sake sabon mana wa yake jin tsoro tunda kudi zan samu sai na samu wanda yafi na da ma.

   A ransa yace lallai Mufeeda yarinya ce yanzu ta yarda,nima a raina nace dadi a banza kuma a bani kudi nice da riba ka hadu da ni,Muryarsa naji yace to yanzu duk kukanki da shagwabarki Maza sauketa a kaina ki samu kudi kuwa da yawa yarinya,Nace ai ba sai kace ba yanzu zan nemo hanyar arzikina mota,gida da kasar waje ko da kafar katako,jikinsa ya jawoni muka fada saman Bed ba kunya na fara kuka na irin na dazu,shi kuwa lallabani ya farayi yana mene ne Pretty na? Na koma shagwaba kala kala yana biye min tare da fara sarrafani,a raina nace da haka kawai ina can zanyi kwanan kunci tunda hakane Meenat na gano yanda zan dinga baki aiki idan ta baci,Aayan kuwa a ransa dadi yake ji marar misaltuwa yana godewa Meenat dama ya kasa bacci ko kadan ni kawai yake bukata.








AsmaBaffa
[1/19, 12:07 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

  KASUWANCI NA




         76-80




Official




By
AsmaBaffa


Ina mika dubun godiya ta gereku
MAMAN 2 KIDS
AUNTY SUMEE
MEENAL SIDI
MRS HAMZA
ADABIYA ISAH
SAMEERA AHMAD
JAMILA SULE
MAMAN MEENAT

    Sai manya manyana ina jinjina muku
MAMAN MEENAT
MUM SUHAIL
MAMAN HAIDAR
QUEENMERMU
MAMAN WALEEDA
JIDDER ZARIA
MARCYCOOL
PHERTIMARH
AUTA
FLOWER ina kike kwana biyu Allah yasa lfy?
BIBA
HEENDU
HUMAIRAH



Page naki ne AYSHATABDULLAHI Me hadarin Sharhi na gode.👍😍




        Kwance nake a jikinsa na lafe luf muna huce gajiyar harkoki da muka kwasa,kin taba soyayya Ne Mufeeda? Naji muryarsa yana tambayata,wow yanda ya furta Mufeeda kamar wasu Aljanu ne suka fada Sabo da dadin sunan ba a cewa komai, kamar gaske nace ae na taba yi,gabansa ya fadi sosai ya shiga damuwa har kishi ya cika shi ya daure yace da wa? KUDI nace ina na san wani so ni ban san komai ba ai ni imani na kudi,ni kudi ne masoyina,Dariya yayi a ransa yasan ban san ma kudin ba ban san dadinsu ba Amma ina kirarin nasan kudi,a fili kuwa yace yanzu idan na baki million daya a hannunki me zakiyi da ita? Yanzu duk kuna ci kuna sha da Sutura ga schl baku da matsala da ita,ta ya zaki kashe million daya fada min naji? Kwanciya ta na gyara a jikinsa tare da fadawa tunanin ta yanda zan kashe kudin da ya fada,na gama tunani na nace na dinga cin kayan dadi,na fantama na Sa kaya irin na matan shugaban kasa,na dinga zuwa wajen da ake gasa kaji ina ci,na siyi fili kato,da mota,dariya yayi yace to kuna da motar hawa duk wacce kuke so akwai,me kike so kici wanda babu a gidan nan?Sannan kuna cin na wajen ma ai ko? Ae to ni dai ina so ace nima ina da nawa na kaina ba na wani ba,sabo dame?kayan mijinki ai naki ne, a'a ba nawa bane kafin a baka ma sai kayi yar murya,ko kuma a dinga bata rai ko kasa mutum ke ebowa ya baka watarana sai ya gaji,sannan Maza dan suna ma abu sai suyi ta juya ka ana ma kallon wata shatara, matan Hausawa kenan kike nufi duk abinda yasa suke karatu da aikin Gomnati don kawai su samu kudi ba sai sun saurari na mijinsu ba,kuma most of them badan Allah suke so su samu kudin ba kawai biyayya ce basa so suyiwa mijinsu shi yasa suke neman kudin, ya fita kin fita,bai Isa ya saki kiyi ba,wani ma in kudinta yafi na namiji zai sha wulakanci dole shi zai kwantar da kai yana mata biyayya.

    Nace hakane ko Ilmi macen tafi namiji sai kaga ko kudin albashi ya dauka ita zai kawowa sai yanda tayi dashi,shi yasa Maza suke tsoron auren macen da ta fisu Ilmi ko ta fisu albashi,sabo da matan Hausawa basu iya samu ba,mace daga tana daukan dan Salary sai kuga ta fara wulakanci kowa taka shi takeyi ita me kudi,dan Allah mata mu gyara halayen mu,wasu gidansu kaje da kyar suke kallonka ma bare mutunci ya hadaku Sabo da tana daukan Salary,mazan sam basa jin dadinsu,ga jarabar son kudi da neman kudi aje nan aje nan ba hutu ba lokacin me gida kuma bai Isa yace komai ba tafi karfinsa sai abinda taga dama,idan ma kishiya zaiyi cewa zatayi ya kara me ya dameni suje can su karata da kudina me nake nema a wajensa ko Sakina yayi zan iya rike kaina da Yara na,abin haushin kuma da zasu rabu sai aga ta koma bin Maza kanana tana kashe musu kudin da ta kasa taimakon mijinta dasu.

    Mun dade muna hirarmu dashi yana wasa da dukiyar fulanina wani dadi na shigata na juyo ina facing dinsa tare da kara shigewa jikinsa,yace ya dai? Wani sonsa nakeji yana ratsani ta ko wacce gaba dake jikina,baki nasa ina lashe lips dinsa kamar mayya nan ma haka muka kara birkita kanmu mun dade muna farantawa juna rai,ni kam yanzu son Aayan ya gama ragargaza min zuciya,kwakwaran numfashi banayi sai da tunaninsa,komai nasa birgeni yakeyi,ji nake kamar a hademu na zauna cikin jikinsa har abada abin fa ya wuce gona da iri yanda nake jin son Aayan ya zarta hankali har mamaki nakeyi,bani da burin da ya wuce na ganni tare dashi ina jikinsa,kallon Aayan kadai idan ina yi a Cikin gidan gaba daya sai naji dadi da sanyi marar misaltuwa,nayiwa zuciyata fada abin yaci tura,ko schl naje ba komai nake ganewa ba kawai tunanin Aayan yafiye min komai a duniya.
     Kwanaki sun dan ja,Ameer ko yaushe yana part dinmu kusan kullum sai yazo,a nan yake cin lunch da Dinner haka kullum suke fada da Meenat,Ma'eesha ce kawarsa kullum suna tare suna danna waya da jin wakoki aikinsu kenan, Meenat bata da time yanzu karatun waec da Neco sukeyi,Ma'eesha kuwa za a shiga Ss1 kwana nan,ni kuma ina ss1 going to 2 Sabo da ya tsallakemin jss3 ban karasa ba aka sani a ss1 shi yasa Amma da Ma'eesha ma ta fini class.
   Ma'eesha ta zama yan mata Sabo da kansu daya da Meenat kusan ma tafi Meenat girma ta kamoni Sabo da dama tana da saurin girma tsayin kafa tayi sai ka rantse ma ba Meenat ce yayarta ba,Sabo da zama da suke yawan yi da Ameer Ma'eesha har ta fara son Ameer sosai Amma boyewa takeyi dan kar mu gane sai dai kullum bata da zance sai Na Ameer.
    Kudi masu yawa Aayan ya bamu muje mu sake uniform tare da schl bags da takalma amma sai yace yasan idan nice me araha zan siyo mu tafi tare da su Meenat Driver ya kaimu.

     Muna mota Driver zai kaimu store nace canja hanya Baba ka kaimu Kasuwar kofar Wambai yafi araha,Meenat tace wlh mu store za a kaimu masu tsada yace a siya mana,Baki na make mata tayi shuru,ya kaimu Kofar Wambai muna gaban table din masu takalma ina ta zabga cikiniki yaki daidaita,na daga wani baki nace nawa wannan Malam? Dubu uku yace,a garin ina za a siyi wannan dubu uku Malam Dubu daya da Dari biyar idan ka siyar, Ma'eesha ce ta matsa gefe tare da kiran Aayan a waya Hello Yaya taki kaimu store wlh muna kasuwar Kofar Wambai kuma a kasuwar ma table din masu araha wai dan Dubu daya da Dari biyar kuma suna ta Surutu da masu saida kayan dan Allah da aurenta fa Yaya.
    Mata masu zuwa kasuwa a zauna ayi ta Surutu da masu saida kaya,da aurenki zaka ga wasu har canja murya suke suna lankwasheta abinda basa yiwa mazajensu sai siyiwa yan kasuwa sabo da suna neman a rage musu ayi musu araha su siya a banza.

   Aayan kuwa kishi ne ya sokeshi da bacin rai wai yacewa yarinyar nan  suje Mall amma ta kaisu kasuwa cikin maza ana ta cakudewa yanzu haka ma wani ya gogar masa jikin matarsa nan take bai San sanda ya shiga mota ba ya bar Office driver ya ja suka tafi,a hanya ya kira Ma'eesha ta fada masa inda suke minti kadan sai ga Aayan ya danna musu Horn tare da sauke glass.
    Ina ganinsa hankalina ya tashi na rude ko ta kan me kaya banbi ba nayi sauri na isa motar mu na fada ciki,Meenat da Ma'eesha suka shiga bayan mota kusa da Aayan da Kansa ya kaisu Shopping ya siya musu wanda suke so masu tsadar gaske komai har ni ma suka siya min nawa,ni kuwa tuni nasa Baba Driver ya maidani gida.
     Da suka dawo da kyar na fito palo,Ranar da dare nasha warning wajen Aayan sai da ya min ba dadi ina bashi hakuri.

    Anyi mana hutun schl Meenat tana zana waec da Neco dinta,yau Sunday muna zaune a palo ina yankewa Aayan Farce,Ma'eesha na karatu a wayarta da Ameer ya siya mata me kyau,Meenat kuwa abinci take ci dawowarta daga schl kenan yamma lisss,wayar Aayan ce ta fara ruri,da hannuna na daga kiran naga ansa Bobo nasan Yarima ne na kara masa a kunne yace Hey frnd  ya kk,Yarima yace gani a gidanku fa bude min kofa, Ma'eesha yayiwa magana yace budewa Yarima kofa Angel dama haka yake cewa Ma'eesha,Meenat kuma yace mata Preety, ni kuma daga ke shike nan sai ta mugun baci zai ce Mufeeda ina takaicin wannan abun da yake min Amma ya na iya tunda ni ba a sona.

     Ma'eesha na bude kofa Yarima yayi arba da ita wow ya furta a ransa da gani ba sai an fada ba yasan ma kanwar matar Aayan ce Sabo da kama da muke kawai haske zan fisu kadan shima idan baka sanni sosai ba baza kace na fisu haske ba,ba wani me yawa bane,Maeesha akwai fara'a ta gaisheshi tana murmushi sai kallonta yake ta gama Tafiya da Imaninsa gaba daya, bashi da burin auren yarinya karama Amma akan wannan kuwa sai dai a mutu, da sallama dauke a bakinsa ya shigo,Gaskiya Yarima ya hadu Chocolate ne me haske karshen kyau yana da shi dan fulanin Asali ne,ga wanka iya wanka dama duk irin abokan su Aayan ai haka suke basa muamula da garori, Ma'eesha kuwa kunya ma taji irin yanda ya mata Kwarjini gashi ya hadu sai kuma irin kallon da yake mata.
    Yana zuwa ya mikawa Aayan hannu suka tafa shegen gari kwana biyu Aayan ko Saudiyya banga kaje Umrah ba last wk ina can ina ta jiranka kace zaka je har na dawo bamu hadu ba,Tabe baki Aayan yayi tare da cewa gwauro shike yawo lokacin da yaga dama,dariya Yarima yayi lallai Aayan ka canja,juyawa nayi muka gaisa dashi a mutunce yana tsokanata da Abokinsa yayi kiba ya kara kyau me nake bashi ne,Meenat kawo masa ruwa,Kallon wacce aka kira da Meenat yayi tana can Dining tana cin abincinta da alama bata San anyi bako ba,Yarima a ransa yace su wannan gaba daya kama sukeyi da juna amma Ma'eesha irin muryata ce da ita sak,Meenat ce muryarta tafi tamu siranta sabo da iyayinta ta maidata siririya,kayan sanyi ta kawo masa iri iri kana ta gaisheshi a ladafce ya amsa tare da cewa Mufeeda wannan duk kannenki ne? Ae mana wannan Ma'eesha wannan Meenat,yace ke kuma Mufeeda triple M kenan yeah Ma'eesha ta amsa muna dariya,Meenat yan mata uwar iyayi tana ji da yan matan ci sai girman kan tsiya watarana kamar wata yar sarki aka take komawa magana ma sai taga dama,watarana kuma ta zage ayi da ita,Muna zaune ana hira sai ga Ameer ya shugo an ci wanka yazo dan ya birgeni ni Mufeeda wacce ban san me yake bama,Maeesha har taji sanyi data ganshi kusa da ita ya zauna ta gaisar dashi,Yarima ya fara kishin Ameer ya zauna kusa da Ma'eesha kuma yaga Ma'eesha sai wani Fara'a take masa sun fara surutunsu da alama sun saba da juna,s hi kuwa Ameer gaba daya Hankalinsa na kaina yanda na hade cikin Lace riga da skert ba karamin kyau nayi ba,abinda ya bashi haushi ganin ina yankewa Aayan farce gashi kuma kafafun Aayan gaba daya saman cinyata ya dorasu yana kwance dan naji dadin yanke masa farcen.

    Muna zaune daf da Magrib wata yar aiki ta shigo wai Meenat tazo tayi bako,Meenat tace ita bata da bako baza taje ba,tun kafin ta fara magana Ameer ya fara dariya,haka Aayan ma,nima na gane me suke nufi ko irin su Kwaja ne suka zo,Yarima yace mene haka daga ana kiran yarinya zaku fara mata dariya bai dace ba,Yar aikin tace a wata fyallelliyar mota yazo Hajiya da gani dan wanine,Nace mu ai bamu damu da wani me mota ba ko talakane indai yana da aikin yi,halaye masu kyau to alhmdllh zamu bashi ba wani sai me mota ko kudi etc,Aayan yace Pretty jeki kiji idan Bai miki ba ki dawo,kawai sabo da Aayan ne yace shi yasa ta figi Hijab tana fushi zata fita,nace ba kwalliya haka za a je? Kallona tayi kamar zatayi kuka ta fita abinta haka, taga mota iya mota tana jira taga wani Handsome ya fito sai taga Fela Gala da gani ba motarsa bace arota yayi, fitowa yayi tare da tsayawa yasa Hannu a aljihu harda Harde kafafu ya basar a jikin mota sai yanzu ma ta gane Ashe Motar tana ganin su Haneefa a cikinta,wato sune suka bashi aro azo a raina mata hankali.

   Ko saurarar Fela batayi ba tayi gaba abinta sai gata ta shugo kamar zata fashe tana wa Aayan magana dan Allah Yaya ka ganshi can ya biyo ni har gida wlh dan Allah ka koreshi sune suka kara turoshi, Ma'eesha tace Fela Gala ne wlh tun daga sunan Yarima shima ya fara dariya bai Sha dariya ba sai da ya leka ya ganewa idonsa harda rike ciki sabo da dariya,Ameer kuwa ba a magana,Aayan ne ya fita ba shiri yayiwa Nasuru fata fata da gudu ya fice daga gidan ya bar motar dama ta gidan ce.
   Meenat ta kalli Ameer tare da zuba masa Harara ta wuce Bedroom ta barsu suna bawa Yarima labari duk kwalliya da iyayin Meenat irin su Nasuru Fela ke zuwa wajenta,Yarima ya kalli Ma'eesha tare da cewa to ke yar ficika wanne kala ne naki? Dariya sukayi Sabo da Fela Gala ne yace mata Yar ficika,Maeesha tace ni yarinya ce ba yanzu ba,wani dadi Yarima yaji a ransa,Maeesha kuwa a ranta cewa take insha'allah Ameer ne ma,Shi ko Ameer tunani ma yake yaushene zai mallaki Mufeedansa,Ni kuwa ina nan zuciyata dankare take da son Mijina Aayan wanda naga Sam bai damu dani ba.
    Sallah sukaje masallaci har Isha basu dawo ba,lokacin na tattara su Meenat muna kitchen muna karasa abincin da muke,suna dawowa na fito da ludayi a hannuna ni ga uwar girki na manta ma da Ludayin juya miyar na fito,Ameer yace ina zaki abun miya kuma? Nace na manta sauri nake nasan Babyna yanzu wanka zaiyi,Ameer nan take mood dinsa ya canja amma ni ban gane ba nace bari ka gani na koma kitchen na ajiye ludayin na fito naji muryar Ameer yace mu dai ki koma ki karasa mana abincinmu yaran nan jagwalgwalo zasuyi mana,murmushi nayi nace sun iya sosai ba matsala,ya kara magana pls Aunty kije ki karasa da kanki,nufin Ameer dan kar naje wajen Aayan shine ya hada min wayo wanda ban sani ba ni kuma sai na koma kitchen din,n a tayasu muka karasa komai na barsu su gyara kitchen tare da shirya Dining,dana fito nace Ameer ina Aayan fa? Baki ya tabe yace suna wancen palon shi da Yarima,palon da ya fada min na nufa

    Direct naje shiga palon naki muryar Aayan yana cewa kyaleta ai wahalar da kanta takeyi bari nayi ta gama shiga hannu zata ga wulakanci,sai suka tafa da Yarima,nan take naji jikina ya dauki rawar sanyi,tsoro da fargaba tare da bakin ciki ya dirar min,ban san wa suke nufi ba,ban san akan me suke maganar ba sai na fassara maganar da naji kawai ba bincike ban tsaya naji dalili ba ko da wa yake nufi kawai sai na yanke hukunci cewar ni suke nufi dani suke,wato ni ya gano ina sonsa wahalar da kaina nakeyi,ya bari na shugo hannu ya wulakantani,ni zai wulakanta ma tab lallai dan Adam,duk abinda nakeyi Ashe baya gani a banza sai ma mugunta da yake hada min,nan take na fara tunano tun farkon haduwarmu irin tsanar da ya nuna min,Ammah ta da suka kashe min tunda sune suka jawo duk so yasa na manta,har aurenmu irin abinda ya dinga min a farko na wulakanci ina ta binsa,so yasa na manne masa nake kai kaina har dakinsa na sakar masa jiki,nasa yaji dadi,na godewa Allah da yasa ba ayi sex ba.
    Mata da dama suna irin wannan daga jin magana bata kai ta kawo ba,basu san ma akan me akeyin ta ba,amma da yake kullum a zargin mazajensu suke irin ko sun daina sonsu,ko suna kula wata,musamman ace suna da kishiya ko zai kara aure,ko wani dalili yasa dai taga mijin ya dan canja to zargi zata kasance a ciki iri iri,komai yayi laifi ne a wajenta,magana idan ta ji ko da abokinsa sai ta fassarata ta koma tashin hankali Babba,wata ma har abokin zata daina kulawa,ko ta masa rashin mutunci,miji na neman aure abokin dole shine a gaba wai dan me zaiyi nan fa zata kulla masa wata ma sai ta rabasu sun bata sun daina abotar,wata kuma duk abokansa ta daina kulawa ko ta ci musu mutunci wai sune suke zuga mijinta,duk da cewa ana samun masu hakan amma mata mu daure mu daina zargi tare da saurin yanke hukunci,ko magana akayi sai a dinga fassara ta bai bai sabo da ba a son zaman lfy.

     Ni dai ina tsaye naji kamar ma zazzabi zan fara sabo da yanda nake son Aayan ko kaina ban so haka,bani da burin da ya wuce naga ya soni back amma sai gashi abinda naji ma daga bakinsa,Hawaye na share na daure na shiga palon fuskata ba walwala nayi Sallama suka amsa,Nan take Aayan ya kafeni da idonsa yana ganin yanda lokaci kadan na fita daga hayyacina,dazu lfy lfy muke,kamar ma kuka nayi,ganin yana kallona nayi kasa da kaina,tunaninsa ko yan gidansu ne suka yi min rashin mutunci ya tabbatar idan kuwa sune suka sa na dawo haka yau sai anyi yaki a gidan nan,baya son a taba masa ni yanzu ko kadan, kasa jurewa yayi yace ina zuwa Yarima yaja hannuna mukayi waje dashi muna fitowa a jikin kofar yasa yatsansa tare da dago da fuskata yana kallona sannan a hankali yace lfy? Me akayi miki? Nayi shuru,Hajja ce? Su Haneefa nan ma shuru sai Hawaye dake biyo min a kumatuna a raina ina kara cewa yanzu wannan zankadeden rabuwa zaiyi dani,shike nan baya sona? Yace am asking u me suka miki ya fada da tsawa,duk ya shiga damuwa lokaci guda ya rude Allah sarki So,so banza ne kawai sai ya bani tausayi kuma na batawa wanda nake so rai,har bana ganin laifinsa sai nawa sabo da Aayan baya laifi a wajena so hana ganin laifi,tunowa da maganarsu dana jine yasa na kara birkicewa,kawai nace ni ba wanda ya min komai kawai ji nayi bana son auren Kasuwancin nan ko nawa zan samu,ko yanke talauci ne wlh bana sonsa dan Allah ka sakeni na tafi, wani dum yaji maganar a bazata to ko dai itama sun mata wani asirin ne ko kuma sun sa mata wani abu taci ai ko wlh bazai iya sakinta ba har abada sai dai duk inda zata je da aurensa,jikin Bango ya Dafe kawai yayi shuru yana Innalillahi kawai yake maimaitawa duk zarginsa tunaninsa Su Hajja ne ko asiri ko kuma wani abu suka mata wanda baza ta iya zama ba, da kyar ya dago muka hada Ido sai da na rumtse Idona yanda bazan iya kallonsa ba ya Zama wani iri idonsa yayi jajir,Hannu na ya figa kamar zai tashi sama ya jani muka Haura samansa har Bedroom ni dai kawai binsa nakeyi,a ciki ya tsaya tare da rike kugunsa da hannu biyu kansa ya daga sama yana danne lips dinsa na kasa da Hakoransa yama rasa ta ina zai fara, maganarsa naji a hankali yace Mufeeda! na kalleshi tare da sadda kaina kasa,yace ki fada min me ya faru dake me kike ji me yake damunki ko kuma a gidan ne wasu suka ce miki wani abu ni dai nasan ban miki komai ba,ko kema sabo da bamuyi Xxx ba zaki tafi? Da sauri nace a'a wlh ba haka bane,yana kallona yace to ko bana Haihuwa kike nufi? Nan ma kafin ya rufe baki nace wlh ba wannan bane,to mene tell me,karki rufeni ko ki cuci kanki just tell me what's is going on? Ina Hawayena nace ni kawai na gaji da auren ne Bana son kudin yanzu,Wait bafa Business muke ba wannan wasa ne kema kin san aure ne na sunna aka yishi ba wai akan kudi ba,nace ae na sani kawai bana son auren ne nace ma ni bazan zauna ba kawai,ok yace ko gidan nan ne bakya so? Fada min sai na Canja muku gida,kai na girgiza a'a, yace ko Wacce kasa kike so fada min wlh zamu koma can indai kina so,a raina nace jibeshi kamar gaske salon ya kara mallake min zuciya yaji dadin wulakantani da kyau to bazan je ba,nace bazanje ba ni a fili,Abuja fa?nace ko villa ne banso,to kiyi Hakuri idan wani abu aka yi miki addua akeyi akan komai ba fushi ba haba yan mata nan ya dinga lallashina,sai nayi kamar zan Yarda naji tausayinsa sai kuma na fasa nace nifa bazan zauna ba.

   Yana gajiya ya tamke fuska ba mutunci yanda na sanshi tun farko,nan take naji tsoronsa jikina ya fara rawa, tahowa yayi kamar zai makeni na fara ja da baya yana Huci yace bari kiji bude kannenki wallah kinji na rantse har uku bazan sakeki ba kuma ba inda zakije idan kika fita ma ko gate ne bada izinina ba sai munyi Shari'a dake a gaban Allah ban yafe miki ba,kiji ni da kyau ba wani Business auren za ayi as from today ni kuma duk Hakkin ki daga yau zan fara baki,yana gama fadin haka ya kwanta a saman Bed yana Dafe kansa dake Sarawa, tausayi kuma ya bani sosai yanda ya nuna ya damu a kaina gaba daya sai na tsani kaina me yasa nayi haka,amma dai zuciyata ta hanani na hakura,ido ya rufe sosai still yana Dafe da kansa ya rike sosai da alama ciwo yake masa da yawa,Hankalina ya tashi nima,mikewa yayi tsaye kamar wanda yasha giya yana maye da tangadi,haba ban san sanda tausayinsa ya gama rufeni ba gaba daya naga ya fini shiga damuwa yazo ya ratsa ta gefen zai wuce ya fita tuni na damko hannunsa ya tsaya cak tare da juyo da fuskarsa ya kalleni gabansa na koma tare da fadawa jikinsa na rungumeshi kam kam sosai da sosai kamar za a kwace min shi, baiyi hugging dina back ba,da kaina cikin kunnensa na rada masa Rug me back am so sorry, bai kulani ba babu zato naji bakinsa cikin nawa ya fara tsotsa ya rabani da kasa dan dagani yayi sama yanda tsayinmu zaizo dai dai ba sai yasha wahalar sunkuyoba,haka muke tsotse bakin juna kamar mun samu wani kayan dadi na tsotsa,wannan kiss din yafi na kullum dadi,gardi,tare da nishadi,yanda nakeji  ya zarce na fada muku,muna ta yi ba ji ba gani kamar zamu cinye kanmu ko nayi kamar zan kwace bakina sai ya kara rikeni kam ya hanani sai da muka dauki dogon zango a haka sannan da kyar na zare jikina daga nasa,amma duk da haka kara jawoni yayi jikinsa tare da fara lashe min wuya,tsigar jikina tashi take kawai gaba daya ya gama kara min sonsa a zuciyata, da kyar nake iya tsaiwa da kafaguna shima haka,ya fara kokarin cire min kaya na tuna yayi maganar hakki dazu da sauri na rike masa hannu tare da cewa abinci still dai ban saki raina ba bana wani nishadi kamar dazu,kyaleni shima yayi fuska ba walwala yace let's go,sai da muka saita kanmu sannan muka sauka kasa,Gaba dayansu Har Yarima da Ameer suna Dining suna ta cin abincinsu muka sakko duk kayanmu ya nuna da gani anyi yamutse yamutse,ga T-shirt din Aayan Fara kar ce duk jambakina red da Powder a jiki duk na shafa masa ba tare da mun sani ba sabo da murzar juna,Yarima da Ameer duk sun gane me akayi,Meenat ma ta gane gani ba jambaki a bakina sannan duk ga wani nan a bata gefen bakina,Aayan harda digon jambakin a hancinsa duk sai yanzu ma muka kula da hakan,Yarima sai dariya yake kunshewa yana kallon Aayan, dan Iska wlh zaka bar gidan nan banza munafiki Cewar Aayan,Yarima yace to me nayi kuma? Bayan ka shanyani,Ameer kishi ya hanashi kallon kowa kawai tura abincinsa yakeyi,Aayan har yau yana cikin damuwa ya kasa cin abincin kuma yunwa yake ji,ni kuwa bakin ciki baya hanani cin abinci ko cuta nake sai naci na koshi haka nake bare kuma kafin naji Maganar da su Aayan sukeyi tun a kitchen muna girkin na cika tumbina, ganin ya kasa ci na Mike tare da Zama kujerar dake kusa da tashi zan bashi da kaina,kafin na fara Ameer ya ajiye spoon yace ina zuwa bari nayi waya ya fice da sauri zuwa part dinsu,Yarima yace nima tafiya zanyi Ma'eesha zo ki rakani mota nan yayi mana Sallama suka fita,Aayan yace sai nazo zanyi maganinka ya furta da alama kawai danne bacin ransa yakeyi,Meenat ma tuni tayi Bedroom zata fara karatu,daga ni sai shi ya Dafe kai tare da rafka tagumi da gani yana cikin damuwa me yawa.

     Hannun da yayi tagumi na janye a hankali ba tare da nace komai ba na ebo abincin a spoon na fara bashi da kaina yanda yake ci zaka San baya jin dadinsa ko kadan,kamar kurame haka muke har yace ya koshi nace ko spoon biyar baka ci ba fa? Zan fara masa magiya ya Mike kawai ya haura sama ya barni a nan,ban damu ba na tattara komai na kai kitchen tare da gyara komai na shiga Bedroom dinmu nayi wanka da duk wani abu da zanyi nayi nasa Night gown dina da kawata Sayyah ta bani wai inji mamanta kala Uku hadaddu amma basu fiye tsaraici ba nasa light blue din masha Allah nayi gaskiya karshe na daura ta samanta na fita lokacin Ma'eesha ta dawo daga wajen Yarima tana nuna min chocolate masu Uban yawa da kudi masu yawa wai a bani inji shi,na karba nayi godiya nace bari na nunawa Aayan kafin Ku fara sha nayi waje zuwa Bedroom dinsa,gefen Bed na hangoshi a zaune yayi shuru kawai yana kallon sama da alama tunani yakeyi yaji Sallama ta,amsamin yayi kawai tare da kwanciyarsa saman Bed ya barni a tsaye,banji dadi ba ni kaina muna zamanmu lfy na jawo bacin rai kuma shi dama kafin a lallasheshi aikine.

    Haneefa ce Zaune tare da Mommynsu suna hira,Mommy tace Ameer naga fa kamar kwanan nan ya Mannewa wajen yan iskan can a part dinsu ban san ko Hajja tasan labarin ba,Haneefa tace Mommy ki barshi ai da alama bata sani ba gwara ma da kika tuna min bari naje na fesa mata tayi maganinsa ya daina zuwa na tsani Su Mufeedan nan Shegu wai su masu kyau,Mommy baki ta tabe tare da cewa je ki sanarwa Hajja ni ma yau zan fadawa Abbi abin na Ameer yayi yawa, da sauri Haneefa ta tafi part din Hajja,ta samu Hajja sai Mulki take zubawa tana wani takama da isa tare da bawa yan aiki umarni.

     Haneefa ta zauna gefenta tare da cewa Hajja wani labari na kawo miki marar dadi so sad wlh abin kunya ma,Ina jinki Hajja ta furta tana gadara,Haneefa ta gyara Zama tare da sanarwa Hajja yanda Ameer ya koma bangarensu Mufeeda.
   Hajja da masifa tace to azukwi uwar munafunci me yasa kuke takurawa Ameeru ne,ina ruwanki Algunguma to nasan da zuwansa aikina yake ni na turashi,kinzo da guntun munafuncinki ai zai shigo ne zan fada masa me kika ce ya farfasa miki jiki,Haneefa ta fara bata hakuri daga fadar gaskiya sai a lullubeni da fada to daga yau bazan kara fada ba ko mene zai faru ya faru,Hajja ta dakko yar sandarta ta karfe tayi kan Haneefa da gudu ta fice ta bar Hajja na Masifa ta gaji da Gulmar Ameeru da akeyi a gidan nan.






AsmaBaffa
    Loves u all ❤😍
[1/20, 11:23 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

   KASUWANCI NA




           81-85





Official





By
AsmaBaffa




   

Page din yan TASKAR SURAYYARMS ne wannan ina jinjina.

   Gidiyata bazata irgu ba gareku Yan HOUSE OF HAUSA NOVELS
ASMABAFFA FANS CLUB
TASKAR FIRDAUSI SODANGI
UWARGIDA

Na gaisheku masu Sharhi a ci gaba.




        Hajja tana nan tayi gaho da baki tana sauraren Ameer yazo suyi maganar komawa wajen Malamai tunda yanzu taga ya shiga jikinmu sosai zai iya aikata komai,Abbi sai Haushin Hajja yake ji ta hanasu aikata nasu ita kuma ta kasa komai ta biyewa wani Ameer.

    Na dan Dade a tsaye ina tunanin me zance masa sai da na gaji nace gashi Yarima ya bamu,juyowa yayi yana daga kwancen,kudin na mika masa tare da bude masa ledar kayan zakin iri iri,a hankali yace ki basu kuje ya kyauta,To ka kirashi ka mishi godiya,Ba musu ya jawo faskekiyar wayarsa ya dannawa Yarima kira bugu biyu ya dauka suka fara suruntunsu na abokai naji Yarima yace to ya zamu shirya mata Plan din,Aayan yayi dariya tare da cewa ka bari sai mun hadu zanzo gobe ko jibi idan na samu time,ok anyway shaa cewar Yarima,Aayan yace dazu Ashe har wani wahala kayi na kudi da Sweets tnx, ban son Godiya Malam Good night I forget to tell u gobe Umma na zasu dawo tare da Abba, good to hear that sai nazo nayi missing girkin Umma tun muna London,Yarima yana dariyar Jin dadi yace ga matarka nan tafi ma Umma iyawa,Uhm gaskiya ne Night nan suka yi Sallama,ni kuwa na kuma jin ance ya plan dinmu a kanta nasan ma nice kawai na kara Jin haushi,Na kumbura kamar zan fashe da kuka,Kallo na yayi yaga yanda nayi a ransa yace to fa wannan na kasa gane meke kanta,ni kuwa Harda Haushin yace yayi missing girkin Babar Yarima wato nawa ni ba dadi bai dameshi ba har girkin wata yake tunawa yafi nawa ma wani haushi ya turnuke zuciyata naci gaba da tsaiwa a kansa rike da kudin tare da ledar kayan da Yarima ya bamu.

   Kallo na ya karayi yaga kamar zance na shiga uku na lalace na hada girar sama data kasa na cokalo lips gaba kadan nake jira kuma na tsaya masa a kai, light ya kashe ba tare da yace min komai ba nima ban motsa ba kamar me gadinsa haka nake tsaye gefen bed din, mun dauki lokaci a haka yaga dai ko matsawa naki yi nan ya kara kunna light haske ya mamaye dakin,inda nake haka nake, kallona ya sake kare min ni kuma tunani nakeyi ba a sona ni ban san tsakin da Naja ya fito fili ba,a fusace ya Mike tare da dirowa daga saman bed sai da na firgita,ban kara tsurewa ba sai da naga ya zaro wata wayar wuta doguwa ya nufo inda nake da gudu na watsar da kayan na fice da shegen gudun da rabon nayi irinsa tun ranar dana je guess house Hon Chairman neman tallafi.
   Dariya ma abin ya bashi dama gwadawa yayi yaga karshen rashin kunya, ban tsaya ba sai dai Su Meenat suka ji na banko musu kofa tare da fadawa Kansu,da gudu suka Mike daga baccinsu suka yi waje can Palo da gudu basuyi tunanin nice ba sabo da tunaninsu ai can nake kwana,Dariya suka bani na fito ina ce musu kai nice fa,Meenat ta manta ni yayarta ce sai da ta dura min ashar daga baya tace yi hakuri wlh na tsorata kin bani haushi muka dinga dariya Ma'eesha harda bige kafa da jikin Bed, ganinsu da kayan bacci nace ku koma Bedroom kar Aayan ya fito ya ganku a haka,Ko kunya kishinki yayi yawa cewar Ma'eesha,nace ae naji dai,suna shiga kafin na shiga suka banke kofarsu tare da Sa key wai sai daí na nemi wajen kwana.
    Ni kuma tsoro nakeji na kwana ni kadai ban saba ba,lallabawa nayi na koma dakin Aayan kamar munafuka ko wacce taje yin sata haka nake sanda kamar Soja ana kwanton yaki,a hankali na tura kofar dakin Allah ya taimakeni ya kashe light ya kwanta saman Bed Amma ba bacci yake ba tunani na yakeyi gaba daya ya kasa bacci yanzu na gama sangartashi tare muke bacci idan bana kusa matsala ce a gareshi kasa bacci yake.
    Lallabawa nayi yana tunaninsa baiji motsina ba har na hau saman Bed din gefe daya can na kwanta a hankali ina dauke numfashi na, nayi shuru kamar ansa wata na'ura me jawo ruhin mutum zuwa na dayan haka nakeji,gashi a kusa dani Na kasa sukuni burina na rungumeshi mu kwanta yanda muka saba,idan na taba shi kuma ina tsoro kar ya mike da fushi ya zaneni,Shi kuwa ya lula tunanina kamar yaje ya dakko ni,ji yake ma me yasa ya koreni gwara ai ina dakin ko banza ya dinga jin motsina.

    A hankali nake matsawa kamar ana jana ban san sanda zuciyata ta Gaza hakura ba,idan na matsa sau daya sai na huta dan kar yaji,ji yayi kamar abu na motsi a bayansa ya firgita shima,ya kara ji ana matsowa,Sandarewa yayi gaskiya aljanune suke shafar mutum a gidan nan,shima gashi sunzo masa,na kara zakudawa kamar tsutsa,a bin yaji yayi yawa kawai ya kunna Haske dal ya haske dakin,ni kuwa Sabo da tsoro har Hawaye ne ya zubo min nasan zanji jiki yau dukana zaiyi,waje daya na dunkule a saman Bed din,wani farin ciki ne ya mamaye masa zuciya Amma bai nuna ko Alama ba, ba tare da yace komai ba ya sauke ajiyar zuciya sannan ya kashe light again ya matsa can karshen Bed ya kwanta wai kar ma na taba masa jiki bayan yana so.
    Juye juye na farayi ina wash cikina wayyo,bai kulani ba har na gaji nace bani da lfy fa,ya min banza,nace da gaske nake fa,shuru nan ma,nace ba karya kasan bana karya fa,nan bai ce min komai ba,nace ita dai Duniya da ake ganinta ba matabbata bace,wa ya sani ma ko Bazan kai gobe ba,ko jibi ma ba lallai na rayu ba wa ya sani ma,yau in kaine gobe ba kaine ba,duk wannan abin watakila ma Baza mu kara yi ba a duniya,mene abin fushi da juna,ni ba cewa nayi sai an soni ba,ni bance ace ana sona ba,ai ba a so dole,maybe ma idan an fada din ba lallai ayi soyayyar ba mutuwa tazo ta riski mutum,ni dan anmin shuru ina ruwana bana gaba da mutum,kuma bana rike mutum a raina kamar zuciyar Fir'auna ni ba haka nake ba ana yi min abu nake mantawa na mai da komai ba komai ba Sabo da Duniya ai ba kanwata bace Meenat ko Ma'eesha bare ta daga min kafa,Ina maganata yana jina yana dariya a boye, muryarsa naji yace ina ruwana to sai me kuma,a raina nace iyye lallai ta tabbata baya so na na gama wannan tunatarwa ta mutuwa Amma ko a jikinsa nama mutu kenan,nace to in Allah ya yarda Bazan mutu ba sai naga Yayan jikokina da tattaba kunne idan an tsaneni a harbe ni,shuru ya min kamar bacci yakeyi,nace Hmm ba komai Watarana ana kallo a gidan nan zan shanye fiya fiya ko Blitch na wanke toilet,Yace ke kika huta da duniya mu ina ruwanmu, bakin ciki ya kamani nace Allah sai na ma yanke gashina,yace kinwa kanki ke zaki daina kyau ki koma Horror me ruwanmu,nace hmm za a gani ai dai ko Allah ya kaimu gobe,naji yace ga almakashi ma yanzu zan baki idan kina so, na rasa ma me zance nace to in ba tsoro ba ace na tafi gidanmu na bar gidan nan a gani,Dariya yake a ransa,muryarsa naji yace target nake hada miki first,nan take na tabbatarwa kaina maganar nan gaskiya ce ni ake hadawa plan shi da Yarima suna so suga bayana,ni kuma sonsa ya min yawa,ban sanda na fara kuka a hankali ba,Yaji da gaske Kukan kuwa nakeyi kuma da gaske ba na wasa bane wannan,Juyowa yayi ya kara juyawa tare da cewa Hawayenki ne zai kare ki koma na jini, ina shesheka nace da...dama...Hawaye na ka..rewa?Yace sosai ma sai Jini ya biyo baya.
   Da Sauri na goge hawayena na daina Kukan nace kar naje jinina ya fito,sai kuma Hawayen ya zubo na goge da Sauri ina ta gogewa yana zubowa na fara yaki tsayawa wayyo jinina na kara wani Kukan nace wlh yaki dainawa,yace shike nan anjima kadan sai Jini saukar min a Bed kar ki shafa min a Bed,na Tsorata da gaske,yace kai kamar ma jinin ne yanzu ai gashi nan ya fada yana kallon idona ina kukan Kar jinina ya fito ta ido,Ya zanyi ni na furta da muryar kuka,

yace badan halinki ba matso na hure miki yanzu Zai tsaya Hawayen kafin jini yazo,da Sauri na matsa jikinsa ya daurani a samansa sosai kamar shine katifar tawa,fuskata a saman tasa ya gwale min ido yana Hure min ido,ni kuma jina a jikinsa ban san ma hawayen ya tsaya ba tuni,sai nayi tunanin da gaske shine ya tsaida hawayen,yace to ya daina saukar min a jiki, nace kai dan Allah daga dan hawa, ki koma wajenki ko na rama nima,jin haka nace wayo zan ma a raina,na ki sauka kuwa sai ma kara gyara kwanciyata da nayi a kansa,shima wani dadi yakeji yana godewa Allah,amma sai ya nuna na takura masa sai na bar masa jiki,saman Bed ya maidani shi kuma ya haye min jiki kamar yanda nayi Amma bai sake min nauyinsa ba,tunani na nice na iya shanye nauyinsa,nace ashe ma baka da nauyi kalli yanda na iya daukanka, dan munafunci irin nasa sai yayi wani likimo yana ta faman mutsu mutsu a kaina yana jin dadinsa Amma wai sai yace a'a ni kin dameni sai mutsu mutsu kikeyi,nace Allah kaine kake motsawa,sai ya sa cinyarsa ko da hannunsa ta dabara ya girgiza min jiki sai yace ke mene haka wai baki da karfi sai wani sukur sukur kikeyi duk abinki sai na rama abinda kika min, nace wlh kaine kake motsi fa baka gani wai? Ba wani nan ni me zaisa na motsa, yasa hannu ta dabara ya zame min rigata kasa Amma sai ya dinga masifa ke abin naki har ya kai haka?to duk abinda zakiyi ko tsirara zakiyi Bazan hakura ba sai na rama, Allah kaine ka cire min ai ina jinka,nan ya dinga masifa wai ba shi bane nayi masa sharri ina ji ina gani sai shuru nayi masa,can naji ya bankaro min kirji tare da manneni a kirjinsa da Sauri nace ka gani ko gashi nan wlh Allah kaine nan kake matseni sai kace wani nice gashi na kamaka,dariya yakeyi a boye yace a'a kawai dai kice min kin lalace yanzu haka kuma kika koma yarinya dake Amma kina son dadi kema,nayi fushi tare da cewa yaushe nace ma ina so duk kabi ka makalkalemin jiki zaka ce nice,ki fadi gaskiya yarinya ya furta tare da cewa juya bayanki bana son yanda kike bankaro min kirji haka bari na karasa ramawa a bayanki Allah yasa naga kinmin wani abu kuma zaneki zanyi, Nan kuma ni har ga Allah dadin abinda yake min nakeji bana so ma a daina ko kadan,har haushinsa naji yace na juya baya a raina nace bari nima na kala masa sharri  kawai na masa wayo naji dadina.

   Na juya baya na tare da kifa cikina uban Hips da tudun mazaunai na kara yin sama dasu kamar zasu tashi sama🤣 Aayan dadi ya kamashi a ransa duk ya zauce ya birkice abin ya sha masa kai,Sai da yasa hannayensa ta kasan cikina ya rungumo dukiyar Fulanina,da Sauri na lumshe ido na Gaza gane a ina nake ma,maganar naji can sama kamar irin da nisa tsaka ninmu haka nake Jinta,yace me ya kawo wannan abubuwan hannuna kuma? Ko kulashi banyi ba lokacin maganarsa gida biyu nake Jinta,iri biyu take tashi a kunnena bana ganewa ni kamar na sha barasa shi kanshi gani nayi ya rabu gida wajen biyar ban san wanne Aayan na gaske ciki ba.

     Wasu irin abu yake min a bayana masu nauyi da Wuyar fassara mun gama fita daga hayyacinmu niko ban san sanda na zake ba na koma ina masa abubuwa masu nauyi mun manta inda muke ko wannenmu yana jiyar da dan uwansa dadi marar misaltuwa,mun rabu da kayan jikinmu kaf ba tare da mun sani ba,Aayan ya kai kololuwa yau yaji bazai iya jurewa ba ya kamata ace yau ya gwada babbar harka,a hankali da kyar ya iya magana cikin dishewar murya tana rawa yace Babyna ki yarda yau muyi pls mu gwada ko za a samu Baby mu Haifa,Haushi ya kamani wato dan a samu da ma za ayi badan yana so na ba,nan naji gaba daya na dawo hayyacina ban nuna naji Haushin maganarsa ba nasan halinsa da mugun zuciya sai nace a'a ni bana so yanzun nan kace nice nake takura ma ina taba ma jiki, yaushene zaki daina wannan kuruciyar taki?bakya ganewa wai? Ke fa Matata ce mene idan munyi ai abin jin dadi ne ma,ga lada kuma mu Haifi danmu,a raina nace wai bazai ce yana so na ba ni ban yarda da wannan ba kawai ya min ciki ya juya min baya,gwara yasan daraja ta tukun ni ban gama yarda dashi ba kuma naji me suke Plan a kaina Bazan yarda ba,da ace dai banji hirarsu ba to ko dan na faranta masa zan yarda ya gwada ko dan mu tantance lafiyarsa ta samu ko a'a, a fili nace a'a ni bana so daga auren Business ai kai kace banda wannan , dadin aure Bazan sani ba Amma yanzu kuma kace sai naji dadin ni bana so, cike da marairaicewa yace baki san Allah yana canja komai ba? Pls ki bari muyi,na makale kafadata kamar zanyi Kuka,so kike na mutu? Baki san yanda nake ji ba baki da Imani?Nace ae ni dama bani da Imani bani da tausayi haka nake ni haka Allah ya yoni, Ok to Hakkin auren fa? Kin san dai ba wani Kasuwanci a aure ko wasa a cikinsa da gaske akeyinsa Ki bari mu sauke wannan hakkin,ni dai a'a ban yarda ba,aure fa da kike gani ba haka kawai ake yinsa ba,Sai da Allah ya saka dokoki tare da ka'idoji sannan ya gindaya sharudai ba wai kawai abinda kaga dama zaka yi ba,dole abinda Allah yace shi za ayi ba wai ra'ayin mutum ake bi ba dokokin Allah ne,wanda yanzu musulmai abinda sukeyi kenan aure ba a yinsa yanda Allah yace tare da bin dokokin Allah sai kawai abinda naga dama shi zanyi,shima mijin abinda yaga dama zaiyi shi yasa auren baya karko,idan ma yayi karko sai kaga ma'auratan basa jin dadin auren sam Sai fada yau fari gobe baki,kullum cikin bacin rai,daga mutum yayi aure 1yr tayi yawa zaka ji ana Complain both Maza da matan,bakin cikin da suke sha yafi farin cikin yawa,me ya jawo wannan? Sabo da ba a bin abinda Allah yace,ba aiki da fadar Allah abinda kowa yaga dama yakeyi a gidan auren,ya kamata Alumma musulmai Maza da mata mu san me mukeyi a aure wlh ba haka kawai akeyi ba,sai da bin dokokin Allah  dake cikin tsarin aure Amma kowa sai ka rantse ma ba Allah ne ya tsara sharudai a Cikin aure ba yanda naga dama,ko yaga dama,ko taga dama shi mukeyi a daure a nemi sani sannan ayi aiki dashi sannan komai zai tafi dai dai.

     Haka Aayan ya dinga min nasiha da wa'azi akan me Allah ya tsara a zaman Aure,nasan gaskiya ne kuma nima na sani sannan ina da burin aikata komai Insha'allah Amma a wannan bangaren Bazan iya ba yanzu bayan ina kokonto akan Aayan ba wani so na yake ba,kuma haka ma zan yarda ba wani gyara etc nima wlh kamar yanda Amare masu gata sukeyi nima haka zanyi nan gaba da Izinin Allah,ba irin salon da bai billo min ba,tare da rokona har ma wa'azin naki yarda,nayi tunanin Zaiyi fushi ya daina kulani sai naji akasin haka yace sha zamanki na fita hakkinki Bazan miki dole ko na takura ki ba, Allah ya ganar dake gaskiya,Dariya nayi nace Ameen kayi hakuri dan Allah sai nan gaba,ba komai karki damu ci gaba da dariyarki yanzu na tabbatar da Imaninki kadan ne ashe da gaske ne?Dan Kar ma yayi tunanin zan ji tausayinsa na canja shawara sabo da kuruciya ban san a me zai kalleni ba da Sauri nace ai ni haka aka haifeni bani Da tausayi ko kadan,yace Allah?Nace Imani ko digo bani dashi ni ko me mutum zaiyi ba ruwana,ya gane dalilina na fadan haka Amma sai ya fuske yace uhmm lallai kice ke ko dan mutuncin nan babu,gani nake nifa na gama birgewa nace ko na digo banda shi ni ai kowa ya sanni ni akan mutunci ma ko a Unguwarmu ba a shedata,Aayan yace kin birgeni ai yafi hakan,ban san kawai biye min yayi ba yana ganina yarinya me kuruciya,  da yawa yanzu mata da Maza sunfi so a yabesu ba ta Kalma me dadi ba,basa ma so ace wance me hakuri ce,me mutunci,me hankali,ko wane Allah Sarki ba ruwansa da duniya etc, anfi so aji ana wance ai shegiya ce,wance bata ji ai bata da kunya,ko Wane Allah yayi shege anan,wane tsinanne ne, ai shegiya wance bata da mutunci tana birgeni,bata dagawa kowa kafa sai kaga a haka wai dadi ake ji har ana kara zakewa ana kara goga iya shege dan ayi suna a shedar banza, muyi kokari  mu samu shedar arziki ta kirki a ko ina muka shiga.

  Aayan a ransa shi yasan ba haka nake ba ina da Imani da tausayina sai yace to karasa ladanki karki gwada min halin wannan Lalatacciyar unguwar taku tunda baza ki bani Babban ba karasa min sauran yar Mufeen Ammah ,tausayinsa dama nake ta faman ji sosai sai da na zage na tsundumashi a nishadi tare da faranta masa yaji shi fes kuma inda yaji haushi yau ma ya kara Releasing a banza naki yarda ayi.

    A hankali ya rada min a ina kika iya abubuwa haka? Murmushi nayi tare da rufe ido na sabo da kunya,nace karantawa nakeyi a wani littafi Sai watarana zan fada ma,to Kunji Readers wani sirrin zamu ji inda Mufee ta iya abubuwa na birge me gida a Bed,Aayan kuwa kullum mamaki yake yanda akayi Mufeeda ta iya abubuwa haka wanda bashi ya koya mata ba,kuma bai nuna mata ba,gasu gingima gingima ba kowacce kwararriya ce ta iya irinsu ba,yanda kuma take iya sarrafa shi gata yarinya abin yana daure masa kai,yasan kuma matarsa bata san Namiji ba ko kiss a kansa ta sanshi,wasu ma suna da aure ko sun san Maza tun awaje Amma basu iya sarrafa namiji yadda yakamata ba,kuma ba updated bane su kullum abunda suka sani shike nan ba canji,ba a ci gaba da samo new zafafa ana juyawa me gida Brain,iya style dinki ya gama saninsa a daina bacci Hausawa a daina tsayawa ana ci baya kullum maimakon ayi gaba,a dage a nemi Ilmi akan komai,a san abubuwa wanda zaki garara a wajen megida,a daina kunya ana cutar kai, Aayan ya tabbatar Mufeeda ta gama dashi gani yake ma ko wata ya aura baza ta iya gigitashi haka ba,baza ta iya da shi ba sai Mufee yar yarinya me zukar Fura.
     Kara makalkaleni yayi yana shafa gashina har bacci ya kwashe mu me dadi da nauyi.

    Nina fara farkawa washe gari da Safe ban iya janye jikina a nasa ba sai a hankali na zauna kusa dashi ina karewa suffarsa hadaddiya kallo a raina ina Allah yayi baiwa a nan Bazan iya rabuwa da shi ba, wani sonsa ke kara ratsani ina kallon yanda jikinsa ke sheki,komai sumul lumi ban san sanda nace  a hankali Allah ya barmu tare ya sa maka sona kamar yanda nake sonka,sumarsa taci kudi me santsi da laushi na kalla tare da shafata a hankali na zare hannuna tare da jinjina kyai a raina nace Allah me baiwa.
    Ina zaune sai naga ya juya tare da shafo gefen da nake da Alama ni yake nema jin bana wajen ne yasa ya bude idonsa a hankali ya sauke su a kaina tar dasu,wani shock naji har raina da bargo na,Murmushi ya sakar min nima na maida masa tare da gyara rigata da na maida jikina,da hannu ya yafito ni wai na matso ba musu na matsa jikinsa, kissing din bakina ya fara,lokacin na tabbatar mun cika masu Tsabta wanda dole nayi respecting dinsa shima dole yayi respecting dina ta wajen tsafta a ko ina,sabo da sai mutum ya cika me Tsabta ta gasken gaske ne zai tashi daga baci kaji bakinsa bai canja ba babu wani wari ko wani canji,mata sai dai an dage mijinki yaji ko daga bacci kika tashi zai iya yin kissing dinki babu wani fargaba ko zai ji wani abu daban,zai kara girmamaki ya kara sonki yasan lallai kin hadu a Tsabta, a dinga shan abubuwa masu wanke dirty na ciki sannan Brush atleast sau biyu Safe dare,sai kuma ki siyi aswaki kina yi duk time din da kika ci wani abu ko haka kawai ma,Ana wanke Harshe da can ciki wajen makogwaro,Ana amfani da gawayi toothpaste tare da gishiri,ko toothpaste da lalle, Baking Powder da Lemon tsami sai toothpaste,kullum da Safe ki samu ruwa me zafi rau rau a hada da gishiri kina kuskure bakinki dashi, a tabbatar ana yawan cin Fruits,ko lemon tsami da zuma a zuba a ruwa me dan zafi ko dumi 1  cup kullum zai wanke miki dirty ciki ba ruwanki da wari ya fito daga cikinki,na baki kuma ga yanda zaki tsaftasheshi,a dage ana samun matsala ta nan mata.
   Shima idan bai sani ba bayayi a dinga ganar dashi cikin dabara,ki dinga bashi yana yi ta sigar dabara.

     Aayan yasan lallai yayi dacen mata me Tsabtar gaske ko ba turare a jikinki baza aji wani ordor a jikinki ba matukar kina tsafta yanda ya dace.
    Zamewa nayi daga jikinsa tare da cewa ko Brush banyi ba fa,to so what? Ya furta yana kallona kamar maye, Ni na fara shiga toilet Sabo da ya fini dadewa wajen wanka,wanka nayi tare da Brush na fito shi kuma ya shiga,mun kusa makara da Sauri na shirya tare da tayar da Sallah ina idarwa ya fito shima ya fara tasa,munyi azkhar sosai sannan na cire Hijab dina tare da busar da gashi na na gyara shi Neat na maida kayan bacci na,shima haka sai muka koma bacci.
     Ma'eesha ce ta shirya mana Breakfast,sai 11am na bar dakin Aayan na koma namu tare da sake sabon wanka na cakare cikin Shadda Dark Brown yar gaske dinkin zamani doguwar riga,Na kafe dauri kowa yasan na gama haduwa kamar Balarabiya,Meenat tana schl zana exam,Maeesha sai koda irin kyan danayi takeyi kamar wata Hajiya haka na fito na zauna a Dining ina jiran Aayan.
    Kamshi naji ya cika sashin ba tare da na juya ba nasan ma waye wani sanyin dadi naji a raina ban ma san Sanda na juya na kalleshi ba cikin 3qtr da riga yayi matukar bala'in kyan da ban ma sanshi dashi ba sai yau, Na kalleshi kamar nace kayi kyau sai na fasa kar ya rainani,Shima yana ta kallona da kyar kamar dole yace u look Good,tnx nace tare da fari da idona ina wani wanashi warrr,bai san sanda yayi dariya ba yace naga wannan,Na kara waresu na lumshesu,murmushi yayi tare da cewa wannan ma na karba, na kara juya idona suka kalli up and down,Nice One yace dariya nayi tare da rufe idona da tafin hannuna yace wannan ma ba laifi na kara kyalkyalewa da dariya tare da fara zuba masa abincin.

     Ameer ne gaban Hajja yana zaune tana tambayashi to Ameer yaushe zamu je ne wajen malaman karfa muyi sakaci,dan karta gane yace ah Hajja ai na gama shiga jikinsu ni dama Umarninki nake jira muje kawai Saturday ko Sunday ba matsala,Hajja tana ta murna tana yawwa yanzu naji magana bana kauna na bude ido naga yaran nan a gidan nan,wlh bana kaunarsu,babu wata mace dana tsana a duk matan da Aayan ya aura sama da wannan,nema take ma ta rusa min kan zuria ta,abinda na dade ina ginawa take nema ta rusa,Ameer yace gaskiya dai nima bakiga yanda nake jin haushin shiga part dinsu ba,ba a son raina ba,bana so ko kadan basu da kunya,Hajja tace ai babbar cikin itace duk shegiyar ita ke juya komai Mufeeda ba,Ameer yaji haushin zagin Mufee da Hajja tayi Amma ya danne sai yace a'a Hajja ai ta tsakiyar data karshe Meenat da Ma'eesha sune shegun,Hajja taja tsaki jibi wani suna na Aljanu malam,tun daga sunan ma kasan na aljanune wai Ma'eesha,Dariya Ameer yayi yace Hajja kenan ni na matsu ma muje a gama da yaran nan baki daya,Hajja tace Allah ya kaimu asabar sammako za muyi asubanci da wuri.
     Ranar Asabar da wuri Hajja ta shirya tsaf ta nufi wajen Ameer, ta fara buga masa kofa yasan itace kawai sai ya koma kalar me cuta ya kwanta kamar me cuta ya fara numfarfashi kamar zai mutu,Hajja taji shuru ba a bude ba nan take ta tura kofar da kanta,ai ta hango Ameer na murkususu da Sauri ta shiga tana lfy dan nan ina can ina shiri ashe kana cikin wahala me ya sameka?ta furta kamar zatayi Kuka tana girgiza shi,Da kyar Ameer yace Hajja.....ba...na...boye..miki...komai...aure...nake...so...ciwon...sha'awa ne...Ya motsa...Me yasa baka fada min ba tuntuni idan ka mutu ka barni ya zanyi tashi muje asibiti,Ameer yace Nasha magani Likita ya kawo dazu yanzu zai daina,Hajja tace ai ko dole ayi maka aure ko da Sajeeda ne,Ni wlh idan aka bani Sajeeda sai dai ciwon ya kasheni bari zanyi ya kashe ni Bazan iya yin komai da wannan ba,Hajja tace to kwantar da hankalinka sannu kaji,mu bar tafiyar sai wani satin idan Allah ya kaimu,Allah baka lfy kaji,Ameer a ransa murna yake yace Ameen yana jin dadi an fasa zuwa.






AsmaBaffa
[1/21, 11:08 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

   KASUWANCI NA





         86-90





Official









By
AsmaBaffa






    
     AGAS, MMN HUSNA,AMINA AMINU, Mom Ammar page dinku ne domin jin dadinku.






      Ameer yana ta rashin lafiyar karya sai Sunday yace ya warke da yamma ya feso uban Wanka sai part dinmu lokacin kawata Nawwara sarkin son jin Gulma da munafunci tazo min ziyara nasan badan Allah tazo ba,ganin kwakwaf tazo taje ta samu labarin fesawa,Kuma Alhmdllh taga gida iya gida,yau ta tabbatar da gaske gidan kudi nake aure ba abinda ban bata taci ba na jin dadi munyi mata babbar sauka, taci kwalliyarta ta masu rufin asiri tayi kyau kuwa ba karya, muna Hira a palo ta dameni sai ta gano Cikin Bedrooms nace to muje na rakata ko ina ta gani banda dakin Aayan,wai sai tace to dakin mijin naki fa ko duk yanda muke dake baza ki barni na gano kayan alatun ciki ba? Shuru nayi mata,tace kefa Amaryace gidan Amarya nazo gani kinga kuwa dole na ga ko ina,Nasan gulma ce kawai Allah kiyashemu mu abinda akeyi kenan yanzu.
    Murmushi nayi nace banda dakin mijina ko baya nan baza ki gani ba bare yanzu da bacci yake ma,ina laifi da na nuna miki sauran me kike so ki gani?

   Tabe baki tayi tare da cewa a hankali zamu shiga na kalla bazai tashi ba ta ya zai san mun shiga ma tunda bacci yake,Hmm Nawwara kenan ki hakura haka yafiye miki Bazan bari ki jawo ya tashi daga bacci ba,bai dade da farawa ba ma da kyar na samu ma ya kwanta Sabo da ya huta jiya bamu samu munyi bacci da wuri ba shine kuma zan bari a tasar min shi,ke a hankalinki ya dace ki shigarwa mace har dakin miji? Bada ni ba,Nawwara tace yaushe kika koma haka Mufeeda? Dariya nayi kawai na jata muka koma kasa nan muka hango Ameer ya shigo yana zaune,Ameer lfy kwana biyu kuwa? Murmushi yayi tare da cewa ai baku da kirki kunga shuru ko ku nemeni,Nawwara ta gaisa shi ya amsa tare da dauke kai can gefe,Nawwara sai gyara riga take tana kara bude mayafi tare da karairaya don kawai ta birge Ameer yace yana sonta itama ta shigo gidan kudi Amma ko kallo bata ishe shi ba, waye wannan fa?Nawwara ta tambaya, cousin din mijina,tace ok,muna haka sai ga Aayan yana sakkowa daga samansa yaci uban wankan Wani danyen yard  Fari kar yanda ya hadu ba a magana ma,wani kishi ya soke ni bana so Nawwara ta ganshi kar taji tana sonsa nasan duk wacce taga Aayan sai taso ace shine mijinta,Aayan kuma shima bana so ya ganta Sabo da tayi kwalliya harda jambaki kar ya kyasa shine nake kishi sosai.
 
     Nan take na bata rai kamar na boye Nawwara Amma ba hali,mikewa nayi da Sauri na Isa gabansa,Murmushi ya sakar min tare da cewa zanje wajen Daddy ne sai na fita wajen Yarima akwai wani abu da zamu tattauna a kai,Baki na turo gaba ina shagwaba ni...to wai me zaku tattauna? Kallo na kawai yayi ya share maganar yana kokarin wucewa,Nace dan Allah zamu je Saloon anjima,na aiki Drivers din gidan nan basa nan gaba daya kowa da inda na aikeshi, sai muje a Napep ko Ameer ya kaimu,a'a ke baza ki fita ba fa yace Direct,na marairaice pls kaji,ki ebi kudi ki bawa su Meenat Ameer ya kaisu Amma banda ke, ki wanke naki a gida mana, ina nuna kaina ni din?Yace kefa din,ya wuce zai fita bai ma kula ko da bakuwa ba har ina murna sai ji nayi Nawwar tayi shishigi tace Ina yini, lfy Alhmdllh ya furta da fara'a tare da tambayata frnd dinki ce? Nace ae tare muka taso a unguwa daya sunanta Nawwara,yace Ok thts Good Amma kina gani zan fita baki fada min ba,da Sauri na share zancen ina jin Haushi ana kalle min Aayan dina nace Zaka biya Office ne? Me zai kaini Office yanzu kuma,a dawo lfy Allah ya kaika ya dawo da kai lfy,yace Ameen kafin ya karasa na bude masa kofa kawai Sauri nake ya bar gidan Nawwara kar ta ganshi,yana fita na rufe kofar sannan na kalli Ameer nace Ameer Saurayi mijin yan mata,masu tashe da ji da kai,Allah ya hadaka da mata ta gari zukekiya Amma da ta sha kallon wanka da iyayi,Dariyar jin dadi Ameer yayi yau Ina yabonsa da kaina sai yace haba Aunty  ai mijikinki ya fini,nace daga shi sai kai kusan irin halinku daya,wlh ya fini dan mijinki ne ba kya ganin laifinsa,nace uhmm to me kake so na baka kaci yau? tuwon danyar shinkafa miyar Kubewa danya da kifi Amma sai dare,Nace ka gani ko na fada ma irin halayenku daya da Mijina,Nawwara tana zaune tayi shuru sai tunanin Aayan take ya gama Tafiya da zuciyarta gaskiya zata dage da zuwa wajena kullum ko Aayan zai so ta ya kara ta biyu da ita ta shigo itama ta kwace gidan,ko hannunka ya rike ai ka dace wannan,cin Amanar Mata bama kawai a aureshi ba kawai a shigo a kwace gidan,a kori uwar gida ko a wulakantata su kuma su zama sune a gaba.

    Ameer ka kai min su Meenat Saloon mana dan Allah,Ameer ya turo baki Amma Aunty kin san Meenat bata girmama ni ko dama Ma'eesha ce Amma wannan sai girman kai bana son kulata ni dai,kayi hakuri ka jira yanzu Meenat Zata dawo sai ku wuce Ma'eesha tana daki,kasan ina ji da kannena nafi so kullum na gansu sun hadu,Ameer yace ai ku dama Hadaddu ne Aunty,amma in kana da kyau ka kara da wanka.

   Muna hira har dai Meenat ta dawo tana cin abinci nace su shirya,dama sun dameni zasu je Saloon,kudi na basu Ameer yace haba Aunty ina wajen sai kin basu kudi ina da kudi,Meenat tace mu dai a bamu kudinmu Sis Sabo da tsaro, na basu kuwa,tana karba ta Radawa Ma'eesha kinga munyi cuwa cuwa mun samu na kashewa mu kara a schl,shi kuma ya biya mana na Saloon babu ko sisinmu,Ameer yaji Me Meenat take fadawa Ma'eesha.

    Ya kaisu hadadden wajen Saloon tare dashi suka shiga yaki fita wai sai yaga kalar gashinsu kamar na Maza ne ko dogo ne yanda zai musu dariya da kyau, Meenat ta zauna tare da warware gashinta Ameer ya dinga mamakin tsayinsa kamar na larabawa,haka Ma'eesha ma yace Allah ya taimakeku kuna da gashi yau da sai na dauki pics nayi status a social media,Meenat tayi dariya tare da cewa ta Allah ba taka ba to yaro,nine yaron Amma kin san na girmeki nesa ba kusa ba ma kuwa,Maeesha tace kaine ma Kwaja karewar girma nan suka fara dariyar Kwaja,yace zanje na dawo kafin a gama muku,Meenat tace a taho mana da me zafi tare da Me sanyi,fada kawai tayi sai ko gashi ana gama musu ya dawo,suna shiga mota suka ga Take away guda Wajen biyar wai duk nasu ne har Nima da nake gida,Gasassun Kifi da chips,sai Hanta lafiyayya taji hadi,ga su ice cream da yogourt.

    Suna shigowa lokacin Nawwara ta min Sallama ta tafi har kudi na ebo cikin na Aayan na bata Dubu biyar da kayan kwalliya iri iri ta dinga murna tana godiya,ni kuwa Zama nayi na fara tunanin irin kyautar da nayi mata kamar wacce tazo da asiri na bata kudi masu Uban yawa haka kuma wai harda kayan kwalliya ma.

    Su Meenat ne suka gyara min gidan ni kuma nayi girkin na shirya komai a Dining sannan na Shiga wanka ina tunanin Aayan yanzu suna can suna Hada min plan a raina nace duk kuyi Ku gama zaku San dani kuke zancen,yau ba Sallah nake ba shi yasa kwalliyar da nayi har da Nail paint nasa a farcena sky Blue nayi wani red wani Blue ba karamin kyau yayi min ba,nasa wando tight 3qtr me kyau baki,sai rigata Sky blue ta hadu gashina yasha gyara sai kyalli da kamshi nake ta ko ina ka rantse Balarabiya ce ni,na fito tare da Shiryawa Meenat Abincin Ameer a wani kwando me kyau nace ta kaiwa Ameer can part dinsu sabo da shi yace bazai dawo ba na bayar a kai masa abincin.
    Meenat ta karba ba musu ta fita me aiki ce ta nuna mata ta shiga part dinsu su uku Mazan Ameer,Khaleel tare Mujaheed gaishesu tayi sannan ta ajiye a gaban Ameer tace ya Ameer gashi inji Sis,Yace na gode,ita kuma ta juyo zata dawo,Khaleel Kansu ya daure sai mamakin Ameer su ke yanzu abin nasa har ya kai haka? Gaskiya zasu fadawa Abbi me yake shirin faruwa kuma fa dasu aka cinye abincin nawa.

     Sajeeda taga lokacin da Meenat ta shiga ta fito daga part din su Ameer shike nan ta dinga fesawa cewar Meenat bin maza takeyi abin har part din su Ameer,da sauri ta shiga sabo da kishi ta samu Ameer ai wlh Allah ya Toni asirinka dama abinda kakeyi kenan,to sai kowa yaji macuci yanzu har ajinka ya zube da zaka nemi wannan?ai gwara ko me kake so kazo wajena.
   Khaleel da Mujaheed suka Mike tare da basu waje,Ameer ko kallonta baiyi ba har ta gama masifarta,yace ai ta fiki daraja da mutunci a idona ta kuma fiki class,asararriya me rabawa mazan waje,ke kike haka shi yasa kike tunanin haka kowa yake irinki,Sajeeda ta rushe da kuka tare da ficewa da Sauri.

    Washe gari Sayyah kawata ce ta min waya zasu zo min ziyara tare da wasu kawayenmu yan Schl Mardiyya da Islaha,So nake Aayan ya bar gidan kafin suzo kar ma su ganshi wata ta soshi,5pm suka ce zasu zo ni kuma 4pm ina yin Sallah na bar kitchen na shiga wani Palo da nasan Aayan yana can sunyi wani meeting da abokan kasuwancinsa,Nasan ba kowa yanzu shi kadai ne,yana zaune ya baje yana cike wasu takaddun Office,Sallama nayi masa a hankali tare da Zama kusa dashi har muna gogar juna nace sannu da aiki,lemo ya kurba sannan yace Yawwa har kin gama aikin? A'a wai yau baza ka fita ba har yamma tayi? Tabe baki yayi tare da cewa no,nace yau fa Tuesday guda ai ya dace ace mutum yana aiki,Yau bazan iya fita bane shi yasa,Shuru nayi can na kara cewa gaskiya kana hutawa da yawa baka fiye fita ba jiya ma fa baka fita ba sai yamma liss,yau ma hakan take ai sai yamma zan fita,gashina na gyara na gaba nace yau muna tare kenan har dare? Bironsa ya ajiye sannan ya kalleni sosai yace korata kike?so kike na fita kenan anya kuwa kina da gaskiya tsakanin jiya da yau,jiya ma fa har murna kike na fita,a'a ni bance ka fita ba tambaya nayi na Mike zan bar palon ya riko min riga na koma na zauna amma sai nace aiki fa nakeyi kasan zanyi baki, je ki karasa aikin to,mikewa nayi na fita,har na rufe kofar na kara budewa a hankali tare da leko da kaina muka hada Ido na washe baki tare da cewa to ko zaka koma Bedroom dinka zan gyara nan? Wai wayo zan masa kar ya fito yace zaije samansa bakina su ganshi, ban san me kike nufi ba zo ki kwashi papers din sai na koma can din,Da murna nazo na kwaso masa ina bayansa yana cewa mutum da gidansa sai yanda akayi dashi ya zanyi,ina dariya har muka je Bedroom din na ajiye masa komai tare da cewa asha aiki lfy ranka ya Dade,murmushi ya saki yasan dana ce Ranka ya dade ko Yanlabai wayo na shirya masa wai zan masa.

    Sai da na gama shirya lafiyayyan girki kala Hudu ga kayan Sha iri iri ko ina na gyara sai kamshi ke tashi,wanka na fada na tsantsara kwalliyata cikin fitted gown black and Silver,gogorona Silver na daurashi dan dagwas,sarka da abun hannu duka silver color wow ga red jambaki na saki gashi yalala.
    Ina fesa turaruka naji sallamarsu suna knocking, fita nayi tare da bude musu su uku  Sayyah,Mardiyya da Islaha yar gidan Wata babbar lauya, idanu suka zuba min yanda suka ganni kamar wata Queen,nan suka hau yabon kyauna Sayyah tace shegiyar kin ganki kuwa muna ganinki a Uniform muna rudewa Ashe kinfi ma haka gaskiya mijinki yayi dace ya huta,Mardiyya tace zai kwashi harkoki,dariya mukayi gaba daya nace kufa baku da mutunci,Islaha sarkin jiji da kai,bata kawa sai da me kudi,nima ganin mijin da nake aure masu kudi ne yasa ta biyo su dan ta tabbatarwa idonta,ta kuma taba ganin Aayan a TV tana sonsa sosai shine yanzu ta samu hanyar da zata ganshi face to face ko zata dace ni ko ban sani ba.

     Zama mukayi a Palo suna kalle kalle duk sun Zama yan kauye suna kallon haduwa,Maeesha na kwalawa kira,yau sabo da na kara kankaro girmana bance Ma'eesha ba wai nima fa na Zama yar gayu sai da nayi zaman Hajiyoyi a kujera irin me ji da Hutu da Naira sannan na wani Kebe baki tare da cewa Angel...sai ga Ma'eesha ta fito da Headphone a kunnenta tana Jin waka cikin English wear riga da skert tayi kyau, da fara'a tare da ladabi ta gaishesu suka amsa Sayyah tace Ma'eesha ko,Marrdiyya tace gaskiya kuna da kyau Mufeeda,nace tnx Dear, Islaha kuwa sai wani cin magani take tana yanga sai danna waya take,tana kishi da bakin ciki.
   Angel kawo musu ruwa,Maeesha ta cika musu gabansu da kayan abinci dana Sha iri iri,nace to ya akayi Frnds Gist me mene News?
    Sayyah dama itace muke so close tace bari mu fara cin abincin Amarya muji ko kin iya,Nace ai kema kin sani yarinya,muna ta hira sosai banda Islaha,ko abincin taki ci sabo da bakin ciki,mu kuwa bamu San meke ranta ba ko ta kanta bamu bi ba.
   
    Kamar Aayan yasan yau kankaro girma na da mutunci na nakeyi gaban Frnds,lekowa yayi ta sama tare da dafa jikin Karfen steps din sannan yace Baby ina kika sa min Envelop din nan,bana so frnds su gane min shi,amma munafuka Islaha tana Jin murya tasan shine da sauri kamar wata engine haka ta daga kai kamar kadangare tana ta faman kallonsa,wani haushinta na naji kamar na koreta daga gidana, gani nayi zai sakko kasa kuma yasha wanka da alama fita zaiyi, nace bari nazo na dauko ma,ina yauki da kisisina muka hadu dashi a steps,su Sayyah kallo kawai suke Sha,a gabansa na tsaya ina murmushi kamar zan shige jikinsa na zura hannayena na rungumo bayansa amma bamu hada jiki ba,kyakyawar fuskata yake karewa kallo da idanunsa masu kyau,hannu na zare tare da saka hannuna cikin nasa nace muje ka gani,ba musu ya Bini tare da zame gannunsa,ina gaba yana bayana ya daura hannayensa biyu a waist dina sai kare musu kallo yake har muka shiga Bedroom.
    Islaha kasa kallon tayi sabo da bakin ciki,Sayyah da Mardiyya kuwa kunya suka ji lallai Ashe suna ganina yarinya ba ruwana da duniya Ashe haka nake sai kuskus sukeyi suna dariya,Islaha na zabga musu Harara.

     Muna shiga yace na fasa fita ni duk ya wani birkice min,nace dan Allah? da ka kyauta dama a raina bana so ya fita su ganshi,yace amma sai dai in zaki zo mu kwanta,baki nayi kaga ai bazan kwanta suna Palo ba ka bari sai dare,to bazan zauna ni daya ba bari na fita,ba yanda zanyi dole na barshi ya fita tunda ina da bako,kallona yakeyi kamar zai hadiyeni kinyi kyau shine sai da zaki baki kika yi wannan kwalliyar su kika yiwa? Wani idan ya shigo fa ko Ameer,dadi ne ya kamani ko dai ya fara kishina,nace ai kasan dai ina yi kullum iri iri sai wannan kadai zaka ce tafi kyau?, bafa nufina kinyi wani kyau can da yawa ba,kin danyi dai kyau kadan,addini kuma ai baice kiwa wani ya gani ba sai Muharrami ba nufina wani abu ba is just tht na tunatar dake addi ne.
    Murnata ta koma ciki haushi naji,kawai nace tnx na dakko masa Envelop da ya nema nayi waje abina ko saurararsa ban kara yi ba.
    Ina fita muka dora hirarmu sai gashi ya fito zai fita,Sayyah tace ina wuni? Sai lokacin ya gane da mutane a palon,Amsawa yayi kawai da fara'a ya kara gaba,zumbur muka ga Islaha ta Mike wai ita gida zata tafi,Sayyah tace amma kin San haka ne yasa kika ce Muzo ki kawo mu a motarki? Sai Ku hau Napep ni na gaji tafiya zanyi,Nace ki Bari Driver na zai kaiku ga motoci a gidan nan sai kun Zaba,gaba tayi tare da cewa sai mun hadu a schl.

     Sauri take ta cimma Aayan dan ta samu dama amma karaf sai suka ci karo da Ameer zai shigo part dinmu,karo sukayi da kai,dama tun asali kun San yan gidan basu da mutunci ko wanne bako ne babu me kulaka,yana dagowa yaga tayi ma gaba abinta,cikin zafin nama ya jawo rigarta baya tare da wanke ta da mari are u Mad zaki buga min wannan katon kan naki ki wuce baki da hankali,Hawaye ne ya zubo mata ba Marin ne ya dameta ba irin asarar da ya jawo mata bata ga Aayan ba sai fitar motocinsa taji.

     Kyaleshi tayi ta wuce shima ya kara gaba yana takaici,Tana yin gaba ta hadu da Su Haneefa,Sajeeda tare da sauran yan matan,Gefe su Khaleel ne ke buga game,Tazo wucewa Haneefa tazo daukan Ball dinsu sai ta sata a kafa ta saita kan Islaha ta buga mata da karfi sai ga Islaha Tim a kasa nan ta saki Kuka baki ya fashe,su Khaleel da sauran suka dauki shewa da dariya,Bata kula su ba a tsorace da gudu ta fada yar karamar motarta ta bar gidan a gigice dama gidan idan rashin kunyarka bata kai karshe ba to baza ka iya shiga ka fita lafiya ba.

   Bayan sallar Isha nasa Driver ya maida su tare da kudi ko wacce Dubu biyar kuma a kudin Aayan nake shiga kawai na ebo na basu tunda ni ba wasu kudi nake kashewa ba kuma ba baki nake ba yana dawowa nake fada masa na ebi kaza yace ba damuwa sabo da yasan ina da hankalina.
   Aayan baya fita ya dade a waje ko wanne time daga aiki sai gida ko masallaci,Hankalina ya tashi Meenat bata dawo ba tunda ta tafi schl zana Exam,Kuma 4 zuwa 5pm take dawowa Normally amma gashi har bayan Isha bata dawo ba yau.

   Ma'eesha tace Sis  Meenat fa ya zamuyi Innalillahi har yau bata dawo ba,hankalinmu ya tashi sosai har na fara kuka ma ni ganin har Aayan naji shigowar motocinsa amma Meenat shuru,Kuka nake sharba ko sace Meenat akayi wayyo,Aayan yana shigowa yaga muna kuka yace lfy? Nace Meenat bata dawo ba tun safe har baki na sun tafi gashi mun kira mutane da dama har schl mate wai sunce ta taho gida,ina zata tsaya dan Allah idan ba saceta akayi ba,Aayan yace zata dawo ne ai mene na kuka bari ki gani,Aayan ya dinga bige bige waya ba labarin Meenat,Kawarta Husna na kira nace dan Allah da kuka tashi ko kinga Meenat sanda ta hau Napep ko Taxi? Husna tace wlh wani me Napep muka gani Anty yayi parking a bakin schl da yawa student sunje zasu hau yaki daukan kowa amma Meenat ganin yamma nayi taje tace ko zai kaita gida ba musu yace tazo su tafi yanzu Anty bata dawo ba? Ina kuka nace bata dawo ba wlh Husna an sace Meenat.

   Shi kanshi Aayan jikinsa yayi Sanyi ya rasa me ma zaiyi,amma baya so ya nuna mana kar hankalinmu ya kara tashi sai ma lallashinmu da yakeyi,Muna haka sai ga Ameer ya shigo shima yace lfy? Nace Meenat Babu ta bata an saceta ina kuka na bashi labari,shuru yayi tare da Zama a kujera yace maybe wani tayiwa rashin kunya ya saceta,nace zata aikata gaba daya haka muke ba a taka mu muyi shuru sai mun rama bama daukan raini.

    Ameer yana ta tunani sai kuma ya Mike yace Zo muje Ma'eesha mu bincika wani waje muji,da sauri ta maka Hijab ta bishi tana Hawaye, mota suka shiga ya figa da sauri,suna tafiya ya kira wayar Sameera Yar daba bugu daya ta dauka tare da cewa Hello waye? Ameer yace Driver din Rabiu Rabson ne yace na nemeki akwai Deal,Sameera ta kyakyace da dariya tare da cewa shege Rabson Ashe yasan dama ina nemansa,zo Ku dauki karamar shegiyar nan gata an kawo min ita har gida wlh sai sun gane cewa ba a ja damu,Ameer ya kara kumbura Murya ta yan daba yace kadan daga aikinki ice ko akwai kudi karfa ki mana yawa,tace ai ko nawa ne zan kashe akan wannan yarinyar yanzu ma nasa a sauya mata kamanni.
    Ameer yace wanne gidan kuke yanzu?gidan karshen layin nan can dajin da ka sani na wajen gari nan Sameera ta gwada gidan,Nan take Ameer ya kashe waya ya kira wani cikin yaran Sameera ya kara tabbatar masa nan ne gidan,yan Sanda ya saita da komai suka nufi gidan.

    Suna zuwa yan Sanda na labe Ma'eesha ta cika da mamakin Ameer yanda yake abu kamar babban soja ko Dan sanda,gashi da basirar gano matsalar abu har ya iya yin tunanin Sameera ce zata iya aikata haka,zauna a mota Ameer yacewa Ma'eesha shi kuma ya shiga gidan,ta kan me gadi yan Sanda suka fara Damkewa sannan suka shiga,Sameera na Zaune ta hakimce a saman kujera ga kartin Maza sun zagaye Meenat,mutum daya a ciki ne yake dukan Meenat duk ya fasa mata jiki da katuwar bulalar wire ta Wutar Nepa.
    Meenat sai kuka takeyi Sameera tace sai ta bata hakuri ita kuma tace akan ta bata hakuri gwara a kasheta.
   Yan Sanda tare da Ameer ne suka fado dakin, Meenat tana ganin Ameer shi kadai ta sani ta Mike da gudu ta fada jikinsa tare da kankameshi, Ameer yana tsaye kikam ya kasa komai,yan Sanda suka kama su Sameera da yaranta gaba daya aka hankada keyarsu,Sameera ta kalli Ameer tare da cewa u r smart zan dawo kanka sai na fito.
   Ko kulata baiyi ba ya dauki Meenat kamar jaririya sabo da sun mata rauni da yawa zata bata masa lokaci, suna tafiya yace ki min shuru ni ko na jefar dake,Meenat da iya shege sai tayi Murmushi tana share hawaye ta kara wani kwantar da kanta a kirjinsa,yace anji jiki me laushi da kamshi dallah tashi da badan Anty Mufee ba bazan zo ba,a hankali tace Na dai gode yaron kirki,nine yaron naki? Shuru tayi,Maeesha tana mota ta hangosu ta danji haushi a ranta kishi tana son Ameer amma kuma ta tuna ai yar uwarta ce ko Ameer din take so ma zata barwa Meenat shi kuma ma ai ga jikinta da rauni taimako ne,
    Sai murna takeyi ta fita da gudu,Ya sa Meenat a bayan mota sannan yaja sai asibiti,ya hana a fada min ina ta faman Kuka na Aayan yana lallashi,Anyiwa Meenat abinda suka dace a asibiti sannan suka taho gida,sai ganinsu nayi gaba daya Meenat na dingisa kafa,murna wajena da Hamdala ba a magana,Gaba daya muka zauna a Palo,Maeesha ta bamu labarin komai sai godiya mukewa Ameer har Aayan,Aayan yace ya akayi ka gane Sameera ce? Ameer yace tunda muka je Birthday party naji furucinta nasan sai ta aikata,ina jin ba Meenat nayi tunanin itace sabo da sunyi fada a wurin party Aayan yace sunyi ma da Wannan marar jin ya furta yana dungure min keya.

    Na dinga tsinewa Sameera kuwa,Meenat tace to sarkin Mita yau kwana za ayi ba bacci kina nanata zancen nan,ai kuwa Ameer har ya tafi idan na tuno sai nace Ohhh ke duniya Allah dai ya tsinewa Sameera,Aayan yace addua zaki mata,bazan bata bakina ba nace,Meenat sun kwanta nima munyi shirin bacci ina kusa da Aayan yana zaune Saman Bed yana danna waya, nace Hmm Amma Sameera Allah ya wadaran Halinta,kallona yayi yamin shuru har ya gama abinda yake yace kwanta ki daina damuna da wata Sameera,nace Allah ai Sameerance yar Iska ta bani haushi na kwanta a jikinsa,munyi shuru har bacci ya fara tafiya dani na tuna nace Wai Sameera tana da iyaye,tsaki yaja ya juya min baya,juyowa ya sakeyi tare da rungumeni ya fara Romancing dina na zare hannunsa daga jikina tare da cewa kyaleni naji da jimamin abinda ya Dameni Sameera Allah ya kwaso jarabar duniya data lahira ya.....bakinsa baji cikin nawa,Na kwace baki na nace inba sai naci uban Sameera ba Allah ya....Ni ba Uban Sameera ba dai cewar Aayan,sai na tuna me yake nufi nayi shuru duk yanda yaso na bashi dama mu Sha murje murjenmu naki yarda ni jimami nakeyi,muryarsa naji cike da haushi yace Allah ya isa tsakanina da Sameera tazo kawai ta Rusa min Harka,Dariya nayi tare da cewa kaima ka dawo hanya ke nan? Yace yau kwana zanyi ina kwashewa Sameera Albarka ta cuceni.
    Zancen muka Dena amma ya hanani sakewa da tabe tabe ban san sanda na mika wuya ba muka Sha romancing dinmu cikin nishadi da jin dadi.

    Kwana biyar tsakani yaune kuma Hajja ta tasa keyar Ameer suka tafi karbo magani dole ba yanda zaiyi gudun kar ta gane ya bita sai da suka gama zagayensu dama duk ta sanar musu a waya an hada komai, duk wajen Malamin da suka je sai Ameer yace Malam to kuma me zamuyi wannan magani ya karye ko munyi aiki dashi bazai ci ba?ya dace mu sani gudun kar mu bata rawar mu da tsalle,Hajja har murna take Ameer me kaifin basira ne,bata San so yake duk ya karya maganin ya watsar dasu ba,bai so ya kona kar azo wani abu kuma ya samu Su Mufee,gwara komai da ilmi.

sai da suka huce gajiyar Hanya tace to Ameer gasu ka tafi dasu duk nayi ma bayani yanda zakayi amfani dasu,dana abinci,dana sawa a cikin pillow,kasan gado,da wanda zaka samu ka yafa mata a jiki ba tare da ta gane ba,Ameer yace an gama ya wuce da magunguna,cikin dare duka ya fito dasu wani Malamin yace ana musu fitsari sun karye,nan Ameer ya fada toilet ya tsula musu fitsari ,wasu Kuma akace idan aka kona etc duk yabi yayi musu yanda Malam yace in anyi baza suyi amfani ba sun karye, sannan ya juye komai a toilet yayi Flowshing gaba daya suka tafi.
    Kwana biyu tsakani ya samu Hajja yana murna yace aiki ya kammala na gama komai sai saurare,Hajja tace badai su kamaka ba ko?yace haba ai na girmi tunaninsu.

   Kusan kullum sai na je na gaisar da Daddy haka Su Meenat ma, yau ma na shiga Bedroom din Aayan domin mu kwanta na tadda suna waya da Yarima,Aayan yana dariya da gani a raina nace ta mugunta ce wannan, sai naji yace Saura kadan da kanta zata San inda ta nufa ai komai ya tabbata na gane ta gama fadawa sai kuma yanda zan tarwatsa komai,baki na bude a boye na kara danne kirjina sabo da tsorata da nayi ba Shakka ni suke nufi, wani kuka yazo min a raina nace sai an sakeni,yana gama wayar kamar me Aljanu na fada kansa Saman Bed ina kuka sosai na fara cizonsa da yakushi ina kuka nace sai an sakeni wlh bazan zauna ba,yana kokarin cireni a jikinsa ya kasa,Mari ya kwada min har biyu wanda yasa nan take na dawo haayyacina amma ban daina kukan ba,kallo na kawai yakeyi da mamaki bai San me ke damuna ba,shi yasan bai min komai ba,ni kuwa kukana nakeyi,ya kasa cewa komai duk nasa fatarsa tayi jajir inda na yakusa da cizo,jikina yayi Sanyi kuma naga ban kyauta ba,da alama na bata masa rai matuka Allah sarki ina son mijina ni dai Bana fata a sakeni bacin Raine kawai da zuciyar banza me kai mutum ta baro sai an aikata ayi dana sani marar amfani,Shesheka nakeyi naga ya Mike tare da cewa miko biro da takarda a fusace,Nan take jikina ya fara bari ina addua kar ya sakeni,a hankali na kalleshi shima ni yake kallo,nace Dan Allah karka sakeni kaji? Tsaki yaja yace kawo min nace ko,nace dan Allah ni dai dan Allah pls na fasa wlh kuskurene ina son Aurena,Yace ni ance miki mahaukacine ko yaro ne irinki da zakice nayi abu ba tunani nayi,dakko min biro nace ko ya daka min tsawa,jiki na bari nace gashi na dakko na mika masa kuma na rungumeshi tare da dabaibayeshi ta ko ina,a hankali nace in dai akan na yakushe ka ne kayi hakuri bari na biyaka fatarka,Toilet na nufa ya Bini da kallo kawai,ruwa me Zafi a bowl tare da dan towel karami fari na dakko,ban kulashi ba na cire masa riga tare da kwantar dashi tunda yana daga Zaune, yana kallon ikon Allah na gasa masa jiki,yace kin gama?nace ae,yace to kawo min takardar da biron a rude na fara ina ina da soshe soshe na kashe light duf na cire kayana duka na shige masa jikinsa gaba daya na sukurkutashi,yace ba abinda kike nufi zan rubuta ba fa abu zanyi Jotting na Office nace ni gobe kayi banda yau,Sai salo nake masa,yace fada min me yake damunki?idan baza ki fada ba kuma fitar min a room,cike da shagwaba na sanar masa komai da na naji suna fada,Dariya ya dinga yi tare da cewa amma ke anyi sakarai,kin jawo na mareki A banza, to a  kan Business muke magana wanda ya hadamu da wata take shirin damfarar mu wai zata mana wayo mu kuma mun fita wayon shine fa kawai,dariyar jin dadi nayi nace budurwa ce ko bazawara? Yace Bazawara ce mene? Hmm ba komai dan Allah tana da kyau? Yace ae mana sosai,baki na tabe jikina yayi Sanyi nace nifa?Ina da kyau? Dariya shima yayi sosai yace ae kina da shi mana,nace hm yaudara dai ko,am serious ya furta nace taya zaka ce tana da kyau nima kace ina dashi ai daya zaka dauka.
    Kina da kyau to,nan ma nace ban yarda ba na fara ja da baya zan Mike na bar room din,ya fisgoni na fado jikinsa yace banda Negative thinking Baby ya hade bakina da nasa yana min zafafan kisses idon na lumshe ina mayar masa da martani tare da bashi hakurin abinda na masa shima yace kin jawo na mareki am so sorry,kumatuna  na shafa cike da shagwaba nace amma na Maru wlh da zafi kayi min









AsmaBaffa
[1/24, 8:17 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

   KASUWANCI NA





           91-95





Official









By
AsmaBaffa





       

        HAFSAT KHAIRAN, NAFEESAT UMAR,CATTY,SUBYUSMAN10  jinjina gareku tare da gaisuwa me tarin yawa ina godiya da Sharhi.

     Page na HADIZA MUKTAR  yar albarka ina godiya.










    Dariya Aayan yayi kadan tare da cewa bakya jine sai kin Sa mutum ya zaneki kin jawo yanzu Bazan taba yafewa Hannuna ba, ba wani nan dama ka saba Marina tun farko ba Imani ka min Dukan tsiya kamar nayi accident da mota ko ina muka hadu sai ka Mareni bai ma dace ace na kulaka ba shine Sabo da banyi ma tunani ba na aureka, Murmushi yayi tare da cewa na daina to ko me zakiyi as from today  hannuna bazai taba jikinki da niyyar duka ba,sai da niyyar me to? Romancing,Caring etc ya furta wai dole bazai ce love ba shi, har yau ban gamsu ba ni nafi so a dinga cewa ana sona Amma sai na hakura nayi shuru.
    Na manta ban fada ma ba na bawa bakina kudi da kayan kwalliya cikin wanda ka siya mana sai an siyo min wasu na bayar da nawa Sababbin, nawa kika basu,nace hm nayi Barna fa ni kaina naji kyautar nan da nayi har tunani nakeyi ban kyauta ba kayi hakuri Dan Allah dubu goma na kwasar maka,murmushi yayi yace me yasa kika basu har goma bayan ke nasan baza ki iya kashewa kanki goman ba? Hmm kawai naje ne naga kudin naka sunyi yawa wlh gasu a jere a jere suka birgeni naji nima yau so nake na kankaro mutunci na, na zama Hajjaju kawai shine na irga na basu,amma fa a schl suna koya min abubuwa sosai kuma ko me nake so suna min musamman Sayyah,ina wannan rigunan baccin dana dinga sawa masu kyau har kala biyar ka tuna su? Yace ae na gane to Maman Sayyah ce ta bani su da naje gidan,shine na basu dubu biyar biyar ita da Mardiyya,Badan Allah kika basu ba ke nan? Dan ki kankaro mutuncinki kika ce,kin basu kuma kina jimami kina tunanin kyautar da kikayi bata dace ba dama baki basu ba,kinga ba lada kenan kuma Sabo da suna miki kema shine kika rama musu,ba haka ake kyauta ba,iya wacce kikayi niyya ita zakiyi kuma da zuciya daya kisa Iklassi dan Allah kawai ba wani tayi min bari na mata ko ki Bada ki koma kina tinanin kudinki dama baki bayar ba,kinga ba lada sai ma ko Zunubi,kuma 10k ma tayi kadan nayi tunanin ma sunfi haka,amma abinda bana so shine indai kaya ne ni na siya miki to bana so baki amfani dasu ba ki bayar wata tayi,ke na siyawa ke nake so kiyi kwalliya dasu Sabo da ina so naje na siyo da hannuna wasu ma baki san tsadarsu ba shi yasa,idan kina son kyauta to ki karbi kudi wajena kije kisiyo ki ajiye duk wacce zaki bawa ki bata a naki,wanda na siya miki sai in kinyi amfani dasu ko na canja miki new sai ki bayar da wanda kike amfani dasu, haka akeyi ba a daukan kayan miji da ya siyo ki masa kwalliya ko amfani baki dashi ki dauke ki bawa wasu in kina haka Bazan kara bari Frnds dinki su zo.
   Mata wasu don son gwaninta sai miji ya siyo miki kaya dan ki masa kwalliya ki birgeshi sai a dinga gayyato Frnds ana basu maza basa Jin dadin hakan.
 
     Sai kuma tambayata yaushe kika je gidan su Sayyah ban san zancenba baki fada min ba? Jikina yayi sanyi nace daga schl rannan mun tashi frnds da yawa suka ce ba nisa daga schl zuwa gidan su Sayyah zasu je gaida Mamanta shine nima na bisu muka tafi tare,su basu da aure ai?ae duk yan mata ne,ke kuma fa? Ina da aure mana, sai akace miki matsayinku daya yanzu? Zaman kanki kikeyi da zaki je wani wajen ban sani ba? Da kika dawo baki fada min ba mala'iku na tsine miki,shi yasa mazaje da yawa basa so matansu suyi aiki ko makaranta idan sun aure su sai a fake da wajen aiki ko schl ayi ta yawo mara amfani,wasu ma daga can suke samun hanyar bin malamai da bokaye ko tarbiyyarsu ta lalace yanzu badan Allah ya kawo zancen ba baza ki fada min ba kenan? Kuka na fara yi masa to kayi hakuri Bazan sake ba tunanina ba wani abu bane,Shi yasa har kasuwa na raka wasu ma daga schl,munje gidajen wasu ma siyo wasu abubuwan da yawa Ban fada ma ba kayi hakuri na daina,kishi ne ya kama Aayan harda kasuwa ma gidajen mutane Maza nata kallonki kamar budurwa? A rude nace ai ban kula su ba Allah duk da yawa sun tareni wai suna sona nace ina da aure,Aayan takaici ya kara rufeshi ana gane masa mata wasu sunji muryarta ma yace daga yau ko an koma schl kin daina zuwa tunda bakya jin magana ni bana son irin wannan, kuka na nakeyi nace ni me nayi to dan Allah? Kayi hakuri Bazan kara ba daga schl wlh sai gida, na yafe miki ai Amma karki sake ki san kina da aure bana son irin shirmen nan na student,kamar an matse bakikin ki gashi kinzo kin fada min ana miki fada ki fara wani kuka,

nace to yanzu duk abinda kaine ka siya min kar na bawa kowa? No ba haka nake nufi ba,sai kinmin kwalliya dashi sosai idan na canja miki wasu sai kwashe sauran ki bayar tht's what I mean, na gane Insha'allah ba matsala,dama kana son kwalliyar tawa ne? A'a kawai dai ke kiyi kyau,wani haushi ma naji kawai nayi shuru har bacci ya kwashemu.
    Sati biyu tsakani Meenat ta gama Exam tare da Ma'eesha suka shirya zasu tafi can kauyen Ammah wajen dangi za suyi sati daya daga can su Wuce Maiduguri nan dangin Abba za suyi sati daya, na hada musu goma ta arziki tare da Driver suka tafi abinsu,ni kuwa ina gida tare da Aayan,sai Ameer da yake dan shigowa idan yaga dama bai son yazo yaga muna tare da Aayan kunya yake ji,na tambayi Aayan ya bani kudi na fara zuwa gidan su Sayyah wajen Mum dinta gyaran jiki,haka take gyaran tana bani kayan tsumi,duk na kara cikowa skin dina sai sheki,santsi tare da kyalli ga uban laushi.

    Nawwara ta min waya zata zo min again nace bana gida munyi Tafiya bana so tazo,amma Sabo da naci yau Saturday ina kitchen Aayan ya ce na mishi Shawarma na gane yana son Kalar tawa,knocking naji sai da na leka ta yar kafa naga Nawwara ce,abin ya daure min kai to uban me tazo yi nace mata bana nan ana dole ne,komawa nayi kitchen naki budewa tayi ta danna Door Bell shuru.
   Khaleel yazo wucewa ta wajen ya ganta a tsaye tsawa ya buga mata wanda ta kusa sumewa uban me kike mana a gida kamar na ubanki anki bude miki ki tafi mana kin cika mana gida Nonsense,jiki na rawa Nawwara ta kama gabanta,Haneefa tana kallonta ta saman Bene tunaninta daga wajena take zata tafi shine taji Haushi an fara cika musu gida da baki,Sajeeda ma tana wajen suna kallo akwai ruwa a hannun Sajeeda roba guda ta dakko zata sha sai ta fasa sha ta saita kan Nawwara ji kake Gaf zafi ya ratsa Nawwara tunaninta Bom ne ya fashe ta kurma ihu ta fadi kasa tana Bom...Bom...ta mike da kyar tana faduwa tana tashi da Rarrafe ta Isa bakin gate,Haushi ya kama masu gadi ta ruda su tana Bom tsawa suka buga mata tare da turata waje suka jefar kamar wanki suka kulle kofa.
    Nawwara tana karasawa gida ta fada Toilet tare da barkewa da zawo ga gefen gashinta ya fashe.

    Na gama hada masa Shawarma na shirya komai a tire na wuce Bedroom dinsa zan kai masa na bude zan shiga kenan Naji  Aayan yana amsa gaisuwa da Alama da mace suke waya da Sauri na shiga Amma sai naji yaci gaba da wayarsa, kwana biyu kiyi Hakuri Ban kira naji ya kike zama a kasar ba,Da Sauri na zauna a gefensa tare da gwara kaina da nasa na jonesu waje daya wai so nake naji Muryar macen ko Budurwa ce Amma bana jin komai,Ya matsa nima na kara matsawa jikinsa,ya matsa na kara matsawa again,kasar akwai dadi yana Murmushi harda wani Ladabi yakeyi na musamman ina jinshi ya gama wayar sannan yace min Allah ya shuryeki nace Ameen ina turo baki idan wayar gaskiya ce a fadi sunan wacce ake waya da ita Mana aji,yace to yar Us ce Sarkin zargi, wa kake dashi a can me jin Hausa na furta nayi kicin kicin,ki bari zata zo Soon kasar nan zan kawo miki ita idan tazo sai ki fada mata haka in kin Isa, baki na turo tare da cewa ni mutunci gareni an cema Allah bata Isa ta zo nan gidan ba ko wace sai na balla yarinya,murmushi ya saki tare da cewa ai ni zan tare mata fadan,da kai zan hada ai sai na mayar mata da fuska ta koma baya,keyarta ta dawo itace fuskarta,Dariya yayi yace Allah ya kaimu dan baki san wace ba shi yasa, ki shirya min kayana zanyi tafiya,gaba na ya fadi rass nace ina zaka je?Us daga can zan wuce Saudiya,Hawaye na fara tare da turo baki cike da shagwaba nace yanzu ni kadai zaku bari? Amma kasan Tsoro nake ji ko ni kadai ban iya zama a gidan nan,Ga Ameer nan zai dinga zuwa yana tayaki Hira Amma da dare kuma sai dai ki kwana ke daya,Yarima na jirana tare za mu tafi zanyi 2-3wks, ganin kamar bai damu dani ba nima kawai na share shi nace a dawo lfy bari na hada ma kayan, zuciya ta a jagule gaskiya baya so na ya kasa sanar dani zai Tafiya sai yau da zai tafi kuma ko ajikinsa irin bai damu da rabuwa dani ba,Allah ya gani nayi kokari na da zan iya,da ace bana sonsa da tuni na fita daga harkarsa Amma zuciyata ta kasa hakura dashi na rasa me yake damuna gaba daya,shi kuwa shawarmarsa ma yake ta ci ko a jikinsa dama Already naga yayi shiri tare da hadewa cikin kana nan kaya.
  Harda goge yar kwallata ina hada masa kayansa na gama komai tsab yanda ya dace na ajiye a gabansa, yana cin abincinsa na dauki paper da Biro nayi dan dogon rubu a takardar me Santayana mutum zuciya amma fa ba na love ba,na adduar Tafiya sannan na Sa a tsakiyar kayansa ba tare da ya sani ba.

    Yana gama ci ya mike yana kara shiryawa ni kuma na sauka kasa ina palo a zaune saman kujera duk raina a bace yake kadan nake jira sai gashi ya sakko cikin shiri ya kalleni tare da zuwa gabana ya zauna a gefe na jikinmu na Gugan na juna a hankali yace zan tafi Baby, ban san sanda na zabga masa uwar harara ba nace Ina ruwana to ni na nasan da wata tafiyarka ne,Kallona yayi tare da cewa shirya mu tafi tare am serious wlh i wl be missing you is Better na tafi dake,Harara na kara watsa masa ae ai dole kace haka tunda zaka tabe min jiki to Bazan je ba,ba Us ba ko birnin Sin ne Ban zuwa,Har fa Germany? ban san sanda nace Allah yasa Agadaz zamu je hhh ya dinga dariya in bake shashasha ba kin taba ganin inda Agadaz tafi Germany zaki Hada Niger da Germany ne,ina turo baki nace to ko Birkinafaso ce ehe,Dariya yayi yace ke ana maganar Europe kina kawo África,nace to ko Egyft ce harda Morocco kai ko Algeria ce,nan ma yana ta dariya,yace to Saudiyya fa? Nace ko Qudus ce,dan Allah shirya a yau za miki komai mu wuce bana son bana ganinki kusa dani,uhm sai kayi kuma zancen kake so Karuwa taji me Wa'azi tace aiki ne bai isheka ba, Marairaice min yayi sai da nayi mamakinsa kamar wanda ke so na da yawa, wai sai kuma naji tausayinsa Amma na rantse Bazan bishi ba,nace ni Bazan je ba fa,wai harda jin haushina ya juya tare da fara Tafiya,nace Aayan... Juyowa yayi nace zo pls,tunaninsa zance zan bishi ya dawo nace nasan me kake so a jikina tattaba ka tafi abinka kaji,wani haushina yaji me nake nufi?au tunanina ma jikina yake so shi yasa yake taba ni etc Amma tunda haka nake tunanina zai nuna min,tsaki yaja ya juya abinsa,nace a dawo lfy Allah ya kiyaye Hanya ayi addua me yawa Sabo jirgi zaka shiga ba dabara ga wanda aka kwashewa kafafu kasan duk wanda aka kwashewa kafafu kana sama to dabara ta kare sai du'ai,dariyarsa ya danne kawai yayi gaba,Yana fita Ameer ya shigo nasa Katon Hijab dina,jefi jefi muke hira yana ta bani labarin yan matansu da suke yaudara muna dariya, gaskiya Anty gidan ba dadi Ba Maeesha da wannan yarinyar da na sani ma na bisu munje tare naga Kauyen,Bani Address na bisu Allah zanje,Ni kuwa ya ban mamaki kawai dai na bashi Address din, tun daga Lokacin Ameer yacewa Abbi da Hajja tare da yan gidan kaf wai ya tafi Abuja interview Zai nemi Visa a wani Embassy idan ya samu,Hajja tace bazai tafi a mota ba Amma yace a mota zai je,Nufinsa tunda Rimin Gado zai bi su Meenat sai ya kaisu a mota har Airport su shige jirgi sai Maiduguri gaba daya har da shi,Hajja ta damu ita bazai je har Abuja a mota ba sai a jirgi haka ya hakura Driver ya kaishi har Airport,Driver na Tafiya ya shige Napep har inda zai hau motar Rimin Gado ya shiga Drop fyalleliyar mota karama ya biya kudi shi kadai har Cikin kauyen Rimin Gado can rugar fulani.

    Da tambaya ya gane gidan da su Meenat suka sauka yan fulani sukace yan matan Larabawa yan birni ga gidan can,Ameer sai wani make jiki yake yana karkabe kayansa tare da tabe baki yana kyankyami wai,a kofar gidan ya tura yaro wai Meenat da Ma'eesha suzo inji Ameer dan Birni,Meenat ce ta fito kofar gidan tasha Atamfa riga da Zani me style tayi kyau,tasha mamaki ganin Ameer ne da gaske to ko lfy ko Mufee ce wani abu ya sameta Meenat ta tambaya da tsoro a fuskarta, kin wani tareni da tambaya zuwa nayi naga kauyenku to Anty ce ta bani Address bakwa gida duk ba dadi shine nazo,Murmushi Meenat tayi tare da cewa kayi Kokari bari na fadawa Inna to,
   Wajen Inna tsohuwa tazo ta sanar mata,Inna tace to kuma sai ki barshi a waje gidan tsohuwa ne kice ya shigo,Maeesha ce ta fita tana dariya tace lallai ya Ameer kayi Kokari ina motarka?ke zan mareki ko wacce sai tambayar tsiya,shugo to ciki,Ameer yabi Bayan Meenat suka shiga gidan,komai na kara ne dakuna Uku irin na ruga,Tsohuwar yayar Ammah ce ita kadai ce a gidan sai jikanta babba kuma ya tafi kiwo can wani daji sai shekara ta zagayo zai dawo gida tare da shanunsu.

    Gidan Babba ne me dan fadi tare da katuwar bishiya a tsakar gidan,yasha shara tsaf dashi,Ameer da Ladabi ya gaisar da Inna,da Fara'a ta Amsa sannan tace to ajiye kayan naka ga dakin da zaka zauna can,ke Meenatu kai masa kayansa,Meenat ta rakashi dakin tabarma ce katuwa sai katifa yar siririya dai dai mutum daya ko juyi sai daí ka mike sannan ka juya,Ameer ya dinga dariyar katifar tare da cewa sai kace ta jarirai wannan har katifa ce,ni Yanzu ya zan iya kwana a nan kato dani? Daki yasha tsafta dai ba laifi Amma katifar nan gaskiya kice ta canja min wata,Meenat da Sauri ta sa Hannu tare da toshe masa baki tare da cewa rufa mana asiri kunnenta kamar micijiji yake masifaffiya ce wlh ta gaske bar ganinta haka kunyi faran faran yanzu tayi mana tatas a gidan nan.

    Hannunta ya janye a saman bakinsa tare da cewa ke baki da kunya ni kamata zaki toshewa baki kamar yaronki kato dani,ni gaskiya ki fada mata ta canja min katifa,Ai ko karaf a kunnen Inna sai muryarta suka ji tace Iyyeeeeeee... Kai kake bani kudin?ko jikana yana gari ai bazai canja ma katifa ba,duk girman wannan makekiyar katifar yo ni Allah na tuba duk ranar dana kwana a saman ta kasa Sallar asuba nakeyi,har makara nakeyi sai rana ta fito nake tashi Sabo da laushi da girmanta,ba karamin daraja mutum nake Ba zan barshi ya kwanta saman wannan katifar tawa,ai wlh ko su Meenatu basu Isa ba,amma zaka nuna min kai dan birni ko kinibibinka ne? Murmushi Ameer yayi jin yanda take ta mita tana yabon katifar da take duk ta jeme  duk ta side tudun babu Sabo da taci duniya ta gaji gata siririya ta gaske,Ameer ya fito wajen Inna yace Inna ta dakina da nake bacci a birni sai tayi girman tsakar gidan nan gaba daya,kinga Bed dina kuwa like...Hannu Inna ta daga masa kaji shakiyin yaro yo ko Sarki ne ina zai samu katifa kamar girman tsakar gidan nan in ba karyarku ta yan boko ba,sai dai ka shiga gidan Radio a Sa zancenka a labarin nishadi na tatsuniya  Amma ba a wajena ba baza ka samu karbuwa ba

   Dariya Ameer yayi tare da cewa dan kawai baki sanni bane Inna kalli fatata fa kalli kyauna, me yasa kasan da haka baka Sako gadon naka a mota ka taho dashi ba karka dameni kaje kayi wanka ga abinci miyar harda Naman Zabo,Maeesha sai dariya suke har suka kai masa ruwan wanka bayi,yaga bayi ba rufi ba komai fayau ko murfin kofa babu gashi na kara da Ameer ya fito tare da cewa shi ya fasa wankan Tafiya gida zaiyi kar dare yayi masa bazai iya amfani da toilet dinsu ba,Toilet ce kadai zata koreshi daga kauyen,rokonsa sukayi yamma Liss yayi Manage zuwa gobe sai ya tafi,ya shiga haka ba yanda ya iya kayansa ma daya cire sai ta saman katangar ya mikawa Meenat ta rike masa su,

Ya mike yana wanka jikinsa duk kumfa wata yar fulani da kwaryar nono ta bayan gidan zata wuce sukayi ido hudu da ita ta kalleshi ya kalleta Amma iya kansa zuwa kirjinsa take iya hangowa ta wajen gidan,Ameer yaga taki dauke idonta ya ware mata hannu alamar zagi dakuwa yace karbi wannan kan Uwarki,bata gane ba ta tsaya tace me kace yace baki gane ba? Hakan nana yana ware mata yatsu wai yaren mutan kauyen ya mata na zagi Haka nanan,Tace ni yace a'a ubanki nake nufi baza ki bar nan ba sai na fito na fasa miki baki,Yar fulani tace yo ni ina ruwana da kai dan zanje tallana, ko tsirara na kalleka me zai firgitani,Kaga naga kalar ta Iro,Nasan ta Ja'e,har gaisawa na kanyi data Lawalli duk ranar kasuwa iya kaci kace ta wani fara ta wani ba to duk cikinsu ta Ja'e ce Baka wuluk me zaka bude min ido dashi ta ja tsaki tayi gaba,Ameer ya zaro ido waje tare da bude baki yana mamaki yace Ana iya shege a kauye ba kunya ba komai,ana cewa yan Fulani masu kunya etc ashe duk karyace, ya kwalawa Meenat kira ta bashi kayansa nan ma sai kanta ta sadda kasa sabo da kunya kar ta hango kirjinsa.
    a gaggauce ya karasa wankansa ya karbi kayansa ya fito,Abincin ma ba dadi kasa ci yayi yace shi wlh gobe zai tafi da Safe,Gari na wayewa ko karya wa yace bazai yi ba,dama tun jiya ya karbi number din me motar da ya kawoshi jiya yace ya dawo gobe da sassafe ya daukeshi,Me mota yaji yanda ya samu kudi da Sauri ya Amsa, ai kuwa 8am sai gashi yazo daukan Ameer back to Cikin Gari,Ameer da murna ya dauki jakarsa tare da basu kudi da yawa har Inna sai godiya take tana Sa masa albarka, ya musu Sallama Meenat da Ma'eesha har mota suka rakashi ya shiga yana musu gwalo ta Glass suna dariya sai gida.

     Yana dawowa Yace wai ya fasa Interview din ne shi yasa ya dawo ya bincika yaji bazai yuwu ba,Hajja sai murna take ya dawo lfy,  toilet ya fada ya dinga dirzar jikinsa ya dade sannan ya fito ya shirya sosai ya nufo Part dinmu.

    Ina kitchen ina Hada Chips na ganshi,Na dinga dariya naji abinda ya koroshi,nace ai kyaleka kawai nayi,Gaskiya Anty baku dace da Ruga ba ina sam kauyen baiyi ba,Abinci na zuba masa ya dinga ci Sabo da ya kwaso yunwa,yana ci yana bani labarin irin wahalar da yasha,Anty toilet ba rooping bare kofa ina Bazan iya ba, yasu Meenat fa? Ameer yace sunfi kyau acan,a kauyen zasu fi kyau Ameer? Ameer yace sosai Anty baki ga Meenat ba har wasu kumatu takeyi,Ina ta dariya nace to ko dai ita zan baka? Ameer yace wannan Masifaffiyar ai sai ta kashe ni ma gaba daya.

    Yau kwana biyar da tafiyar Aayan kenan da kyar nake bacci tunaninsa ya Addabi zuciyata,na ma rasa inda zan Sa kaina gaba daya duniyar bata min dadi kullum ni kadai gashi yace Bazan fita ko ina ba, sai gyaran jiki da nake zuwa, tunda ya tafi bai kirani a waya ba nima ban nemeshi ba Amma ko bacci bana iya yinsa sosai Sabo da tunaninsa, Shima can Aayan hakan take baya iya komai sai tunanina,Yarima ya gama gane Aayan so ne kawai ya kamashi,ya kasa nutsuwa,baya iya bacci,abinda ya kaisu ma ya kasa komai,har Zazzabi yakeyi cikin dare na rashina kusa dashi.

Ameer ne kadai yake debe min kewa idan yazo muyi hirar ya tafi,idan ina bukatar abu shi zan bawa kudi nace ya siyo min Amma bazai taba karbar kudin ba da kudinsa zai siyo min komai me tsada da kyau, kullum idan ya dawo daga Office sai ya shigo kuma bai taba nuna min ko sona yake ba,ko wani abu na banza bai taba shiga tsakaninmu ba,mutuntani yakeyi yana bani girma na yanda ya kamata,
Shi Ameer ma tuni ya tuba da son Matar wani tunda yaji wani Wa'azi me Zafi,yaga ina bai kyauta ba,nan take ya fara Istigifari ga Allah ya cire komai a ransa,kawai ganin mutunci na yake dana Aayan sosai,sai kannena yanda suka daukeshi kamar dan Uwansu.

    Idan ta kama watarana ko kitchen ya shiga idan yaga wanke wanke banyi ba sai ya tsaya ya wanke min ya gyara min kitchen sannan ya tafiyarsa,hakan yasa abinci sai kalar da yake so nake mishi ance ka kyautatawa me kyautata ma.yau da dare ina bacci wayata ta shiga Ruri ina ganin Number ce ta kasar waje naki dagawa nasan Aayan ne,kullum haka yake min har sai da muka kwashe kwana Uku kullum sai ya kirani yafi a irga Amma bana daga masa waya,har ya cika sati yana kirana kullum kuma bana dagawa.
    Muna haka dashi katsam da yamma nasha wanka na cikin doguwar riga Ready made ina palo gidan yasha gyara littafin Hausa nake karantawa a wayata ina ta dariya ni kadai ashe Bell nata kara banji ba sai gani nayi an turo kofar a hankali har ya shigo ban sani ba,sai kamshinsa naji kawai ya cika wajen,da Sauri na daga kaina sama da Sauri ido hudu muka yi ba karamin Kyau yayi ba cikin kana nan kayan ya hadu karshe, Sallamar na Amsa kwarjini yasa na kasa yi masa abinda nayi Niyya,wani dadi,Sanyi,farin ciki,sonsa ya kara shiga jikina gaba daya na wani diririce,nace sannu da zuwa ka dawo lfy?kai da kace 2 to 3 wks zakayi Amma yau Sati daya ka dawo lfy? Harara ya watsa min tare da zama gefena muna gogar juna yace Baki da kirki Mufeeda,bani wayarki ya furta tare da fisgewa yaga Number ta kasar waje da ya kirani da ita har Saving nayi da sunansa Amma naki dagawa,kallona yayi yace kin ma san nine kika ki dagawa saima Saving da kikayi kin kyauta.

   Kallonsa nayi nace kayi hakuri,kin hanani yin abinda ya kaini gashi dole na dawo me zaki fada min,Yaushe na hanaka? Yatsuna ya rike ya fara wasa dasu yana mirzasu ina ji har na fara jin wani canji a jikina,Gaba daya naji wani yarrr,shi kuwa har idonsa ya canja,ban san sanda na rungumeshi ba, mun dauki lokaci ya kankame ni a jikinsa sosai Nace ina zuwa na mike tare da nufar kitchen,

   Da kallo ya bini kamar zai hadiyeni Sabo da canjin da ya gani a jikina komai nawa kara canjawa nake na kara cikowa,ga kyau dana kara ina sheki,  lemukan dana hada na fruits na kawo masa tare da Dambum naman Kaza da nayi na ajiye a gabansa tare da zuba masa lemo a glass cup na bashi a nutse, yana kallona yana sha abinsa ni kuwa shuru na masa tare da dauke kaina har ya gama ya mike tare da da cewa bari nayi wanka naga bakiyi Missing dina ba,shuru nayi masa,yace sabo dake fa na dawo,a raina har ga Allah dadi nake ji marar adadi baya misaltuwa Amma a fili nayi masa banza sai ma turo Lips dana shiga yi.
    Mikewa yayi yana murmushi yaja akwatinsa yayi samansa tare da shiga wanka yana tunanin canja masa da nakeyi kwana biyu bayan bai min komai ba.

    Su Abbi da Hajja sun sawa Ameer ido a boye ba tare da kowa ya sani ba sun gano cewar karya kawai Ameer yakeyi ashe soyayya yakeyi da Kanwata Meenat,sun gama tabbatarwa ne lokacin da suka Sa CID daya ya dinga bin bayansa har lokacin da ya bisu Kauye ya dawo kuma,tare da Sauran bincikensu,nan take Hajja ta fusata me tsanani haka su Abbi ma,Abbi yace kyale shi zanyi maganinsu gaba daya Har Ameer din,Hajja tace Yaro ya maidani sakara lallai bai san wace ni ba idan na gano cewar mutum ya munafunce ni,wlh wlh nasan Malamaina basa karya Amma dan Iskan yaron nan nasan shine ya lalata komai,kuma ba shakka shi yasa yan fashi suka tare mu kwanaki tare da amshe maganin da muka karbo,Amma kyaleshi zai san ni yayiwa haka kuma sai ya auri Sajeeda.

    Abbi yace abu na farko da zamu ladabtar dashi shine mu kwace aikinsa da na bashi a Company na,da mota sannan muce ya bar mana gidan gaba daya,kuma nasan basa shiri da Aayan bare yace zai taimakeshi,Abbi Sani yace ai ko suna shiri da Aayan kasan shi Aayan bai shiga sabgar mu bare zuriarmu,sabo da haka bazai taimakeshi ba.
    Bayan sun gama shawara suka nemo Ameer ba mutunci suka masa tatas yana basu hakuri yana Abbi kai fa Mahaifina ne amma kamar baka so na? Abbi yace nafi son uwata da kai dan Iska ajiye min mukullin motar dana sai ma,amma ai da kudina na siya,Mari Hajja ta watsa masa a dalilin wa ka samu kudin aikin ai shi ya baka har ka siyi motar,Abbi yace na kwace aikin ma kuma ka bar gidan nan Banga Amfaninka ba baka bina baka bin uwata har ita zaka yaudara? Abbi bani da kamar ku fa bani da inda yafi nan ina kake so naje? Abbi yace part din nan kasan dai namu ne to kaje wajen ubanka Aayan ya baka inda yafi nan,Umman Ameer ma tana kuka tace kayiwa kanka wlh ba ruwana,kasan dai danginmu kaf talakawa ne baza su iya rike ka ba bare nace kaje can kai ka jawowa kanka kuma kasan Aayan bazai saurareka ba,Abbin America Baban Aayan kaine ka fara masa rashin kunya ko kulaka baya yi ka san da haka,kuma ka sani nan gaba zasu ce ka dawo gida kasan ba a ja dasu dole ka dawo kuma lokacin zasu daura ma aure da Sajeeda.

   Ameer takaici ya kamashi yasan dama ko dansu ne na cikinsu basu da imani idan ya musu laifi horo me tsanani suke masa, ya shiga part dinsu ya kwaso kayansa da dan yawa ya fito yana jan trolley dinsa idonsa Jajir ya fito lokacin zan shiga mota zanje Gidan gyaran jiki,tunda na hangoshi nasan ba lfy.

    Su Abbi duk sun leko ta saman Bene suna kallonsa yanda zai kare,Sai suka ga na fito da Sauri har wajen Ameer nace Kanina lfy?Ina zaka je haka? Murmushin karfin Hali ya kakalo tare da cewa Abuja Abbi ya aikeni,wlh ban yarda ba Ameer da gani ba lfy kuma nasan bazai wuce a kan kana shigowa part dinmu suka ce ka bar gidan ba nasan tsab zasu horeka ta haka baka ji maganarsu ba,shuru yayi min,nace haka ne ko? a hankali yace ae hakane Abbi ya kwace aikina da motata, to amma ai iya part dinsu zaka bari tunda gidan ba nasu bane su kadai ko?kai ya daga min gwanin tausayi,nace  muje ga Bedrooms da yawa a part dinmu sai ka Zaba ma fa ka dawo namu,Anty kina ganin ya Aayan zai yarda? Kuri na nayi nace ai sai abinda nace a gidan nan ka kaddara nawa ne ma,Dariya yayi kawai ya biyo ni su Abbi suna kallo ta sama baki bude.

    Muna shiga na bashi Bedroom daya me kyau a kasa Kusa da na su Meenat,yace ki fara fadawa Ya Aayan nace yana Office zan masa waya karka damu,Bari naje gidan gyaran jiki yanzu zan dawo akwai komai a kitchen idan kana so na fita abina na barshi ciki yana Hamdala ga Allah.

    Waya nayiwa Aayan na sanar masa komai yace ba Matsala alfarmarki ce Baby baki da damuwa komai kikayi nasan ba matsala I trust u,kuma nasan Ameer baya shirme irin na sauran na yarda dashi bazai yi abinda zai sabawa Shari'a ba da matata ko wata. murmushi nayi nace na gode.




AsmaBaffa
[1/27, 11:26 AM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

   KASUWANCI NA




          96-100




Official







AsmaBaffa






    
     MEENAL AMFAL and MMN ADNAN ths page is for u tnx

   MMN AMATULLAH Ina turo gaisuwa me tarin yawa.

REAL MAMAN WALEEDA jinjina da godiya Littafin yana Sweet yanda kika fara Lfy Allah ya baki ikon gamawa lfy tare da mu masu karatu,Allah ya kara Basira.

    Kuyi Hakuri Fans yan ASMABAFFA FANS CLUB ne suka ce sun bani hutu na kwana biyu weekend na huta ba laifi na bane su suka jawo muku,kuma ko yau suka ce na huta zan huta😅



      Na wuce gidan su Sayyah inda Mum dinta ke koya min yanda ake kula da miji etc sannan ta fara min Gyaran jiki ina shan na tsumi,sai wurin Magrib nayiwa Driver waya yazo daukana muka tafi gida Sayyah sai tsiya take min an kusa gamawa Aayan ya kwashi harka, ina dawowa na Iske Aayan da Ameer suna hira a palo kamar wa da kani na jini da Alama wata muhimmiyar magana sukeyi ta sirri, Ameer yace sannu da zuwa Anty nace yawwa ya hutu,Ya Aayan nace tare da daga masa hannu zan wuce Bedroom ya yafito ni da hannu ina karasawa ya miko ko min kumatu nasan me yake nufi cut nabashi kiss a kumatu na wuce, duk da cewa tunda yayi Tafiya ya dawo bama wani shiri dashi dan Romancing dinma da mukeyi ya daina taba jikina ko da wasa akan nace jikina yake so shine zai nuna min ba jiki na yake so ba,da dare da kyar muke iya bacci Sabo da mun saba idan mun kwanta muna yin abubuwa masu dadi tare da shiga rai,ina ta faman gyaran jiki Amma baya nuna min komai ko irin nayi kyau ko Ya rude a akaina abin yana kona min rai Amma ai ni na jawo.
    Wanka nayi tare da shiryawa cikin wasu arnayen kana nan kayan da ya kawo min daga tafiyar da yayi,nayi kyau na fitar asiri sai Hijab na Sa har kasa Sabo da Ameer,Kitchen na shiga na fara shirya mana abincin Dare kamshin girkina ya cika gidan.

    Ameer kuwa tuni Aayan ya bashi mota guda fyalleliya yana shiga su Abbi sai mamaki sukeyi,Daddy kusan kullum sai naje na gaisar da shi mun sha hira abinmu in ta bashi labarin mu,Sameera yar daba dukansu tare da yaranta an yanke musu hukuncin a gidan kaso na watanni 8 Sabo da Sameera me kudi ce ta basu cin hanci maimakon na shekaru sai na watanni kuma a hakan ma sunce baza suyi 8 mnths ba wata daya ma za a sakesu Sabo cin hancin da ta basu,kasar nan ba gaskiya a cikinta, Aayan kaji wai 8mnths kacal za suyi nace masa ina tura baki,yace Hmm bana son halaka ne da sai na Bada kudin wanda yafi nata a barta a ciki to Allah ya hana cin hanci da me karba da me bayarwa akwai ranar da Allah zaiyi maganinta gaba daya,Amma in kina so a bayar hakan to? Nace ae a bayar kawai dan ubanta ai akan gaskiya ne,a Bada kudin a tabbatar musu da hukunci me tsanani,Kanwata guda da aka bar min Amana nice kamar Uwarsu fa ai wlh Bazan yarda ba da Ammah na da rai kake jin zata yi alfahari dani Na karasa ina zare masa idanu kamar shine Sameeran,Dariya yayi yace to ke mene tunda Allah yasa ta fito lfy? Bazan yarda ba sam kamar kudin ubana haka nake fada Bazan yarda ba dole na tsaya a tabbatar da gaskiya a sharia ka bani kudin Kasuwanci na sai na biya dashi a tabbatar da anci uban Sameera a gidan kaso,yace za a baki tsigai,nace ae a bani kuma dole muje da kai ka wuce gaba ayi komai da kai,yace an gama Uwata, da kansa yaje ya kashe case din ya biya kudi masu mugun yawa aka canjawa su Sameera shekaru Har uku ba tare da nasan anyi ba,sai da ya dawo ya sanar min,nace kash Uku kacal? Laifin Kidnapping tare da niyyar kisan rai? Uku fa ai wlh ba a ci uban Sameera ba sam baza ta koyi darasi ba,sai kace kasar turai da suke da Imani,a Nigeria muke fa inda ba Imani ba a dauki dan Adam da daraja ba,Dariya ya dinga yi to so kike a kasheta wai ko ba a kashe ta ba nafi so ta tsufa a prison,sai gashinta yayi fari tass lokacin na kusa aurar da yan biyun da zan Haifa nan gaba yan mata,Aayan ya bude baki dama har yan biyu kike so ki Haifa?Nace ae Insha'allah su dinga min girki kullum,Aayan yace sai ki dage ki haifo su ai,Wai Ya Aayan ta ina ake Haihuwa kuwa? Yace ta cibi zaki ga ta bude kawai jariri ya fado,dariya nayi nace ba wahala ashe ma.yana ta min dariya yana tunani Allah yasa ya warke ya yi maganin gaba daya.

   Bayan na gama girkin daren nawa Ameer yau bai dawo da wuri ba daga ni sai Aayan muka ci,.  8pm nayi shirin bacci da komai a dakinsa shi kuma naga yana ta cin kwalliya kamar ranar daurin aurensa sai fesa turaruka yake faman yi,nace ina zaka je? Yace wajen yarinyar nan ta Us ce tazo kuma a Hotel ta sauka ba dadi Budurwa kamarta ta zauna a Hotel ai ba mutunci ko kawai zanje dakko ta ne ta zauna damu kafin ta koma.

   Kamar ana zuba min ruwan zafi haka naji a zuciyata,ji nayi kamar zanyi hauka gaba daya hankalina baya jikina Sabo da tsananin kishi,nace idan an Isa Allah ya dau raina yau ba sai gobe ba, nace Wayyo Jama'a ga Kwarto,Ameer ya dawo yana kasa yana juyowa ina ta ihun Kwarto a sama,shi dai yasan Aayan yana gida Amma yace bari ya gani kar ko wani ne daban da Sauri ya karaso Saman yace Anty Mufeeda lfy waye,Aayan ne ya fito cikin shirinsa yace kyaleta jeka kuruciyarta ce ta motsa,Ameer yana dariya yace Ya Aayan kaine kenan Kwarton Aayan yace ae fa gani,Ameer ya juya yayi tafiyarsa yana dariya a ransa yace Mufeeda itama irin yan fulanin garinsu ce kenan,Ni dai ko a jikina na fara kuka yana daukan Agogo zai fita na dakko Jambaki da Sauri na bude shi na dinga shafa masa a rigar ta ko ina na jefar da jambakin na kama rigar na dirje lips dina da ita kalar pink jambaki ga wancen Red,yace kinyi ta banzan dole zanje ya bude kofa kenan na jawo rigarsa ta baya,ina ta uban nishi ina Hawaye,hakan baza ta kaini ba na tsuguna na kwaso kafafunsa Amma ko motsi baiyi ba,sai ya biye min ya tsaya don yaga me zanyi masa tunda Hannunsa nake ta ja da karfi,sai ya biyoni tunanina ni nake jansa ta karfi ina nishi na jawoshi har Jikin Bed,ya tsaya kuwa,nace kwanta to dan Allah kaji ina ta kukana,yaki kwanciya na kara mikewa na danna shi kan Bed ta karfi,nan ma gani nake ai karfi nane ya kwanta sharab,yana kokarin mikewa na fada kansa na kwanta daf daf tare da rufa mana bargo tare nace ka dubi girman Allah ka kwanta,Sabo da me? Aljanune suka ce kar na barka ka fita kana fita zaka samu matsala,a lokacin kuma da Aayan yake son fita lokacin Abbi ya barbada masa Wani garin magani a kofar fita wajen part dinmu suna jira ya taka wajen,mu harga Allah bamu san da wannan ba kishi na ne yasa na hanashi fita.

   Sai da Abbi Sani ya Kira Aayan a waya wai ya fita yanzu ga abokan Daddy nan sunzo duba Daddy daga Abuja kuma karya yake burinsu kawai suga Aayan ya taka maganin kafin gari ya waye,idan har gari ya waye to ya karye maganin ko an taka bazai yi ba,shine suka rasa yanda zasuyi ya fito suka hada abin da Wai Bakin Daddy sun san yanda yake kaunar Daddy dinsa.

     Ta inda Allah ya tsare Aayan sai a ransa yace bari ya tsokaneni yaji shine yace ai wajen wata zaije,ni kuma uwar kishi shine sai da nasan yanda zanyi na hana fitar ta dole,a hankali na kai bakina zan masa kiss yace karki taba ni,why? Kince Sabo da jikinki nake taba ki so na daina taba ki,to Sabo da me kake tabani? Fadi gaskiya naji?  Murmushi ya saki sannan yace Do not judge a person by their looks or the things they have. You do not love some one for their appearance or their nice cloths but because of their personality, their thoughts etc u have to Understand kinji?
   Shuru nayi ina jin dadi yaci gaba Sometimes people don’t tell you how they truly feel about you but they will always show you so pay attention ki gane ba sai ance kullum ana sonki ba kamar yarinya ku yan mata haka kuke.

Baki na turo tare da cewa ni dai duk da yanzu ina jin turanci kayi min da Hausa yafi shigata sosai kai turancinka na turawa kakeyi duk a harde, murmushi yayi yace Ok ku mata sai kuyi shekara yafi goma tare da mutum yana ta nuna muku yana sonku Amma wai in dai bai ce i love u ba to kawai ba sonku yake ba,wani ma sai ayi ta cewa ai kawana ne,kuma in ka sake kana gani zata auri wani ta barka,sai kace daga baya ina sonki tace me yasa baka fada min da wuri ba bayan duk abubuwan da ka nuna mata na zallar so ne.

   Murmushi nayi nace uhm munfi so muji gar da gar, kumatuna yaja da dan karfi sai da nayi kara sannan yace I LOVE YOU......I DO REALLY LOVE YOU,I NEED U,I LOVE EVERYTHING ABT U,U ARE MY SOULMATE BABYNA ya karasa furtawa tare da hade bakinmu waje daya yana sha,Dadin da nake ji ya wuce a fade shi,nan take na kara kankameshi,naji yana nema ya zarce nace bari nayi fitsari,a hankali ya sakeni na shiga toilet,na kulle tare da jingina da jikin kofar ina sauke numfashi da ajiyar zuciya bakina yaki rufuwa Sabo da murna,dama Sabo da kar ya gano ni yasa na gudo toilet Sabo da nayi murnata ni kadai,harda tsalle da murna ina yarfe hannun dadi,sai da na dade ina murna sannan na hade rai na fito daga toilet irin ko a jikina bana murna, gefensa na kwanta ya kalleni tare da saka hannunsa cikin nawa Baki ce komai ba Baby, akan me fa na furta ina yanga,do u love me too? Yatsina fuska nayi tare da cewa sai nayi tunani na duba naga ko ka dace,Murmushi kawai yayi tare lumshe ido ya jawo ni jikinsa Amma Sabo da iya shege sai na ja baya kadan tare da kwace jikina.

     Shima bai takura min ba ya kyaleni kawai tare da daukan wayarsa dake uban ruri sunan Abbi ne a jiki,sai yanzu ya tuna Abbi ke neman Sa yaje tarbo Bakin Daddy,amma abin mamaki baki daga Abuja su rasa lokacin zuwa sai dare kawai dai yace gani nan yanzu su jirani,Abbi yana ta masifa ka wulakanta mutane Sabo da kai ga me kudi ko to kayi gaggawar fitowa,burinsu ya fito ya taka maganinsu,Ni kawai ban yarda da fitarsa ba kishi nake ko wayo zai min macece da yace daga U.S take,nan take na fashe da kuka ganin ya mike da gaske fita zaiyi, a hankali yace mene ne? Ni..Allah ba inda zaka fita,Indai ka fita Bazan kara tayaka kwana ba kawai baka so na,mirmushinsa me tsada yayi tare da cewa kina jin yanda Abbi ke fada bakin Daddy suna jira na kiyi hakuri naje naga ko su waye mana,Yanzu wasu bakin kirki ne da Dare haka ni Dai Allah baza kaje ba na sani ko wajen budurwarka zaka je.

    Hakura yayi kawai da fita Sabo da yaga da gaske tunanina yana da budurwa gudun Zargi sai yace Ok na fasa to,murna na fara yi tare da kashe wayoyinsa gaba daya na ajiye gefe,shi kuma yana zaune gefen Bed na zagayo ta bayansa tare da Zura hannayena ta cikinsa na rungumeshi gaba daya a jikina,bai san sanda ya lumshe ido ba jin yanda Albarkatun kirjina suka sauka a bayansa,Kasa jurewa yayi ya juyo tare da matsane a kirjinsa gaba daya kamar zai fasa min Kashi, gaba daya ya tafi dani ban san sanda na biye masa ba alhalin nace na daina yarda yana taba min jiki yanzu sai na bashi wahala Amma sai gashi na kasa jurewa,har mamakin kaina nakeyi yanda nake da Feeling me karfi kan Aayan bana jurewa.
   Da Zafi zafi muke Sarrafa juna kowa na nuna kwarewarsa Har Aayan ya dauki Hanyar Cinma burinsa Amma sai kawai sha'awarsa ta tsaya cak ya gagara komai,ni kuwa dama gyaran jikin da nayi nace shike nan na hakura ya samu abinda yake so Sabo da son kudi na bana so nayi asarar kudin gyaran jikina gwara ko mutuwa zanyi kawai ya Mori kudinsa tunda dama danshi nayi gyaran idan ba ayi ba ai na rafka asara tare da bata lokacina.

     Kallonsa nayi da tausayi sosai Sabo da yana da sha'awar abin Amma kuma bazai iya ba wannan Masifa ce,sai dai yayi ta shan wahala,shuru kawai naga yayi ya fada dogon tunani,Nace Man ya akayi ne? Har yau baka warke ba ko? Kai kawai ya daga min,da kyar yace min am so sorry na kasa baki hakkinki shi yasa bana son auren nan,amma kiyi hakuri idan kinga da matsala ko zaki shiga wani Hali tunda ban san ranar warkewa ta ba ki fada min duk da ina sonki nasan da kyar idan zan rayu babu ke zan iya hakura, Hawayen tausayinsa ne ya ziraro min nan take nayi Sauri na rufe masa baki nace karka kara ambata in Bazan iya ba zamu iya rabuwa ka daina ba kai ka daurawa kanka ba Allah ne kuma watarana zaka warke,kayi hakuri itace Kaddararmu ba shi nake so a tare da kai ba wlh ko shekara nawa zakayi a duniya zan iya hakura mu zauna tare,Allah idan har kaji ni Mufeeda nace ka sawwake min ko mu rabu ko zan bar gidan nan abu na farko da zaka min kawai ka kaini gidan malamai masu Rukiyya kawai ba kalau nake Ba ko Aljanu sun shafe ni ko an min asiri kaji na rantse.
   Ka daina damuwa ko kasawa kanka tunani, na gode Baby Na gode yake ta maimaitawa I love u so much My wife,yanzu in naji kince mu rabu ko zaki barni na...da Sauri na karasa ka kaini Ruqiyya wajen Malamai kawai asiri aka yi mana,Dariya yayi kadan tare da kara kankameni a jikinsa.

      Can kuwa su Abbi suna ta faman kiran Aayan a kashe ma wayar,Abbi yace iyyeeeeeee ehhh lallai yaron nan fa ya fara tsallake iyaka dan muna daga kafa ne kawai idan mukayi sake muna jiran Hajja to lokaci zai kure mana,da gani yar iskar matarsa ce ta hanashi fitowa wlh bazai wuce ita bace,Abbi Sani yace dama naga Alama yanzu sai abinda tace Gwara mu fara maganin shegiya,akwai Maganinta Hanifa ko Sajeeda zan bawa aikin su zuba mata a abinci inda da kanta zata bar gidan a nemeta a rasa taje can tayi ta garari a duniya.
   Abbi yayi dariya sannan yace ai har kannenta kar a bari su dawo tunda sun tafi dangin ubansu to su zauna can ko su Bita ita Mufeedan su karata can,da banyi niyyar kulata ba Amma yau ta shiga gonarmu,Washe gari da Safe Saturday Ameer yana Bedroom muma haka na hada mana break na shirya a Dining na koma ina taya Aayan shiryawa Sajeeda ta samu yanda zatayi ta bude kofar ta shigo a hankali tare da kallon gefe da gefe ta tabbatar ba kowa a wajen sannan da Sauri ta karasa saman Dining ta bude duk kalolin abincin dana shirya ko wanne ta barbada garin maganin sannan ta rufe a hankali ta juya zata tafi duf Numfashinta ya dauke na wasu dakiku sakamakon ganin Ameer da tayi tsaye a bayanta ya harde hannaye a kirjinsa,yana mata wani wulakantaccen kallo.

      Nan take jikinta ya fara mazari, ba zato taji mahaukacin Mari ta ko ina,zafi ya hada ta kamar an dosana mata wuta a fuska,Fisgo wata waya yayi ya fara tafkarta yana Ball da ita,tun tana neman agaji har ta garara,ni kuwa munji kamar hayaniya amma hankalinmu bai kawo ba,Ameer ne ya samu Kwalaba ya fasa tayi cako cako ya jawo Sajeeda kiiii har palo ya zauna saman Kujera,Fuskarta ya rike da karfi tare da dagata,tana kuka tana bashi hakuri tasan Ameer bashi da Imani zai iya yankar jikinta da Kwalaba,kamar me aski ya fara karta mata Kwalaba tun daga goshi jini na tsatsafowa,Sai yanzu muka fito nan muka hango irin muguntar da Ameer ke aikatawa,Aayan ne yayi magana da karfi Ameer me ya faru wannan wanne irin rashin Imani ne?

    Gashin Sajeeda ya fisga da karfi tare da cewa confess dan uwarki,nan take Sajeeda tana kuka ta fara tonawa kanta asiri da Abinda Abbi ya sata aikatawa,Ni Mufeeda Salati na fara nace Ameer hada da kirjinta duk ka karce shege a Zane mata ko ina,Aayan yace no..Ameer kyaleta taje mun godewa Allah ma haka tunda ya nuna mana,baki na turo nace ni dai baza a barta ba sai an cire mata farcen kafa na Babban yatsa ta karfi zan tsige shi,Aayan yace ba a nan gidan ba ke tashi ki tafi,tana mikewa na damkota  tare da yarda ta kasa Aiko Sajeeda ta fini karfi kawai sai ta rufeni da Duka sosai na koma neman a taimakeni,Aayan yace au Sajeeda naji tausayinki an barki shine zaki dukar min Mata to na fasa,Sajeeda da fuska duk zanen Kwalaba da jini tace ae din tare da gallawa Aayan Harara kafin ta maida idonta ya kafeta da Mari hagu da dama tare da bude kofa yayi short da ita waje ya maida kofar ya rufe,Ameer yace na fada ma basu da kunya.

    Nace ai wlh sai naci ubanta idan na kamata sai na karya mata hakori sai na tsoma mata yatsa a ruwan zafi, dariya Aayan yayi yace ai tafi karfinki gashi zata ji miki rauni a banza nan nace ai kyaleta nayi kawai Amma mu fada a wajenmu harda na siyarwa dan Babanta. Kwashe abincin nayi gaba daya na juye a leda na kai Dustbin Ameer ya fita dasu waje,haka na dan dafa mana saukakakken abinci abincin mu me dadi muka karya,s ai mita nakeyi na hana kowa sakewa.

    Tunda Hajja da Abbi suka ga abinda aka Yiwa Sajeeda suka shirya Tafiya can kasar Kudu cikin wani kauye wajen Babban sabon bokan da aka basu lbr anyi,
   Har wanda ya basu labarin bokan gaba daya da shi aka shirya yayi musu Rakiya banda Hajja ta dai ce Abbi yayi komai.
   A jirgi suka sauka a Enugu daga nan suka dauki Taxi wai ya kaisu wani daji ko a garin Enugu tsoron bin hanyar Dajin akeyi Sabo da matsafa sunyi yawa a dajin, Driver yayi ta Maza yana Tafiya dasu yana tsoro ko yan yankan kaine,yana Tafiya yana jan tsaki yana Chaiiiiii Alaji,suna jinsa har dai ya kaisu dai dai inda zasu dan shiga dajin da kafa mota ko machine basa shiga sai da kafa,Suka sauka tare da bashi kudi yace Alaji always making juju Money,go and Meet ur Malam is Better than to visit ths land wooo, u have to be very careful with ths place,ahhh see me see troble because of Money so people can do anything in ths world they can even kill them self,Abbi yace Abeg carry ur Wahala and Go stupid Taxi Man,shi dai me Taxi ya figi motarsa bayan ya gama surutunsa.
     Dan cikin dajin suka shiga kadan sannan Me Rakiya yace anzo wajen,Abbi yace ya sunansa kace? Mutumin yace sunansa SHAKYLGANCY sai kace dan India cewar Abbi,ai a india ya koyi har kar nan Alhaji cewar me Rakiya.

     Suna zuwa wajen anyi Ado da komai Red Abbi yace Shakylgancy.....Shakylgancy.....Sai ga Shakylgancy bugul ya bayyana kamar Aljani wani me mummunar suffa,Cikin harshen turanci Abbi ya koro baya nansa,Shakylgancy ya kece da daria sannan yace shima cikin turancinsa yace 1million Amma baza a biyashi sisi ba sai in magani yayi suka ce Shakylgancy baza mu iya dawowa nan ba karbi kudi kawai ko yayi ko baiyi ba karbi kawai zamu dinga contacting dinka a waya idan ta kama dole nayi kokari mu dawo,Shakylgancy ya washe hakoransa tare da wani hancinsa kato kamar tattasai ya karbi kudi yace suje zasu ga aiki.

    Bayan su Abbi sun fito gefen titi tare da Dan Rakiya suna neman Taxi wata mota ta yan Mafiya matsafa ta shararo da gudun tsiya dan Rakiyar su Abbi shine a gefen titi motar na zuwa tayi gaba dashi ta markadeshi a titin fit kansa ya dinga gare gare kamar Ball a saman titi,su Abbi sunyi mutukar firgita shi da Abbi Sani nan suka ga fa an kashe banza motar ko slow down bata yi ba,aiko su Abbi suka take da gudu suma suka mike titi sambal suna ta yi kamar yan tseren gudu basu san sanda suka watsar da takalma tare da babbar rigarsu ba,dama Abbin Sajeeda cewa yayi suje sun wakilceshi shi tsoron zuwa kudu yake yi tunda watarana a Crossriver akasace wani a gaban sa shike nan ya firgita.

     Sai da su Abbi suka yi Nisa sannan suka samu Taxi da kyar ta kaisu Har airport a Hanya suka siyi Sababbin takalma Amma Sabo da rashin Imani ko Jimamin Mutuwar abokin Rakiyar tasu basu yi ba sai Abbi da yayi karfin halin daukan hoton gawar a waya Sabo da ya nunawa iyalansu gashi wancen talaka ne shi da iyalansa Amma an mutu a shirka,nan ba aci ba can ba a ci ba,a kiyaye talaka ka lallaba kanka ka samu a Aljanna.

    Yau ni kuwa shirye shirye mukeyi Su Meenat zasu dawo daga Maiduguri Ameer yafi mu Zumudi wurin Magrib sai gasu kuwa da kaya Niki Niki sun shigo sai murna lokacin Yarima yazo sun finta tare da Aayan,sai hira mukeyi muka ci muka sha,Ameer yace Duk kunfi kyau a Kauyen Rimin Gado har kumatu kuka yi,Meenat tace ai baka kyauta ba tunda ka wani gudo,yana dariya yace tab ina wani zan iya zama a wannan garin toilet ce tashin hankali ana kallonka a waje,ga wata katifa kamar ta jariri,dariya mukayi gaba daya muna haka sai ga Aayan tare da Yarima,Yarima yana ganin Ma'eesha wani sanyi ya fara ratsa shi ita kuwa Ma'eesha kunyarsa takeji kwarjini yake mata wata uwar signa ya mata da ido ai ko Nan take gaban Ma'eesha ya fadi rass Sabo da lokacin Ma'eesha ta cire Ameer dama shakuwace Sabo da yawan mu'amula da sukeyi ganin kuma kamar shi wata mace bata gabansa yasa tace ke Ma'eesha shafawa kanki ruwa,
    Ma'eesha tana Satar kallon Yarima ta gaisheshi ya amsa cike da fara'a, duk ta kasa sukuni ni kuwa ina gefen Aayan nayi shuru na lula tunanin asara da zata hau kaina kwanan nan na gama kashe kudin gyaran jiki mijin bai mora ba,danni a kan ayi asarar kudin nan gwara na kusa mutuwa na farfado kawai.
   a hankali Aayan yace ya akayi? Ya rada min a kunne,ajiyar zuciya na sauke nace kai dai bari kawai asarar kudade nake ta yi kwanan nan,ina ta zuba adashin da ba a dauka,Aayan bai gane me nake nufi ba yace ke na rasa inda kika gado son kudi haka wacce asara kikayi na biya ki? Nace baza ka gane ba a bar zancen Amma ko ka biyani Bazan iya daina tunaninsu ba,tunda har yau me kayan ma bai yabe su ba ko da baki yace kayan nan sunyi sun kuma hadu etc ba a ce min kala ba bare naji dadi da kwarin gwiwar karbar asarar danayi tunda bai samu damar siyan kayan ba.

    Aayan iya tunaninsa ya kasa ganewa me nake nufi wani kuma waye wani?to Business sukeyi? Nan fa kishi ya cika shi tab yasan zata iya indai Mufeeda ce zata iya, Yarima Ya rasa inda zai saka kansa dama yake jira kawai su dan kebe da Ma'eesha ya karbi Number ta kullum cikin tunaninta yakeyi,Sai ko Ya mike yace zan tafi Aayan sai mun hadu,Aayan yace bari na rakaka,a'a zauna ban son Rakiyar Katon Gardi ni Ma'eesha kawata ce zata rakani,Dariya mukayi gaba daya Ameer yace da Alama Ya Yarima girma ya fadi ka fada akan yar wannan yarinyar,Meenat tace Ss1 kawai fa,Ma'eesha ta harari Meenat tace Gwara dai ni ko a hanya duk mutanen kirki ke tareni suce suna so ke kuwa fa Kwaja,Fela etc ku bari na dawo wlh na fasa rufa miki asiri dama kince kar na fada na yarda to na fasa Bari na dawo na baku latest a Maiduguri da Rimin Gado,Ameer dama kadan yake jira yace muna jira Sauri yau wlh komai dare bazan kwanta ba sai naji.

   Aayan yana Dariya yace gaskiya a rufa mata asiri,Meenat tayi mukus tasan yau Tata ta kare,Yarima ya dan jima yana jan Ma'eesha da hira sama sama duk shima akwai ji da kai bai fiya magana ba Number dinta ya karba ya bata tasa sannan ya bata kudi taki karba,babu yanda baiyi ba Amma taki karba nan ta kara birgeshi sosai.
   To yan mata pls a rage nuna zalama wajen Saurayi ko idan kika ga mutum ya fiye yi miki kyauta dan Allah watarana ki dinga jayayya kice baza ki karba ba ko da kina so ki dan dinga kai zuciya nesa sai ki kara birgeshi,sai masu jarabar Rokon Samari abu kawai yan mata Direct kice yi min Kaza ko bani Kaza ko yaushe kuma ba kunya ba komai wlh ba tarbiya ce ba,kina zubarwa kanki mutunci da na iyayenki a dinga daga kafa ana hakuri da yanayi na  Babu ba har ayi ta roke roke ba, ko ina wasu zakiji suna wancen ina ba yar manya bace Bazan iya ba na tsani me roko etc.

     Ma'eesha na dawowa Ameer yace matso nan Hajiyata ki bamu mu musha,Meenat tace Sis Mufee kin gansu ko,Mufeeda tace nima baza kunne nayi yarinya, Babbar banza cewar Aayan,dukan wasa na danyi masa kadan tare da kwanciya a cinyarsa , Ma'eesha tace kai Allah ya bawa Meenat farin jini samari iri iri tun daga Rimin gado yan fulani suka dinga cika kofar gida.

    Farko mun fita siyo pure water muka hadu da wani zai je kiwo da shanunsa ya tare mu yana washe baki idan kun ganshi abin dariya yana busa hayakin wiwi Yace hooai Yan Birni aradu wagga Bingel tana Burgeni, wannan ke nake so ya nuna Meenat tare da cewa Sunana TSITO, nan muka fara dariya jin sunansa Ma'eesha tace in kun ganshi wlh yaci sunansa Tsito wani siriri ne kamar a busheshi gwara Kwaja ma yana da Katon ciki Amma Tsito shi ba dan cikin ma,Meenat tace to Dan Uwarki ai Tsito yafi Kwaja lfy da ganin cikin Kwaja ai na cuta ne,kuma Tsito kyakyawa ne,Ameer yace mu dai ba ruwanmu Tsito muka sani,Ina dariya nace karki kara zagar mana Uwa akan kice dan Uwarki gwara kice dan Ubanki Better,Make min baki Aayan yayi shi Abban shine ba a so ba kyau,baki na turo cike da shagwaba nace da zafi fa...Zan rama ne.

    Ma'eesha tace Daga Tsito kuma sai NA AGWAGWAJI  shi kuwa a yan fulanin ma dan Daba ne duk wanda yaga Meenat tayi masa magana sai ya farfasa masa jiki,Ameer yace kice dan karamin yaki ta hada,Meenat tace Allah ya bani ya zakuyi dani ehe,Dariya muka dinga yi Jin har Dan karamin Saniya Na Agwaji ya bawa Meenat tana can gidan Inna an daureta za a sata cikin Shanu ana kiwata mata ita,Nace Business Sabo Sarkin Kasuwanci cewar Aayan jin yanda nake ta murna Meenat ta samo Saniya zata girma ta Haifo yayanta.
    Ma'eesha tace Arzikin Meenat bai tsaya a nan ba kullum samarinta suna hanyar kawo mana kaji da zabbi muna yankawa mu sha farfesu iri iri,Na ciji yatsa nace me yasa kika cinye a ciki banzaye maimakon ku siyar ku tara kudin ku kawo min ko dankunnen Gold na siya muku dan karami,Aayan ya kalleni baki bude yace da kudin kajin? Nace of Course.

   Ameer yace inye to wannan buhun kayan naku fa? Ma'eesha tace duk Samarin kauye ne suka tara mana su danyar Gyada,gero,wake etc,A Maiduguri kuwa samarin Meenat harda Conductors na mota,yan Napep etc me dubu daya me dubu biyu haka muka cinye musu kudi,Nace to ke kuma fa in haka ne kece me bakin jini,Meenat tace tsakani da Allah duk wani me kudi indai kinga rantsatsiyar mota ta tsaya to ba shakka wajen Ma'eesha aka zo zance,ni dai Meenat ina ga asiri akayi min daga me kaji sai me Saniya,gyada da gero tare dasu waken Suya hhhh muka dinga dariya,Aayan yace sorry Sis zaki samu wanda yafi kowa kudi kuma na gari kema,ni kuwa nace Meenat haka Allah yake lamarinsa ni kam Ruwa ta sha aradu,Rankwashi Aayan ya zuba min,Ameer yace ni wlh ji nayi gwara haka ita ba iyayi ba dama Allah yasan manufar jaki shi yasa ya hanashi kaho.

     Meenat ta gaji da abinda Ameer yake mata ta mike cike da shagwaba tayi kansa wai zata kwala masa spoon ya mike suka fara zagaya mu a palon muna zaune, sai da na gaji nace Meenat kun damemu can u stop ths Nonsense pls? Meenat tace ai kuna jinsa abinda yake ce min kun kasa yi masa fada,Maeesha ce abar duka ai ba Ameer ba tunda ita ta fada mana,Haushi Meenat taji ta jefar da spoon din tayi Bedroom abinta .

    






AsmaBaffa
[1/28, 10:00 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

   KASUWANCI NA





          101-102






Official







By
AsmaBaffa





   
         Mun dan jima muna hira bayan tafiyar Meenat sannan na mike nabi bayan Meenat Bedroom dinsu,Maeesha ma ta shigo,Ameer ma ya tafi shirin bacci,Aayan yana samansa jirana yakeyi nazo mu kwanta,Ni kuwa yau dakin su Meenat nake son kwana Sabo da musha hira ta ganin juna,Meenat tace ban gane ba?Ya zaki zo nan ki Kwanta mana mijinki fa?Nace hira zamuyi,Maeesha tace shike nan mun shiga Uku Meenat baza muyi bacci ba yau,Meenat dariya tayi hmm ai mijinta zan kira mata idan mun gaji,ina kallo sukayi shirin bacci nima na mike na feso wanka na shafa turarukan kamshi iri iri sannan na kwanta gefe,Maeesha tace wai Mufee har yau baki ciki ba? Gaskiya ya kamata ace kina da cikin Aayan,baki na tabe tare da cewa mu ba yan iska bane a kujera yake kwana ina Bed,dariya sukayi Ma'eesha ta kalle ni lallai Sis maida Karuwa yar Iska ni mamakina Banga kinyi rashin ko yar lfy ta first night ba,nima kullum zura ido nake Amma ai nasan tuni Su Mufee an san kan harkar Cewar Meenat, zanci ubanki wlh ni sa'arku ce wai dan kunga kunyi saurin girma,so kuke ko me na kwashe na fada muku? Meenat tace mu ina muka Isa daukan wannan maganganu na manya ki rike abinki dama shawara zamu baki munga ko kamar Aayan yana da matsala ne shine muka samo mafita a Maiduguri.

    Masifa na fara wacce mafita uban wa yace muku mijina nada matsala idan banda ta Family nifa bana son Sa ido Meenat ku kiyayeni,Allah baki hakuri ai gani mukayi mu da ke duk daya ne ba wanda ke boye maganar dake damunsa yaushe Mama Mufee ta dawo mana haka bamu sani ba bayan Ammah ta bar mana wasiya rike zumuncinmu,yau miji yafi mu daraja shike nan.
   Jikina yayi sanyi nan nace ai kune wlh bakwa ji sam Amma akwai matsala Meenat,lokacin Aayan yana can yana ta faman jira nazo muyi baccin mu Amma shuru shuru sai tsaki yake faman ja yana juyi.

    hannun Meenat na rike muna kwance nace Meenat kuji ni ina cikin neman taimako na addua Asara ta hauni,na tafka babbar asara,jikina da kyauna duk nema yake ya kare a banza,jibi uban Hips dina,kalli tun ina karama Allah ya hore min na shanu masu kyau da birgewa,kalli skin dinmu,amma a haka aka ce idan kana da kyau ka kara da wanka kalli yanda nake zabga uwar kwalliyar da shiga iri iri a gidan nan,yanda nake kashewa jikina kudi bai tsaya a nan ba sai da na dangana ga zuwa gidan gyaran jiki na biya makudan kudi an tsunami nasha an gyara skin,lungu da Sako anyi masa filla filla Amma ku kanku da kallona kun san na kara kyau da canjawa,kalli yanda nake sheki da walwali,kalli yanda nake kamshi ko abu na rike sai ya tafi da kamshi na,kalli ku kanku yanda kuka rude da kyauna gashi komai ya kara cika duk da cewa kun sanni Amma sai da kuka Koka yanda nake sheki da uban kyau,

   Meenat tace mun gane,to asarar tayi muni da kashe kudina yayi yawa Amma kun san Aayan asiri na jikinsa har yau bai warke ba,bazai iya komai ba sai tabe tabe,kinga ko ba komai Sabo da lafiyarmu ma ya dace ace an daina taso da sha'awa kuma taki kwanciya,kamata yayi ace mijina yana alfahari dani kamar ko wacce mace,amma ni kaina nake zargi ko nice ban iya yanda zansa yayi amfani dani ba,bayan wannan asarar kudin gyaran jiki so nake nima ace kwalliya ta biya kudin sabulu ace mijina yana yabo na yana susucewa a kaina,amma ace ina sheka Ado bana ganin ya zauce ina kanta.
   Dariya Ma'eesha tayi tare da cewa wlh ya susuce kece bakya ganewa kinga yanda yake binki da uban kallo duk inda kika Gilma,kuma kin gama zautar da shi,bakya ganin yanda yake kishinki me kike so kuma? Meenat tace akwai matsala ace mijinka bazai biya bukatarsa da kai ba,kuma ribar soyayya da aure a hayayyafa,to ki kwantar da hankalinki kinga Wani Saurayina a Maiduguri dan gidan gawurtaccen malamin Sunna ne Malamine na Sunna basa tsafi ko shirka addua zasu baka kayi suma su tayaka kuma ba kwandalarku ana dacewa,Maeesha kin tuna Masa'udu Shekare wanda akace yayi shekara da shekaru a Cikin Uwarsa kwantacce kafin a haifeshi? Wanda ke zuwa kusan kullum yana damun mu da Fassarar Hadisai? Ma'eesha tayi dari tare da cewa au wai Shekarau kike nufi? Dalla Shekare yake ba Shekarau ba,ae gaskiya ne kam malamai ne,ni kuwa nayi tsalle na dire cewar Bazan tonawa mijina asiri ba gaskiya,Meenat tace to kin gwammace ya zauna da cutar wani abun sai ana fada ake samun mafita,ai ba wanda yafi karfin cuta a duniya ba a kunya a cuta gwara a daure a fada muji shawara ina da Number su,kinga ko a nan talaka cikin Samarin za suyi rana,shi yasa ba a raina dan Adam kowa da ranarsa kuma da baiwarsa,nace haka ne Meenat Allah ya kaimu gobe sai a kirashi.

    Da haka muka fara baccinmu bilhakki,Aayan yana can yana fama da rashina,sai faman jirana yakeyi har ya gaji da latsa waya da laptop ya mike nan take ya sakko kasa tare da nufo dakin su Meenat,Yana zuwa knocking ya shiga yi yaji shuru sai da kyar Meenat ta farka taji tsoro ko abin cutarwa ne tace Mufee ku tashi yan Fashi ne,Da Sauri na fada lungun Bed nayi flat,Maeesha ta fado kaina itama,Meenat ta mike tare da bude sip ta shige ciki ta dunkule waje daya,jikinmu na rawa gashi sai bugawa akeyi,Da kyar nace waye? Nine naji Muryar Aayan,Nan Naja tsaki ina tsinewa Meenat dake fitowa daga Cikin Sip,Maeesha tace Amma kin cuce mu saura kadan hawan jini ya kamamu,a hankali na bude kofar kawai naji yayi sama dani ya tura kofar da kafa ya daukeni kamar Jaririya haka muka je har Bedroom dinsa, nace me ya faru muna baccinmu wlh ka Tsorata mu,Murmushi yayi tare da cewa akwai wani babbar kyauta da zan miki amma ba yanzu ba,tunanina kudi ne na fara Murna nace sai yaushe? Hararar wasa ya min tare da cewa nasan kyautar tafi kudi tafi komai na duniya a wajenki Amma sai ranar nima da nake cikin nishadi wanda soon nake Sa rai,a kirji na cijeshi kadan tare da cewa Allah ai ni babu abinda yafi kudi a wajena a yanzu ko mene shi tunda ba kudi bane na daina murna.

     Murmushi yayi me sauti tare da cewa wannan kayan baccin fa? Karki kara Sa min su sunyi nauyi da yawa gashi sun matseki sosai Bazan iya ciresu da wuri ba,Ai yau banyi niyyar kwana nan ba dumin yan uwana nake ji, a kunne ya rada min pls ciresu ni ki daina Sa su bana sonsu kawai,suna miki kyau Amma wahalar cirewa zasuyi harda wani Wando me tsayi fa, kunya nake ji bana son na cire sai na daga zan cire sai na fasa shi kuma ya kafe ni da ido yana faman kallon kirjina tun kafin na cire ma,nace ka kashe light to na karasa a shagwabe kamar zanyi kuka,Kara wani kishingidewa yayi kamar Sarki yana kallona dai dai tare da murmushi,a hankali naji muryarsa yace Babyna kin san me? Nace a'a sai ka fada yace Kinfi kowa kyau a duniya wanda na taba gani komai kin hada Allah ya baki,Murmushi kawai nayi nace hmm tun baka je Palace din ba kenan ka gano haka,Baki ya bude dan baiyi tunanin nasan harkar ba ma,idona na rufe ina dariya hannuwa na biyun ya rike kam yana kare min kallo harda wata Palace da ake zuwa dama? Nace uhm am just kidding u fa,Sai kin fada min naji,Nace to kaima ka sani ai Kingdom kenan ai me matakan tsaro,au wani sunan ne wannan? Nace ai Baza ka gane ba sai ka tsallake border Amma ai kaima yaron ne tunda ba sani kayi ba sai lbr kamar ni.

   Ido ya dan ware kadan tare da cewa bacci nake ji pls cire  kayan mu kwanta,jikinsa na kalla daga shi sai Boxers dan gutsul,Haka cike da kunya na fara zare rigar tun kafin na zare ya fara Murza Albarkatun Kirjina.

      Abbi an dawo ana jiran Boka Shakylgancy ya aikata Aiko sai waya da sukeyi,Cikin dare Boka ya Cillo tsafinsa zuwa jikin Mufeeda sai akayi dace Aayan yasa munyi wankan tsarki don shi ba a ko kara 1hr da najasa a jiki ko na Sunna ne,Yace to Ki daure muna Nafeela ko raka'a biyu ne duk dare mu daina bacci ,Mufee ba musu na bi bayansa muka fara Nafeela,lokacin Boka yana ta jefo tsafinsa baya Tafiya,ya buga ya buga shuru,bayan mun idar sai da sukayi dogon Azkhar lokacin boka yana ta faman jefo bala'insa Amma shuru,Har ya hakura yace sai gobe zai kara yi.
   Washe gari da sassafe ya fara tsafin irin ko muna baccin Safe kawai lokacin nan ma azhkar mukeyi na Safiya,da rana bai samu nasara ba lokacin karatun Qur'ani Meenat take kara min,yamma ya gama shiri tsab lokacin kuma Azhkar na yamma nakeyi zuwa Magrib,still daga Magrib zuwa Isha duk bashi da sa'a.
    Kwana na biyun kuwa na fara period Amma ko yaushe ina da Alwala,ga addua a bakina har kitchen ni ba wake wake nakeyi ba sai addua nan ma boka ba labari,lokacin kuma mun kira Saurayin Meenat Shekare ya hada mu da babansa na bashi labarin komai nan Malamin ya bamu adduoi ta waya da yanda zamu yisu, na fara ma yau kuma Ma'eesha ta tuna min zamu je gidan kawarsu ana bikin yayarta,haka na damu Aayan ya barni naje da kyar ya yarda yace Amma sai daí Ameer ya kaimu,Haka muka ci uban kwalliya bana cikin sahun matan aure,a gaban Aayan sai nasa Katon gyale Amma muna shiga mota na cire gyalen na ajiye a bayan motar Ameer gashina na saki jelarsa,abinda mata keyi yanzu kenan Ba a gane wace matar aure,nima sai na birge kawai,muka je Dinner wurin 9pm ana ta rawa da kade kade,Har wurin 11pm muna ciki ana cashewa na manta da wata addua ma gashi nasan mijina bai so a kalle masa ni,amma na zalunceshi bai sani ba na bari Maza na kalle min sura tare da gashina wanda nasa ne shi kadai Allah ya halitta masa,tunanina na masa wayo ban san kaina nayiwa ba,har shiga filin rawa nake muna gogaggaya da matan manya kowa ya ganni yasan matar hamshaki ce ni ko yar gidan wani ce yanda nake zubar da Naira.
     Abin haushi Boka shi aikinsa yakeyi dama aikinsa ne kullum ta nan yake samun kudinsa kamar yana Office ne,kuma basa saurarawa kullum aiki sukeyi suna gwada sa'arsu ko zasu samu wata dama daya tak su samu nasara musamman yare da zaka ga sunfi Musulmin bahaushe Amana basa karya alkawari.
    Wufff Ya turo min Aljani ta tsafinsu yana zuwa yaga na shagala ya samu dama nan yayi wuf zai shigeni Amma ba ta inda zai iya shiga jikina da wuri ai tuni ya ankara cewar Gashina gashi nan a waje nan fa yayi wuf ya bi ta gashin ya shiga jikina,nan take naji kaina ya fara ciwo sosai sai nayi tunanin ko Gajiya ce,kawai nace suzo mu tafi,haka muka dawo gida ina fama da ciwon kai me tsananin gaske kamar kaina zai tarwatse,na fara Hawaye na samu Aayan a daki yana jirana yana ganina haka yace mene lfy?,nace kaina ciwo kin gani ko sai da nace karki je kika ki yarda,zo ki kwanta na baki magani,kafada na make tare da cewa Bazan sha ruwan gidan nan ba,indai ruwane na gidan nan Bazan sha ba,Aayan ya zata tsokanarsa nakeyi yayi dariya yace kwanta,nace na rantse Da Allah me Rahma in na kwanta a gidan nan yau Allah ya tsine min albarka,bude baki yayi yaga fa da gaske ne dan ba alamar wasa a tare dani,yace to ina zaki kwana nace wani gidan Amma ba wannan ba,kaina na dafe nace wlh ni a fitar dani daga gidan nan idan na zauna a gidan nan shegiya nake,wlh in dai na kara kwana a gidan nan Allah ya tsine min albarka wannan tsinannen gidan dukka ma tsinannu ne ku yan gidan,Aayan ba a kanta ya fara ganin hakan ba tunda Mommynsa tayi da suka mata asiri haka matarsa Nafisa tayi itama da Ruky, Amma ai munyi alkawari dake baza ki bar gidan nan ba,Alkawari? Amma ka cuceni Allah ya Isa me zanci da wannan gidan,nan na sauka kasa da gudu na fara hado kaya ta ko ina,nace Meenat ku tashi mu tafi,sis lfy? Zanci kutmar ubanku dan uwarku dan ubanku ku tashi mu tafi wlh idan baza ku taho ba ku zauna,Ba yanda su Meenat basuyi dani ba Amma zagi kawai suke sha iri iri,haka Ma'eesha tace mu Bita Meenat kar a samu matsala ta fada hannun bana kirki ba,haka suka kwashi akwati har Uku,Aayan tuni ya fito ya nemi Ameer ya kora masa bayani,nan Ameer yace shawara ka bawa Meenat key din Wani gidan naka can daban sai na kaisu can su zauna,Haka Aayan a gigice ya mika masa yace kuje dayar sabuwar GRA ka gane gida Dana siya last wk pls ko me Mufee na take so a bata, kar ka dawo gidan nan ku zauna ka kula dasu kafin nazo,Ameer yanda yaga Aayan ya fita daga hayyacinsa gaba daya abin ya bashi tausayi kamar ya masa kuka ya ma rasa me zaiyi gaba daya baya hayyacinsa za a rabashi da Mufee dinsa wayyoo.

    Yana gani Yanda Mufee ta gigice sai gumi take hadawa ta fita da gudu har Jikin mota hakanma da kyar Ameer ya lallaba ta hau motar tasa cewa tayi in dai motar ta gidan ce baza ta hau ba,Aayan ya Kira Meenat da suke kuka ganin abinda Mufee keyi ya zarta hankali,kwantar musu da hankali yayi tare da cewa karku kara kuka kinji ko,kai kawai Meenat ta daga Masa Kudi ya mika mata masu yawa yace rike zanzo ltr kuyi amfani dashi.
   Meenat ta karba ta fada Mota suka tafi,Abbi yana Saman Bene yana dariyar mugunta dan sunyi waya da boka,Aayan Innalillahi yake maimatawa kawai sai Hawaye sharrrr ya kwararo masa da kyar ya lallaba kansa ya mike,ya fito a fusace fuuuu sashen Abbi ya farayi yana shiga ya shaki wuyan Abbi ya bugashi da Bango nan take idon Abbi ya firfito ya shakeshi iya Shaka sai kakari yakeyi,su Haneefa suka fara ihu nan fa su Hajja da kowa ya hallara ana kokarin cire Aayan Amma an kasa Abbi na neman shekawa Lahira,Hajja ta fashe da kuruwa za a kashe mata da ta fara Dukan Aayan,Aayan ya make Hajja ta fadi kasa dabar yace wlh akan a taba Mufee gwara kowa ya mutu a gidan nan bana ubanku bane,ku bar min gida, nan ya saki Abbi ya shiga daki daki yana watso musu kaya tun daga Sama zuwa kasa komai nasu jefowa yakeyi,nan take yace Duk na kwace aikinku kar na kara ganin kowa cikin ku a Company na kuma duk dukiyar bata Daddy bace bare kuce dan uwanku idan baku sani ba ku tambaya kuji kudina nane dukiyata ce gaba daya,Nan fa suka rude harda Hajja sun san tasu kuma ta kare yace wlh wlh ko mota daya baza ku fita da ita ba,nan take yace na baku 15mnt ku bar gidan nan,Nan ya Kira Sojoji har mota biyar suka zo da igwa ta feshin ruwan zafi tafashashe,ba shiri suka tattara kayan da zasu iya dauka na sawa suka fara fita manya da Yara daya bayan daya Maza da mata suna kayi hakuri mun tuba zamu karya asirin,Aayan yasan karya sukeyi kawai yasa Sojoji suka rakasu kaf suka bar gidan,Abbine bai fita ba wai zaiga Daddy haka Hajja ma tace dole zamuyi magana da Dana ehe,nan ma Aayan yasan so take Daddy ya tursasa shi dole ya Barsu kawai yace ba inda zasu Sojoji suka tasa keyarsu sai da suka hau Taxi har guda hudu sannan Aayan ya sallami Sojojin ya koma part din Daddy.

    Tunda Daddy ya ganshi gabansa ya fadi yasan ba lfy ba,Gefen Bed din ya dire gwiwoyinsa tare da daura kansa saman Bed din da Daddy ke kwance ya fashe da wani kuka me tsuma zuciya,Daddy ma tunda yaga Aayan yau yana kuka haka to matsala ta afku babba ma kuwa,a hankali yace me ya faru ne My Son? Nan Aayan ya sanarwa Daddy komai,Daddy murna ya fara yi Aayan yanzu yana son matarsa,amma bai ji dadin abinda ya Samu Mufee ba Amma yasan Allah na nan kuma da saninsa, Daddy ne ya kalleshi be a Man Aayan kamar mace ba abinda zai faru Insha'allah muna addua karka damu nan Daddy ya shiga lallashinsa sosai yana kwantar masa da hankali har ya hakura yace Daddy bari a rufe gidan nan kawai mu koma wancen,sai lokacin Daddy ya san Aayan ya kori duka danginsa har Hajja mahaifiyarsa,fada ba irin wanda baiwa Aayan ba ko ba komai ai Uwa Uwa ce sai na bita zan shiga Aljanna,Aayan yace ai zan dawo dasu Amma ka kyalesu Daddy su dandana wahalar,shi dai Daddy masifa ya dinga yi Amma Aayan yayi mursisi dashi haka yasa masu kula da Daddy suka daukeshi har mota suka koma sabon rantsatsen gidan Aayan wanda su Meenat ke ciki yanzu,ni kuwa sai da muka fito daga gidan hankalina ya dawo jikina,sannan na samu nutsuwa ko ciwon kai bana ji sai ma hira data barke a tsakaninmu dasu Ameer.
    Gaskiya gidan ya hadu fadar kyansa da haduwarsa bata lokaci ne,nan Ameer ya zabi Bedroom,haka su Meenat ma,nima sai da na zabi nawa sai yanzu nake tunanin ina mijina Aayan ina ya shiga? Ameer banga Aayan ba lfy? Ameer yace yana nan yanzu zai dawo unguwa yaje,nace Ok to Amma bai fada min ba,Ameer ne ya shige Room ya Kira Aayan yana sanar masa me nace murna Aayan ya farayi yace gamu nan zamu karaso,Aayan suna karasowa yasa suka kai Daddy can part dinsa daban tare da abincinsu gaba daya sannan ya wuce Direct part din da muke gidan baya bukatar gyara ko ina fes yake Sabo da ma'aikata ne ke yi kullum,wanka nayi da ruwa me zafi daga ni sai towel na gama shafa turaruka na masu azabar kamshi ina taje gashina cike nake da tunanin ina Mijina ya boye,ina haka sai ji nayi an rungumeni ta baya wani shock naji da ban taba jin irinsa ba a duniya, da Sauri na juyo tare da rungume Aayan a jikina ina kare masa kallo yanda duk ya wani hargitse me ya faru Muka dawo nan gidan My Man? Kallona yayi yace kece kika ce bakya son wancen sai na canja mana nan,na cika da mamaki sosai Hawaye ya zubo min sharrr,A hankali ya girgiza min kai tare da kawo fuskarsa saitin tawa sannan ya fara lashe min Hawayena da suka ki tsayawa,saki na yayi ya shiga toilet da Sauri,ni kuwa ina nan tsaye inda ya barni ina Hawaye har yayi wanka da Komai ya fito da towel yana goge jikinsa,Sai da ya gama feshe feshen turarukansa tare da shafa Lotion sannan yasa Boxers still ina tsaye ina ajiyar zuciya na Kukan da nayi,Har gabana ya karaso sannan ya tsaya kamar zai shiga jikina a hankali cike da nutsuwa ya hade hancinmu waje daya yana gogawa a hankali ya ciji kunnena kadan,nayi yar kara tare da murmushi kadan yanda nake jin sha'awar yau ta wuce hankali ban taba jin irinta ba ban san dalili ba,shima a wajen Aayan hakan take Amma yasan ba lafiyayye bane,Bakinmu ya hade waje daya kalar numfashin da muke fitarwa ya zarta hankali,a hankali ya zare min Towel dina tare da jefar dashi gefe ba tare da na sani ba sabo da dadi, Saman Bed ya daura ni shima ya kwanta yana min abubuwa masu rikita tunani yau a Romancing dinmu yafi na kullum da mukeyi mun kasance cikin Nishadi da jin dadi, yanda Aayan ke Surutai ka rantse babbar Harka ake bugawa,cikin kalamansa yace My  wife pls love me, say u Love me,do u love me?,sabo da na tsokaneshi nace a'a ni dai,cik ya tsaya da tsotson albarkatun kirji na tare da shafasu,why Baby nan da nan naga ya birkice min,cike da shagwaba kamar zan narke nace ai baka so na tunda ko yabona bana ji kana yi,kuma ma ai ni baka lallaba ni kana ji dani kamar kwai,duk ba wannan ne zai hanaki so na ba sweetheart,Tunda bakya so na Bazan miki dole ba yana gama fadar haka ya mike zai bar saman Bed din, na riko hannunsa ya dawo saman Bed tare da cewa da cewa Lfy? Bana so na takura miki ne, a hankali na kara bakina a saitin kunnensa tare da cewa I love u My Man nayi shuru tare da rufe fuska da tafukan hannuna.

    Cike da farin ciki kamar an masa Bushara da Gidan Aljanna yace Are u serious Baby?yeah My Man,harshena kawai naji ya cafko yana aika min da sakonni masu zafi nima na shiga maida mishi da martani,kukan dadi kawai mukeyi abin ba a cewa komai Haushi nake ji nayi asarar kudina na gyaran jiki nasan bazai iya yi min komai ba, nace Allah ya baka lfy My Man banyi tunanin yaji ba ashe yaji a kunnensa,nan take ya shiga neman Hanyarsa ni kuwa na saki ma jiki bazai iya ba tunda bashi da lfy sai dai naga yau yanayinsa daban yake da kowanne,a hankali yace kin shirya Mufee na? Murmushi nayi da kyar nasan bazai yuwu ba nace why not am Ready, wani Radadi naji marar misaltuwa a kasa na kamar an zuba min Attaruhu a Cikin gabana,cike da Rauni nace wayyo....Allah....zafi.....Amma Aayan baya gane me nakeyi gaba daya aiki yake yi bilhakki,sambatu da Kukan Dadi kawai yake min iri iri wanda ni Sabo da zafi bana kulashi Amma kuma banyi kuka ba,har naga an kwashe lokaci me tsawo yana aikinsa bai gaji ba,kamar raina zai fita haka nake ji,sai da ya dade Sabo da gwarzontaka kuma shima yasha wahala yaune na farkonsa, sai da ya kawo sannan ya wani ki zare jikinsa wai a kasance a haka har abada kawai ya kwanta a kaina da zafi da wahala gashi a jikina ya kwanta,sai da ya huta sosai sannan ya zare jikinsa ya koma saman Bed ya kwanta sai kuma naga ya kara dawowa ya makale a jikina,Aayan yafi mace son jiki,sai murna yakeyi ya rasa inda zai Sa kansa yace ashe alheri ne da muka bar gidan can? Sannu Babyna Allah miki albarka na wahalar dake gashi ban san zamuyi ba ko sallah bamuyi Nafeela ba ta Sunna,amma tunda nayi addua ai ba komai ko Ya karasa yana kallona Sabo da ya kunna haske,nace uhm shike nan dai ai za muyi ltr,amma kin bani mamaki Mufee na bakiyi kuka ba sannan duk kin jure wahalar da karfina,a hankali nace kwalliya ta biya kudin sabulu yanzu banyi asarar kudina ba,ai dama ni asarar kudin ce bana so ayi,kuma gashi kaji dadi Alhmdllh Allah yasa ka warke gaba daya,kasana ya kalla har jini yake Sabo da raunin da yaji min gashi farkon mu ne,yace Bari muyi wanka nace to Amma kaji dadi? Babban yatsanta ya daga min tare da cewa babu wacce za a samu kamarki Baby ni a wajena Bazan ma samu ba,,ai kinga yanda na zauce ke dai bari ba a magana,ni kadai nasan kyautar da zan miki,duk zafin da nakeji sai da nace kudi? Yace ae harda abinda yafi kudi na washe baki nace kayan dadi ne? Yace ae harda su kullum daga yau zaki samu,ban gane ba nace tam Allah ya kaimu zanji dadina,wani kallo yake bina dashi na musamman wanda sai kin cika mace Namiji zai yi miki irinsa,Na daure nace ya dai? Yace  Carkwai matsagwai sarkin dadi,Allah ya taimaki Mufee,Allah ya taya miki,Allah ya rika miki kuma Allah yaja zamaninki Mufeedan Ammah Amma yanzu ta Aayan ce,ban san sanda na fara sheka dariya ba yanda yake ta yi min kirari harda daga hannu kamar yana gaban Sarki, kamar ba Aayan ba ban taba sanin haka yake ba sai yau.

     A raina sai dadi nake ji yanda naga Aayan ya wani rude ya gigice sai tarairayata yake kamar zai cinye ni,a raina nace dole na ci gaba da bashi hadin kai yana nuna min so haka,dauka na yayi da kyar na bari ya gasa ni sosai sai shagwaba nake masa har yayi min wankan Sabulu nayi na tsarki shima yayi ya dauko ni muka fito,take away din daya shigo dasu dazu ya bude mana kaji gasassu sun sha hadi,ga kayan sha iri iri ya hada min ruwan tea me kauri,bayan mun shirya jikinmu Sallar Nafeela mukayi tare da addua tunda dazu bamu yi ba,sannan nace yunwa,zaman ma da nakeyi sai da dabara da kansa yayi Feeding dina naci na koshi shima haka,Brush mukayi sannan muka kwanta nan ma yaso yayi kari da kyar na lallabashi sai gobe da sassafe,bacci ya kwashe ni shi kuwa farin ciki da murna da kyar ya samu yin bacci yana tunanin me zai min a duniya ya faranta min.

    Abinda ya jawo Aayan ya warke shine asirin dasu Abbi suka masa a wancan gidan sukayi sun haka rami suka binne,shi yasa malamin nasu yace bazai masa tasiri ba sai in yana wancan gidan,amma idan baya wancan gidan sha'awa ta motsa masa me karfi to zai iya saduwa da matarsa,shi yasa suka zuga Hajja kan Aayan ya dawo su zauna tare,duk kuma matan nasa dama bai gwada saduwa da su ba sai niyyar ya fara kuma aka samu akasi,yanzu sun manta da hakan burinsu su raba Ni da gidan tare da kannena sai gashi ta wani bangaren Ashe alkhairi ne.
 
    Hajja basu tsaya ko ina ba sai gidan Abbi dake Na'ibawa can cikin yorubawa dake zaune a unguwar,gidan kuma karami ne rashin dabara yasa suka kasa yima kansu planning su mallaki gidaje,motoci etc gaba daya sai suka dogara da Arzikin Daddy suna ganin babu abinda zai Sa a raba su da wannan katafaren gida,Abbi ne kadai yayi karfin Halin siyen karamin gida a Na'ibawa gidan kuma ba wani babba bane ba kuma me kyau bane can,gashi duk Aayan ya kwace motocinsa,Sai Gold din matansu kawai da suka mallaka gashi basu da aikinyi,Khaleel da Mujaheed suka ja tsaki tare da cewa Ameer yayiwa kansa gata gashi yana can cikin daula. Abbi da yan uwansa sai bige bigen waya suke yi,haka Haneefa dasu Sajeeda sai hararar Hajja suke kan wai dole ta tursasa Daddy ya dawo dasu,Hajja tace gobe zamu koma Insha'allah Allah zamu je mu sameshi dole zai barmu.
    Hajja bata san basa gidan ba sun barshi kuma basu san sabon gidan da suka koma ba,g ashi duk wayoyin basa shiga .









AsmaBaffa
[1/30, 1:28 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

   KASUWANCI NA




          103-104





Official







By
AsmaBaffa




         ❤Kai Fans Masoya wannan Novel nawa sunyi yawa wai wa zan bawa page ne ma a cikinku ko wanne Gp gaku nan da yawa,ina Godiya fans dina wlh ina matukar jin dadi kuna birgeni.
     Kuma ina rokonku dan Allah ko wata tayi min magana taga banyi reply da wuri ba,ko ta kira ban dauka ba dan Allah ayi min Uzuri ba yanga bace kuma ba wai wani abu bane sai in bana kusa ko ina wasu aikin,sannan Dan Adam ajizi ne a dinga hakuri da Halina,ko a gp za ayi comment aga banyi magana ba ayi min Uzuri kwana nan bani da time sosai ne.love u all.

    Wannan page kacokan na yan albarka ne YAN NIGER naku ne Masoya na yan Niger band yan Nigeria.😅

 




       Koda gari ya waye da kyar Aayan ya iya fara farkawa ya lallaba yayi alwala ya fara Sallah ya idar azhkar din ma kadan yayi ya koma ya kwanta kawai tare da kara kallona yana murmushi nan take ya kara makaleni a jikinsa sai baccinsa, jin laushin jikinsa yasa nayi mika tare da kara shigewa jikinsa harda Kukan shagwaba shi kuma yana wani jijjigani kamar Jaririya,haka har bacci ya sace shi again,bacci muke ba ji ba gani.

    Meenat tace Ma'eesha abin nan na Mufeeda na lfy ne kuwa? Kema kya fada gashi har mun gyara ko ina yan aiki har sun gama nasu suma sunyi gaba,Ameer da Alama yunwa yake ji muna ta jira muji me zamu dafa kin santa sai tace mijinta baya ci sai an sake wani kalar,Meenat tana dariya tace muje muyi iya namu kawai,Suna kitchen sai ga Ameer ya fito a birkice daga gym yake ya motsa jiki sosai kamar zai fadi Sabo da yunwa,gashi bai iya shan fresh milk ba Amai take sashi idan ya sha da Safe,
    Gefen Meenat ya tsaya tare da cewa ya akayi ne ta Tsito?  Harara Meenat ta aika masa,Maeesha bata ma san me suke ba tana can tana fama da tunanin Handsome Yarima da yake kasheta da kalamai masu dadi ita kadai take murmushinta.
    Meenat tace Ameer da kasan kyau irin na Tsito da baka yi magana ba,Ameer ya tabe baki tare da cewa ai dai nasan kaf kauyen su Tsito basu da kamata yarinya bare ki min gori,Handsome kamata kema dan kin sanni ne kina ganina a banza kije kiga yanda yan mata suke rubibi na kulasu,da ace baki sanni ba da tuni kin mato a kaina,Allah ya kiyaye ai ni shekarunka sunmin kadan yaro dakai, Wukar da nake fere dankali ya karba ya fara taya mu yace ku matsa so kuke yunwa ta kashe mu a gidan nan, hmm Mufee ce taki fitowa ko lfy? Cewar Ma'eesha,Uwar Sa ido ina ruwanki dan bata fito ba mace da Mijinta ya kamata a aurar daku kuma ku daina sawa mutane ido,Maeesha tace mu ina ruwanmu dan tani su shekara a Bedroom in dai lfy shike nan, wurin 11am da kyar Aayan ya tasheni nayi wanka tare da Brush na sake gasa jikina na daura alwala tare da tayar da Sallah,Lokacin Aayan ya shirya cikin wani yard me Laushi Dark arsh color,Ina kallonsa yanda yayi kyau ya zarta kwatance, nayi adduoi na mike a hankali kamar yar kaciya na lallaba na shafa Lotion da turaruka tare da Sa Gown me kyau simple English wear doguwace har kasa sama ta dan dame kasa ta bude pink color nayi kyau sosai,powder kawai na shafa tare da lipgloss red sama sama na yafa dan siririn gyalena a kaina,uban gashina nayi acuci dashi.

    Aayan sai bina yake da kallo so yake sai ya kara yi Amma na ki yarda ko fuska ban bashi ba,na dan dingisa har gabansa na zauna gefensa a saman Bed na kwantar da kaina a cinyarsa ina kallonsa nace ina kwana ya rufe min baki da Sauri tare da cewa ni ya dace na duba lfyr ki My Dear,ya jikin?Nace da sauki yunwa nake ji kasan bana jure yunwa ni,Ki kwanta bari na kawo miki abincin da kaina nasan su Meenat sunyi ma yanzu,Yatsunsa nake wasa dasu nace so kake su gane sai yanzu ka angwance gashi sai murna kakeyi kana fita zasu gane tunda ka kasa boyewa jiya ka kwashi dadi,Dariya Aayan yayi ashe dai matar tawa bata da kunya da yawa,fuska ta na boye a kirjinsa,tashi muje Amma tafiyarki ta canja ya za ayi kawai ka rikeni sosai irin soyayya ce,haka za ayi.
    Hannunsa ya zagayo ta kuguna ya manneni a jikinsa tare da rikeni sosai muka fara Tafiya a hankali,nace wash Allah ina famuwa wajen da zafi kawai ka daukeni Bazan iya bin Steps ba.
    Ba musu ya daukeni kamar Jaririya tare da cewa kin tabbata baza kiji kunyarsu ba? Nace waye bako na ciki,Ameer ne kuma shi baya shiga sabgar wani bazai ma kalle mu ba.
    Suna Dinning suna Break suka hango mu muna sakkowa,Meenat ta Radawa Ma'eesha sabon Salo yau suka canja,Maeesha ma a kunne tace Mufeeda yanzu ko kunya bata da ita,Ameer yace nima dan rada min naji,Dariya sukayi Ma'eesha tace Bada ni ba,Meenat tace dole kai sai kaji nan a hankali ta karkata gefen Ameer tace Sabon salon su Aayan muke kallo a sama ko kunya babu kallesu,Ameer yana dariya ya dan Saci kallon yace uhmm wannan harka tayi nima Allah ya kawo ranata har sun tayar min da tsohon tsumina.
    Suna ganin mun karaso suka daina kuskus duk na tsargu nasan halin Meenat.
   Aayan suka fara gaisawa sai ni,sun saba kullum faran faran ina jansu da wasa Amma yau suka ga shuru sai dai na kwanta jikin Aayan lagwaf, Aayan yace ina abincin fa naga Table sai kadan? Meenat tace bamu dafa daku ba Sabo da Sis sai tace baka cin Kaza da Kaza shi yasa muka yi iya namu in ta fito sai mu tayata tayi muku naku.

    Aayan ya janye na gaban Meenat ya mikawa Mufee,ya janye na gaban Ma'eesha da Ameer ya mikawa Mufee Amma na Ameer shi ya cinye da kansa matarsa baza taci ragowar wani ba,Meenat baki bude take kallonsu hankali kwance suke cin chips and Egg dinsu harda tea din,Aayan yace kuje ku dafa wani ku in kun gama kuci,Mufee ko magana banayi cin abincina nakeyi duk Aayan ya wani rude ya rasa inda zai Sa kansa ya rasa ina zai sani ko me zai min bakinsa a washe yau shi kadai yake ta hira a Dining Ameer mamaki ne ya kamashi dan shima bai san Aayan haka yake ba da surutu gashi ya kwace musu abinci sun cinye musu,Meenat ya kalla da suke ta kallo na yace kuje ku dafa ma kanku wani abun,Darling me zaki ci? Ko kin koshi yanda yake min maganar ma a hankali kamar Jaririya sai da naji kunya,ido na daya na kashe masa sannan nace farfesun Kifi nake so da dambun naman Kaza,Aayan yace to Kunji ayi mata yanzu da wuri kar a dade kai Ameer kuje ko wanke wanke ka tayasu,Dariya Ameer yayi tare da cewa Yaya harda ni ina namiji kasan ni ban iya shiga kitchen ba bayan haka ma Meenat ta gama rainani a gidan nan zagina takeyi,Meenat tace wlh sharri yake min ni ko hararar Sa ban taba yi ba fa, Ma'eesha tace dan Allah muje muyi Sauri zanyi bako ni anjima,Meenat ta kalli Aayan Ya kasan Bakon nata? Aayan yace pls kuje mana kun dameta da surutu kanta zai fara ciwo,ina jinsu sai dai nayi musu Alama da hannu kamar wata sarauniya wai ni ga me miji ana so na nace kuje pls da kyar na furta hakan cike da yanga.

    Kitchen suka wuce har Ameer din shi abin ma dariya yake bashi na Aayan to yau me Mufee ta bashi ne haka,Maeesha sarkin kida bluetooth speaker ta dakko ta ajiye a kitchen tare da hadawa da wayarta ta fara Sa musu kida sun cika kitchen da kida, Ameer da Ma'eesha sai bin wakokin sukeyi dama sune sarakan waka,Maeesha ita a wajen rawa ba kunyar uban kowa takeyi ba rawarta take cashewa suna aikin,Ameer kuwa Babban yaro ne sai dai yayi Alama da hannu,Meenat kallo take kawai tana dariya suna girkin suna cinyewa duk dambun naman sun cinye rabi dama kadan sukayi,Farfesun kifin ma haka,Ameer yana ma Meenat magana a daina cinyewa bata ji sanda yayi maganar ba ya dauki spoon daga Cikin farfesun ya dau zafi sai da ya dan tsaya yanda bazai Konata ba Amma zata ji zafi ya daura mata a bayan hannu,a zabure Meenat ta juyo tana yarfe hannu nan take ta koma gefen sink Bowl dauke da ruwan da suka wanke kifi da nama hannayenta biyu ta tsoma ciki ba tare da Ameer ya sani ba sai jin tafin hannayen Meenat biyu a fuskarsa gefen sajensa tana shafa masa kamar me shafa mai, karni yaji da Sauri yaja baya yana dauke numfashinsa ga Ameer da tsantsami  baya son karni ko kadan yanzu zai fara Amai,Meenat bata sani ba har sumarsa ta bi ta shafa masa ta karfi yana zillewa.
    zuciyarsa har ta fara tashi da Sauri taga Hankalinsa ya tashi ya fito da Sauri tare da wuce mu a Dining ya fada Bedroom,tunaninmu da Meenat sukayi fada Aayan yace Meenat ce ta bata masa shi kuma ga fushi wlh aure zan daura musu,Dariya nayi nace hmm Ai Ameer ke tsokanar ta.
   Ameer yana ciki sai wanka yake shekawa kamar zai cire fatarsa ya dade yana abu daya ya fito zuciyarsa na tashi still haka ya shafa Lotion yayi sabon shiri kayan da ya cire a leda ya zuba su tare da fitowa ya wuce mu ya jefa su a dustbin na Compound,Ya kara dawowa Bedroom da Sauri sai kakarin Amansa muka jiyo,Kaji kamar Ameer Amai yakeyi,Aayan yace wani abu ya gani na kyankyami ko karnin kifi yaji haka yake yi,Amma kasan haka kace ya taya su? Na manta ne sai yanzu na tuna Amma tambayi Meenat ko dama bashi da lfy ne.

     A hankali na mike da kyar nake Tafiya har kitchen nace Meenat me ya samu Ameer,ba komai spoon me zafi ya Dora min a hannu shine na shafa masa ruwan kifi a fuska,Maeesha tace wlh har sumarsa ta shafa masa,fuska na bata baki da kunya dalla jibeki ta Tsito kawai sai kije kiyi jinyarsa gashi can yana ta sheka amai a toilet Aayan yace baya son Karnin kifi danye baki kyauta ba,Kirji Meenat ta dafe tare da cewa wlh ban sani ba Sis Allah Sarki to me zanyi in na je ma? Harara na watsa mata ki wanke toilet ki gyara ko ina.

    Lokacin Aayan ya shiga wajen Ameer dake toilet yana ta faman Amai,Doctor ya Kira tare da sanar masa nan take Doctor yace ga magani nan ya bayar a kawo,15mnt  wani Nurse yazo a mota har gidan dake Aayan duk ya sansu suka gaisa ya Bada magani a leda tare da yanda za a shasu ya tafi,ni kuwa uwar son abin duniya har Dustbin naje na zakulo kayan Ameer da ya jefar nace wannan ai fariya ce na bawa me wanki nace ya wanke su ya goge idan ma Ameer baya so sai na kaiwa Shehu me kanti na tsohuwar unguwarmu wanda muke buga masa waya ya kaiwa Ammah.

   Meenat Zata shiga Bedroom din Aayan yace ai sai kinyi wanka sosai zaki shiga Sabo da kina zuwa kusa dashi yaji wani karnin amai zai kara yi,Cike da tausayi Meenat ta wuce Dakinsu a ranta tace shi yasa suna fara taba kifi yaja baya ya koma karshen Kitchen ya zauna a can,amma kuma yana cin kifi kadan kadan kawai danyen ne bai son karninsa kuma.
    Ma'eesha ce ta karasa komai tare da shirya Dining ta gyara kitchen da komai ta wuce Bedroom lokacin Meenat har ta gama hadewa cikin Lace Sky blue riga da skert tasha kyau ga iya kwalliya,turare tayi ta shafawa iri iri Sabo da kar taje Yiwa Ameer Sannu yaji Karni a jikinta ya fara Amai,ta fito Aayan ya mika mata maganin ki tambayeshi me zaici ki bashi,ina kwance saman cinyar Aayan nace Meenat kar ki sake wlh ki masa rashin kunya Kinji na fada miki,Dariya Meenat tayi sannan tace to ni ina ruwana dashi?
    Shiga dakin tayi da mamaki yanda Dakin yake komai Neat kamar na mace,saman Bed ta hangoshi ya dukunkune cikin bargo yana rawar Sanyi,Meenat ta karasa gefensa da Sauri tace Sannu Ameer kayi hakuri ban san Baka son Karni ba,duk da ciwon nasa sai da yace ta Tsito in ba shirmenki ba wa yake son Karni? Murmushi nayi me zaka iya ci yanzu? Ba komai,to tashi kasha magani inji Ya Aayan,haka yace ai sai dai ki hauro saman Bed ki bani Bazan iya tashi ba, farko dai Dan zuba min ruwan tea me zafi ki zuba zuma spoon Uku sai ki matsa lemon tsami kadan ki kawo idan na sha sai na iya shan maganin,dan da nan tayi yanda yace ta Hau tsakiyar Bed din sannan ta bude blanket da kyar ya fito tare da dan Zama kadan,ta daura masa cup a baki ya shanye zumarsa tas,sai ta mika masa ruwa da magani kala biyu ya shanye sannan yana rawar sanyi ya koma ya kwanta, Amma ba amai kawai ya saka harda zazzabi ba? Meenat ta tambaya, Ameer wanda yasan shi dama ciwonsa na Sha'awa na motsawa sama sama to harda shi yau,Yace baza ki gane ba Meenat ciwon biyu ne suka hadu,Da tausayi Meenat tace Sannu Allah baka lfy.

    Ameer ya dan kalleta kadan yaga zata bar dakin nan take ya fara nishi yana ohhh wash cikina da Sauri Meenat ta dawo gabansa a gigice ta haura saman Bed din tana ciki kuma again?ko maganin ne ai Ameer fari ya kama yi da ido wai ya sume,Meenat ta rude harda kuka tana dan Allah ka tashi karka mutu kaji tana jijjiga Ameer ya kara lumshe ido Meenat taga fa kamar ma ya dauki hanyar mutuwa gashi ya wani kankame cikinsa dai dai mararsa ya dafe wajen kam kam,Meenat da kyar ta iya cire hannunsa saman Marar ba riga a jikinsa sai Wando 3qrt Shakewa taji yayi yana shidewa kawai sai taa maida hannunta saman Marar tasa tana latsata ko ina ba tare ma da tasan me take ba,Ameer dadi ya gama kasheshi sai nishin dadi yake da numfarfashin dadi, a ransa yace Hajja ma na girmi wayonta bare ke,zaki kasheni ban shirya tafiya ba, ita kuma tunaninta zafin ciwo ne sai ta kara dagewa tace kana jin sauki?Yace da kyar banji me kika ce ba fada min a kunne na,so yake kawai tayi masa magana ya kara Jin sweet, haka ta kara bakinta a kunnen Ameer tare da cewa kana jin sauki? Wani sanyin dadi yaji nan take kafin kace me Ameer ya wani rike Meenat gam gam yana shidewa Meenat ana kukan Tausayi wai yana jin jiki, sai ga Ameer har ya warke ras ya samu nutsuwa zazzabi ya sauka sai gumi ke keto masa Sabo da dama cutar tasa ta Sha'awa ce kuma garin latse latse ta sauke masa ita ya dawo hayyacinsa.

     Muryarsa taji yace ba kyau Allah ya hana taba mutumin da ba muharraminki ba kin jawo min Allah zaiyi fushi dani ki tafi zan fito naji sauki na gode,da Sauri Meenat ta cire hannunta daga Cikin Ameer tana Harararsa ta sauka daga Saman Bed din da Sauri tayi waje abinta ta bar Ameer yana dariyar jin dadi yasan yau daba dan Allah ya kawo Meenat ba da maybe mutuwa zaiyi da ciwon Sha'awarsa tuni dan rage zafin ma da yakeyi da mata ya daina,yanzu ya tuba baya kula ko wacce ya mace Sabo da yaga duk bata lokaci ne.
   Meenat na fitowa ta tarar na zauna daram a cinyar Aayan yana bani farfesu ina ci,sai shagwaba nake masa ina Hawaye yana lallashi, tunanin Meenat zanji kunya kawai sai taga nayi mursisi ko a jikina sai ma kara lafewa da nayi a jikinsa ina shakar kamshinsa,da Sauri Meenat ta fasa wucewa ta koma dakin Ameer Sabo da wai taji kunya, dariya nayi kawai,Meenata a ranta tana to wai Sis me aka yi mata yau ne komai kuka shi kuma yau ya Zama maye a kanta gaba daya lfy kuwa?

    Ameer lokacin ya shiga wanka Meenat ta dan jira wai ko zata ga mun tashi Amma sai ta dan leko ta kofa taga muna nan muna Holewa haka ta hakura ta fito da Sauri ta shige Bedroom,Maeesha kuwa tana palon baki tare da Yarima suna hira.
    Aayan ne ya daukeni tare da cewa an koshi haka muje ki kwanta zanje wurin Daddy, ka gaishe min dashi   sai na warke zanje,h ar Saman Bed ya kwantar dani tare da rufa min Blanket bai dade da fita ba bacci me nauyi ya kwashe ni.

    Yau Daddy kansa yasan Aayan yana cikin farin ciki me tsanani,Daddy ya kalleshi tare da cewa fada min Son wanne abin farin ciki ne ya same mu?Aayan ya fara dariya wacce Daddy ya rasa gane ta mene,Aayan nasan baka boye min komai sanar min mene? Daddy kunya nake ji fa abin kunya ne,Sanar min naji muyi farin cikin tare,Daddy na Warke jiya ya fada tare da rumtse ido wai kunya,Murmushi Daddy yayi na jin dadi tare da cewa Alhmdllh Son Allah ya kara lfy me dorewa da nisan kwana, jeka tunda yau kunyata ka koma ji,da Sauri Aayan ya bar part din Daddy ya dawo namu,kayansa ya cire da Sauri daga shi sai boxers ya shigo blanket dina ya shige jikina sai bacci.

   Sai wurin 3pm na farka na ganshi a jikina kara lafewa nayi a jikinsa ina shakar daddadan kamshinsa me sanya nutsuwa,hannunsa ya daura saman kirjina yana baccinsa cikin nutsuwa,tunawa nayi bamuyi Sallah ba ga La'asar ta kusa fuskarsa me matukar kyau tare da sajensa na shiga shafawa a hankali,shima a hankali ya bude idonsa ya saukesu a fuskata me cike da nishadi,bamuyi Sallah ba muna ta faman bacci na karasa ina sauka daga Saman Bed din sai toilet, nayi brush tare da wanka nayi alwala na fito sai lokacin ya shiga shi ma,ban jirashi ba na fara yin sallah sannan na shafa Lotion tare da turaruka nasa kayana lokacin ya fito La'asar tayi na yi Sallar sannan na zauna gaban Mirror na tsantsara kwalliya tare da Sa Atamfa green riga da skert nayi kyau na mamaki,ina gyara Bedroom din ya idar da sallolinsa tare da addua,na gyara room din har toilet komai Kal kal duk da ba wani lfy ce dani ba Amma Haka na daure na yi.

    Hajja ce Tare da Abbi suka shigo gida sun dawo daga gidan ko zasu ga Daddy Amma gidan an kulle ba kowa haka suka dawo jiki ba kwari,takaici ya damu Hajja,Abbi yace yanzu ina zamu gansu? Hajja bakin cikinta bata dauki kudi ko sisi a gidan ba,yanzu bata da ko kobo,haka kowa na gidan babu me shi,Gold din matan su Abbi ma iya na kunnensu ne da abin hannu basu da komai,ga ba abinci,har Companies na Aayan sunje bai je aiki ba kuma an hanasu shiga,zama sukayi kowa yayi jugum jugum,Abbi sani yace Hajja bafa aci ba,me zamu ci a gidan dole ciki sai ana bashi hakkinsa,Abbin Ameer yace idan fa na gaji wlh zan tsinewa Ameer na huta yaro dan iska tambadadde ya barmu ko kallonmu baya yi yana can yana jin dadinsa, dama Hajja tana cikin fushi ai ko ta hayayyako da masifa rufe min baki dan Iska da bayanka me zubin na Kwadi, Ameer din nawa zaka la'ana ahir dinka duk jikokina nafi sonsa, Mujaheed yace ai ba shi ya kar zomon ba,duk ba kece kika jawowa kowa ba yaja tsaki,Hajja ta Harare shi da gogoronta irin na yorubawa tasha bakin kwalli a ido bajagau,Khaleel yace mu kawai a san yanda za ayi damu muci abinci,Umman Ameer tace ga dankunnen Gold dina a siyar a siyo abinci,Haka ma matar Abbi Mustapha,da Abbi Sani sai Matar Abbin Yara duk sun Bada nasu,Hajja tace Kai Sani kaje ka siyar dasu ka siyo kayan abinci,sannan ka kawo min dubu goma a ciki zan ajiye a aljihuna kasan zama ba kudi masifa ne,Abbi yace haba Hajja ko masu dankunnen ba a bawa ko 1k ba sai ke za a baki har 10k kin san fa abinci har kayan girki sai an siya,Haneefa ta bude Jakarta tace ni gashi na taho da 10k gashi a bawa Hajja mu huta,da Sauri Hajja ta fisge kudin ba ko godiya,Sajeeda tace dubu biyar gareni kwandala Bazan bawa wata katuwar tsohuwa ba gashi Mujaheed da Khaleel ku rike a hannunku,haka Meenal duk cikin yan matan tace ga Wata 3k Ni Abbi Mustapha zan bawa nawa Sabo da shi ke bani kudi idan na rasa ku kuwa dazu duk ni na siya muku Waina da miya kuka ci kuka koshi Bazan kara muku ba.
    Hajja tace Allah sarki duniya Aayan da Daddy tunda suke mana komai basu taba yiwa kowa gori ba.

   Wani dan yaro Sabeer yace Mommy ruwa zan sha babu,Hajja ta taso da Masifa zaka ci ubanka kai baka san babu ba ance ba ruwan roba a nan ko purewater babu dan Iskan yaro matsiyaci,Sajeeda tace kaje ka balle kan pampo yaro ka kwankwadi ruwa idan typoid ta kamaka ne hanji ya bule ka sheka lahira dan ni nasan wlh indai a haka zamuyi rayuwa ba shakka mutuwarmu ta gabato cututtuka kadai sun ishemu ruwan pampom ma wasu gurbatattun abu ke fitowa ta ciki.

   Haneefa ta sosa cinyarta tace karzuwa ce zata kamani kwanan nan ,Meenal tace ya Ilahi muna karbar rayuwa,Mujaheed ya sheke da dariya tare da cewa ths is just the begining matukar Hajja na raye,kwana biyu kacal, dundu Hajja ta zuba masa a baya.
   Kuka akaji Hajja ta saki tana komai ace nice Allah ya Isa abin ya kai har mutuwa ake jawo min da lfy ta da kwari na, Abbi yace kiyi hakuri baza su kara ba,Hajja ganin yayanta Maza na wajen ta fara shure shure tana mutuwa zo ki daukeni na huta ga jikoki birjik suna ji sai Khaleel ne yaja tsaki tare da cewa wuya kika ji shi yasa kike kiran mutuwa da sanda muna gidan daula da jin dadi me yasa baki nemo mutuwar ba,ki rufawa kanki asiri wlh karki mutu yanzu sai kin tuba idan ba haka ba Ki ci duka wajen walakiri da bulalar wuta, Hajja tana Hawaye tace ubanka da uwarka ka fadawa haka Mutuwar tazo ya fiye min wannan rayuwar ta talauci.

   Su Abbi an dan siyo kayan abinci matan suka siyo kayan girki tare da na cin abinci duk na talauci haka gidan sai Abbi ne yaje ya karbi bashinsa hannun wani da yake bi Dubu Dari sune ya samu ya siyawa kowa katifa karama sannan aka sawa gidan kaya da sauran kaya haka na talaka,kitchen ma aka kara yan kayan cin abinci da kayan abinci ana dan cin garau garau, duk yanda suka so ganin Aayan ko Ameer ya gagara,har Yarima sun nema yaki saurarar su,ganin haka Hajja tace su hakura ai indai Daddy ne zai nemeta tunda uwarsa ce kuma yana yi mata biyayya su danyi hakuri na dan wani lokaci,gashi yan samari da yan mata sun hana a siyar da wayoyinsu manya tare da laptop dinsu sunce a mutu da yunwa akan a siyar gashi abincin da yan makaranta duk sun cinye kudin su Abbi,a bincin ma sabo da suna da yawa da wuri ake cinyeshi gashi babu me aikin yi ko fita basa yi a unguwar yaran ne kadai ke zuwa schl Abbi yace kudin makaranta na karewa sai dai a maida su ta Gomnati,Mujaheed  da Khaleel kuwa su Abbi sunyi sunyi dasu su karkade takardunsu su fara fita neman aiki amma sunki Sam,sabo da ba a musu tarbiyar neman na kai ba,ba a nuna musu tun farko cewar ka nemi naka yafi akan ka dogara da kudin wani ko na ubanka,basu san wahalar duniya ba.
    Su Haneefa yan mayuka masu kyau duk sun kare an fara duhu duk da cewa suna da haske amma sabo da ba irin rayuwar da suka saba ba kenan duk sai suka fita daga hayyacinsu sai masifa da rashin kunya da suke yiwa kowa a gidan musamman Hajja da suke ganin laifinta ne. Saurayin Meenal ne ya bata Dubu ashirin suka samu aka sa carpet a Palo da bedrooms,shima sai da ta dinga rokar shi ta zubar da ajinta sosai ya dan Sha minti da ita sannan ta samu kudin.
    Matan su Abbi kuwa yanzu yar biyayyar da sukewa su Abbi Ashe duk ta kudi ce yanzu fada da masifa kawai ke tashi a gidan babu me Zama lfy,Hajja da tayi magana su zageta,Hajja ba kudin zuwa wajen bokaye sai cin goro da take tashen yi ba dare ba rana.
   Tun daga wannan Rana Hajja Sabo da bata son talauci take kiran mutuwa ko a dakinta sai kaji tace mutuwa kizo ki daukeni da wannan rayuwa,tace to yaran wai ina suka buya haka ko ina an kasa ganinsu da ace sun bude mana gidan ma sai mu kwashi yan kadarorinmu da kudadenmu ko banza ma kafa kanmu cewar Hajja,Haneefa tace ah Hajja kiwa Daddy da Aayan baki mana wlh da nice ke tsinewa Daddy kawai zanyi.

  Harara Hajja ta zabga mata tare da cewa to ai yafi ubanki dan uwarki ubanki Abinci kadai ya kasa daukan nauyinmu bazan tsine masa ba idan uwata ce ke sai kisa na tsine masa munafuka da hakora kamar na gafiya.
   Kullum yan gidan Hajja ta Gallabesu da kiran mutuwa kawai sai dan  Matashi Sabeer yau da dare ya shirya cikin fararen kaya tas,komai fari yasa tare da shafa chalk a fuskarsa ya koma kamar dodo,ya shiga dakin Hajja cikin tsakiyar Dare ya wani tsaya a kanta tare da canja Murya yace Hajja.....firgit ta buga ihu daga kwance taga haka tunaninta Mala'ika ne ko Aljani,yace kin dade kina kiran mutuwa yau gani nazo nine Mutuwa yanzu zan daukeki,Hajja sai ta fara ihun Kuka tana bada hakuri,Sabeer ya fice da gudu ya boye a dakinsu ganin Hajja zata tara masa jama'a.
   Tun daga wannan rana Hajja bata kara ambatar sunan mutuwa ba.
 
   Abbi cikin su uku kowa yana da daki shi da matarsa,sai na Hajja daban,Yan matan gidan kuwa manya da yara gaba daya daki daya suke gwamitsa wurin su takwas,kowa da shimfidarsa anyi kwanciyar kai da kafa,Haka mazan ma Kowa a daki daya jal manya da yara haka kullum Suke fada da masifa ba ji ba gani ba zaman lfy a junansu sai dambe,Hajja ma ta Bullo da rigimar ta gaji da zaman banza gwara a siyo mata taskira hhhh irin ta tsofaffi da Mazarin kadi tare da Alli zata fara kadi tana murza Mazari tana saka zaren auduga,Khaleel suka dinga dariya tare da cewa anji wuya za a kare a taskira kuma wato yanzu kin yarda kin tsufa har zaki hada Taskira guda ana tauna goro anci goggoro ana kadin Zare,hhhh yaran kowa yana dariya wa Hajja,Hajja anji wuya cewar Meenal sanda ake goge hakora da Cinyar kaji ba a gode Allah ba sai yanzu da ake gogesu da goro,Nan take Hajja ta fashe da kuka amma ko kiran sunan mutuwa ba a ji tayi ba kus kake ji sai hawaye.

    Aayan kuwa shi tuni ya hana Ameer fita kuma kar ya kunna wayarsa yanda su Hajja baza su samu ba,yace sunyi hutun zuwa Office ba me fita ba me shiga sai ya gama Amarcinsa zasu tafi Abuja,Yarima kadai ke zuwa wajensa ko wajen Ma'eesha,Daddy kuwa shi kanshi yanzu hankalinsa yafi kwanciya yafi jin lfy ma a jikinsa amma duk da haka indai Aayan zaije wajensa sai yace ya maida Su Hajja gida sai yace to amma yayi shuru abinsa.
   Aayan ne ya sameni a Bedroom ina karanta Novel a waya yau kwana uku kenan naki yarda Aayan ya kara ko kissing dina ba yanda baiyi ba naki yarda, gefen bed din ya zauna jikinmu na Gogan juna wayar ya karba a hannuna tare da ajiyeta can gefe yana kare min kallo na maita,Kunyace ta kamani duba da kayan dake jikina riga ce me dan fadi me hannun vest iya cibi tsayinta sannan sharashara komai a na gani kamar mataci,sai wando Jean white pencil nasha kyau gashina kamar na Baturiya.
    Hannun Aayan naji na yawo a kirjina yana murzasu,ban hanashi ba sabo da nima wani dadi nake ji sai dai shagwabe fuska da nayi kamar zanyi kuka.





😍😘😍😘
Afwa fans abubuwa kwana biyu ne suke dan min yawa shi yasa zaku ga bana baku pages a kai a kai ba haka na so ba.
❤❤❤❤❤




Typing error ko kuskure ayi hakuri idan an gani.




AsmaBaffa
[1/31, 10:53 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

    KASUWANCI NA





            105-106




By
AsmaBaffa





   ZAINAB ATIKU SALAMA ths page is for u tawajena.













           Shuru nayi sai ma kara gyara masa nayi ina so na hanashi amma bazan iya ba gaskiya,bazan iya shanye wannan shagali ya wuce ni ba banma san sanda na fara mayar masa da martani ba cikin salo da birgewa,muryarsa naji da kyar yana I need u Babyna pls ki yarda a hankali zan miki ba zafi,Yanzu Yamma tayi ka bari sai dare maybe na yarda,no ni ban yarda ba yanzu nake so sai dai idan baza ki bani ba dama tunda ni bakya so na,Haka nace ma bana sonka? to in kina so na ai zaki ji tausayina amma ke ko daya babu a idonki, murmushi nayi sabo da ina sonsa bana son na yi masa laifi ina ji ina gani cike da tsoro nace to ka kara yi kadan amma,yace dan mitsili zan yi,nace to tunanina da gaske dan mitsili din zaiyi,jikinsa na rawa ya fara sarrafani a Fagen sarrafawa sai dai mu sarrafa juna sabo da ta nan ba a bari na a baya sabo da dadi ne ke kwasata kawai nima naji na iya na fara nuna kwarewa ta,a hankali yake bi dani har ya samu Hanyarsa Yanda nake da Niima sai dai a shafa Fatiha, Kai..kai..yau ma da zafi Allah ni bazan yarda ba,Aayan a lokacin yayi nisa kara kankameni yayi ba ta inda zan iya motsi,a hankali yake aikinsa ina ihun Zafi bakinma toshe min yayi da nasa sai Sambatu yake iri iri,in nace ya dagani sai yace dan Mitsili zaiyi sai da ya mugun dadewa sannan ya samu nutsuwa,ya gamsu sosai.

    Kukan Shagwaba nake masa yana ta lallashina tare da rada min dadadan kalamai,yau ma naji jiki a hannunsa,nace aka sake Allah Hijira zanyi na bar garin,Dariya yayi ina zaki koma? Can yankin Mambila sai muyi Hijirar tare kafata kafar matata,Ina shafa kirjinsa nace ai bazan je da kai ba tunda kai zaka jawo nayi Hijira, Do u knw what? Sai ka fada, I love u,i love ur everything,u r so sweet Baby ban ma san yanda zan miki bayanin ba, kwanciya ta na gyara tare da juya masa baya,Juyowa dani yayi tare da cewa wa yace miki ana juyawa me gida baya? Mantawa nayi shi yasa wanka za muyi haka ya daukeni har toilet na Sha gashi sannan mukayi wanka tare da tsarkake jikinmu.
    Sai da muka kwanta har bacci ya kwasheni naji Aayan yana shafani sai Shan albarkatun kirjina yakeyi,a hankali na tsinci muryarsa yace My Mufee pls dan Dis nake Needing,baki na turo kamar zanyi kuka haka dazu kace Dan mitsili yanzu kace Dan Dis Allah akwai zafi in ba so kake wajen ya   samu matsala ba,Insha'allah bazai samu ba dole na hakura ya kara yin na biyu.
    Amma wannan kam kasa hakuri nayi kuka nayi ta barkawa sabo da zafi,na tabbata da ace akwai wasu kusa damu sai sunji irin yanda nake Magiya da kuka,Aayan shi baya gajiya ko kadan Sambatunsa kawai yake yi wanda bai ma san inda yake ba.

     Washe gari ma again da safe kasa tashi nayi sabo ya min raga raga jiya,Shi ya min komai da komai ina jin Brush kawai nayi da kaina sabo da duk kakale kakalena Aayan uban gida nane kamar zai cire makoshi ni ko nace ya bani nayi, har shafa mai tare da sa kaya shi yayi min mukayi sallar Asuba da Azkhar ya kara gyara Bedroom din sannan muka koma bacci sabo da Bala'i kari naji zai nema kawai nayi baccin karya daga haka na gasken ya daukeni,shima yasan idan ya sake nema baiyi adalci ba haka ya danne jarabarsa yayi bacci da kyar.
   Meenat ma yau shuru suka jini sun kasa gane kaina kwana hudun din nan,yanzu basa jirana ma Kansu suke mawa girki in na fito aci damu idan bana ci su dafa min wanda muke so ni da Aayan,Ameer kadai suke kira suci abinsu.
    Suna kitchen duk kusan Meenat ce ta gama komai Ma'eesha waya takeyi da Yarima da safen nan tana yanga tare da kashe murya.
    Hello Dear cewar Ma'eesha,yeah ina jinka,Yarima ya wani yi juyi saman Bed tare da cewa am just missing u,Maeesha tayi wani murmushin jin dadi Miss u much more Dear,me kikeyi yanzu,Ina kitchen,wow shi yasa naji kamshi cewar Yarima, uhmm kai ina wani kamshi a girkina na yan koyo,Ba wani yar koyo ai Ameer yace duk kun iya girki kinga na huta.
   Dariya kawai Ma'eesha tayi sannan yace ltr,ok Allah ya kaimu sukayi Sallama lokacin Meenat ta gama komai har gyaran kitchen.
  Tace gashi nan Ma'eesha ki shirya Dining ni kuma bari nayi wanka,wa zakiwa wanka yanzu ki Bari muci sai kiyi ke wai ko da saurayin ki a gidan nan ne?bakya ko fitowa Palo sai kin yi kwalliya.
    Meenat jin sharrin da Ma'eesha zata kulla mata ta fasa zuwa tayi wankan,doguwar rigar ta bari Blue a jikinta da dan siririn gyalenta tace muje to mu karya.

    Sun Zauna Dining kenan sai ga Ameer yaci uwar wanka kamar zaije wajen Daurin aure shadda light blue tasha aiki dinkin kamar a jikinsa aka dinka das das dashi sai kamshi yake bulbulawa yayi wani Fresh sumarsa me yawa sai sheki take ga gemu na matasa dan firit tare da saje kadan.
   Ma'eesha tayi dariya tace gaskiya yau kayi fa, kafi ko yaushe kyau amma Yarima ya wuce ka,Meenat kuwa na kallon Ameer sai ko tayi sauri ta tsuguna a kasan Dining ta buya gyalenta tasa tana ta goge fuskarta wai kar aga maiko, Ameer yace Yarima Din me yarinya Bobonki bai kaini haske ba,amma dai baza kace baki ko chocolate bane ka sani dai ga Hanci kamar biro dan gayu na karshe,Dariya Ameer yayi yace ke kika sani kuma wannan.
   Kamar naga Meenat a nan Ameer ya furta,Maeesha tace tana kasan Dining yau aljanunta ne suka motsa tsoron mutane take ji,daga nace wa zata yiwa kwalliya da safe shine taji tsoro na ta fasa fita,Yanzu kuma tana ganinka shine ta buya kasan Nan wai tsoronka take ji,Aljanun tsoro ne suka shigeta,Dariya Ameer yayi tare da tsugunuwa kasa ya leka sai ko Meenat ta kara yin kasa tare da boye fuskarta,yace yau sai naga me kike boyewa yayi kamar zai kamota ta fito da rarrafe ta Mike da sauri ta koma Bedroom,Meenat ta saba da kwalliya idan bata yi ba bata Jin dadin rayuwarta,wanka tayi ta shirya cikin Doguwar rigar Lace tayi kyau matuka,sai lokacin ta fito suna ta cin abincin su ma sannan itama tazo ta zuba nata ta fara ci,Ameer ya kalleta ya kara kallonta sannan yace baki gaisheni ba yau,Ina kwana?ka tashi lfy? Yace lfy lau, u?tace lfy yace good kin kyautawa kanki da badan haka ba yau da sai kin fadawa yan garinku,dariya suka yi gaba daya.

    Meenat yau ta fita zuwa Islamiyya schl dinsu ta kai wani kudi tana kan hanyarta ta dawowa  gida da yamma wani Saurayin matashi wanda bashi da makusa ta ko ina cikin dalleliyar motarsa ya dinga bin Meenat ta saurareshi amma taki sai da suka zo har gida,Matashin ya firgita da ganin irin wannan katafaren gida,A ransa yace da gani dama kalar masu kudi ce, haka yake ta kallon gidan da Meenat ta shiga da yake Islamiyyar ba nisa da nan gidan,Me mota dai haka yayi shahada ya tura daya daga cikin ma'aikatan gidan cewar dan Allah ya kira masa waccen yarinyar,Me gadi yace Meenat sunanta ai bari a fada mata,Ina Palo muna tare da Ma'eesha dake chat sai Ameer,Me gadi yayi Sallama tare da cewa Meenat kinyi bako yana waje wani me jar mota,Nasan wannan me nacin ne,Ameer yace kina ji fa Kije maybe yayan Tsito ne,wani haushin Ameer Meenat taji da ta rasa gane na mene kawai tace kace ina zuwa, Meenat ta Mike ta shiga daki Don ta kara dan gyarawa ta fita,Kafin ta fito Ameer ya fita wajen Saurayin kawai yace yayi hakuri an kawo kudin auren Meenat shi Yayanta ne, saurayi yace ba komai Allah tabbatar da alkhairi ya shiga motarsa ya tafi yana cike da jin haushin Ameer ko karya ma yakeyi oho a ransa yace suje da yarsu dan Ubansu an fasa aura wannan abu na rufawa juna asiri.

    Ameer ya koma inda ya fito ya zauna yayi mursisi,Sai ga Meenat ta fito anci uban gayu kamar zata je Dinner Ameer yana boye dariyarsa Meenat ta wuceshi da yanga tare da Galla masa harara dan ta ganeshi dariya yake mata,ta fita tana kunkuni tace Sa'idini kawai,Sai da taje taga wayam ba kowa,har waje ta leka,Me gadi yace ranki ya dade ya tafi yarsa ina daki naji karar motarsa ya figeta a fusace,ko dan kin dade ne yayi fushi,su kansu Masu aikin basu ga sanda Ameer ya kori bakon ba,Meenat a ranta tace yayiwa kansa, gaba ta kaini tuntuben me choge.

    Tana shiga Palo ta zauna gefen Ameer, har ya tafi? Meenat tace ae mun danyi magana sama sama,Ameer yace da Alama kina sonsa? Meenat tayi banza dashi tana latsa waya,sai daga baya tace ya Ameer dan Allah ka kaini gidan kawata da yamma mana kaji? Driver dinku me yakeyi? Sis Mufee tace yaje ya duba Iyalinsa can kauye sai mun koma hutun schl zai dawo,Ya Aayan ya hanamu fita sai nan da wani lokaci ki Bari idan mun tambayeshi ko zai yarda sai na kaiki.
   Ok to kana gani tun safe sunki fitowa abincin ma Shi yazo ya daukar musu na kasa gane meke damun Mufee, Aayan kuma sai nishadi yake kullum cikin farin ciki sai wani kiba da kyau ma yake karawa,Ameer baka fahimci komai ba? Ameer shi yasan dalilin komai Aayan warkewa yayi shi yasa yanzu angwanci yake yi su Meenat basu gane ba. Kallon Meenat Ameer yayi tare da cewa ki Bari kije ki tambayeta da kanki kiji tunda ke bakya gani ki kyale sai kinji dalili.

    Aayan ne da Misalin 5pm ya shirya tsab ya fito zaije wurin Daddy ni kuma na danji sauki haka na gyara toilet kal kal tare da Bedroom din yana kamshi ta ko ina,nayi wanka da ruwa me Zafi na shirya cikin kaya marasa nauyi,Meenat ce da Ma'eesha suka shigo da Sallama,Lokacin ina Jikin Mirror ina fesa turaruka,Maeesha tace kinyi kyau Mufeeda,Tnx ya kuke? Lfy sis bakya fitowa kamar baki da lfy muke ganinki Meenat ta furta,Wani kuka ne ya taho min sabo da Aayan kullum baya daga min kafa ko kadan na damu gaba daya yaki bari na dan warke ma,Meenat tace subhanallah me akayi miki kuma kuka? a jikin mirror na kifa kaina ina ta kuka da shesheka suna kallona duk sun shiga damuwa.

   Dan Allah ki fada mana mene ne?meke damun ki?me ya faru? Ina hawaye nace Ina so na fada muku amma Allah ya haramta ba kyau dole bazan fada ba wai sai dai nayi shuru, Meenat tace to wai tafiyarki ce duk ta canja mu bamu gane ba,nace Aayan ne yake ta abu daya ni wlh bazan iya ba gwara ayi asarar kudin gyaran jikin,ni da nasan hakane bazan yi gyaran ba,Sai yanzu Su Meenat suka gane me yake damuna,Dariya sukayi tare da cewa uhm wannan kuma tsakaninku ne wannan fadan ba ruwanmu babu me iya miki maganin abun sai dai muce aci gaba da hakuri kafin ki saba muji kinfi ma Aayan din maita suna ta dariya,nace
    Dan uwarku Ku fitar min a daki tunda dariya kuka zo yi min,Ficewa sukayi suna kuskus.

    Hajja ce take rera wakarta tana gaguda kwalli a idonta tana Yareye iyee nanaye...Ayyeee riyalle duniya.....Haneefa dake kusa da ita tayi lamo a gefe sai yanzu take tunanin aure,da can me yasa bata samu cikin samarin ta masu kudi ta fitar da miji an mata aure ba ta zauna tace ita karatu sai tayi Masters, yanzu ko mijin ma ta fito dashi wa zai mata kayan daki? Mikewa tayi ta bar wajen Hajja ta koma dakinsu inda ta tarar da Su Meenal tare dasu Sajeeda sunyi jugum suna tunani,Kallonsu tayi tace ya akayi ne yan mata? Meenal tace hmm ke dai bari Wai yanzu Abbi yazo duk mu cire layin wayar mu mu basu harda masu computer kowa ya kawo tasa wai za a siyar a siya mana kana na Irin su Dagani Gara, harda wata waya Dagani Gara kuma? Ae mana tana nan wata me uban nauyi yar China ko Camera babu,Yanzu dan danna wayar ma da muke tana ebe mana kewa karbesu za ayi kwarai kuwa dan har an kwace ta yan mazan gidan nan tare da Sauran yara kaf za a siyo kayan abinci me yawa wanda zai dan Dade ana ci,Abbi kullum suna fita neman aiki duk tsufansu amma ba a dacewa.

    Khaleel ne ya fito daga wanka ko Vaseline babu a dakinsu dakin su Haneefa ya shigo da gajeren wandonsa kai Ku miko min Vaseline na labta a jikina,Sajeeda tace kamarka da shafa Vaseline,to ya zanyi kawai a bani na labta haka,kune ance Ku samu aiki kunki ai da mun huta,Khaleel yace baki da hankali in mutum yayi aikin ma ai sai abinda Hajja tace wlh akan nayi wannan tsohuwar ta Dameni gwara na bar gidan nan na koma gidan frnd dina. Haneefa suna dariya tace nayi mamaki da yanzu kowa baya ragawa Hajja to ko dama wai tsafin nata can gidan ta binne su ne? Ita ta sani ai gashi tun ba a je ko ina ba sun jawo mana muna gane kurenmu gaba daya me yafi zaman lfy dadi Ameer tun wuri ya shiryu gashi ya huta Allah sai ya zareshi a cikin mu suka koreshi Ashe gata suka yi masa aikin banza ni dama ni suka kora wlh da wannan wahalar,Khaleel sai masifa yakeyi yana shafa mansa a dakin ya gama sannan yace to Ku ban aron Cumb,Meenal tace Cumb daya tal a gidan nan na Umma da ta zo dashi a jakarta shi yake yawo a gidan nan kowa dashi yake taje kansa mata da maza bari na karbo ma, yanzu wannan Sumar dana tara ta common Cumb ba bu bare man gashi da sauran kayan gyaranta ai kamar mahaukaci ma zan dawo soon zanje wajen me aski dole na sauketa, Sajeeda tana dariya tace haba gayu tana ma kyau, gyara ne yasa yanzu da babu zaki gani very soon dole ina ji ina gani na sauke ta, gaskiya Aayan baida mutunci Allah wadaran sa daya kore mu akan shegiyar Mufeedan nan,

Khaleel yace ah lallai baku fara nadama ba me tayi muku yanda haka kawai muke biyewa su Abbi da Hajja muka sasu a gaba musamman Ku,Aayan ko wacce shara shi ake turawa,tun bai San kasar nan ba Hajja ke tura masa asiri tun muna yara har muka girma,ki tuna takura da akayi masa shi da Ubansa,kalli matayen da aka sa ya aura kuma aka sa ya sakesu,kalli irin yanda ake nuna masa shi da Ubansa ko makiyinka ai baka yiwa haka ba bare dan Uwa na jini,Allah wadaran halin Hajja me zuciya kamar ta fir'auna danka da jikanka ka jefa su a wani Hali duk sabo da son kudi.

    To mu ba irinku bane Sajeeda shekaran jiya dukkanmu Maza muka zauna muka tace tare da tankada mukayi rairayi munyi lissafi ya bulle dai dai dan haka mu Maza duk mun tuba wlh Allah ya ganar damu gaskiya kuma Aayan bashi da laifi yama yi kokari yayi biyayya,yana da damar da zai tattara su koma kasarsu amma ya zauna damu yana Shan bakin ciki,to mu dai yanzu ma Istingifari mukeyi ko mu nan ance miki Hajja haka zata barmu ba tare da ta asirce kowa ba, tunda tayiwa danta da ta haifa wa zata kyale kuma Uwa fa guda, yanzu kalli inda su Mommy suke mata rashin kunya kin San kuwa asirinta ne yake ta karyewa zai tonu,gamu dan muma mun gano gaskiya,da ai bamu gane ba musamman Ku mata masu karamar kwakwalwa,mu dai sai Aayan da Mufeeda,Allah ya bar mana Anty Mufee sai Mufee.

    Sajeeda tace kato da kai kana kiran wata yarinya karama da Anty anji kunya,ai ke bakin cikin naki harda Hassada cewar Khaleel kinga tafi ki kyau,ta auri Aayan sannan Ameer ma maybe Kanwarta zai aura,Me yasa yanzu samarin naki yan iska basa zuwa? Duk sun gujeki wlh tun wuri ki gane gaskiya,Haneefa tana ji da sauran mata duk sunyi shuru Khaleel ya gogesu tas ya kara gaba abinsa.

    Gaba daya sun hallara a Palo ana cin shinkafa dafa duka tasha manja tana tiri tiri sun saba da cin girkin yan gayu duk sai suka ji wannan ba dadi kowa turawa yake da hakuri,Abbi mamakinsa daya shine dare daya suka koma talakawa me yasa basu yi planning sun mallaki kadarori ba,a ransa ya tuna da fa talakawa ne su sai rufin asiri kuma aka samu Daddy ya basu aiki suka koma gidansa da zama,da sun San haka ne gwara a ginawa kowa gidansa daban da yanzu ba ruwansu,duk kudin kuma da suke samu a wajen bokaye suke karewa aikinsu kenan,kawai kudi suke kwasa a Companies suna abinda suke so basa tunanin su tattala sabo da gaba sai burin kawai su kwace Dukiyar Aayan data Daddy,Hajja kuwa ko a jikinta bata da niyyar tuba sai ma kwantar da hankalinta da tayi tasan dole Daddy zai nemeta ta dawo dasu dole su dora daga inda suka tsaya.
    Meenal ce a palon tace duniya budurwar wawa,Abbi ya harareta tayi shuru,Abbi sani kuwa kallon Khaleel yayi tare da cewa dan ubanka baza ku aske Sumar nan ba ko sai kace kan mahaukata,Khaleel yace haba Abbi yawa kuke ba kudi ba komai me kuke so yan mata su gani a kanmu mu birgesu dashi yar wayar duk kun kwace kuma ya kuke so muyi shike nan mu baza muyi nishadi ba kenan, Mujaheed yace ni wlh aka sake barin gidan nan zanyi me ake min sai fada safe da rana da dare.
   Hajja ta Galla musu Harara ba wanda ya kulata wanda ta tabbata da ace da ne da tuni sun bata hakuri,Hawaye Hajja ta fara tare da cewa an rainani bani da iko da kowa,shuru ba wanda yace mata kala,ta mike tsaye tare da cewa ai bani na dora muku talaucin ba da zaku tsaneni me nayi muku? Wlh in na gaji bar muku gidan zanyi,sai nayi magana ayi Banza dani wata tsiyar nayi muku da za a dauki karan tsana a dora min,to duk Wanda ya fasa baya kaunar uwarsa da ubansa,Abbi yace me akayi miki kuma wai? Gasu nan bani da iko nayi magana sai cin mutunci to wlh zan bar muku gidan nan, Hajja ta fashe da kuka, yaran gaba daya tsaki suka ja tare da mikewa daya bayan daya suka bar palon su Abbi ne ke bata hakuri.

    Zaune nake a palon Sama na Aayan,naci uban kwalliya cikin English Gown iya cinya nayi kyau,Yau na samu Salama Da kyar Aayan ya fita zuwa wajen Yarima yana nemansa yace bazai je ba da kyar na lallabashi sabo da ya Dameni da fitina ko kasa bana sauka sai dai su Meenat ke yin komai kullum sai ya sani kuka yace zan saba ni dai yau 1wk kenan ban saba ba.
  Abin mamaki 40mnt sai gashi naji sallamarsa har ya dawo, duk da damuna da Aayan yakeyi bana ganin laifinsa kuma bana jin ya isheni ko naji haushinsa Sam bana jin hakan sabo da sonsa da yayi min yawa bana jin akwai abinda zai nema na hanashi a duniya,Da ya fita ma duk sai naji ba dadi gidan amma jin sallamarsa wani Sanyi da dadi ya ratsani har na kasa boye farin cikina,. Tsayawa yayi yana kare min kallo yanda yaga na wani yi mugun kyau kamar a sace ni,murmushin da nasan yana kara min kyau na sakar masa tare da walwali da Idona cike da jan hankali ina daga zaune na bude masa Hannu ya kuwa karaso a hankali tare da shigewa jikina a hankali na mayar da hannuna tare da rungumeshi gwiwoyinsa suna kasa,Hannayena nasa tare da tallafo fuskarsa muka hada Ido nace sannu da zuwa kana na shiga tsotsar bakinsa kamar na samu Alawa me dadin gaske.
    Hannu na daya na sa a cikinsa nace muji ko kana jin yunwa dariya yayi sabo da yanda nayi kamar irin dana din nan, ina Sonki My Queen ya furta yana dariya sabo da yanda nake masa cakulkuli a cikinsa, mikewa yayi tare da kwanciya saman doguwar kujera ya daura kansa a saman lumtsumemiyar cinyata wacce ke sheki da santsi ga tsoka da girma sai kamshi takeyi ta ko ina,Yar rigar dama guntuwa ce,Hannu yasa ya wara cinyata wai bude min Kingdom din taki na gani ya warke jiya fa sau daya kika bani tal, shagwaba na fara

nace Allah a'a amma ai ya dace ka dinga danne maitarka kullum ba fashi ka bari na warke sai na baka amma kullum kace Dan Dis,gobe kace dan Mitsili,gata kace kadan,nasan yau kuma cewa zakayi....kafin na karasa yace Dan Kucili, dariya mukeyi gaba daya yace tunda nake koyan hausa in baki labari wannan words din ne suke bani Wahala da dariya,abin dariya,wai Dan Kucili,dan mitsili,dan dis,dan kadan,dan Kis,Dariya mukeyi nace ai har dan Kucilili ana cewa,yana dariya yace to na yau Dan Kucili zanyi,nace naki sai na warke 1wk sai next wk,Ido ya zaro waje tare da cewa kawai mutuwa kike so nayi ni bazan iya ba,Ina wasa da gashinsa nace gidanmu na gado wai ya za ayi dashi ne? Aayan yace ki Bari kawai a gyarashi a sake sabon Gini sai a sa yan haya mu jira muji nan gaba ko Abbanku yana da rai ko ya rasu dole bincike za ayi first,nace to Allah ya kaimu,Ameen yace sai me kuma?nace uhm...uhm.. da dai zan fada kar kace ina da son kudi ne,fadi mana idan ma kina so waye baya son kudi kuma ai kudin mijinki kije so ko? Kai na daga ae,Lefe ni fa ba ayi min ba,dariya yayi tare da cewa duk kayanki? Ai wannan kawai siya mana kayi kuma ma ai har su Meenat lefe kuwa iya Amarya akewa, Ki kwantar da hankalinki idan ma har biki kike so sai ayi miki,nace a'a ni bana son biki ko wata Dinner kawai lefe nake so sannan ayi min Kamu, mene kamu kuma? Kamu da akewa Amarya idan ana gobe za a daura mata aure a sata a lalle,to ai gwara Dinner dashi,nace a'a ni duk wannan basa birgeni kawai Kamu za ayi min nima shine yake birgeni a duniya bazai yuwu ace ni har abada baza ayi min ba,kullum burina naga anyi min Kamu a biki sai kuma haka ta faru to duk da haka ban makara ba shi yasa nake jin tsoro kar na samu ciki ba ayi min Kamu ba,idan na haihu ai magana ta kare kuma na haifi dan dakan Kuka,Dariya Aayan yake tayi tare da cewa lallai har yau Kuruciya na nan,Dan dakan kuka kuma shege fa kenan,Dariya nayi nace ae ayi min Kamu ni dai ko idan na haihu nace dan dakan Kuka na haifo.

   Jibi Birthday na sai a hada da kamuna,Waye zaiyi Kamun to? Zakiyi Birthday party ne? Nace a'a ba wanda zan gayyata Meenat da Ma'eesha sun isa su sani a lalle,ga Ameer da kai kuma Ango kun isa shike nan,Aayan yau dariyar Mufee kamar ta kasheshi da shirmena,yace to sai na gayyato Yarima ma yazo ayi dashi ko,nace to Allah ya kaimu,Aayan ya kalleni yace Amarya an kusa saki a lalle,nace haka yake next wk zamu koma schl ma,Nan Aayan ya hade rai yana jin haushin schl shike nan bazai dinga gani na ba sai yamma,yace a bari sai nan da 2wks ki koma kinga kin kara 1wk kenan ko? Nace ae Allah ya kaimu,Bazan iya yini ban ganki kusa dani ba, schl ta wani dawo ya furta tare da sauke ajiyar zuciya .

    Na kalleshi nima nayi shuru sabo da bana so mu rabu ko na 1mnt,hannunsa naji ya tura cikin rigata yana Murza kirjina, sakon dai dai yake shigata babu gargada ban san sanda na shiga Maida masa da martani ba,daukana yayi cak yana rada min dan Kucili za a bani,banyi musu ba sabo da bana son na bata masa kuma kar ma yace na fiye Complain ba dama miji yace zaiyi wani abu sai mace ta fara Complain sai ki ga yana jin tsoron neman hakkinsa yana danne sha'awarsa sabo da yawan Complain,ko miji ya dinga zargin kansa Shi ba namiji bane ko bai iya komai ba baya sa matarsa taji dadi dashi sai kiga duk ya shiga damuwa da tunani baya birge matarsa shi.
 
    Meenat ce zaune Saman sofa tana Shan ice cream dinta tana kallon American film a Tv,Ameer ya shigo ya zauna gefenta shima sanye da riga me gajeren hannu da 3qtr sai kamshi yake yi,yace San min na Sha Ice cream din,Dazu ya Aayan ya kawo mana da yawa yana fridge,bana iya Sha da daya ni kawai in zaki bani a naki ki bani,Meenat ta turo baki haka ta ebo a spoon tace duk zaka rage min quantity ni ungo ni karbi ya bude baki kuwa Meenat ta zuba masa ya shanye tana Sha tana bashi sai da suka shanye robar guda sannan Meenat tace kaji dadi hankalinka ya kwanta mun shanye da kai,karo wani mu shanye again ,au dama kana iya Sha da yawa dan kar nasha nayi kiba kazo ka raba ni dashi, Ma'eesha ce ta cakare ta fito kamar zata je Dinner,Meenat kawai sai ta hade rai tam, Ma'eesha tace Sis zanje wurin Yarima yana palon baki,Meenat sai lokacin ta saki ranta tace to maza ayi sauri a dawo lfy ki gaisheshi..me Meenat ke nufi da fushinta da farko? oho.

    Kallon film dinsu suke yi sai katsam budurwa da saurayi suka fara kissing din juna a haukace,Americans ba kunya sai gashi ana tube kaya za a fara Sex,Meenat duk kunya ta rufe ta da sauri ta dauki remote zata canja Chanel,Ameer yace mene haka sai da kallo ya dauko dadi ai nan shine ainihin film din Horror movie ne ki tsaya ki gani abinda zai faru mana,Meenat tace ni ba yar Iska bace tana Satar kallon Tv kuma,tace haka kawai mu dan Allah ka kawo remote a canja ka wani kwace basai mutum zai kalla ba, Meenat taji ana shidewa a Tv Ameer ya ba da Amanna yana kallo ta dan kallo ta dauke kai tace yan iska kawai sai taga Masoya sun koma abin tsoro dama Horror film ne sai suka koma fada da zako zako hakora,mace ta bude bakinta wommm...Sai da Meenat ta buga kara tare da fadawa jikin Ameer, Ameer yana Jinta dan munafuncin Sa sai yace ai film din nan abin tsoronsa yayi yawa yanzu zaki ga ma sun koma kamar Dujal ance har mafarkinsu akeyi, na gani a BBC wani Horror rannan ana kallo a wani gida ya fito daga TV ya shiga jikin matar kin San Aljanune, Meenat ta kara kankameshi ta boye fuskarta a jikinsa taki dagowa,Ameer yana jin dadi a ransa a fili yaci gaba da cewa ai ba a barin irinku su kalli wannan sabo da idan suka ganku sukan iya Faso TV suzo wajenku,ni tsoro nake jiye miki dan yanzu zan fita sai ke daya bari na Canja Chanel,ya canja Chanel ya fara kamar zai Mike Meenat ta rikeshi kam ta makale a jikinsa tana roko Karya tafi,yace to sai dai ki dakko Ice cream ki dinga bani a baki sai na zauna idan ba haka ba tafiya zanyi.
   Da sauri Meenat ta dakko tace bari na baka idan Ma'eesha ta dawo sai ka tafi kawai,nan ta zauna damfamfam tana bawa Ameer Ice cream a baki yana sha yana latsa wayarsa ya Zama dan gata,a ransa yace wlh aure zance Aayan ya min kwana nan na huta nima.




AsmaBaffa
[2/2, 12:41 AM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

    KASUWANCI NA





         107-108







Official





By
AsmaBaffa






HOUSE OF HAUSA NOVEL,TASKAR SURAYYARHMS,TASKAR FIDDAUSI SODANGI,UWARGIDA,ASMABAFFA FANS CLUB gaba dayanku gps na gode da Sharhi da kuke yawan yi kunfi kowa shi yasa wannan page naku ne.

    Tnx etc da ake yawan fada basu damu Writers ba anfi son Sharhi Readers Ku daure kuci gaba munfi jin dadin typing da posting.Gp dina naga ana sanya da Sharhi ko an fara gajiya ne da Novel din a tafi Hutu?😍😍😍 Love u all fans.











     Ameer yana tunani ya zaiyi ma shima yayi auren nan ya huta,kwanciya yayi saman 3seater tare da Jan eriyar tunaninsa ya shiga nazari,Meenat na gefensa ta gama bashi Ice cream tana waya da kawarta ta schl,yawancin yan makaranta musamman yan Boarding schl idan suka hadu da kawayensu zage zage zaka ji yana tashi kawai ana shegiyar ya gari etc,yanzu Meenat ita da tayi Day schl ma wannan tsabiyar ta zauna mata Ameer na gefe ta daga waya kawarta tana dagawa Ameer yaji kawar ta duro ashar, Meenat tana dariya tace amma dai Allah ya tsine miki,Shegiya ai baki da mutunci,Kawar tace dan ubanki ke Hafsat Salisu ciki ne da ita daga biki, Meenat tace ke Dan Allah? ke Amai take yi,Meenat tace ai Hafsat Salisu matsiyaciya ce,ai Allah yayi yar iska a nan wajen,Kawar Meenat tace hmm ke dan uwarki Aisha Balarabe wai aure zatayi shegiya, Meenat tace ai tsinanniya ce Aisha ta kirki zamu je gidansu ai soon, duk wayar tasu a zage zage ta kare har suka gama wai nan hira aka Sha kuma sai gulmar frnds,Abinda yan mata keyi kenan ai bin diddigin kawaye ana munafunci wance taci gaba ko baya taci,taci gaba da karatu ko a'a,anyi mata aure dadi take Sha ko wahala,ya ta koma ya gidansu yake aikin kenan sa ido,haka ma'aikata ma burinsu suga a ina abokiyar aikinsu take kwana ya gidansu ko gidan mijinta ayi ta gulmarta,duk iyayinta Ashe kaza kaza, frnds cikin su idan ba wata a kusa sai ayi ta gulmarta kema kina tashi ayi taki gulmar aikin kenan ya kamata ayi gyara mutum yaji da kansa ma matsalarsa ta ishe shi,amma sai abinda ba ruwanka zaka damu kanka.

    Ameer ya kalli Meenat yace yanzu wannan wayar taku mene sunanta mene amfaninta? Gulma ko zage zage? Shuru Meenat tayi,abinda kika koyo kenan a schl din taki zagi da gulma,ki daina ba kyau kawai kuyi ta zagin juna sannan da hirar wasu kuna zagi wannan bai kamata ba babu tarbiyya a ciki,Last warning na miki wannan idan na kara Jin wannan zage zagen am serious sai na Zaneki a gidan nan,Meenat baki bude take kallonsa da mamaki yanda ya zage yake ta mata masifa ba ji ba gani,kuma ba alamar wasa a idonsa ita dai tayi shuru.

   Lokacin munzo sakkowa ni da Aayan muka ji wayar da Meenat ke yi har ta gama,haka muna tsaye Ameer ya fara mata fada,naji dadi kuma ya birgeni,yau na tabbatar Ameer yana da hankali sosai kuma yasan me yake,kuma na kara yarda da zancen Aayan cewar Ameer ya tuba ya canja halayensa sabo da ace da ne ba ruwansa.
   Karasa sakkowa mukayi nace Weldon Ameer na gode haka ake so idan Zama ya hada ka tare da mutum yayi ba daidai ba ka gaya masa gaskiya na gode,Ke kuma Meenat haka Ammah ta bamu tarbiyya?Ni ban sanki da haka ba wlh,Meenat zatayi magana nace dalla rufe min baki Banza ko kunya bakya ji,Aayan yace to fadan ai ya isa haka taji ta daina ko Kanwata? Meenat tace ae.

     Zama Aayan yayi tare da cewa Meenat ku shirya gobe akwai Kamun Amarya a gidan nan,Meenat tace wace Haneefa ce ko Sajeeda ko a cikin su Meenal ne? Aayan yace My wife Mufeeda,tace Kamu take so ayi mata kamar ko wacce Amarya, Meenat tace tabara ce kawai da samun waje kaine ma kake biye mata,ni kuwa nace ae anji din ina ruwanki,Meenat tace wlh ba wani Kamu da za ayi miki ya wuceki sai kallo,Ameer yace ina ruwanki? Ma'eesha ta shigo itama dariya tayi tare da cewa bata lokaci ki Bari a hada da sunan Baby idan kin haihu a kama ki,Haka duka suka ki yarda dole Mufee sai hakura nayi nace Birthday din ma na fasa shiryawa a gidan,Aayan yace to gobe Ku shirya akwai surprise a gidan nan kuma gift ne na wife dina, amma kar wacce tace zata ji tsoro,muka ce to Allah ya kaimu.

    Washe gari mun gama shiri muna jiran Surprise na Aayan,Ameer ma yace baza a barshi a baya ba,5pm dai dai sai ga Aayan ya shigo tare da securities dauke da akwatuna ana shigowa dasu sunfi guda Ashirin,baki muka bude muna kallo aka gama jere su kaf suka fita, sallamar Yarima Bobo muka ji tare da Mace dattijuwa a bayansa amma ta rufe fuskarta da Mayafi sai dai da ganinta Hutu da jin dadi ya ratsata, gashi kafafunta da hannayenta da muke gani fara ce amma ba kar ba sai sheki takeyi,wani lace ne a jikinta na alfarma da gani yar gayu ce,sai kamshi takeyi, Doctor din dake Kula da Ammah kafin ta rasu muka gani, Uwata zauna ga kujera cewar Aayan,mamaki ya rufeni wai uwarsa,to wai wace ne haka,dattijuwar ce muka ji tana kuka amma kamar mun San muryarta,a hankali ta bude mayafinta tare da Cewa Mufeeda ta,zo nan Mufee ta,Meenat Ma'eesha nice fa Ammanku,Ammah ce,nan take muka kalleta sosai ba Shakka Ammah ce ta Sha Hutu,to ita bata rasu ba,nan tsoro ya kama mu na tashi da gudu ina fatalwa...fatalwa....Meenat ma suka Mike tare da rufa min baya muka fada Bedroom tare da boyewa,daga su Yarima har Ammah dariya sukeyi,Haka ma Ameer duk da bai Santa ba,Qur'ani na dauka,Meenat ta dauki carbi,Maeesha ta fara Rabbana atina muna ta yi kamar makarantar allo,tafiya muka ji za a bude kofar muka kara Volume din muryarmu ina Yaseen....Meenat na Lahaula Wala quwwata illabillah,
   Aayan ne ya shigo aiko muka manne kanmu waje daya,yace baku da hankali wai Ammah taku ce bafa mutuwa tayi ba,idan fatalwa ce taya zaku ganmu da ita,dama ba mutuwa tayi ba turai muka kaita akayi mata magani,shine abinda nake ta cewa zan baki wanda yafi miki ko mene a rayuwa,ita ce gift din tawa,surprise dina kenan,Mufee tace kuji haka kawai munga gawarta kiri kiri kuce waye waye, wlh Allah bata mutu ba Ammah ce kuzo muje Yarima zai muku bayani.
   Da kyar Aayan ya lallaba mu muka fito,amma sai buya mukeyi a bayansa na manne fuskata a jikinsa Meenat kuma taja rigata ta rikeni,Maeesha kuwa da tafin hannu ta rufe idonta.

     Har Palo muka zauna can nesa inda ba ruwanmu da Ammah,Ammah mamaki takeyi Ashe duk son da kakewa mutum ya mutu kana ihun Kuka da ace zai dawo kowa gudunka zaiyi bazai Zauna da kai ba,Allah me iko,Muryar Yarima muka ji yace a bude taro da Addua Ameer,Ameer  Ashe Malam ne yanda ya dinga zazzaga addua ba a magana.
    Yarima yace Mufeeda kece Babba ya dace Ku bamu hankalinku,Alhmdllh kamar yanda kuka gani Ammah ce taku ba mutuwa tayi ba kuna mamaki sabo da kunga gawarta a kwance,to wannan ba shirin kowa bane face nawa,idan baza ki manta ba lokacin da akayi aurenki da Aayan ya tafi bai kara waiwayonki ba,ko gaisuwa bai miki ba,kuma zaki tuna da kika ce masa Ammah ta rasu ko damuwa baiyi ba,sannan nace nan gaba idan kika ji rawar dana taka a aurenki da Aayan har kyauta sai kin min,nace ae anyi haka duka.
   Zakituna me Daddyn Aayan ya fada miki cewar labarinki da Aayan ya bashi shine yasa yace dole sai ya aureki ko? Nace ae haka ne.

    To lokacin da Aayan ya sameni da Zancen ni na kara cewa kin dace kuwa ya aureki yace shi bai yarda da tarbiyarki ba kuma da alama kina da son kudi,baki sani ba sai da muka dinga bibiyar rayuwarki sabo da ba auren mutum haka kawai shi yasa ake so har kullum ace mutum ya Zama na gari sabo da irin wannan kuma alhmdllh bamu samu wani mummunan Hali naki ba sai wanda ba a rasa ba wanda kowanne dan Adam yana da aibu ko yaya ne bazai yuwu ace 100% kake ba,nace ae, idan munzo miki da zancen ba lallai ki yarda ba a wancen lokacin,kuma lokacin kin kawo bukatar taimako na aikin Ammah idan muka ce gashi gashi zaki ce ba dan Allah muka zo ba,kuma lokacin Aayan baya son wani aure umarni kawai yabi,shine nace mu bari sai mun kai Mahaifiyarku asibiti tunda ba ranga ranga take ba sai mu fada mata muji,bayan an kaita likitan yace Ku fita za a duba ta lokacin muna Office din a can ciki,a nan muka sameta da maganar,Tayi farin ciki kuma tayi Naam,amma tace mana ko da ta rasu ga Amanar yaranta nan Aayan ya rikesu,kuma mun karba,sai tace kina da wani Hali daya wanda bata Sonki dashi Aayan yayi kokari ya canja ki,nan tace mana ke akwai son kudi bata so abin yayi nisa ya kaiki ga halaka duk da cewa tasan talauci da nauyin dake kanki yasa wannan halin ya shige ki.

    Tace amma baza ki canja ba sai in kinsan bata raye sannan Zama ki yarda ayi auren,nan ta shirya mana dabara,Ammah ce tayi magana tace kwarai Mufeeda nice na shirya musu komai sabo da ki fara koyon Darasi a duniya ki san cewa Kudi ba shine komai ba,duk abinda Allah ya tsara shi zai faru,sai karfin addua kan sawa Allah ya canja,ina Sonki fiye da komai a duniya shi yasa Nace suce miki an farkeni baza a dinke ni ba sai kin yarda anyi aure nasan wannan zai sa ki yarda ayi miki auren sabo da Yarima ya bani Labarin Aayan kaf a asibitin,kuma naji tausayinsa,na yarda yaron kirki ne zai iya rike min ke da Amana,kuma naji kina jin tsoronsa shine ya dakeki kika min karya kika ce kwalabati kika fada,shine ya daukeki ya hukunta ki kika ce min kina gidan kawarki neman taimako sabo da kar hankalina ya tashi,to Mufee kin yarda kuma kinyi abinda nake zatonki wato dangina da dangin Mahaifinki sun daura miki aure,sun sani kuma makwafta sun sani,Alhmdllh an baki sadaki kin taho da burin Ammah dinki dole ta tashi sabo da tuna ninki kudi da aikin asibiti shi zai sa na rayu ba Allah ba,ya kika ji da kika ga basuyi tasiri ba na rasu a lokacin kinga hukuncin Allah,Meenat baki manta ba nace muku naji a jikina ta hadu da Alkhairi kuma na bar muku wasiyya Ku bata ko? Meenat tace ae kuma mun fada mata ashe dama kin San komai duk abinda kika fada kuma ya faru,Murmushi Ammah tayi tace to lokacin da kuke kuka kuna suma lokacin aka canja gawata wacce a asibitin idan baku manta ba Doctor ne ya daukeni tare da canja min daki lokacin aka daukeni aka kawo wata baiwar Allah wacce tayi hatsari da dadewa an rasa danginta tana motuary aka yi mata wanka tare da hada ta za a sa Alummar musulmai su sallaceta akaita makwanci ,Dangina dana Babanku duk sun San ban mutu ba,kawai kallonku sukeyi,a boye Yarima ya sanar musu amma basu San dalili ba,shi yasa kuka ga basu wani damu ba suna ta harkarsu ko? Nace kwarai kuwa ko a jikinsu a lokacin.

   Shi yasa aka hanaku Ku bude gawar lokacin da za a kaita kuna ihu da kuka lokacin ni kuwa tuni anyi min Visa ina Kukan rabuwa daku cike da tsoro kar na mutu da gaske,Aayan da Yarima ne suka kaini U.s acan aka yi min aiki da komai na warke,naso nazo na ganku Amma Aayan yace min baki shiryu ba kina nan da son kudinki na jira tukkunna.

    Aayan ne ya karbe zancen da cewa shine dalilin da yasa kika ga na Dade ban zo wajenku ba kina Amarya,ina U.s sai da Ammah ta samu sauki muka dawo ni da Yarima lokacin baki ga dana zo ba bana baki ko kwandala ba ban kuma siya miki komai ba,lokacin kuma tunanin ki zaki samu kudin Kasuwanci,ni kuma na nuna na fiki wayo,na hanaki sisi,sannan dana kaiki gidana na baku abinci garau garau Ammah ce tace nayi miki haka zaki kara hankali,tun kina tunanin zan saki kudi kuji dadi sai kika ji shuru,abinda kika ce na baki shi nake baki bana kari,sai da naga kin fara gane gaskiya,sannan na fara sakar miki sai naga ma kawai ma baki San wani kudi ba,sabo da Dubu biyu a wajenki kudi ce,nayi ta miki gwaje gwaje da dama baki gane ba,yanzu Ma Ammah ce tace ta gaji tasan yarta ta fara hankali ta girma ta hakura gwara ta dawo ta ganku,kuma da baki hankali kin canja ba da baza ki ganta yanzu ba,Yarima ne karfin shirya komai kuma shi ke yawan zuwa ganin Ammah a Us,shi yasa rannan muka je tare har kika yi fushi dani dole na dawo ba shiri, gata nan Ammah taga ina sonta da yawa sai garani takeyi na Zama mijin tace,Dariya Ammah tayi tare da cewa Allah kyauta Aayan,Yarima na dariya,Ameer kuwa sai yanzu ya fahimci komai,yace Ammah sannu da zuwa ni Cousin din Aayan ne ga Meenat nan ta rainani gaba daya kullum sai ta zageni a gidan nan,Dariya akayi gaba daya amma banda ni wacce nake hawayen bakin ciki,sam ni abinda Ammah tayi naji haushi gaskiya kuma bata kyauta ba,akan wannan ta iya sawa aka shirya ta rasu jibi irin kukan da mukayi da halin da muka shiga na rashinta, yanzu baza ta iya yi min fada na Canja ba kawai sai tayi mana haka yau gashi har Meenat tayi Candy anfi 1yr, kuma tasan Aayan a lokacin ba sona yake ba dan tana tunanin na gari ne kawai sai ta yarda nayi wannan auren da wuri gashi ni har ma nafi sonsa,kuma har Aayan ya rufeni shi da Yarima, gaskiya Ammah bata kyauta mana ba ni banga amfanin hakan ba amma wata zuciyar a raina tana sanar min fa ai na shiryu kuma nayi hankali sau nawa Ammah na min fada na daina abinda nake amma naki ji,to kuma idan ma naso kudin ai duk akansu ne tunda su nakewa komai,dan su nayi,sai kuma aga laifi na ai kowa da halinsa, ya Ammah za tayi da mutanen unguwa fa wanda suka Santa lallai za a dinga fyalla gudu kuwa.

    Meenat kuwa da Ma'eesha duk sun tafi sun makale a jikin Ammah suna ta murna da hira tana shafa Kansu,Ameer ma yace shima Allah sai ta sa masa albarka,haka ta shafa kansa daya tura mata,amma kuma Ammah hankalinta baya jikinta ya tashi matuka,hankalinta na kaina wacce tafi so a duniya ganin ina kuka naki kulata,kamata yayi ace ni ta fara shafawa ba wasu ba,Aayan ma hankalinsa ya koma kaina yar gwal dinsa na kuka kyautarsa bata birgeni ba kenan,Ammah ce       tace Zo Mufee ta kinji? Ta Mike zata zo wajena da sauri na Mike tsaye tare bin hanyar wani Bedroom wanda nake so na dauka cewar nawa ne ni kadai a sama kusa dana Aayan da muke kwana,nan na shiga kawai nayi kwanciyata a saman Bed,da sauri Aayan ya biyo bayana amma na sawa kofar Key,ko waye gaskiya zai iya jin ba dadi idan akayi masa haka Mufee tana da gaskiya cewar Aayan a ransa.
 
   Magiya da lallashi ba wanda bai min ba naki ki magana,Haka Ammah tazo da kanta tayi tayi naki,su Meenat ma,Yarima da Ameer duk sunyi sun hakura,Aayan yace suje kawai zan huce ne.

    Suna Palo suna ta hira har Ammah ina jiyo hayaniyarsu,Suka ci suka Sha,Ammah kuwa Aayan cewa yayi ta hau sama ta zabi daki ko a bata part guda tace a'a a dakin su Meenat zasu dinga kwana suna hira da yaranta kafin ta koma gidan can tsohuwar unguwarmu.
    Yarima yace Ammah Aayan ya miki magani kin warke ni kuma ai na siya miki gida hadadde ciki zaki koma,Ammah harda kuka su Meenat sai godiya suke masa,Ameer yace to ni kuma Mota zan sai mata insha'allah,Mamaki Ammah takeyi har ni kaina da nake labe ina jin hirarsu Allah haka yake ikonsa ka gama Shan wahalar duniya ba sai ya yanka ba wasu ma sai kaji dadinsu,suji kanka lallai ba a san wanda zaiji kanka ba a duniya ba sai lallai danka daka haifa ba.

    Ammah duk wannan baya gabanta hankalinta yana kaina dana ki kulata,Haka har suka tafi tare dasu Meenat tayi wanka tare da shirin baccinta suma haka sai suka ci gaba da hirarsu suna ta bata labarina da abubuwan da suka faru bayan bata nan,da halayen yan gidan su Aayan etc da kyar Ammah ta iya bacci sabo da tuna nin naki saurarta na kasa yi mata Uzuri,kuma Danni tayi hakan dan rayuwata ta inganta amma na kasa Fahimtar me take nufi,Kuka nake tayi a daki ni an tozartani a gaban kowa ance ina da son kudi har Uwata tayi karyar mutuwa sabo dani, kuka nake sosai Aayan yana jikin kofar yayi yayi na fito mu kwanta naki yarda,shi kuma bazai iya bacci  babu ni ba ya riga da ya saba,kukan nan nawa yana kona masa rai,tun yana rokona na fito mu kwanta har ya hakura yaje ya kwanta amma kasa bacci yayi gaba daya ya shiga damuwa sai tsaki da juye juye yakeyi ya rasa ya zaiyi ya iya bacci ba tare da ina jikinsa a kwance ba,Bai kara Sanin lallai Ashe yana sona kamar ransa ba sai yau,ko baiyi komai ba ace yana ganina a kusa dashi.

   Cikin dare wurin 1am ya kara zuwa ya rokeni na bude masa ko bazan je wajensa ba naci gaba da bacci na ina jinsa,har ya gaji ya tafi,2am ya dawo wai dan Allah to na bude ya bani abinci naci tun rana banci komai ba, nan ma naki kulashi Sai ma baccina da nakeyi.
   Haka ya kusan kwana a hanyar dakina da dakinsa sai da yayi sallar Asuba sannan bacci ya daukeshi cike da bacin rai.
   Washe gari Har Ammah suka shiga kitchen suka shirya abinci ana ta Harka ba Aayan ba ni,shi yana baccin gajiya,ni kuma naki fitowa nayi wanka na da komai yunwa na kwakulata amma naki fitowa ko kadan,Sai haka suka hakura sukayi breakfast har Ameer, misalin 12pm Aayan ya Sha wanka direct dakin da nake ya nufo cike da hasala yace bude kofar nan ko na bude da kaina yanzu kafin na irga 3 tsoro da tausayinsa naji tun jiya yake abu daya na tabbata ko kansa bazai wa haka ba,ina fushi kamar zan fashe na turo baki na bude kofar, shigowa yayi da sauri ya rungumeni a jikinsa yana why? Babyna me yasa haka? Zaki kasa Fahimtar mu,idan laifi ne hakan kiyi hakuri baza a sake yi miki ba amma dan Allah ki Kula Ammah ko zata ji sanyi baki ga yanda ta damu ba sai zancenki take min kullum bata da burin da ya wuce Mufeedanta ranar nan ma fa da kika Dameni ko da budurwa nake waya nace miki watace yar Us Ammah ce fa kuma lafiyarki ta tambaya a lokacin,dan Allah kiyi hakuri ko abinci kici kalli duk har kin rame,ina jikinsa yana ta lallashina ina sheshekar kuka harda na shagwaba,yace ni Allah bazan je wajenta ba tunda tayi min haka ta tafi ta barmu Ashe tana raye kuma ka boye min bazan je wajenta ba,Ok to naji ya isa haka kukan Zauna bari na kawo miki abinci kici kinji mufeen Ammah? Nace Allah ni ba tata bace ka daina fada min,a raina mamaki nakeyi wai Aayan ke nuna min so haka,ashe yana sona haka ai har tsalle nayi da birgima a saman Bed sabo da murna Aayan na so na da yawa.
  Ammah ya fara gaisarwa cike da girmamawa,su Meenat suka gaishe shi yana tsokanarsu sun samu Ammah sun manta da kowa,Ammah tace ina mutuniyar? Yace  hmm da kyar ta yarda zata ci abinci sai yanzu ta bude kofar da kyar sai da na Sha fama tun jiya nake abu daya,Farin ciki Ammah tayi lallai Aayan yana son yarta sosai kuma yana kula da ita taga zahiri a jikin mu kuma su Meenat sun bata lbr,Abinci Meenat ta hada masa a tire ta abawa Aayan,Ammah tace nasan Halin abata akwai zuciya ka bita a hankali zata sameni ne,Aayan yace to ya nufo dakina, sai da yasha fama kafin ma naci abincin sai da kansa ya shiga bani a baki shima yana ci,da kyar nake karba,sai yace dan Allah ki hadiye pls sannan zan hadiye,idan ya takura min na fashe da kuka,bayan mun koshi nace to sai ya fitar min a daki,yace kai Sweetheart ki Bari ko hira muyi mana naji dadi kinga jiya ko bacci ban iya ba bakya kusa,nace ni ba ruwana ka tafi ko na barma dakin kawai,Haka ya hakura badan yaso ba ya fita,naji tausayinsa sai nace dawo to ka kwanta amma 2hrs kawai zaka tafi,ba musu ya dawo na nuna masa bed tare da cewa kwanta to zan tayaka baccin,Dadi ya lullubeshi nima haka sabo da nayi missing dinsa so nake naji duminsa,key na sawa kofar sannan na kwanta a gefensa ina kunkuni,jikinsa ya jawo ni yana aikin lallashina yana so ya danyi Romancing dina amma yasan bazan yarda ba fushi nake dasu gwara ya lallabani haka kan kace me bacci ya kwashe mu muna makale da juna dama baccin bai ishe mu ba,Ammah duk ta matsu ta bar gidan sabo da kunya take ji Zama gidan yarta jira take Yarima yazo a canja mata gida.
   Ameer har sun saba da Ammah kamar ummansa haka yake ji da ita.

   Kwanan Ammah uku a gidan nan ban kulata ba ko ganina bata kara yi ba tun zuwan farko,Aayan ma bana sakar masa fuska bana bari ma ya rabeni tun rannan da nace zan tayashi bacci ban kara bari ko yatsa ya rike min ba,ya shiga damuwa har ramewa yake yi,Ammah kuwa har da na sani takeyi da bata shirya hakan ba ta barni da halina,Yarima yace suyi hakuri zan sakko ne,Ammah tace tunda ta huta a kaita gidanta tare dasu Meenat gaba daya,Aayan yace ai shi bai yarda ba baza a dauke masa su Meenat ba,Ameer ma yace gaskiya basu yarda ba,Ammah da kyar ta lallabasu tare da ganar dasu har suka hakura,Aayan yace Mufee fa ai dole a tambayeta,Ammah tace kyaleta ba komai itama zata zo da kanta ne ta neme mu,Yarima suna zaune su Meenat murna kawai sukeyi da zumudi ko ta kaina basa bi suka tattara nasu ya nasu kaf suka shirge a mota,sannan Aayan ya rakasu wajena wai zasu bi Ammah su wani bakin ciki ya kara dirar min,mun saba da rayuwa tare da yan uwana kullum muna tare ina ganinsu ina jin dadi muna abubuwanmu sabo da tare dasu Meenat nazo gidan miji ban san zafin rabuwa da yan Uwa ba sai yanzu gashi mun kara shakuwa,tare muke kashewa mu rufe,su bani shawara na basu,su suke tayani ayyuka da komai ba ruwana da wasu masu aiki sai masu wanki da gyara Compound,nan take na kallesu kawai na fashe da kuka,suma suka rushe da kukan suna bani hakuri,nace Meenat kuma yanzu shike nan kun tafi ni kadai zaku bari?ai sai ku bari sai nan da kwanaki sai ku bi bayan Ammah amma ba komai kuje rayuwa ce, ita Ammah ai ta saba da zama ba mu,ta saba da rayuwa ita kadai shine yanzu daga zuwanta zaku manta dani Ku bi bayanta ko? Meenat tace gani mukayi idan mun barta baza taji dadi ita daya ba,ae Amma ni kuma fa kunyi tuna nin haka? Ita da tayi tafiyar muke tunanin bata raye fa mun hakura ma da ita shine zaku bita tun yanzu? Shike nan mun fasa Binta bari sanda kika yarda shike nan,Da sauri su Meenat suka fita suka sanarwa da Ammah,dariya tayi tace da gaskiyarta lallai Mufeeda na yarda ta Zama Babba ta kara hankali kuje Ku dawo da kayanku ni zan tafi Ku bata hakuri daga baya sai kuzo ku yini kwa dinga yi min.
  Haka suka dawo da komai nasu inda yake,Ameer yafi kowa murna,Aayan ma yaji dadi da basu tafi ba sabo da yasan an bar baya da Kura shi zai sha wahala dani kafin na huce.
   Ma'eesha ta dawo tace Ammah sun tafi da Yarima sis gamu mun dawo,Good for u nace kawai sannan na juya nayi kwanciyata.

     Bayan sati daya da dawowar Ammah Yarima ne ke dawainiya da ita tare da Ameer su suka kaita danginta can kawai tare da Maiduguri duk sunyi murna tayi musu bajinta ta dawo katon gidan da Yarima ya siya mata na alfarma,ga yan aiki mata dattijai masu kwari har biyu,da me gadi namiji daya, gidan ba abinda babu na kayan alatu da ci da Sha.
   Haka ta zauna a dan gidanta,Yarima ya kai Ma'eesha da Meenat sau biyu sun mata yini guda,ni kuwa ba ruwana fushi nake da kowa bana kula kowa sai Ameer,Haka Aayan ma kullum da sha'awarsa yake kwana yana tashi,bana kulashi babu yanda baiyi dani ba amma naki lallashi ba adadi,har Ameer yasa ya bani hakuri naki ji ,Yarima yace ba ruwansa sai dariya yakewa Aayan yanda duk ya fita daga hayyacinsa ya rame kullum tunani  da damuwa yakeyi,har kasa jurewa yayi ya Sanarwa Daddy wai idan nazo gaisheshi ya bani hakuri ya lallaba ni,Daddy yace ba ruwansa ya kula da matarsa kowa haka yake hakuri.
   Ni kaina tausayin Aayan nake ji sosai ganin halin damuwar da yake ciki,kuma shi yake kula da ganin naci na koshi,amma ba ruwana da shi kuma ba wai dan bana sonsa ba sai ma tausayinsa da nakeji.
  Sati gudan da mukayi bana kula Aayan kullum gyaran jikina nakeyi tare da Shan tsumi na masu Inganci,ina gyara jikina wanda Maman Sayyah kawata ta koya min hadawa da kaina,maza irin su Aayan sai da gyara sosai kwai kwarzaba,nayi mamakin da naga yana iya daurewa amma nasan a wahala yake kawai na rashina,Meenat ma duk sun fahimci yanda yanzu bana kula Aayan yana cikin damuwa, zuwa wajena suka yi tare da min nasiha sosai ba laifi kuma ta shageni sun tunatar  dani ina cikin fushin Allah da Mala'iku, bayan sun tafi na tafi Dakin Aayan amma baya nan,gyara dakin nayi sosai tare da toilet,haka gaba daya part din mu sai dana gyarashi Neat sannan na sauka kasa,Ameer dasu Meenat sai murna sukeyi da alama na daina fushin,da kaina na shirya girki na me shegen dadi,Pounded yam da egusi soup sai farfesun Kaji nayi tare da shirya lemuka kala biyu na gama komai na kwashi na Aayan a flasks na Alfarma na kai tare da shiryawa a bedroom dinsa, lemuka ne kawai na barsu a fridge sai ya dawo zan kai masa.

     Ina yin Sallar Isha na shirya cikin kayan bacci na ala tsine ba abinda ba a gani a jikina sunmin kyau,ko ina kamshi nake fitarwa abina nasa Hijab kato da niyyar sauka kasa naci abinci tare dasu Meenat,ina fitowa Aayan kuma ya hauro saman muka ci karo,yana ta kallona ganin haka yasa na juya zan koma Bedroom da sauri,hijab dina ya jawo na dawo baya,ido muka hada ina shirin fara kuka yace me nayi miki wai kike min haka? Shuru nayi yace fine jeki Allah ya gani kuma yana kallonki yayi gaba abinsa ya barni a tsaye,fasa sauka nayi nabi bayansa zuwa Bedroom dinsa yana kallona yayi banza dani ya fada toilet tare da yin wanka ya fito ina kallo ya gama shirinsa ina zaune Saman Bed,na fita na kawo masa lemuka tare da Fruits salat na ajiye,ya kalla tare da cewa kwashe abincin bana ci ni alhalin yunwa yake ji, shuru nayi ban kwashe ba,tsawa ya buga min ba dake nake ba,sai da na tsorata matuka,zuwa yayi tare da hayewa Bed dinsa yace kwashe ki bar min room bana son ganinki pls,Karfa ko ya daina so na haka nake tunani,kuka na fara masa ba tare da nace masa komai ba, idan na tashi sai na ballaki a room din nan bana ra'ayinki fice min da gani, Kukana naci gaba da yi nace an cuceni ace bazan yi fushi ba,kuka boye min Ammah ta bata raye kuma shine aka zo ake ce min ina da son kudi a gaban kowa duk an rainani,bayan ni ba haka nake ba maimakon a lallasheshi shine za a balla ni,barin gidan ma zanyi gaba daya tunda haka ne.
   Wanne hakuri ne ba a baki ba? Ya kike so ayi miki? Yarinya ce ke? ai dai na hakura har girki nayi ma kace wani baka ci kai,kuma ka tsaneni baka kaunata baka son ganina ai shike nan bari na tafi.
   
   Shuru yayi a ransa yana me jin dadi wani Sanyi tare da Hamdala ga Allah,muryarsa naji yace zo ki zauna akwai maganar da zamuyi kuma in dai baki karba ba kawai na daina kulaki ba ruwana dake,a raina nima sai murna nake,cike da shagwaba na zauna a gefensa nace gani to ai ko ina turo masa dan lips dina me kyau da birgewa,kallona ya tsaya yi na gama birgeshi.




   Wannan page na yan gps ne gaba daya sabo da wannan babban page ne babu wanda yayi zaton Ammah na raye abin mamaki,sai nan gaba za a kara Jin yanda akayi corner dasu Mufeeda ha Ammah ta barsu a zuwan ta mutu dole ba wannan ne kadai dalilin ba akwai wani.

  Tnx fans! ayi hakuri da typing errors.








AsmaBaffa
[2/3, 8:36 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

    KASUWANCI NA






          109-110







Official





By
AsmaBaffa







      MAMAN 2 KIDS and MOM INTEESAR wannan page nakU ne sabo da jajircewarki a Sharhi.

  HUMAIRA sarkin Sharhi ina gaisuwa me tarin yawa.

  AUTA ina kika boye tare da ASYCOOL shuru Allah yasa lfy.

Manya manya maganin kanana Jinjina nake muku
FLOWER
MARCYCOOL
ZAINAB ATIKU SALAMA
SAMEERAN GAYA
HAFSAT KHAIRAN
MAMAN MEENAT
MOM SUHAIL
MRS HAMZA
MRS UMAR
MRA FAROUQ
JANNAT
MAMAN WALEEDA
QUEEN MERMU.




 
           Ido ya lumshe tare da budesu tar a kaina,kallonsa nakeyi cike da so tare da kewa shima hakan,wani kallon so muke aikawa da juna dadi na ratsa mu, magana ya fara yi min cikin nutsuwa,Mufeeda ya furta cikin muryar tausayi da lallashi,Kallonsa nayi sunan da ya furta har kwakwalwata haka naji kamar wata na'ura ce ta ambaci sunan haka nake jin dadinsa.
   Magana yaci gaba da cewa tunanina kinyi hankali Ashe ba haka bane,an miki bayani sai ki fassara abu bai bai,kin kasa Fahimtar me ake nufi,yanzu abinda kikayi kin kyautawa Ammah kenan,mahaifiyarki guda,ta miki komai a rayuwa ance ta rasu kin damu kina kewarta ance bata rasu ba ta dawo akwai dalilin da yasa ta shirya hakan,ba wacce take so sama dake,bata da magana sai Mufeedanta,tazo har gidan mijinki da kike aure amma kika ki Kula ta ko kallo bata isheki ba,mutumin da yayiwa Mahaifiyarsa haka waye bazai masa ba,iyaye fa basa laifi wurin yaransu,Meenat su fiki hankali,mahaifiya guda kika ki kulawa,kika wulakanta,tana can da bacin ranki Allah ma na fushi dake,sannan ni ban miki komai ba ina mijinki kalli abinda kika dinga yi min kan abu kalilan kin bani kunya,yanzu gobe zamu je ki bawa Ammah hakuri ki shirya idan kin yarda idan baki yarda ba to,Da sauri nace ni bazan je ba na daina kulata tunda tayi min haka, cike da bacin rai yace to tashi kije nima ba ruwana dake.

    Kin tashi nayi tare da yin shuru sai da aka kwashe 15mnt sannan ina kunkuni nace to shike nan ai zanje amma Allah bazan gaishe ta ba tunda tace ina da son Kudi,Hararar wasa ya jefo min yasan na hakura ma tunda na yarda zanje,abincin fa baza Kaci ba? Kince baza ki gaisar da Ammah ba ta ya zan ci abincinki,baki na turo ai dai nace idan Naje kawai zance Sannu da zuwa Ammah amma Allah bazan gaisheta ba,to ruwa kawai zan sha nima,kai dan Allah Nafa sha wahala wurin girkin nan na bata lokaci nayi maka da kaina,baka ji dadinsa ba pls Kaci ko kadan ne? Bazan ci girkin wacce bata gaida Mum dinta ba,da ace kina gaisheta sai naci,shuru nayi sai da naga lallai bazai ci ba nace to zance mata Sannu Ammah ni dai bazan ce ina yini ko ina kwana ba Allah sai in kar Kaci abincin kuma ai nayi kokari ma.
  Shi kanshi yasan ma na huce gaba daya sai yace to zanci badan halinki ba,ina murna na cire Hijab dina na ajiye gefe,ya kalleni sama da kasa yaga kayan Harka iya kaya,Nayi kyau ga kayan baccin matsiyata dasu komai ana gani, ina sane nake kara girgiza jikina ko ina rawa yakeyi na zuba masa komai kawai na dauki Hijab dina zan mayar jikina yace noooo pls ki barshi haka zo ki tsaya a gabana,haka ya tsayar dani kamar wata soja yana cin abinci yana kallona na kasa tsayawa waje daya sabo da na tafi da Imaninsa ina sani nake girgiza jikina wai irin na gaji da tsaiwa sai kukan shagwaba nake masa ina dire diren kafafu shi kuwa karfin Hali kawai yake yi tuni hankalinsa baya jikinsa idonsa ya canja da kyar ma yake kokarin cin abincin hankalinsa yana kaina.

    Bai ma gama ci ba naga yace kwashe na koshi,na kwashe komai na mayar kitchen sannan na koma dakina na kwanta a bed tare da yin dai dai wai irin Jan aji nasan dole zai biyo ni,Brush da shiri ya sake ya fito yaga bana Bedroom din,Wayata ya kira yaga ban daga ba,ya kara kira shuru ina kallo kuma,Da kansa ya Mike ya nufi inda yasan zai ganni,hango ni yayi na baje ina baccin karya amma tunaninsa baccin gaske ne,wani juyi nayi me Jan hankali,light ya kashe tare da haurowa Saman Bed din,yanda naga yana abu a rude shi ya bani dariya har na kasa rikewa na saki abata,cakulkuli ya fara min muna dariya yace dama kina kallona ko? Nace Oya let's go,ai Bazan iya matsawa nan da can ba kawai mu kwanta a nan, yau ban bari ya fara min komai ba,ni na fara Sabo da nayi Missing din mijina da yawa,kamar zan cinye masa lips tare da tongue haka nake tsotsesu da zafi zafi, dadi ya gama rufe shi kawai wani nishi mukeyi,Bana iya cewa komai sai dai nace Miss u Baby,Shima haka can kasa naji yace yau Dan Ficici za a bani,Lokacin ina jin dadina ya min yawa bana hayyacina nace a'a yau kamfatowa zakayi,yace Allah? Nace ai Kwaso kawai, yace an gama,ba karya kuwa ya kamfanta dan yau nafi ko yaushe jin jiki a hannunsa,ba karamar wahala nasha ba,tun ina kuka dadi sai da na koma na wahala,sabo da ban wani saba ba,kadan na saba Bazan iya dauke yanda yake so ba ba tare da na dan sha wahala ba yanzu sai nan gaba,har yau sabon nawa ba wani me yawa bane sai kuri idan anzo kuma na fara kuka ido ya raina fata,shi kanshi Aayan ya san iya limit din da nake kaiwa ban gajiba,shine yake so dole na saba sai yazo wanda lokacin na gaji sai ya dinga Dragging dina,Kuma ko yaushe yana ganin ci gaba tunda kullum ina kara samun ci gaba.

    Sai da ya samu nutsuwa muka yi wanka na gasa kaina sosai mun kwanta again yana Sa min Albarka yana jin dadi yace lallai yan matana yanzu ana ta girma kullum, tnx alot My Queen,jikinsa na shige nace ni ba wani sabawa karka kala min ina yar yarinyata.dariya yayi tare da kara kankameni yana shafa min gashina zuwa gadon baya na yace muyi bacci sai gobe kuma zanga wanne salon za a nuna min naji na yau ya hadu kin ba da style,dukan wasa na masa ina jin kunya na kara boye fuskata a kirjinsa ina dariya kasa kasa,wata Kalma na rada masa a kunne wacce saura kadan ayi second round da kyar na lallasheshi yace to ki daina kunna ni,nace kyis na kasheka to,Dariya mukayi gaba daya hannayensa suna saman Mazaunai na yana shafasu cikin Salo iri iri wanda ni kaina hakan yana min dadi.

     Abbi ne kwance saman gadonsa  yana nazarin duniya tare da mamakin canjawar komai da ya samesu a rayuwa,gashi har sun lalace suna ramewa sunyi duhu sosai kamar basu ba,dama ance duk wanda ya saba da rike kudi yana shan wahala idan karayar arziki ta sameshi,kuma dama can taimakon su akayi talakawane gaba da baya, duk gashi har sun zama abin tausayi duniya ta juya musu baya,wai sune a wannan matsayi, Hajja ce ta shigo dakin Abbi tana fada mene amfanin kwanciyarka a gida da tsakar rana haka baza ku fita neman na kanku ba,kudin hannuna sun kare saura Naira dari kamata yayi ko yar dubu biyu ina rikewa a hannuna ni bana iya rayuwa ba kudi,Abbi shuru yayi bai ce mata komai ba Sabo da bakin ciki da me zasu ji, Hajja tace au dan Iskanci kana jina ina magana kamar kaga Kashi eyee,ni na daura muku talaucin idan kudin banza ne me yasa baku yi zuciya kunyi ba, Haba Hajja me nace miki kuma,ya kike so muyi kina gani karatun su Sabeer ma nema yake ya tsaya,ba komai bamu da komai sai bashi ma da muke ci ki dinga tausayinmu mana,idan ba sata kike so muyi ba me zamuyi miki? Hajja Hawaye ta share wai an ci mata mutunci,ta fice fuuuu ta bar Abbi yana bakin ciki.
    Haneefa ce ta fito ta cikin yan uwanta Maza da mata tace to Jama'a ku kalli atamfar jikina ta gaji da wanki har ta kode tana neman jemewa,dama kayan namu kadan muka ebo,Meenal ce ta fado da gudu tace Bazan ji kunya ba bayin Allah nasan masu hankali ne gaba daya dan Allah me Pad always ta san min ko a min karo karo na kudi na siyo,Sajeeda tace ai duk dan kwalayen Ka kayana sun kare a kunzugu rannan,sai dai kiyi amfani da dankwali, Mujaheed da Khaleel suna dariya suka ce kadan kuka gani Yara tun yaushe muke cewa kuyi aure tun da gatanku samari na rubibinku kuka ki gashi na pad ma ya gagareku.

Meenal ta kalli Khaleel tace dan Allah bani gajeren wandon nan naka da naji zaka jefar naga cotton ne sosai zai sha ruwa a jikinsa,Khaleel yace ko kunya bakwa ji wai a gabanmu kuke irin wannan kalamai ba tarbiya ba komai sai kije yana cikin bakar jakar nan ki dauka,Meenal da Sauri taje ta dauki gajeren wandon Khaleel wani me nauyi cotton tasa reza tare da yankashi kashi Kashi ta linka kamar dai Pad haka ta dinga sawa tana kunzugu dashi.
  
   Matayen su Abbi talauci ne ya ishesu gaba daya suka ga gwara su tafi gida tunda yanzu ko sabulun wanka da wanki Rasawa akeyi a gidan,Nan suka tayar da rigima sai an sakesu,Umman Ameer tace ita dama tana jin Haushi an rabata da Danta Ameer ta gaji,Hajja tace ba shegiyar da za a saki kamar yanda akaci daula dasu dole Asha wahala dasu dama in sun koma dangin nasu ma dai talaucin zasu tarar Sabo da duk kanwar ja ce.

   Yaji sukayi wai sun tafi gida sai sun huta zasu dawo,Yaran gida suka ce sama dawo idan sunji Wahala kar wanda ya hanasu,suna shiryawa suka ce mu munyi gaba,Su Mujaheed suka ce a dawo lfy Allah ya kiyaye Hanya,tuna ninsu yaran zasu damu sai suka ga kowa harkar gabansa yake,Sabeer yace mu ai Aayan da Daddy kadai ne zasu ce zasu yi yaji zuwa turai mu damu Amma kawai ba abinda ake tsinana mana ace za a damemu,common toothpaste mu muke siya,sabulun wanka da wanki ba a san a bamu ba,Abbi yace Kai rufe mana baki marasa kunya,Sajeeda tace ai wlh sai daí a godewa Allah Amma ya dace ace a cikinmu akwai Karuwai,akwai yan shaye shaye tare da kasurguman barayi sabo da Halin da muke ciki a gidan nan,kowa kansa ya sani kowa ta kansa yakeyi,Hajja tace ai duniya ce yanzu ma kofa a bude take zaku iya komawa Karuwanci da shaye shaye,sace sace kuwa na wanda kuka gani shi zaku dauka dan ni nawa yafi karfinku😅, Abbi Sani yace Haba Hajja addua ai zaki yi musu ba kice suje suyi ba ai yarane yanzu idan  mune zaki so yaranki su dawo haka?.
     Kai Sani ka rufe min baki shegen kunne kamar malafar Kwadi,Dariya aka dauka gaba daya har yaran Sabo da kunnen Abbi Sani kamar Malafa haka suke kuwa,Abbi Mustapha ne ya buga musu tsawa,shima Abbi babba yace zaku bar palon nan yan Bantan uban Yara.

     Khaleel ne yake ta masifa a tsakar gida an sace masa sabulun wanki wanda da kyar ya hada kudin ya siyo na wanki dan Naira Hamsim wani kato zai dinga cancanawa yana wanka dashi,daga ajiyewa ya juya baya zai dauko bokiti kafin ya dawo har an dauke sabulun yan mintuna kadan,Nan ya fara fakon wanda ya dauka duk wanda ya shiga wanka ko me wanki sai ya duba sabulunsa mata da Maza,Meenal tana fitowa daga wanka ya ganshi a hannunta ashe ita ta sace ta wanke panties dinta tunda period take dole sai da wanka da wanki,Kamar zai cinyeta haka ya kwace abinsa,dan ya bar mata tace kazanta ta na wanke dashi fa period ne duk na shafa masa na wanke da kyar ake gane kalar sabulun dazu wlh dan baka gani ba yanda ya rine kamar jar color aka Sa,abin kyankyami har wari yakeyi, Khaleel ya gano so take ya bar mata shi du, yace ai ko a Abbatuwa mayankan dabbobi aka jefa shi cikin kogin jini bani abina dan Uwarki mayya wlh idan na kara ajiye abina kika dauka sai kin gane kurenki,Meenal tace jaraba akan sabulun wankin?Yace ae din,to yi hakuri dan Allah ka bani na karasa wanke daya pant din nawa yanzu na tuna ban gama ba kaima kasan sanda muna daula bakwa sanin ma time din da muke period yanzun ma babu ce tasa ba yanda zamuyi dole muke yage yar kunyar.
    Khaleel yace ungo badan halinki ba dan dai kawai kina san min Vaseline dinki ne Allah gashi nan saura ki karar dashi,Na gode cewar Meenal ta koma toilet ta gama ta fito ta bashi sabulunsa,Mujaheed ma da shi yayi wanka haka mata da mazan kaf ba yanda Khaleel ya iya haka kowa ke zuwa yana rokarsa dashi sukayi wanka,Abbi ma yace kai Khaleel bani sabulun sodar nan naka zan cude jikina dashi ina so na fita neman Ameer ruwa a jallo dan ubansa ya zai manta da iyayensa,Khaleel yace kune fa kuka koreshi ai ni ya birgeni wlh,gashi sabulun dan Allah nasan wankanka dadewa kakeyi karka silleshi Abbi.

Harara Abbi ya zuba masa ya wuce yayi wanka sannan ya kwalawa Meenal kira tana zuwa yace Bani Toothpaste naji ance kece me shi a gidan nan,Meenal tace Vaseline gareni  ni Katon gaske wlh ko wanka zaka yi dashi ina dashi kamar tulu yake Sabo da girma saurayina nasa ya kawo min shi maganin gidan yawa,Meenal Me Vaseline kenan,Abbi yace dauko min shi na shafa,wace to me abin goge baki?Haneefa ce me su manya manya ita take matsowa kowa da kanta duk yanda kuke da ita sai daí ta Matsa ma da kanta kar ya kare da wuri,Abbi yace kirawota ta bani,Tunanin Abbi ai shi Babbane Haneefa zata bashi ya matsa da kansa yanda yake so sai kuwa yaga tace kawo Brush din,da mamaki ya kalleta ta kuwa bude ta dan difara masa kadan tare da cewa kar ka raina Abbi rayuwar sai da tattali,Hajja ma tazo tace Haneefa ashe kece me makilin matso min a nan na goge bakina,Haneefa tace  rayuwa sai Imani Hajja ku tsofaffi har wani goge hakora kukeyi idan ba iyayi ba da ganin arahar Sa me zaki goge hakora kamar Tsinken tsire duk sun zube saura dai daiku kici goronki shima yana wanke muku baki tayi tafiyarta,Hajja tace ni me na tare musu da aka rainani,ta fara kiran Khaleel sai da yazo jikinsa ba riga, tace wai kai kullum baza ka Sa riga ba kai kenan daga dogon wando sai gajere,Khaleel yace Am too sexy ne Hajja wlh shi yasa nake nuna muku baiwa ya fada yana dariya,Hajja tace ina wata baiwa a nan Da Ameer dina ne ya fada sai na yarda dalla bani sabulu na wanke jikina, Khaleel yace Rayuwa sai Imani Hajja wa zaki wa wanka ke ba miji ba,yo ko miji gareki me zai ci da ke ki sha zamanki haka da Allah wannan Asarar sabulu zaki mana,Hajja ta balbale shi da masifa ko wanne dan iska bani da iko nayi magana sai yace wani Rayuwa sai Imani wata sara kuka samo kuma ko kuwa ni kuka raina.

    Khaleel dai yayi tafiyarsa,Mujaheed ne yazo ya wuce Hajja shima ba Riga sai 3qtr ya tattaro hantsar Wando ya rike gaba daya yana tattalewa yana tafiyar yan gayun samari ga uwar suma duk ta cukurkude,Hajja tace haka dai aka iya yan iskan Yara ayi aure tun tuni kuka ki yi sai aikin rike hantsar Wando Sabo da jarabarbu ne ku mayun mata,Hajja bata san gayu bane ta dauka sha'awa ce ko Iskanci ne ke damunsu,Mujaheed yana Jinta yace Hajja sai Imani ai ko Ya kika ce,Tsaki ta ja tare da tauna
Goronta,Sabeer da Aliyu ne wanda sun kai 24yrs yanzu su kuma boxers ne dan karami suka Sa da yar Singlet ga abar tasu nan a Wando ana gani duk ta mike da wata yar kwarababbiyar waya karama a hannusu suna dannawa suna kallon pics din yan matan turawa kusan tsirara suke,Hajja nan ma ta rasa uwar da suke sai kus kus suke suna dariya suna kallon waya,ta kalli wandonsu a ranta tace na shigesu ni Hajja kar fa a fara cikin shege a gidan nan ayi yar gida tunda ga yan mata nan kuma ba muhararram juna bane wasu to matan ma ya suke bare Maza,Ganin Hajja na Sa musu Ido Sabeer yace Allah wadaran karamin gida sanda muna gidanmu babba wa yasan me wani yakeyi Amma yanzu komai kayi akan idon wani,Aliyu yace muyi maganinta suka samu Hajja tare da cewa Hajja kinga wasu dan Allah sun hadu? Nan Hajja ta kalli waya ai sai taga Mata kusan tsirara,Sabeer yace wannan zan aura Hajja tayi? Duka Hajja ta rufeshi dashi tare da cewa wlh in dai ina raye baka Isa ka auri wannan ba,Aliyu yace musulma ce sunanta Rasheeda,Hajja ta dauka da gaske ne ta dinga tsine tsine ba a Isa ba,kuma tace sai ta fadawa su Abbi,Sabeer yace Hajja masu kudi ne fa yar gidan shugaban kasar Ethiopia ce fa kinga mun washe,sabo da son kudi Hajja sai tace ya sunanta kace? Yace Rasheeda,Hajja tace ayyo yanzu naji zance ai tun daga sunan ma kasan musulma ce,a ina kuka hadu a Internet din naku?Sabeer yace ae tace kwanan zata zo ma kuma zata Aiko min da yar million goma na sha ruwa,kirji Hajja ta dafe tare da cewa kace ina gaisheta kakarka Hajja sunana,yaro kayi dabara wlh kafi su Khaleel hankali ina kallonku yara ashe kune manyan,Aliyu yace Hajja kinji tana kira ma a waya kash Amma bamu da kudin Sa kati kuma dole sai da kati so muke mu tura mata accnt Number tace Sauri take zata turo kudin gashi bamu da sisi,Hajja da Sauri tace zan baku rance ina jin kamar Ina da dubu biyu a hannuna nawa ne Katin da zai isa? Sabeer yace tab ai sai dubu biyar yanzu kuma babu sai daí ayi asarar milliyan goma kenan Hajja ki taimaka idan ta turo zamu baki milliyan Uku a ciki kyauta,Hajja dadi ya rufeta tsohuwa da son kudi nan tace to  dama dubu shida ce ta ragemin a duniya ga biyar sai na rike daya ni kuma,Nan Hajja ta zaro dubu shida a jikinta wanda da haka kawai ne sai daí a mutu a gidan baza ta iya siyan ko sabulu ba.

   Sabeer suka karbe dubu biyar da Sauri suka dauki dubu daya daya,dubu Uku kuma suka siyowa kowa na gidan sabulun wanka da wanki,suka bawa matan kudin kitso,mazan kuma na aski,har pad aka siyawa matan kowacce biyu biyu Sabeer yace gashi naga Alama boxers dinmu an fara sace mana ana kunzugu dasu, har da Sauran dan abinda ba a rasa ba duk sun dan siya me araha,karshe dai Sabeer dari biyu biyu ce ta rage musu,Duk yaran gidan sunji wayon dasu Sabeer suka hadawa Hajja sai dariya akeyi a boye kowa ya washe yau a gidan har kifi soyayye suka Dora a saman shinkafa da wake kowa daya,su Abbi da Hajja basu san me akeyi ba,dama matayen su Abbi sunyi yaji su Haneefa ke girki duk da basu wani iya ba wahala tasa har sun saba.
    Kwana biyu Hajja taga su Aliyu shuru ba 5k dinta ba milliyan Uku sai nemansu take Amma sunki yarda ma su hadu wasan buya sukeyi.Idan taje dakinsu sai su Khaleel su boyesu kowa yace basa nan sun fita,Hajja ta koma me gadin dole a Palo take kwana wai zata ga wucewar Aliyu ko Sabeer amma sai su wuce ma bata ganesu ba.

   Washe gari da Safe ma sai da Aayan ya kwashi Harka ba daga kafa kamar ma baya tausayina, kamar yanda su Meenat suka saba haka sukayi komai girki da gyaran gidan su ma yan aiki suna nasu,sai 11am muka fito bayan Aayan ya shirya ni yayi min komai,ba su Meenat gidan shuru sai guntuwar paper na gani sun ajiye min,.......wai mun tafi gidan Ammah tare da Ameer sai dare.
     Aayan yace ina suka je? Gidan Ammah na bashi amsa a takaice, da kansa yayi Feeding dina muna hira sama sama yana tsokanata wai jiya naji dadi na fara sabawa,na fara Kukan shagwaba ina Ni ba wani dadi,yana mun dariya har muka gama,yace je ki shirya muje gidan Ammah sauri ya furta ba alamar wasa,da Sauri na tashi na je sama nasha wata dakakkiyar shadda yar Senegal tasha aiki Dark purple aikin kuma da light blue and pink na fito kamar wata Hajiya,Shi kuma shadda Light blue kamar munyi ango sosai muka yi kyau.

    Jerawa mukayi wow yau abin kallo ne mu, nace muje wajen Daddy mu gaisa,Daddy ba karamin farin ciki yayi ba da ya ganmu haka sai albarka yake sa mana sannan yace mu gaishe da Ammah, yau ba Driver bane zai tuka mu kuma ba escourt mu biyu kawai,da kansa ya zagaya tare da bude min gaban motar yace ranki ya dade Allah ya taimakeki shiga,Kafadarsa na dan buga kadan ina dariya na shiga ya rufe sannan shima ya zaga ya shiga yaja motar cike da nutsuwa muka bar gidan,Ba wani nisa me yawa bane sai gamu a wani gida dan babba me kyau sosai yayi kyau gaskiya,me gadi ne ya bude mana gate ya Cinna hancin motar Sa cikin gidan,gidan yasha tiles da flowers yayi kyau sosai,jikin wata katuwar Bishiya muka hango su Meenat tare da Ammah zaune a katuwar tabarma suna hutawa,Ameer da Yarima suna gefe suma,Hajja da Katon tire a gabanta tana kwada musu zogale da Kuli yaji hadi sai nishadi sukeyi abinsu.

    Aayan ya kalleni yaga ina murmushi ni kadai ina ta kallon Ammah muryarsa naji yace muje ko? Da sauri na dawo hayyacina na daure fuska irin ba dadi naji ba,murmushi yayi yace kinfi kyau a haka muje dama naji jiya Ammah tace duk tafi so taga kina fushi dariya kike bata,da Sauri na washe bakina nace na fasa fushin tunda tana so,na fito ina ta fara'a ina murmushi wai Ammah ta gani kar taji dadi ma,Aayan yana ta dariya a ransa,a hanya yace Ammah tace tana so taga kina fushi kinki gaisheta,nace aiko sai na gaisheta din,Aayan yace ke duk abinda bata so shi zakiyi ko? To ki daure dan Allah ki nutsu tana son ta ganki a nutse cib dake,Nace haka tace?Yace ae,na girgiza kai nace za a gani wlh Bazan nutsu ba sai na koma kamar bera wasa zan tayi ba nutsuwa.Aayan yana ta dariya mugunta yake hada min.
    Muna karasawa mukayi sallama kowa Murna yake yi nazo na huce,a kunne ya rada min tace ita bata son a durkusa mata da Sauri na durkusa nace ina yini Ammah kuna lfy ya gida ya aiki?irin na bata haushi bata so a gaisheta,sai naga tana ta murna ta Amsa da fara'a harda Sa min Albarka,ni kuma sai yashe baki nake ina fara'a wai ance tana son nayi fushi shine bazanyi ba ni fara'a zanyi,har hannu nake sawa ina kara bude bakina sosai,Aayan yana ta dariya a boye,shima cike da ladabi ya gaishe da Ammah ta amsa da sakin fuska suna hira sama sama,tunowa nayi ance tana son ta ganni a nutse to Bazan nutsu ba,Sai mutsu mutsu nakeyi muna hira da Ameer tare dasu Ma'eesha duk nafi kowa surutu,dan karma ace na nutsu nace Ma'eesha jibi akwai schl kema kin sani ki tabbatar kin mana wanki da guga na furta da masifa kuma da sauri irin ba nutsuwa,Ammah hirarsu sukeyi tare da Aayan da Yarima,Na dauko wayata ina dannawa,na mike na dauko wata kujera fara naki Zama waje daya naki yin shuru kar wai ace ma ina da nutsuwa, ita kuwa Ammah dadi take ta ta ji tana kallona irin na saki jikina a gidanta sai harkata nake yi,Meenat ma da sauran haka suna ta kin dadi.
   Aayan ya zo gefena ya rada min Ammah fa bata so a shigar mata Palo da Bedroom shi yasa tunda taji na mata waya zamu zo sai ta zauna a nan wajen sabo da kar ki je mata dakinta.
   Da gaske kake?yace ina miki karya ne ki kiyaye abinda zai bata mata rai zamu fita da Yarima zan dawo anjima mu tafi, Yarima tashi muje,Yarima yace Madam yau an manta damu? Sai lokacin na tuna bamu gaisa ba da sauri na gaishe shi ina bashi hakuri suka fice daga gidan a motar Yarima.

   Na tuna Ammah bata so a shigar mata Palo da dakinta kawai na tafi na shige can ciki ina ganin haduwar gidan da furniture din gaba daya,Ina haka naji Muryar Ammah a bayana tace Mufeeda ta wai kamar ba ke ba? Tausayi ta bani kawai naje na rungumeta harda hawayen farin ciki,nace kiyi hakuri Ammah kece nan kika yi mana haka me yasa haka? Kin samu kuka da damuwa,kuyi hakuri haka Allah ya tsara da ace banyi hakan ba baza ki taba yarda da auren nan ba,yanzu gashi kina zamanki da mijinki,nasan halinki Mufeeda kamar yunwar cikina,ko kin yarda anyi auren baza ki zauna ba matukar kin San inda zaki ganni,kuma cewa zakiyi sai kin kula dani,zaki dinga dorawa mijinki nauyi yayi tunanin baki da tarbiya,kuma ai gaskiya ce har fa auren kasuwanci kikayi da ina raye yana hanaki kudin zaki barshi,haka kuma akan kudi nasanki ba mutunci,har auren Kasuwanci kika yarda kika yi,shi yasa yana fada min kin yarda da auren kasuwanci nasan kawai son kudin naki yayi yawa shi yasa kawai nace ace miki na rasu naga yanda kudin zasu amfaneki,nayi tunanin tun daga Ranar zakiyi nadama Ashe sai kika ci gaba da son kudin ki dole sai kin ci kudinsa,yanzu ba gashi Mufeeda na ta Zama Babba ba,ta girma,tayi hankali,da mijinta,tana zamanta lfy,tana karatu,ba ruwanta da harkar son kudi rayuwarki ta gyaru Alhmdllh.

   Tafiyar da nayi nace ace muku na rasu nan ma ba iya akan kanki bane akwai wani abu a kasa amma zan fada muku sai lokaci yayi zaku sani insha'allah,Yanzu Aayan ya sanar dani rashin lafiyar babansa akwai wani me maganin gargajiya can kauyenmu Insha'allah wani satin zamuje a kaishi ko za a dace,Allah ya kaimu nace Ammah wai Allah yanzu kece? Na furta ina shafa jikin Ammah,tana dariya tace nice ko kin tuna sanda kike kaini toilet ki dauko ni? Sannu Ammah kinji kinga yanda kika kara kyau da haske Ashe kema fara ce Ammah amma da kinyi duhu, bedroom muka kule da Ammah ta bani labari kaf tun daga yanda Aayan da Yarima sukayi ta dawainiya da ita a turai,Aayan ya kashe mata kudi,yanda ya dauketa kamar Uwarsa yake kula da ita kullum sai sunyi waya ba fashi,gashi komai akan lokaci,abinda Aayan yayiwa Ammah ko uwarsa ce abinda zai mata kenan,Ammah ta fada min irin jin dadin rayuwar da ta shiga a turai,tunda naji haka Aayan ya kara shiga raina,na kara bashi wani matsayi na daban,sonsa da kaunarsa ya kara mamayeni,nan take na fara kukan dadi nace Ammah Allah ya taimakeni ban taba wulakanta mijina ba,shi yasa ake son ko yaushe kayi me kyau,da yanzu kunyarsa zanji,Murmushi Ammah tayi na manya tace abinda naji irin son da kike masa har muna waya ina jiyo muryarki wai wace? Macece?kyakyawa ce? Dariya nayi tare da rufe Idona da tafukan hannuna,Mufeeda an girma,nima na zauna na bata labarin kaf bayan rabuwarmu wanda su Meenat basu bata ba na sanar mata,tace Allah ne yake tsare min Ku Allah yaga halin da muke ciki kuma yaga zuciyar kowa,sai mu kara dagewa da addua,yini mukayi muna ta hira da Ammah ba ji ba gani ina kwance a cinyarta muna labari,tana kara koya min yanda zan kula da mijina da gyaran jiki,Wasu magungunan tsumi data hada min ta bani katuwar leda guda da yanda zanyi amfani dasu,tace ga akwatunan lefanki can ki tambayi Meenat suna dakinsu guda goma sha biyar mijinki yayi miki a wajena ya hadasu can turai ni na hana a baki wancan lokacin sabo da baki hankali ba,yanzu kuma ya hada komai ya barsu wajena,akwati biyu kuma tsarabarki ce ni na siyo miki,Sauran kuma guda hudu nasu Meenat ne nayi musu baya min komai na nuna musu,Ammah to kayanki na gani cikin Sip na sawa ga wasu a akwatuna yaushe kika dinka? Aikin Mijinki ne gaba daya tare da Yarima.
   Ammah Yarima fa Ma'eesha yake so,ae na sani ai ya fada min rannan ma babarshi tazo wajena mun dade da ita mutanen kirki ne ai,yanzu Ammah Meenat ce kadai ta rage,dariya tayi tace tun yaushe Mijinki yace min yayi mata miji wai shi ya samo mata ban san dai waye ba,Nace ni gaskiya a'a wlh Ameer zan bawa ita sun dace kuma baki ga taimakon da yake mana ba,to Aayan ya rigaki zabin Aayan zata aura Insha'allah cewar Ammah,kamata yayi ma su dawo gida wajena Mufeeda kinga an takurawa mijinki bazai sake ba,kai Ammah ni ki bar min su dan Allah,Bakya gane me nake nufi Mufeeda sabo dake fa nake komai da bakya min musu duk abinda nace shi kike yi me yasa kike haka yanzu?kiyi hakuri su dawo zaki gane me nake nufi,to shike nan Yaushe kike so? Yanzu suje su kwaso kayansu idan nace gobe kuka zakiyi in zasuyi miki Sallama gwara kina nan gidan,Nan take kuwa suka tafi da Ameer suka kwaso nasu ya nasu tas har akwatunan da Ammah ta ciko musu da kaya,na gani kaya masu kyau da tsada duk gasu nan iri iri,nawa kuma an bar min su a gidana.

    Aayan ne ya basu Driver guda da mota dalleliya ta gaske za a dinga kai su Meenat schl da kuma unguwa har Ammah.
   Su Meenat ne sukayi Dinner Ameer yace dama shima a barshi a gidan Ammah da yafiye masa,nace ai kuwa baka isa ba sai dai ka dinga zuwa kullum,Bayan munyi sallar Isha Ammah tace bana son shaye shayen maganin matan nan barkatai,wanda na baki sun isa ni na hada da kaina da yayan itatuwa,zan koya miki wasu ki kiyaye kinji,nace to,Dauko ki fara shan wasu yanzu ko period kikeyi cike da kunya nace a'a,ta bani wasu nasha tace nayi matsi da wasu duk nayi ina zaune muka ci abinci da komai,ba na so ma na koma gida nafi so na kwana wurin Ammah muyi ta hira ina jin dadi,nace Ammah Abbanmu fa?, Nan take Ammah ta bata rai karki kara yi min zancensa,gidan nan kuma da kike gani na sa an siyar dashi na kai kudin wajen danginsa dama shike nan abinda ya mallaka tare da yan uwansa mukayi shawara,Ammah idan ya mutu fa ya Zama gado fa? Nan gaba zan muku baya ni karku damu,nace to ba damuwa.

    8:30pm sai ga Aayan ya shigo da Sallama idonsa na kaina, yace Ammah Yarima yace bazai samu Damar shigowa ba sai gobe zai zo,ba damuwa ai yana kokari ma kullum sai yazo,Aayan ya kalleni yaga ina jikin  Ammah a kwance nayi rashe rashe ina danna waya,tashi mu tafi gida,Baki na turo gaba ina shagwaba nace anan zan kwana ni sai nayi kwana uku zan dawo,Su Ma'eesha duk sakin baki sukayi suna kallon irin yanda nake kashe murya,Ammah tace tashi ke ku tafi bana son shashanci shi yasa nasan da ina kasar nan zaman auren ma gagararki zaiyi gashi daga dawo wata zaki fara,Ameer kuwa shima tuni ya tafi gida yace sai gobe.

   Aayan na kalla nace dan Allah fa nace sai gobe to ka dawo mu tafi,Har gida Ammah tazo yanda zaki ganta kika ki yarda sai yanzu zaki ce wani kaza kaza,tashi mu tafi kin ma san bazan iya kyaleki ba,Ammah tace ka daina bata bakinka tasar min a cinya ku tafi, gani Ammah tayi ina bata lokaci tace Meenat kuje Ku kwanta suka tashi suka wuce tare da ce min sis sai da safe zamu zo,Na Galla musu Harara nace dalla...dalla..dalla kuje can ku rufe min baki,ance muku bazan iya zama ni kadai ba ko aikin nawa bazan iya ba na gida,Dariya sukayi suka wuce suna yiwa Aayan sai da safe.
    Ammah ma tureni tayi daga jikinta ta shige dakinta sukayi Sallama da Aayan tace ka rufe mana kofar,Daukan kayan da Ammah ta bani yayi tare da mayafina ,jakata da takalmina har dankwalina,cikin mota ya kaisu ya dawo ya daukeni cancak tare da cewa zaki san kin min musu yau Allah ya kaimu gida,ina magana kina min musu ko,nace wayyo na tuba Allah ni na isa,wlh wasa nakeyi na tuba pls My Man bazan kara ba,yace ai kin jawowa kanki yau.
  Kin san dai Bana son ina magana ana min musu dan kinga Ammah na wajen ko? Da sauri nace a'a am so sorry bazan kara ba.





AsmaBaffa
[2/5, 4:50 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

    KASUWANCI NA





           111-112






Official





By
AsmaBaffa


    AUNTY SUMEE and NAFI ga page nakune an kara muku.

    KASUWANCI NA FANS ina godiya da Jinjina gareku,masu Sharhi kuna birgeni sosai.😍😍😍







          Gaban mota Aayan ya bude tare da sani a hankali ya gyara min Zama tare da rufewa,komawa yayi ya shiga shima sannan ya figi mota muka bar gidan,sai da yayi mana take Away na kayan lashe lashe sannan muka nufi gida,Allah sarki Ameer yau ba abokan hirar tasa duk gidan sai yaji ba dadi,sai yanzu ya tuno da yan uwansa Frnds dinsa Su Mujaheed,Ummansa ya tuna tare dasu Abbi amma me zai musu tunda sune suka koreshi da kansu,Muna dawowa ni na kwashi wasu kayan shima ya dauka muka shiga ciki,a Bedroom muka ajiye komai muryarsa naji yace tashi muyi wanka,kunya nakeji amma haka na dan daure muka cire kayan mu tare da daura Towel, Aayan so yake kawai ya fisge towel dina ni kuma naki yarda,sai da ya shammace ni ya fisgo dan towel din Allah yasa na rike kam ina kallonsa ta gefen Ido,Dariya nayi nace woo ai ina kallonka dai, da gudu na matsa ya biyoni dole sai ya cire min Towel dariya mukeyi gaba daya har muka shige Toilet,Wanka mukayi tare kusan ma ni nayi masa komai sannan muka fito,bayan mun shirya tsaf damu Nafeela zamu fara nace tsaya a bawa Ameer takeaway dinsa shima kar yayi bacci,kyaleshi yanzu ma maybe yayi bacci kuma yaci abinci gidan Ammah.

   A'a amma ai alhakinsa a kanmu yake tunda kai kake masa komai ko bazai ci ba a bashi shima,kawo na kai masa cewar Aayan,ko da yaje ma Ameer dama yunwa yake ji a gidan Ammah bai tsaya yaci abincin ba,tnx yace Aayan ya dawo mukayi Nafeela raka'a biyu sannan muma muka ci kadan Namu sabo da a koshe muke, nayi mamaki yau da Aayan ya kyaleni naji yace naga kin gaji ne, ganin na gaji Tausa ma ya shiga yi min ina lumshe ido kawai bacci me dadi ya kwashe ni,shima bai San sanda ya fara baccin ba, Da Asuba ni fara farkawa da sauri nayi wanka tare da brush sabo da naji na fara period,sai da na fito bayan na shirya kaina na tashi Aayan yayi shima wanka da komai ya fito yayi Sallah tare da azkhar nima duk da banyi sallar ba nayi azkhar dina,Juyowa yayi yana kallona tare da cewa Period kike kuma? Nace ae da Asuba na fara,na ma yi tunanin kin samu ciki,nace wanne ciki tun yanzu ai yayi sauri,Murmushi yayi tare da cewa ba wani sauri a rana daya ma zaki iya samu,yanzu ya zakiyi dani sai da na kyaleki jiya kika huta na gama tanadin yau da safe sai kuma ki wani fara period naji haushi ya karasa kamar wata mace tana shagwaba,dariya na shiga yi sabo da ya bani dariya maganar tasa,na kalleshi cike da so shima haka nace sai dai kazo muyi Romancing zansa kaji dadi Allah sai ma yafi wanda kake so,bazai fi wanda nake bukata ba ke kin San dadin dayan kuwa,Yana saman Sallaya a zaune na koma tare da sakalo da hannayena ta wuyansa na kwanta a bayansa,Ajiyar zuciya ya saki,fuskata tana a wuyansa ina goga masa,Saman bed ya daurani ya shiga murzani cike da kwarewa nima haka ba abinda Bana yi masa har wanda ma ban taba yi masa ba duk yau na dage nayi masa sai da na zautar dashi,Sucking na masa last a nan kuma yace yama fi komai sweet,sai Santi yakeyi ya rude gaba daya,Sai da nasa ya samu nutsuwa kwarai da gaske yana ta jin dadi yana sa min albarka tare da zafafan kalamai.

    Ina kwance a jikinsa muna hutawa na manna masa kiss a wuya nace na gode My Man ban ma san da me zan fara gode maka ba,ka gama min komai,abinda kayiwa Ammah,dangina,yan Uwa da duk Wanda ya shafeni bare kuma ni kaina,ban san me zance ba kafi karfin godiya a wajena, shiiiii naji yace kin wuce haka a wajena kasa ganewa kikayi lokacin ta kasuwancinki kikeyi,Dariya nayi nace Allah ba wani nan,ai kaima ba so na kakeyi ba da,ni ai ba kece bana so ba aure ne Bana so a lokacin kinji nace bana Sonki?sai dai nace bana son aure kece baki gane ba,gashi kin canja min rayuwa da tsari kin kawo min farin ciki wanda na kasa samu,kin yarda kin zauna dani duk da cewa ina bata miki amma kinyi hakuri,d angina duk abinda suke miki kin iya jurewa ai Alhmdllh
   Addua kawai zamuyi Allah ya barmu tare Babyna,nace Insha'allah kuwa,dan Allah kayi ta sona kaji ni bana son ka kula kowa,ke zaki dage ai ki hanani kula kowa ta hanyar yin abinda ya dace ace matar aure ta gari tana yiwa mijinta shike nan.
     Yau banyi dogon baccin safe ba,da wuri na Mike na shiga kitchen na shirya breakfast sannan na gyara ciki ko ina,naje nayi wanka naci kwalliya cikin material black and red nayi kyau,sai kamshi nakeyi ina kitchen ina kokarin shirya Dining,naji Kamshin Aayan kafin nayi wani motsi naji ya rungumeni ta baya yana shinshina wuyana,abinda ko kitchen baya wani shigowa sai yau Ashe sabo da su Meenat ne baya shigowa sabo da kunyar idonsu ba komai zaiyi a gabansu ba,lallai Ammah ta iya gyara Harka na furta a zuciyata Ashe a fili nayi maganar,Murmushi yayi me Sauti yace kin ganki baki da kunya fa kema,Juyowa na nayi tare da boye fuskata a kirjinsa,nace Saura Ameer ma,Baki ya tabe yace ai Ameer ba ruwansa shi har ya canja part jiya in baki sani ba yana daya part din tare da Daddy wai yace Meenat basa nan me zaiyi,Amma ya bani aiki abincinfa sai na kai har can da yar tafiya fa,ga mata nan a gidan ma'aikata nace ya zabi guda ta dinga masa,Amma yau dashi fa nayi ka kirashi a waya yaci a nan,Aayan yace zancen kike so Ameer wai danki ne ko yaro ne shi da kike damun kanki ai ni kadai zakiyiwa wannan.
   Shike nan muje to tare dashi muka shirya komai a Dining, cup din tea dinmu daya,plate na farfesu tare dasu chips duk daya ne tare muka ciyar da juna.a Binda nakeyi wajen kula da Ameer da Daddy ba karamin birge Aayan nakeyi ba,hakan yana sawa ya kara so na Sabo da yanda wasu matan ke wulakanta dangi da iyayen mijinsu,ko kuma miji yana rike wata ko wani a wajensa abinci ma idan bai ce a bashi ba baza a kula shi ba,ko a dinga takura musu ga aike komai na wahala su za a Sa,bare miji yazo dasu nama tare da kayan dadi irin su gashashiyar kaza,yogourt etc wanda ake rikewa a gidan bazai ji ko kamshi ba sai dai idan danginta ne wannan su za a basu,amma sai gashi ni dole duk abinda zamu ci sai na bawa Ameer nasa duk da cewa Saurayin matashi ne,nasan zai iya siya ma yaci a waje tunda da kudinsa,Daddy ma dan kalar abincinsa daban ne,kuma na turawa yake ci,masu dafa masa daban suke.
   Aayan ne ya kalleni tare da cewa  yau zanje Office Amma bazan dade ba da wuri zan dawo,Shagwaba na fara masa dan Allah ka tafi dani kaji,ki zauna anjima su Meenat zasu zo miki fa,Ameer zai kawo miki su munyi waya da Ammah,baki na turo nace ai ni na tsanesu yanzu,haushinsu nakeji gaba daya.
    Dariya yayi yace ke fa kika ce Ammah ta iya gyara Harka yanzu kuma kina jin haushinsu ina son ranar da zanga Mufeeda tayi hankali ta daina kuruciya,wai shekarunki nawa? 18 fa nake yanzu,dole kiyi yan mata,kai fa? Dariya yayi yace kin girmeni ai,nace lallai Ashe saurin girma kayi amma dai nasan ka girmeni dan Allah shekararka nawa? Yace 20, dariya na dinga yi nace Ashe ma kusan sa'a na ne ai da kadan ka girmeni,gaskiya kayi mugun saurin girma na shafa sajensa da gemu nace harda gemu na kyalkyale da dariya,shi kanshi dariya na bashi taya zan kalleshi na yarda 20yrs yake inba kuruciya ba.

    Nace to muyi goyo goyo dama ni ina yarinya banyi wasanni ba sabo da neman kudi kullum a business nake kaga yanzu sai nayi kara'i tunda mate ne kusan ni da kai,Wai kasuwancin nan naki me Dame kike siyarwa? Dariya nayi nace komai,nan na fara masa lissafin irin abubuwan da na siyar,da komai da komai har lokacin dana fara ganinsa na dawo daga kasuwa,da irin Algus din danayi ina zubawa kosai garrin kwaki da jar color a ganshi sutu sutu jajir sai ace yasha kayan miya😍da wahalar da muka Sha har lokacin da yake yawan ganina gidajen yan siyasa,Sai ga Aayan yana hawaye wai na tausayi,ni kaina dana tuna abin sai danayi kwalla,tun daga farkon rayuwarmu na bashi labarin komai, dariyar karfin Hali nayi nace kalli kana kwalla kamar ba namiji ba,da sauri ya goge tare da cewa tausayi kuka bani,amma gaskiya an raina miki hankali ma da muke cewa kina da son kudi, jikinsa ya jawoni na kwanta yana rada min words masu sanyi da kwantar da hankali yace I love u ,love u more My Man,bana son fita ma ina da meeting ne ba yanda zanyi,nace never mind zan iya zama, yace Ok harda tsokanata wai idan na tafi ki cinye abincin nan du tunda bakya iya cin abincin a gabana,dariya nayi nace ka tuna cin abincina a gidanka farko daka sace ni? Dariya yayi shima yace ai naga yanzu kin daina wai dan Allah a lokacin nan kuma kalau kike?nace ras ma kayan dadi ne da ban saba ci ba kuma dama ni inada ci da yawa,lokacin idan naga kayan dadi ko cikina zai fashe sai na cinye,Dariya mukeyi,amma yanzu kin daina ci da yawa amma dai ba laifi akwai cin nan yana nan, ga iya cin abinci abinci a kitchen,sai azo ayi ta min yanga ashe kin gama koshi a tukunya, dariya na dingayi ina rufe fuska tare da cewa ashe ka sani? Ka kureni lallai kamar Aljani haka kake Allah,amma ai gwara naci na koshi ko? Murmushi yayi tare da tura hannunsa a rigata yana wasa da Boobs dina yace ai nafi so wannan su kara girma kullum su zauna a haka kar su rame, oya muje ki rakani zan wuce,Sai da ya kara brush tare da gyara wankansa sannan na rakashi har mota,nan ma a ciki haka muka dinga kissing din juna kamar baza mu rabu ba da kyar na kyaleshi ya tafi ina daga masa hannu.

    Ban dade da dawowa ciki ba na gyara upstair dinmu komai kamshi yake a gidan,sai ga su Meenat tare da Ameer sun shigo suna kwala min kira, fitowa nayi cike da murna nace Ina Ma'eesha kuma? Saloon zata je gobe akwai schl,Ameer ka gujeni yanzu gida daya amma su Meenat sun fini ganinka,Haba Anty ni na isa damuna tayi da waya tayi missing dinki nazo na kawota, mene a flask din nan? Ammah ce tace a kawo miki kunun gyada ne,Godiya nayi na karba tare da kaiwa kitchen,Meenat ta kalli Ameer bari na gano Dakinmu Allah sarki nayi missing dinsa,kyaji dashi cewar Ameer, abincinka fa Ameer tun safe baka nema ba,a gidan su Meenat nayi Breakfast fa Anty,nace lallai Ameer dakai ma za a hada baki a gujeni ka kyauta,dariya mukayi gaba daya, nace ban baka labari ba My Man fa ya min kayan lefe baka gansu ba sun hadu,Ameer yace ai Meenat ta bani labarinsu,munafuka har ta fesa maka? Dariya yake yace haba Anty Ba munafunci tayi ba.

   Magana nayi ba alamar wasa nace Ameer wai Aayan ya maka mata? Ameer yace ni din? Ban San zancen bama,nace to na rigashi ko yace ya baka mata kace na rigada nayi maka mata ni, Ameer dariya yayi yana tunanin wasa nake,nace wlh ba wasa nake ba,Anty wacece takin da kika Zaba to? Nace Meenat,ido ya zaro tare da cewa a'a gaskiya ai masifa zata ta yi min bakya ganin ta rainani gwara dai naji idan ta Ya Aayan tafi sai na karbeta Amma Meenat kina ganin yanda take iyayi tana ji da kanta,dariya nayi nace to ai kafi Meenat iyayi kai,i dan kuma bata sona fa? Nace a'a kai dai kace kawai Zabin Aayan kake so shine dan uwanka,Ameer yace haba dai ai wlh nafi son zabinki Anty,to ko Meenat dince baka so? Ni na Isa yanda take me kyau haka da tarbiya ai ta fiki kyau ma Anty sai yanzu na gane duk Meenat tafiku kyau,Dariya nayi nace karya kake kuma wannan a wajenka dai zaka ce amma a wajen Aayan nice gaba,haka Yarima kuma Ma'eesha ce,muna Hira sama sama sai ga Meenat ta fito tare da daukan uban wanka,da mamaki na kalleta nace dama kuna da kaya a gidan nan ne? Ina kuma kika samu gown haka? aro nayi cikin na lefenki,nace aiko baki isa ba koma ki cire tun ma kafin Mijina ya dawo ya ganta a jikinki ban masa kwalliya da ita ba,Dariya tayi tace to wasa nake da abata nazo a jaka ko Ya Ameer?yace kwarai yana daga kai da sauri kamar uwarsace na magana.

     Gefen Ameer ta zauna tare da masa magana kasa kasa ba a jin me suke cewa sai gani nayi sun Mike wai zamuje mu dawo,nace ina? Ammah ta sani fa gidan kawata, dama ba wajena kuka zo ba ashe,yanzu fa zamu dawo am serious,sai kun dawo to,suna fita sai ga kiran Aayan ya shigo wayata.
   Dagawa nayi fuskata dauke da murmushi na rangada Sallama cikin muryar da nasan ina zuke masa numfashi,zaki sa na dawo Sweet Heart,wannan murya me zaki haka ,Ya Office to,Yace alhmdllh,good kace da wuri zaka dawo amma shuru am missing u,Wani sanyi yaji a ransa yace 2pm zan gama  just wait for me I wl be thr,Fari nayi da Ido kamar yana kallona nace Allah ya kaimu,me zaka ci? Kin san me nake so just make something delicious for me Baby,alright Insha'allah zanyi,kiss ya sakar min ta waya nima na aika masa,ina kukan shagwabata can kasa kasa nace kaga su meenat sunzo sunyi tafiyarsu yawonsu gidan kawaye dama ba wajena suka zo ba kuma tsoro nake ji Daddy yayi nisa da part dinmu da sai naje wajensa muyi hira. Laifin Ameer ne bari na kirashi sannan ya kashe kamar kar mu rabu,nan take ya kira Ameer yana ta Masifa Lallai su dawo su tayani Zama kafin ya dawo,ko Minti 10 Meenat batayi a gidan kawarta ba ta fito Ameer ya dawo dasu yana bata labarin masifar da Aayan ke yi, suna dawowa na dinga musu dariya, kitchen na shiga na fara shiryawa Mijina abincin da nasan yafi so fiye da ko wanne.

     12am cikin dare Hajja ce ta fito direct dakin Mazan gidan ta shiga sabo da wai dole sai ta kama Aliyu da Sabeer,Suna ta bacci gasu nan birjik wasu a shimfida kasa wasu saman katifa,Sabeer yana bacci sai duka yaji a gadon bayansa,yana bude ido yaga Hajja ce sai ya kara shigewa bargo,Hajja ta girgiza shi amma yaki tashi sai ma maganganu da yake wai na mafarki,kan Aliyu ta koma ta fara tashinsa,Aliyu dama ba a tashinsa a bacci magagi ne dashi idan ya farka sai ya rufe mutum da duka kuma a bacci, yana farkawa ya rufe Hajja da duka gashi Namiji hannunsa Zafi ba shiri Hajja ta kwace da kyar ta bar dakin da dan gudunta,Abbi kwana uku kenan yana fita duk inda yasan zai ga Ameer da mutanen da zai tambaya amma babu labarinsa,yauma gwiwa ba kwari ya dawo gida ana Palo a zaune kowa da abinda yakeyi Abbi ya wuce a fusace ta palon ana masa sannu da zuwa ba wanda ya saurara ya kara gaba cikin Bedroom.

    Mujaheed ya bude sabuwar Rezarsa yana yanke farcensa tun kafin ya yanke yatsa daya sai ga Meenal tace idan ka gama dan Allah ka bani na yanke wani farce da ya taso min yaki cirewa, Aliyu yace idan kin gama ki bani nima na yanke nawa,Wata uwar Harara Mujaheed ya zabga musu tare da cewa jarabar gida ko Kashi ka taba sai wani yace ka San masa zai taba shima ba tunanin ma cuta ta shige ku ko ina da ita ku kawai a baku.
   Yana gama yankewa Sajeeda ta karbe ta gama ta mikawa Aliyu,Aliyu ma ya gama ya bawa Meenal,ta gama ta dan ajiyeta a gefen kujera sai ko yar karama Juwairiya ma ta dauke harda zuwa ta kyasta Ashana ta konata wai ta kashe cutar jiki duk kan rezar ya disashe ba kaifi amma haka ta yanke da kyar.
   Khaleel kuwa wanka yakeyi ana ta jiran botiki ya fito ya bayar amma yaki fitowa yan matan duk da daura kirji suna jiran botiki, yana fitowa ya kallesu wai sabulunsa ake jira haka da botiki,sabulun ma duk ya gama narkewa Saura kadan,Ba tambaya ba komai Haneefa ta fisge tare da lakeshi a jikin sosonta,Sabeer ya faki idonta ya fisge har soson nata dama sabulun yana manne jiki bazai fita ba,haka ya shige wankansa yayi da sosonta,Khaleel baki bude yake kallonsu yace wai Ku ina sabulun da aka siya ne shekaran jiya?kowa an bashi nasa fa,sukace to ga wanka ga wankin su Inner wears ya zamuyi duk karewa sukeyi sabo da wanki kasan dai mata ba irin maza bane,kuma wlh gidan nan satar sabulu akeyi da nawa dana Meenal sacewa akayi,Aliyu yana daga Toilet yace nima wlh ina ajiye nawa jiya kafin na je Palo na dawo an dauke kuma Dan masifa ka rasa waye,Abbi ne ya fito tare da cewa wa dauki toothpaste sabo wani karami MyMy a saman gado na? Kowa yace ba shi bane,yace wlh duk Wanda bai fito dashi ba sai na kai sunansa wajen Malami ya mutu kafin safiya,Ko cikinsa ya kumbura dam cikin dare yayi ta tsaga ihu sai ya fito dashi,yan iska barayi,to wlh ban haifi barawo ba,da mu zauna da barawo gwara ya mutu,na gaji da sace sace da akeyi a gidan nan,dan Bala'i ko Guba ce a gidan nan ka ajiye sai an sata,to ko a fito dashi ko gobe wanda ya dauka ya mutu,Dama Juwairiya ce Ashe ta sace bata fi 14yrs ba bata da wayo jin ance mutum zai mutu ko cikinsa ya kumbura sai ta faki Ido ta dakko tace bari na tayaka dubawa Abbi tana shiga dakin ta daga Haukarsa ta sa a ciki,Abbi ya yarda da yarinyar ai yara baza su dauka ba manya ne,tace Abbi ka ganshi kasan hularka idonka ne tsufa ya kamashi,Abbi yace to jeki lallai hankali shi ke gani yarinya,Allah ya taimakesu da yau wani sai ya mutu a gidan nan,yarinya tace Abbi ko yayanka ne?yace kwarai kuwa.

     Haka suka dinga layin wanka jikin mudubin dakin matan kowa ke shiga sabo da Vaseline din Meenal duk sun jere a wajen kowa na shafawa mata da maza,Dan Allah Khaleel ka matsa haka duk ka tare wajen sai wani taje suma kakeyi kazama da ita,Khaleel yace da Namu gashin da naku mata waye nasa yafi tsafta mu kullum sai kanmu yaga ruwa,ku fa mata wata ma sai tayi 3wk gashinta bai ga ruwa ba,kazamai shi yasa Bana son mace ta matso min da kanta kusa dani,Kazamai ba cewar Haneefa amma ba irinmu ba,dariya Khaleel yayi sabulu iri daya dai muke wanka hakan ma ni nake baku na wanki,shi dama Khaleel sabo da sabulu ya dade baya siyen na wanka na wanki yake siya yanzu ga araha gashi kato a dade ana wanka.
    Da su Sabeer zasu siyo sabulu cikin kudin da suka damfari Hajja Khaleel yace kar a siyo masa sabulun wanka na wanki yake so gaba daya,ai kuwa kowa sabulun wanka daya dana wanki daya amma Khaleel nasa Sabulan wanki har guda Hudu da kudinsa shi yasa yake shanawa da abinsa duk an takura masa da aro.

    Washe gari ma sabo na wanki ya fito dashi yayi wankansa,Abbi Sani da Abbin yara duk karbewa sukayi dashi sukayi wanka,dama Khaleel da yaji kira yasan sabulunsa za a karba,shi yasa ma ana cewa Khaleel sai ya dauki Sabulun ya tafi wajen kiran.
   Yauma suna zaune a Palo Abbi Mustapha ya kwala masa kira da sauri ya koma daki ya dauko sabulun Sodarsa na wanki yana kumbura baki yaje tare da cewa gashi ai kuwa Abbi yace yawwa dama kiran kenan jeka, Khaleel ya juyo yana masifa dama nasan kiran kenan,Me ake mana a gidan ba asan a bamu hakkin mu ba,muna bukatar kayan sawa,takalma,kudin kashewa,bare azo kan su mota gida da aure duk banyi wannan yanzu ba sai yaushe zanyi kenan gashi kullum tsufa kamamu yakeyi ace na wuce 30yrs sai yaushe zanyi kudin bare aure gaba daya ma basa ta mu ta Kansu sukeyi

   Mujaheed yace ai ko su Sabeer sun isa aure to bamu da aikin yi bare mu tallafa musu suma ina ma muka iya da kanmu sabulu yana gagararmu,na buga lissafin yaki bullewa, gashi jarabar dangin duk talakawa bare su tallafa cewar Khaleel,Khaleel yace da ace muna da yan Uwa a lagos da wlh tafiya zanyi na makale a wajen wani ko zan samu abin yi,Sabeer yace ina duk suna kauye Wlh babu wani jinin birni ko ace a kudu suke bare muje neman agaji,Aikin ma yanzu sai da hanya zaka samu siyan Offer akeyi,Aliyu yace Ku Allah ma ya taimakeku kunji dadi kun gama Degree gashi har wasu kasar kunje ko ba komai kunci,mu fa?yanzu mukeyi mota ma lokacin Abbi hanawa yayi Aayan ya bamu wai zamu lalace,kai rabu dashi shi bamu San me yakeyi ba a wayarsa duk hotunan yan mata ne yan dagwas dagwas dasu yake chat,wata rannan duk talaucin nan a waya naji sunayi da Abbi wai zai aika mata da kudi za a bata kasonta, ita kuma tana Darling ayi sauri unguwa zanje fa😍😍,Allah Khaleel? Meenal ta tambaya yace tab ai kune mata kuna gida baku san me su Abbi sukeyi ba,mu mun San komai ke ai duk manyan nan dai dai ne na gari,musamman Abbi Sani kina ganinsa haka yan matan da yake kulawa bamu isa mu masu jini a jika muje ba,ai Duniyancinsu kawai sukeyi shuru mukeyi dan kar su Umma suji gwara a zauna lfy.
   Haneefa tace karuwai ne?to mene in ba Karuwan ba cewar Sabeer,rannan zaki ga wasu sanda muna wancan gidan sunzo muke cewa yan maula?ai ciki harda budurwar Abbi Musty,hhhh suka sheke da dariya wato Musty ma? Khaleel ne ya kalli skin dinsa dai dai lokacin Hajja ta fito da kwano a hannu,Khaleel yace rayuwa sai Imani tsohuwa kalli fatata yanda take komawa,yaushe zan ji dadi ne?ga duniya gudu takeyi,maza matasa mutuwa sukeyi tsoro nakeyi kar kwana na ya kare Hajja banyi aure naji me akeji ba,ke kinji dakinki da dan mijinki har kin haifi su Abbi ko? Mujaheed yace kai Hajja ance a zamaninta yar soyayya ce baka ga duk jahilcin mutanen da sai da Hajja ta auri Bature Baban Daddy,Sajeeda tace Allah dai ya biya Hajja anci duniya,s una ta dariya Mujaheed yace ai da munyi rako duniya kuwa idan bamuyi aure ba munji me ake ji muma,Hajja tsaki taja tace yan iskan banza tayi gaba, Mujaheed yace kai yanzu Men cuta ta kama wani a cikin halin da muke ciki ai shike nan kuma sai mutuwa wlh ana kallo zai mutu ba kudin magani,

tagumi Khaleel yayi yace Shege Ameer yana can Allah ya Zabe shi,Haneefa tace idan zamuyi aure yayi mana kayan daki,Khaleel yace a yau naga dama sai na nemo inda Ameer yake wlh amma bazan nemo shi ba duk muci wahalar tare sai kowa ya gane kurensa a gidan nan,Mujaheed yace wlh ana nemoshi tsohuwar nan dasu Abbi zasu koma takurawa mutane kyalesu iyakaci idan mun gaji mu fece wajen Ameer mu barsu.
   Sajeeda tace sai na fadawa Abbi,Khaleel yace fadi dan Allah wlh da sai na barar dake a gidan nan dama cike nake da zafin talauci,Hajja ce ta fito tare da cafko wuyan rigar Sabeer tare da cewa ina kudina dan Ubanka,Sabeer yace  Hajja wai ance miki kudi ne suka makale a Internet zasu zo ta rigada ta turo su suna hanya,Hajja tana zaro Ido tace yaushe zasu iso? Aliyu yace nan da kwana Uku ko hudu,Hajja tace Allah ya kaimu wlh idan basu zo ba sai nayi maganinku,Su Khaleel suna ta dariya Hajja tace zaku ci ubanku gaba daya a gidan nan wlh sai nayi maganinku,dariya sukayi gaba daya tare da cewa hooo Hajja Rayuwa sai Imani, Banza tayi dasu sannan tayi gaba zuciyarta na suya,

A kwana a tashi tun su Khaleel basa tunanin neman aiki har suka yi shawara gwara su nemi na Kansu wahalar ta ishesu haka,amma kuma ta ina zasu fara neman na kan nasu.
   Waye ya daukar min takalmina?Mujaheed yana cigiya,ya fito da masifa Haneefa tace Aliyu ne yasa ya tafi schl,tsaki yaja yanzu sai na jira shi ya dawo gidan nan dan masifa idan kana da abu kowa sai yayi amfani dashi,hakuri zakayi lokacin da muke gidan jin dadi wa yake kula kayan wani kowa da nasa cewar Abbi dake zaune yana jinsu.

    Yau Saturday ba schl tunda dama mun koma hutu,Meenat kuwa tayi Candy wata za a nemo mata University, Ina wajen Daddy Muna hira yace 'yata ki daure kiyi min wani aiki,nace Na mene Daddy? Aayan zaki sa ya dawo dasu Hajja gida tare da yan uwansa,bai dace hakan ba,babu wanda ya isa ya shiryar da wani sai Allah,kuma ba lallai wahala ce kadai ke sawa a shiryu ba,wasu wahala bata sawa su shiryu sai Allah ya so,tunda Allah ya kare mu kawai ya kyalesu a kwai lokacin da komai zai wuce,kuma yanzu ko sun dawo ba abinda zasu iya yi,baza mu zauna gida daya dasu ba kawai ya dawo min dasu kowa ya koma bakin aikinsa abinda nake roko a wajenki kenan tunda yana daukan shawararki watakil idan kece sai ya yarda,Sai da Daddy ya kashe min jiki da nasiha tare da nuna min Muhimmancin yan Uwa da iyaye dole nace Insha'allah Allah zasu dawo Daddy ka daina damuwa.
   Haka muka rabu da Daddy ina tunanin ta ya zan iya sa Aayan ya hakura yanda yayi fushi dasu Haka.
   Ameer na kira a waya nace yazo ina nemansa,da wuri kuwa sai gashi yazo,bayan mun gaisa nace kasan inda su Abbi suka koma?Ameer yace ae mana na sani kusan kullum ma ina wucewar ta layin kuma ina bibiyar halin da suke ciki,amma baka shiga wajensu ba?yace ae wlh sabo da bari nayi su kara dan nutsuwa sai na fara zuwa wajensu kawai sai naga Ameer yana Hawaye,nace subhanallah Ameer lfy? Allah Anty tausayi suka bani baki ga halin da suke ciki ba,sabo da ko kayan sawa Aayan bai bari sun dauka ba,suna cikin wani Hali,yan uwana ne mun shaku dasu sosai tare muke komai dole bana jin dadin ganinsu cikin wannan yanayi wlh musamman su Khaleel,ni kaina sai naji tausayinsu duk da ban gansu ba ganin yanda Ameer yake ta hawaye,yana fada min halin da suka shiga ga Iyayensu mata sunyi yaji yana gama fada min ya goge Hawayensa yace Anty dan Allah kisa ya dawo dasu ko me zasu yi Kansu Allah yana ganin komai bare nasan yaran gidan duk sun shiryu su Abbi da Hajja ne kawai ban sani ba.
   Numfashi Naja tare da cewa tsaya mu tafi gidan nasu,waya na dauka tare da kiran Aayan nace My Man ya aiki?yace alhmdllh Babyna kinyi missing dina?nace sosai ma,dan Allah unguwa Ameer zai kaini idan ka yarda,idan na dawo zan maka bayani inda muka je kaji,ba damuwa sai kun dawo.

   Godiya nayi sannan na shirya tare da daukan wanka cikin tsadajjen lace kamar a saceni nasa glass na yayi brown me tsada nayi kyau sosai kai kace yar Gomna ce gaban motar Ameer na shiga muka tafi har gidan dasu Abbi suke,a kofar gidan mukayi parking,Ameer na kalla har ya fara shirin zubo da hawaye wai na tausayin yan Uwansa,nace dan Allah karka karya musu zuciya pls ka daure kamar ba namiji ba,bazan iya shiga gidan ba Anty jeki ki fito ina jiranki,wucewa nayi ina taku dai dai kwas kwas,tun daga tsakar gida na fara Jin tausayinsu ganin su Haneefa kwance saman tabarma jikin bishiya duk sun rame sunyi duhu gashi duk gayun nan babu sunyi shuru sunyi tagumi,kallo daya sukayi min suka ganeni,da Sauri suka mike zaune,da fara'a suka ce sannu da zuwa Mufeeda,kece yau a nan?wa ya nuna miki gidan?da Ya Aayan kuke tare? Nace a'a ni da Ameer ne nace ya kawo ni tunda ku baza kuzo mana ba,da Sauri suka jani har palo,suna kiran kowa na gidan Maza da matan,Kahaleel duk iyayi da gayu babu naji tausayinsu kowa da fara'a da mutunci muka gaisa muna Hira,abinda bamu taba yi dasu ba kenan,Ruwa suka kamfato min a cup na roba,na karba ba tare da na nuna kyama ba nasha haka,sai murna sukeyi kamar sunga daren lailatul qadri.

   Hajja ce ta fito tana wacece a gidan bakuwa mukayi,ido muka hada da ita nan take ta bata fuska tare da Galla min harara taja tsaki sannan ta juya cikin daki abinta,khaleel yace share ta me bakar zuciya,dariya mukayi gaba daya,sai ga Abbi su ukun duka sun fito Haneefa ta kirawosu Matar Aayan tazo,Abbi Sani da Abbin Yara duk sun amsa min gaisuwa ba yabo ba fallasa haka dai,Abbi Mustapha kuwa tsaki yaja yana muzurai tare da cewa nayi tunanin wata ta kirki ce ma bakuwar ya saka babbar rigarsa yayi gaba.
   Sabeer yace baza su saduda ba fa Anty,Nace to nazo ku sanar musu kawai ku tattara yau da Dare zaku koma gida,Ameer zai zo da Driver ku tafi,ihu suka saki na murna suna tafi ai sai Anty sai Babbar yaya,Allah bar mana ke,ina ta dariya nace Ameer yana waje tare muke dashi,da Sauri suka mike muka fito gaba daya wajen Ameer,Suna ta gaisawa suna tafawa dasu Khaleel,har matan,Sajeeda sai kallonsa takeyi Tana son Ameer kuma tana ikirarin da yardar Allah sai ya aureta, Ameer dai Kuka yake so yayi na tausayin ganin Yan uwansa a haka,na shiga mota ina cewa kowa ya shirya da dare zaku koma Kunji suka ce to.muka tafi suna daga mana hannu abin tausayi.

   Abbi Mustapha da suka ji labarin me nace tare da Hajja sai suka ce ai dama mu mun san dole a neme mu,ai na fada muku dole suzo su samemu,da kar suzo mana banzar yarinya tana wani iyayi da yanga harda Sako glass,ai gidan bana ubanta bane gidan dukiyar dana ce da jikana cewar Hajja,Abbi yace banza a banza ta wani taho tana yakewa mutane baki,Khaleel yace da zaku birge sai kuce muje ku ku zauna a nan kuci gaba da rayuwa shine muka san lallai kun tsanesu,Abbi yace shashasha banzaye wanda basu san ciwon kansu ba,ai dole damu za a koma ko dan ganin bayansu,Meenal tace ta Allah ba taku ba mu dai ba Sa hannunmu,Mujaheed yace sai a fadawa su Umma masu yaji su dawo suma ko Abbi? Abbi Sani yace su dawo ina? Ai basu Isa ba,Hajja tace fyalla fyallan yan mata zaku aura dan ubansu su san cewar kunfi karfin a raina muku hankali,t unaninsu a talauci zamu dawwama matsiyata yayan talakawa.








AsmaBaffa
[2/8, 7:44 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖
 
    KASUWANCI NA






           115-116





Official






By
AsmaBaffa


 


For u all my FANS











     Washe gari da wuri mukayi shirinmu Haka Daddy masu kula dashi sun gyarashi baza kace bashi da lfy ba,Ammah da Aayan sai Yarima sune suka tafi Kai Daddy wurin me magani can kauyenmu.
   Ba yanda Aayan baiyi ba cewar a tafi dani Ammah tace a'a bazan je ba,dole muka hakura amma Allah ya gani ban so mijina ya tafi ba tare dani ba,amma tunda kwana biyu ko uku suka ce zasuyi nace su Meenat su shirya mu dawo gidana mu zauna kafin su dawo.

    2pm bayan munyi sallah tare da cin abinci sai ga Ameer tare da Sajeeda sun shigo da Sallama,dama Sajeeda a karkashin Ameer take aiki company nasu daya sun tashi tace dan Allah ya kawota gidana shine ba a son ransa ba ya taho da ita,ita kuma Sajeeda burinta kenan dama ta ganta kusa da Ameer shi yasa tace zata biyoshi tazo wajena,da Fara'a na tarbeta,Ma'eesha ce ta kawo mata kayan ciye ciye dana Sha,Meenat kam kamar an aiko mata da mutuwa haka ta kumbura,Sajeeda tace Meenat ko magana babu? Harara Meenat ta aika mata tare da Jan tsakin da kowa sai da ya kalleta,Ameer yana kallon Meenat ko me akayi mata oho shi fa Bai son fushinta,mikewa tayi zata shiga Bedroom sai muka tsinci muryar Sajeeda tace Ya Ameer muga wayarka zan tura abu,Fasa tafiya Meenat tayi ta dawo ta zauna kusa da Ameer tana masa rada karka bayar ai ba wayarta ba ce,Ameer yayi dariya yace Sajeeda me zaki tura? To ai kasan bazan ma yi ma komai a waya ba ko kawai abu zan duba,Mika mata yayi,Meenat sai fushi takeyi kamar zata daki mutane ta Mike zata tafi Ameer ya riko Hannunta ta kwace ta fice can Garden tayi zamanta ita kadai.

    Wayarsa Sajeeda ta mika masa yana karba yabi bayan Meenat da Sauri yana dubata har ya hango ta a garden tana zaune tana fushi,zama yayi kusa da ita Kamshinsa na tashi itama Haka,meke damunki Mee.....sai kirrrr wayar Ameer tayi kara ya daga yasan Madinat ce uwar naci tsohuwar budurwarsa, yana dagawa Meenat tana Jin muryar mace tana Haba Sweetyna ka manta dani gaba daya sai na kiraka yafi 10missed calls amma baza ka daga ba,sau nawa zan baki Hakuri Madinat ina da wacce zan aura fa kiyi hakuri kawai kittt...ya datse kiran.
   Baki Meenat ta kara turawa gaba tare da dauke kai can gefe tayi shuru,Ameer ya leka fuskarta yace baki da lfy ne? Meenat Sai hawaye Shar...Shar.... subhanallah mene ne?Ameer ya rude,Meenat ta kara fashewa da kuka wiwi yi take ba ji ba gani,Ameer tunaninsa cuta ce ta kamata,Meenat kuma tunaninta ita bata da wani me sonta a duniya sai irin su Tsito tare dasu Kwaja,ga Ameer nan yan mata sai binsa sukeyi kuma wai ma gashi ashe yana da wacce zai aura shima Bai fadawa kowa ba,tana wannan tunani tana Kukanta,Ameer yace  cikin ki ne yake ciwo? Meenat kawai ta zabga karya ta daga kai kawai wai ae, Ameer ya koma kalar tausayi ya wani rude yana lallashinta yana mata sannu,Ko Period ne? Meenat kawai nan ma tace ae tare da rike mara dan kawai tayi kukanta yanda take so,sai ko ta dinga rafsa Kukanta,Ameer ya rasa yanda zaiyi da ita ma yace Marar ce?tace ae,muje Hospital kinji yana fada kamar zaiyi kuka,tasan Karya takeyi sai tace a'a ni  Maganina yana wurin Anty Mufee, Muje to sai ta baki kisha,Bazan iya tashi ba ni,Ameer ya tsuguna hau bayana na goyaki to,Meenat taki yarda tasan Mufeeda ubanta zan ci in na gansu haka,sai dai ka rikeni,Ameer da sauri ya tallafe Meenat kamar wata gurguwa haka take tafiya yana rike da i ta suka shigo Mana,da sauri Na Mike ina tambaya lfy?Ma'eesha tace Sis Me ya faru da ke kuma,Sajeeda kuwa takaici ya hanata magana ganin yanda Ameer yake rike da Meenat duk ya rude ya shiga damuwa kamar shine bashi da lafiyar, da gani mugun kaunar juna sukeyi,Meenat sai wani kallo me dauke da sirrin so takewa Ameer,Ameer ne yayi min Magana ko Kunya babu Kiyi sauri ki bata maganinta mp ke damunta yana maganar ya wuce da ita Bedroom tare da kwantar da ita,Meenat kuma sai kukan So da kishi akeyi ba a sani ba, Fitowa Ameer yayi yana hada zufa kamar Doctor dan Allah kiyi Sauri ki bata ko muje Hospital gata can kamar zata suma,maybe ma suma takeyi,Bedroom din na shiga ina masifa Meenat karya kike Ba period kike ba nafa San time dinki me akayi miki ke yanzu baki da aiki sai kinzo wajena zaki shiga yi min Iskanci iri iri,gaba daya kwana nan an rasa meke damunki,lallashinta na koma yi bayan na gama Masifa ni irin babbar Anty din nan,Meke damunki haba Meenat katuwa dake yar University guda,Hannuna ta rike na zauna a gefen Bed din kamar me shirin barin duniya tace Sister ni bani da Sa'a a duniya irin su Tsito ne kawai suke so na ta kara fashewa da kuka,san...san..sannan...ma...maaa...wai Ameer yana da wacce zai aura naji yana waya shine ai cin fuska yayi min wai ni zaiwa gori harda wani yin waya a gabana ance masa sonsa nakeyi,ina ruwana ko mata Million ne zasu kulashi,Dariya ce ta kamani wato Du Kishi ne yake damun Meenat dama,Tsokanarta nayi nace Hmm ai kuwa Rannan ma Ameer ya kawo min budurwar tasa,ai ba cin fuska ya miki ba ke da kike frnd dinsa ai labari ya baki,Baki ganta ba wata muguwar kyakyawa duk ta fimu kyau,idan kika ganta sai kin raina kanki,Aayan ya San da ita?Meenat ta tambaya,nace sosai ma ai har kudi ya bata da tazo yar gidan Gomnan Yobe state ce akwai Naira.

    Kuka Meenat ta kara kecewa dashi harda shidewa tana gwara Allah ya dauki raina na huta,Wayyo Duniya...Allah sarki duniya...Allah sarki Duniya...Allah Sarki duniya haka Meenat take ta yi kamar me Aljanu,Ameer dama gaba daya ya rude tunaninsa jikinta ne yayi Zafi,da sauri ya shigo dakin yana dan Allah ki daukota muje Hospital,Yaje kan Meenat dake saman Bed tana Allah sarki Duniya,ya tallafota ai kawai sai Meenat ta shake Ameer ta cukwikwiyeshi gam suka fada saman Bed rigija,ta finciko gashin Ameer suma taci uban gyara tasha kyau Ameer ya dinga kara tana cisgar masa suma, sai da na buga mata tsawa sannan ta saki Ameer kuma tana kukanta,Ameer yace Aljanu ne Anty,jeka waje bari na shiryata sai mu tafi Hospital din,Ameer yace ina Palo dan Allah kuyi sauri Aljanune ina Meenat take da karfi haka ai sai na Aljanu.

   Yana Fita nace ke kuma haka soyayyar taki lallai kinyi Nisa Meenat Allah ya shiryeki,Harara Meenat ta balla min tare da cewa ai kin fini ke baki ga yanda kike wa Aayan ba a gaban kowa,ai gwara ni wlh ke a gaban kowa kike rungumeshi tsotse masa baki,kina fari kina kashe murya,Hips dinki ma yanda kike juya masa shi daban ne mene ne bamu sani ba,kuma sanda yayi tafiya kuka kika dinga yi a daki muna jinki sai da kika sa ya dawo,shine me to ai miji na ne nace,ke fa? ganin Meenat yanda ta koma yasa naji tausayinta nace wasa nake miki banza Ameer bashi da budurwa,da sauri tace da gaske kike sis?nace sosai ma,dariyace ta kwace mata kadan sai ga Meenat ras da ita,tace dan Allah  karki bari Aayan yayi masa auren dole gwara a barshi ya zabo wacce yake so,Dariya kawai nayi wai ni Meenat zata yiwa wayo,kawai nace ki kwantar da hankalinki abokinki baza ayi masa aure da kowa ba sai wacce ya kawo mana amma kiyi kokari ki san wacece yace yana da matar da zai aura?Ni a sanina bashi da ita Sis ko waya da mace bayayi amma sai na binciko ta kuma wlh idan na kamata sai na kusa kasheta,Dariya na karayi nace to ke da kike so ya auri wacce yake so kuma ai sai dai ki tayashi Murna ko? Murmushi kawai Meenat tayi ta miko min wayata gashi Ur Man na kira.

   Da sauri na karba na bar dakin tare da shigewa wani Bedroom din na kwanta sannan na daga kiran har ya kira ma sau biyu,Muryata na kashe tare da lankwasheta can kasa Nayi Sallama,sai da tsigar jikinsa ta tashi yaji kamar ma yayi tsuntsu yazo ya ganni ya koma,Honey na ya hanya da fatan kunje lfy? Ajiyar zuciya ya saki kana yace lfy alhmdllh saukar mu kenan Sweetwife am so tired gashi bakya kusa bare ki min wanka ki bani abincinki me dadi ohhh Am damn missing u missing ur food komai ma,dadi yana ratsani nace nafika damuwa tun dazu na kasa cin komai na kasa yin komai a gidan ma just thinking abt u gobe kuma ina da schl anya zan iya karatun ma? Yau shike nan baza muyi bacci tare ba kenan,abinda nake tunani kenan taya zan iya bacci bakya kusa dani,Yanzu me kakeyi ina su Ammah da Daddy? Daddy yana can dakin da aka bamu,Ammah na cikin gida,ni da Yarima kuma mun fito a kauyen muna kallon mutane kawai kafin anjima muje gidan me maganin,eyya mijina yana Shan wahala a kauye baka saba ba ina zaka huta kaji dadi,I wish muna tare,ai idan naji zamuyi 1wk a kauyen to ki Zama Ready kawai gobe zaki taho kema bazan iya zama bakya kusa dani ba musamman a wannan garin can cikin daji ne fa,nima  nace sai dai kawai Ammah ta ganni nazo indai baza ku dawo da wuri ba bazan iya barinka a nan ba,yanzu me zaka ci?shine nake tunani,ka duba cikin kayan dana hada ma akwai Snacks,dambun nama da Soyayyen naman rago dana Kaji sai Kaci ko da juice ne,Wow Allah Ubangiji ya miki albarka My Wife ina mugun Sonki,kamar kin San tunani nake me zanci Allah ya gani bazan iya cin abincin da aka bamu ba babu dadi wlh,fura kawai na Sha da nono,Karka damu tunda lafiyar Daddy ake nema komai wahala za a daure, cike da shagwaba yace ni dai gobe kawai Driver ya kawoki garin tunda kin San wajen,an gama ranka ya Dade sai abinda kace,dariya yayi yanda nayi maganar kamar ina gaban Sarki shine ya bashi dariya Haka mukayi ta hira ina lallashinsa karshe nace ya gaida Yarima mukayi Sallama kafin zuwa anjima.

    Yana kashe wayar na Kira Ammah muka Sha hira itama na hadata dasu Ma'eesha,lokacin Ameer ya leka dakin  da Meenat ke ciki ya hangota ras da ita hira ma sukeyi da Ma'eesha suna dariya suna waya da Ammah ,tunanin Ameer ni na bata magani ta warke,har wani dadi yake ji a ransa,Sajeeda kuwa tuni takaici yasa tace tafiya zatayi gida ba yanda banyi da ita ba ta bari sai magrib nasa Driver ya kaita amma taki yarda,haka na kyaleta ta tafi gida tana kunci.
   Tana gefen titi zata shiga Taxi sai ga Tsohon saurayinta Saddiq wanda yake mugun sonta kamar hauka bashi da wata makusa ta ko ina amma Sajeeda ta dinga wulakantashi yanzu yayi parking da mota yasha mamaki ganin yanda ta mutuntashi suka gaisa yace tazo ta shiga motarsa ya kaita gida amma taki sai da kyar ta shiga shi Kuwa Saddiq sai Murna yakeyi ya dauki Sahibarsa,dama gashi lecturer ne matashi bai taba aure ba.

    Khaleel da Mujaheed ne suka shirya takanas suka je wurin Iyayensu mata su uku akan maganar suyi hakuri su koma duk da Wahala suke ciki a dangin nasu sabo da talakawa ne amma suka ce Sam baza su dawo ba su sunfi samun kwanciyar hankali a gida,Uwar miji ta gama mallake mazajensu sai abinda tacewa su Abbi,dama aikin Allah ne da sauki amma harkar asiri su kam baza su koma ba,sukace ai da duk bamu gane ba sai yanzu Allah ya ganar damu,Abinda sukewa Daddy da Aayan tare da matansu kadai ya isa ka nemi wajen tsira waye baza suyi wa ba a duniya,Umman Khaleel da suka je wajenta tace da ina da arzikin Shanu sanda ubanka ya Aureni a kauyenmu sunfi goma,Amma duk ubanku ya min wayo ya cinye min shanu kaf shi da uwarsa Hajja,lokacin tun Daddy bai zo kasar nan ba,Itama Mommyn Mujaheed sai da ta mallaki katon gida da Gold ubanka Mujaheed yaje ya lallabata amma ta hanashi sai ko Hajja ta hadata da malamai sai gashi ta dauki komai Nata na dukiya ta basu tun kuna yara,ana zuwa wurin Umman Ameer ta fashe da kuka tace ai wlh tunda har suka iya korar min dana daga gida bazan koma ba,Aayan da Mufeeda Allah yayi musu albarka sune suka rike min shi da tuni ko ya fada shaye shaye amma gashi yana wajensu lfy shi yasa nace yaci gaba da Zama a can,ai zalincin dasu Hajja tare da Yayanta suka yi mana bazai irgu ba,ni dai na gane gaskiya tsakanina dasu sai Allah ya isa,Haka nazo da Kudina Dubu Dari Babana ya bani Naja jari na fara business ina Amarya Abbi uban muguyen gidan kaf ya lallabani yace na kawo na shiga Dashi,sai da na shiga Ashe tuni ya lallaba da daukana yazo ya karbe kudin sai da nace a bani uwar dashi tace wai nice daukan farko mijina ya karba yace nice nace a bani,naji takaicin Abin nan haka na dinga zubin dashi ba dauka har aka gama,bayan nan Babana ya kara aiko min da Dubu Hamsim ya lallaba ya sace,banda sauran abubuwa wanda muka sani da wanda bamu sani ba na zalinci da suka dinga gwada mana wanda Hajja ke sasu komai.
   Mujaheed yace to a bamu yaran mu tafi dasu sabo da schl,haka aka basu su Omar su uku yara yan 5-6yrs suka tafi dasu sabo da schl kar su tashi ba ilmi me kyau.

      Su Abbi kuwa basu da mataye yanzu sai dai suci su sha su sa sutura me kyau,gasu gwauraye illarsu daya rashin kudi babu kudin da za ayi bariki amma duk da Haka Suna yi sama sama neman mata tunda Suna matsawa dole Ameer yana basu kudi,haka su Khaleel suna Jin tausayinsu su basu Ashe ana basu sai su Kama Hotel su kai mace ciki musamman Abbi Sani yafi kwarewa a wannan fagen.

   Haneefa ce ta shigo main Palo taci uban wanka ta Sha kyau sai masifa take,Sabeer takewa fada wlh duk me wulakanta abinci watarana abinci sai ya wulakantashi,ba ku kadai abin bala'in zai shafa ba har mu gaba daya,taya dan Iskanci baza ayi abinci dai dai kowa yaci baiyi kadan ba baiyi yawa ba amma sai kuje kusa ayi ta dafa abincin iri iri kuma a kasa cinyewa,a zubar dashi ko ina kaca kaca daga karshe a watsa a dustbin ga masu aiki kuna sasu wahala,wannan ba dai dai bane,kalli yanda muka Sha wahalar rayuwa amma ko tunawa bakwa yi,wannan bai dace ba babu kyau,Allahu Akbar yaran suka saki kabbara gaba daya Haneefa ta Zama Malama,su Kansu masu aikin gidan yanzu dadi suke ji yaran gida sun nutsu, Hajja ce kawai dasu Abbi ba a shirin tuba sunyi nisa, Haneefa tana gama wa'azinta,Sajeeda ta Mike tace ya kamata mu nemo mazaje,Maza su nemo mataye muyi aure sai ihu yeeeeeee wlh kuwa gwara a dama damu,Sajeeda kinfi kowa iya kawo shawara Cewar Khaleel, Abbi ne ya fito ya daka musu tsawa baku da aiki sai kullum ku cika mana kunne da surutu da ihun banza,zaraf sai ga Hajja tace aikinsu kenan yanzu kullum sai sunyi zaman Palo suna surutun banza da wofi wai su yanzu a dole sun Zama na gari nan wai nutsatsu,Sai kunci ubanku wlh a gidan nan sai na tattaka ku cewar Abbi,Hajja tace gwara haka ai wanda basu San ciwon Kansu ba kwandala bana morarsu gasu nan dasu gwara babu a gidan nan,ni fa takaici nakeyi Ameer baya gidan nan nasan shi kadai ne dan albarka kullum sai ya bani kudi ya siyo min kayan dadi,Abbi yace ai nace masa ya dawo mu zauna yaki yarda wai yafi son wajen yaron can me Jan kunne,ai idan Ameer ya sake sai na masa baki watarana,da Sauri Hajja tace baka isa ba Ameer dan albarka ai duk yafi wannan banzayen,Ameer dina wlh duk Wanda ya ko zageshi bazan yafe muku ba a gidan nan,da dinma da na bari kuka koreshi nayi ne dan ya gyara halinsa badan wai bana sonsa ba. Tabe Baki Khaleel yayi yace mu da kice kina sonmu da ki tsane mu duk daya a wajenmu,kai marar kunya kaji nayi magana da kai shegen Hanci kamar kana Mura kai fa Hasken fatarka na banza ne sabo da bame kyau bane shegiyar Suma kamar ta zabiya,Ameer ne kamar Balarabe,Wannan kuwa ta Nuna Mujaheed ido kamar na dan giya manya dasu,dariya sukayi Sabo da Khaleel Hasken sa da yawa, Mujaheed ma yana da haske amma yafi kowa Dara daran idanu sune ma suke kara masa kyau,duk da Dama su duk gidan kyawawane sosai,Aayan ne yafi kowa ba a hada kafa dashi sabo da shi jinin turawa ne sai Ameer, Hajja ta Gama masifarta ta wuce.

    Su Aayan da dare sunje gidan me magani yace sai sunyi sati daya a wajensa,suna dawowa Aayan ya bani lbr kawai na taho gobe,Ammah kuma ta kara Min warning kar na sake na zo taji labarin Aayan yace zan biyosu,Na roki Ammah ta yarda nazo tace bazan zo ba,Aayan na sanarwa yace tunda Ammah ce shike nan mu hakura haka har mu dawo,kullum tare muke dasu Ma'eesha tare muke girki da komai da ya dace muna zuwa schl dinmu ni da Ma'eesha abinmu lfy, kwanan su Aayan Uku alhmdllh Daddy yana samun sauki domin har yana iya motsa hannayensa da kafafu.

   Muna zaune tare dasu Ma'eesha,Ameer yana Shan Ice Cream dinsa,Meenat tana kusa da Ameer wai sai ya San mata Ice cream dinsa bayan ta shanye nata, wayata tayi kara naga Kawata Nawwara ce rabon da ta kirani tun ranar da tazo su Haneefa suka kwala mata robar ruwa tace Bom ne sai yau naga kiranta bayan ta tafi na kirata amma taki dagawa,ina dagawa nace kin huce kenan?dariya tayi muka gaisa tace Anjima zan shigo Insha'allah,Nace to bari na tura miki address din mun canja gida ba wanda kika sani ba,da sauri tace da gaske?yanzu ba gida daya kuke da yan iskan nan ba?nace ae ya canja min gida,to Alhmdllh gani nan zuwa anjima,misalin 5pm sai ga Nawwara ta rafka Sallama,muka amsa yau ma tayi kwalliyarta,muna ta hira ta gaji sai naji tace ina mijinki?nace yayi tafiya,nan take naga ta bata fuska,nace lfy? Dariyar yake tayi lfy alhmdllh kawai tambaya nayi,bari naga gidan naku gaskiya kinyi dace Hajjaju wannan uban gida haka haduwa,Su Ameer suna jinta tana ta zuba surutu,bari na shiga garden nasha kallo,nace bari na nuna miki,a'a jeki ki dafa min me dadi ni zanje da kaina kawai ba sai kin biyo ni ba,Mamaki ya kamani ni da gidana mace ta nuna ta fini saninsa zuwanta na farko kuma,Jeki to kawai na shiga kitchen na kyaleta,Maeesha suna kallonta suna jinta ta fice abinta ta gama Shan kallonta tana zagaye,Ameer daga baya yabi bayanta amma yana fita yaga kallo takeyi tana Selfie abinta tana tsinkar su Guava a lambu sai ya kyaleta ya dawo,ita kuma Meenat sai aka fara fushi dan me Ameer zai bi bayanta,bayan Nawwara ta gama kallonta sai ta dawo taci abincinta muna hira ta gama sa idonta ta Mike tace zata tafi,na rakata har gate na dawo.
Sameera yar daba da yaranta su har yau suna can a kulle basu samu damar fitowa ba,iya cin hancinta ta bayar ta hakura tana gidan kaso ana fafatawa da ita ko a prison Sameera tana cikin shegun matan da suka gagara.

    Bayan sati Muna waya da Aayan yace  kinji wai sai mun kara sati daya zamu dawo,ni kaina banji dadi ba na matsu Mijina ya dawo,nace amma na kira Daddy a waya fa yace min yana takawa,ae Malamin ne yace wai sai ya karasa mikewa da Saura,ajiyar zuciya na ja nace to ba damuwa Allah ya nuna mana,baki damu dani ba Babyna ko naga ko a jikinki ni ina nan cikin wahalar rashinki,nima na marairaicewa haba Mana karfin Hali da dauriya kawai nakeyi Allah amma bari na kira Ammah idan ta yarda gobe zanzo,da sauri yace yawwa yar albarka tambayeta muji,ina kashe wayar na Kira Ammah,ita kanta ganin Aayan har yar rama yayi yasa tace kizo goben to,Murna kamar me amma dan kar na fadawa Aayan ya sa rai yasa nayi masa shuru nace Ammah bata yarda ba,washe gari cike da zumudi nayi Shiri na barwa Su Meenat komai nasa Driver ya tafi dani Kauyen,Munje lfy kauyen Driver na ajiyeni nace ya juya ya koma,na dauki jakata sai kallona akeyi anga yar gayu ga kyau na shiga gidan Yar Uwar Ammah wato Inna tsohuwa,Ammah ta kalleni tana dama fura tace ai nasan sai kinzo dole,dariya nayi na rungumeta Ina gaisar da Inna tsohuwa,Mufeeda sai yau za azo mana ana can ana cin Amarci wlh kinyi dacen miji yaron kirki sai yabonsa akeyi a garin nan,Inna ai da gani kin San ya iya kiwo ma yanda na koma kalli fa,Dariya mukeyi da Inna tace ai naji kin cika mana gida da kamshi,yana ina ma Wai Inna?Ammah ce ta zuba min duka a baya baki da kunya Mufeeda yaushe kika dawo haka?dariya nayi tare da mikewa na kai jakata dakin Inna nayi Alwala tare da sallah,sai Ammah tace ga ruwa can kije kiyi wanka,Haka na fito nayi wanka da sauri na shafa lotion na sake kaya Atamfa me tsadar gaske Black and Green nayi kyau riga da skert kamar a sace ni,turare na fesa na fito sai mukayi ido biyu da Aayan wanda shugowarsu kenan tare da Yarima,Har zanje na fada jikinsa na tuna su Ammah na wajen,sai kawai na gaida Yarima tare da Aayan,Yarima yace au saida kika biyoshi kenan ko?daki na koma da Sauri sai ko Aayan ya biyo bayana, na juya baya ina murnar ganin mijina sai jinsa nayi ya rungumeni ta baya yana sakar min kiss a wuya ta ko ina,Ajiyar zuciya kawai muke saki,Kamar zai cinyeni haka yake tura kansa ko ina a jikina, yatsu na ya kamo yana kallon yanda nasha zanen lalle ba karamin kyau nayi ba,Dankwali na ya zame yana shafa gashina yana kissing dinsa,kallona yake kamar ya hadiyeni yace kinga kyan da kika kara kuwa?Ni ina nan tunaninki ya hanani sakewa,Bana iya bacci sosai fa,Murmushi nayi ai gani nazo to,amma baki fada min yau zaki zo ba Ashe Ammah ta yarda kizo,Ido na lumshe masa nace zo muje makwaftan Inna wata Tsohuwa ce tukuf sai tsaftar Masifa tana mugun so na ita kadai ce a gidan Masauki me kyau zata bamu a gidanta sai muna kwana a can tare,Ina Daddy fa? Daddy ya Zama dan gari har yana fita majalisa a kauyen nan,yanzu ma yana cikin dattijai can wata bishiya suna hira,Murna Nayi tare da Hamdala,Muryar Ammah naji tace ga abincinku Mufeeda,Yarima yana zaune kusa da Ammah suna ciye ciyensu,Abincin na fita na dakko a tire Fura lafiyayya da kuma Shinkafa da miya da salat,da yake Ammah na nan girki me dadi take shirya musu iri iri ba kamar farkon zuwansu ba da Aayan ke korafi ba dadi,shi yasa Ammah take musu komai da kanta.

  A jakata na dauko Soyayyan Nama na zuba mana saman abinci,na kaiwa su Ammah nasu sai Dariyar Kwadayina Aayan ke yi,yace to ai ga nama nan a abincin amma sai kin kara wani,Nace ai wannan suyar tasha maggi,dariya ya shiga yi yace sarkin kwadayi yau zamuyi bacci tare gobe bazan tashi da wuri ba sai tsakar rana,Murmushi nayi masa me matukar kyau,Yau da kaina na bashi abinci har ya koshi ina lallabashi yana ta shagwabarsa,5pm yace bari nayi wanka muje gidan tsohuwar taki daga nan muje yawo,Ruwa na hada masa na kai masa har Toilet,Ammah tana ta jin dadi yanda taga ina kula da mijina gwanin sha'awa,ina kusa da Toilet din ya dinga min magana kasa kasa wai shugo ki min wankan,nace Ammah zasu kama mu yana gama wankan ya koma dakin da suke kwana ya shirya cikin 3qtr da yar riga fara yayi kyau,Na yafa mayafi na da Handbag na bishi muka fita,shi kuwa Yarima Bacci kawai bacci yace zaiyi ya gaji,Hannuna cikin nasa iska na kadawa muna tafiya cike da nishadi tare da jin dadi,sai da muka dan zaga a garin ko ina sai kallonmu akeyi Yace ana kallona shi mu tafi gida,Gidan tsohuwa Iya Makwafta da gidan Inna muka ya da zango,daki ma sai da na zabar mana,ya kasa hakuri dare yayi muje tun da yamma ya takura yana rokona Na bashi ko dan Kucili ne,Iya muka yiwa wayo wai bacci zamuyi Jiki na rawa ya fara sarrafa ni,Nima haka,yana kukan da karfi na toshe masa baki Iya zata gane mu fa,yace ke wannan Sirri ne Allah yana sawa abin Hijab,kin taba ji an kure mata da miji?sai dai a kure kwarto na bashi Amsa muna dariya,Iya muka ji tace ba kyau baccin bayan la'asar ki fito da dare sai kuyi,Nace Iya ba bacci mukeyi ba Wasu yakardu muke dubawa na sirri,Iya tace yawwa yan Albarka a barwa dare sai ayi baccin haka da kin fito ma kin tayani yanka Kubewa,Nace Da Karfi Iya bazan iya aiki ba yau na....Aayan yasa bakinsa cikin nawa Iya taji muryata ta wani shake tace yau ko yar Hirar ma baza kizo muyi ba kin kule daki da mijinki,Iya taji Shuru dadi ya tafi dani ko jinta bana yi tana ta Surutu ba wanda ya kula ta dama ga Iya da surutu bata iya shuru da bakinta,Yau kam Alhmdllh mun gwangwaje juna,munji dadinmu abin ba a cewa komai yau naji dadin da ban taba ji ba,Cike da nishadi yace to wankan ne matsalar,nace sai yanzu ka tuna Gashi har Magrib ta wuce,Fita nayi wajen Iya nace Iya za a samu Ruwan Zafi kafarsa na ciwo zai gasata,Iya ta gane amma sai tace gashi can na dora har ya tafasa cikin katuwar tukunya zai isheku gaba daya,shuru nayi Iya kuma ta wuce dakinta tare da cewa in kin gama abincinku yana kitchen,nace to Iya,Ruwa na hada mana tare muka yi wanka sannan muka tsarkake jikinmu, mun dan ci abincin Iya sannan nace zamuje mu dawo,Gidan Inna muka koma,Ammah tace ina kuka shiga haka?Nace muna gidan Iya,Yarima kuwa tun daga kallon da yakewa Aayan suna dariya yasan me muka je yi,Daddy yana dakinsa masauki tare da Aayan Mukaje na gaisheshi da murna ganin ya dawo lafiyayye,ina ta murna ina masa sannu,Daddy yanzu yawo ko ina,yace Alhmdllh Mufeeda Ashe kema kinzo cike da kunya nace ae Daddy.
   Daddy yace Alhmdllh kafin Mu bar garin nan Iyayen Yarima zasu zo tare da dangin mahaifinku za ayi maganar auren Ma'eesha,tunda sun shirya Kansu sai kawai a tsayar da ranar biki,nace Alhmdllh tunda Ammah ta yarda ai ba damuwa,Aayan kuma yayi min zancen Meenat da Ameer ina so na wakilci abin ina tunanin Abbi Baban Ameer da kyar in zasu yarda musamman Hajja,amma idan mun koma gida zan tuntubesu da kaina naji.dadi naji nace to Daddy Allah taimaka,mun dan jima muna hira sannan muka fito.

     Bayan kwana biyar Saura kwana biyu mu dawo gida dangin Abbanmu suka zo tare da iyayen Yarima nan aka bada kudin Aure aka sanya rana nan da 4Months,Daddy  yace ya wakilci Ameer ai shima Ubansa ne idan mun dawo zai san yanda zaiyi dasu tare da Hajja har su yarda,Nan ba tare da Sanin Ameer da Meenat ba aka sa Rana suma Daddy ya bada kudin auren da komai,Sannan yace kar wanda ya fadawa Meenat da Ameer kawai ace na Ma'eesha da Yarima kawai za ayi.
  Ana gama komai suka tafi cikin aminci,muma ranar tafiyarmu na zuwa Driver yazo da katuwar Mota muka musu sallama cike da kewar juna,Sunsha kyauta wurin Daddy musamman Malamin da yayiwa Daddy magani.
  
     Mum dawo da kwana biyu Daddy yaje gida wajen Hajja kowa yasha Mamaki ganin Daddy ras dashi ya shigo da kafafunsa,Yaran gida Su Haneefa murna kawai sukeyi suna kwasar gaisuwa ana masa Congrat,Hajja ma taji dadi danta ya dawo fes,Su Abbi ne ko a jikinsu basu damu ba,an gaisa sunyi Hira,Daddy  daga shi sai Su Abbi da Hajja yace Idan baza ku damu ba naga Ameer yana son kanwar matar Aayan suna son juna da sai ayi musu aure,kaga sai a hada ma dana su Khaleel su Ukun,Dafe Kirji Hajja tayi tace Ameer dinne yace yana sonta?Daddy yace ae har Kuka yake min kullum,Hajja dama tana son Ameer a rayuwarta nan tace bana son Matar da zai aura bana kaunar danginsu Amma da ace Ameer yana kuka a kanta gwara a aura masa ita,da Ameer dina ya zauna cikin damuwa gwara ko ma wace a bashi ita,ina Ameer din a nemo min shi karfa ace yana can cikin bakin ciki,Daddy yace ki kwantar da hankalinki Hajja,Abbi yayi tsalle ya dire ba wanda ya isa ya aurawa Dansa dangin Mufeeda dangin jaraba.

    Hajja tace wlh baka isa ba ni kaina bana kaunarsu Amma akan Ameer ya shiga damuwa gwara a aura masa ita,tunda Ameer yana so na yarda ko wace ce a bashi farin cikinsa,Abbi zaiyi Magana Hajja tace kana kara magana ban yafe ma ba,kuma duk Wanda yaki yarda ayiwa Ameer dina Aure da wacce yake so ban yafe masa ba duniya da lahira.
  Abbi yayi shuru yana Hararar Daddy yace ai sai kaje kuyi komai kuma kwandalata babu a ciki,Daddy yace ai gaba daya yaran nan kowa mata da Maza ko ba raina Aayan zai musu komai.kafin Daddy ya tafi sai da ya bawa Kowa na gidan kyautar makudan kudade musamman Hajja dasu Abbi,Su Mujaheed ranar sunsha Gori da zagi wajen Hajja tayi Kudi.








AsmaBaffa
[2/12, 6:12 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

    KASUWANCI NA





           117-118





Official





By
AsmaBaffa






            Fans ina baku hakuri kwana biyu baku jini ba,Biki mukayi bana gida shi yasa kuka ji shuru.nasan kun jirani sosai ina neman Afwarku akan hakan.

    

       REAL MAMAN WALEEDA wannan page naki ne,Allah kara basira da zakin hannu Novel yana Sweet.






       Kwance nake a jikin Aayan ina zuba masa shagwabata a hankali yace ya akayi ne My life yana shafa mazaunai na da suke matukar birgeshi,uhm....ehm....ina shafa kirjinsa naci gaba da ina ina ta kaga ko...just...just...Show...me....love.. murmushi ya saki me kyau tare da cewa nifa kika cewa nine Maye kamar Engine ya akayi kuma, dariya na danyi kadan tare da cewa karya nayi to ai gwara ni da kai amma tunda ma yanga zaka yi min shike nan na fasa ma, dariya yake kasa kasa tare da cewa to shike nan muyi baccinmu naji dadi da kika fasa,Hararar wasa na watsa masa a hankali nace Zaka san ni kayiwa haka ai ba komai,kamar yayi bacci yayi lokacin kuma gaskiya da gaske ina sha'awarsa sosai don gaba daya Bazan iya Control ba,nace na Hakura Amma sai mutsu mutsu nake masa a jiki tare da goga jikina a nasa shi kanshi ya kasa jurewa karfin hali kawai yakeyi,gani nayi ina bata likacina ni da mijina kawai na fara lasar sassan jikinsa musamman wuyansa tare da lips dinsa,Kunne sai kirjinsa tare da cikinsa,yana jina yayi luf yana shan dadinsa bai san sanda yasa Hannayesa ya zare min rigata ba yar ficika da ita,Na gama Zama wet,abinda nake so yasan yana zautar dani ya shiga yi min su nima ina masa shima har muka samu abinda muke so,Jikinsa na shige sosai cike da nishadi,a hankali na dan rada masa Darling u r too sweet,ka iya komai,naji dadin da ban taba ji ba sai can cikin dare sai mu kara yi ko? Shima a hankali yace abinda kike so shi nake so soulmate ai ke kike juyani sai yanda kika ga dama,Murmushin dadi nayi tare da kara narke masa kamar wata jaririya shima biye min yakeyi.

     Ameer yau yana part dinmu yana zaune saman Dining  ya gama cin abinci yana aiki a System dinsa na Office da laptop dinsa Meenat ta shigo dawowarta kenan daga Schl sun fara lecture tuni a BUK agogon dake hannunta me kyau ta kalla taga 5pm Amma yau Ameer har ya dawo mutumin da watarana Sai 6pm yake Barin Office idan yaga dama,Ameer yana kallonta ta gefen ido ita bata wuce ba ta tsaya tana tunani,a hankali ya juyo ya zuba mata idonsa me matukar kyau,Ba karamin kyau ya mata ba,da Sauri ta dauke idonta tare da Sallama tayi a hankali ya amsa mata yana kallonta da Alama a gajiye take,wucewa bedroom tayi da Sauri wanka tayi sharp sharp ta sa kaya marasa nauyi riga da skert English wears ta fito saman Dining ta zauna,Bai kulata ba itama haka,aikinsa yakeyi kawai tana Satar kallonsa tana cin abincinta,shima satar kallonta yake ba tare da ta gane ba,idan ya kalli fuskar System din sai ya dago da idonsa kirr sannan yaci gaba da aikinsa,Itama a nutse take kalleshi ba sai dai ko idan sun hada ido su sakarwa Juna murmushi, Juice ta zuba glass cup ta dan kurba tare da ajiyewa a gefe,Ameer ya dauka ya kurba shima ya mayar mata inda ta ajiye kallonsa tayi shima haka ya kashe mata ido daya dama Ameer ya kware wajen magana da ido,yanzu sai ya zanceki da ido sai dai idan bakya gane yarensa,kallonsa tayi kunya ta rufe ta bata san sanda ta sa tafukan hannayenta ba ta rufe fuskarta tare da mikewa zata bar wajen,Hannunsa taji cikin nata ya dawo da ita shi kuma ya mike tunaninta Tafiya zaiyi ya barta ta sake sai taga kida ma ya kunna abinsa yana yar rawarsa su Zanku Dance tare dasu Shaku shaku dama gashi yaci uban kana nan kaya na yan duniya,Ma'eesha ce ta fito palo basu da labarin ansa bikin Ameer da Meenat tazo kusa da Ameer itama suna ta rawar tare bai san ta zama kanwa kuma suruka ba,itama haka dama sun saba kusan kullum idan suna nishadi sai sun cashe,Meenat dai dariya take sha kawai Sabo da Ameer baya girma maybe ko da dansa ma rawa zaiyi, Su Khaleel ne suka shigo da Sallama Amma kida yasa ko jin Sallamar ba wanda yayi,Sabeer tun daga kofar ma ya fara cashewa Shima,Maeesha kuma taji kunya ta koma ta zauna kamar saliha dama da Ameer suka saba,Mujaheed ne kadai Baya rawa Amma Khaleel ma yana bi da baki yana yi a zaune wakar Olamide latest,Aliyu kuwa harda Handkerchief a hannunsa yana faman sarrafashi yana yi,da Haneefa akazo tare da Meenal dama aikinsu kenan a gida tun farko su kunna kida suyi ta rawa yau tsohon Tsuminsu ya tashi basu ji kunyar uban kowa ba suka dinga yi iri iri,Ameer yana dariya yace Haneefa kin fadi wannan step din Kije Ma'eesha ta koya miki ta fiku iya wannan,Maeesha kamar munafuka tayi kamar bata san ma mene ake nufi ba wai ita saliha, Ameer duk sun zauna suna magana,Sabeer da Aliyu kadai aka bari suna ta rawarsu suna bin Kidan da baki Suna haka sai gamu mun fito tare da Aayan ba karamin kyau muka sha ba kamar kasace mu,Shadda muka Sa me tsadar gaske fara me aiki da bakin zare,nasa dinkin na Maza nawa na mata,kowa ya kallemu sai ya kara kamar wasu wankin engine haka muka fito muna kamshi,dama sun saba ba kunya ce dasu ba bare Aayan da basa jin kunyarsa tun farko basu kashe Kidan ba kuma masu rawar su basu fasa ba da wanda sukeyi a zaune magana baza suyi ba sai hannu suke dago mana wai gaisuwa ce,ina zuwa na kashe Kidan nace haba komai dadin kida shuru ya fishi,Meenat tace gaskiya mu ki kunna rawa muke kallo,Musabiha sukayi da Aayan sannan suka gaisheshi nima haka,Maeesha na Yiwa magana ki kula da kowa zamu fita sai dare zamu dawo,kunyi kyau cewar Meenal,nace tnx Aayan ya sa hannunsa a waist dina yana fada musu su jira baza mu dade ba zamu dawo,ai da Sauri suka ce a dawo lfy,muna fita suka warare uban kida a speaker din katuwar gaske.

   Ko da su Khaleel suka zo suna ta fadawa Ameer Ango Amma bai kawo da gaske suke ba tunani yakeyi ko dama wasa kawai sukeyi,tunda shi baiji daga bakin manya ba ko Aayan taya zai yarda, Abinci Ma'eesha ta kawo musu da kayan sha suna ci suna Santi cikin Santi Meenal tace Allah mun gode ma ku duba hakoran engine na Markade har washi ake kaisu kuma baka isa sunyi shekara biyu ba,haka zaka gansu duk karfe ne amma ya Zama Siri Siri ya gama sidewa amma kalli Hakorin dan Adam yayi tauna yana Markade abinci luwai luwai ba tare da karar komai ba,shekara da shekaru bai lalace ko ya daina kaifi ba,amma hakorin Engine kuwa ana zuba Abin Markade zaku ji karar tasa ma ta canja,Ameer yace ai fa gaskiya girki yayi dadi,kuma su hakoran mutum idan kana tauna ko kara basa yi ba kamar engine markade ba kaji kafkafkafkagkaf dariya sukayi gaba daya.
    Ni da Aayan kuwa tunda muka fita bamu tsaya ko ina ba sai gidan Ammah mun dade a gidan muna tsare tsare bikin su Meenat,daga nan yace Muje mu gaida su Hajja ban so zuwa ba amma ganin Manyansu ne yasa banyi musu ba muka je,Sajeeda dake gidan ita ta saukemu bamu samu tarba me kyau wurin Hajja dasu Abbi ba dama kuma bamu sa rai ba,bayan mun danyi Jimm kadan muka musu sallama muka fito.

    Bayan zuwanmu gidan su Hajja da kwana biyar kawai na wayi gari bana son Aayan ya rabe ni kwata kwata,ni ba tsanarsa nayi ba Amma bana so naje kusa dashi ko yazo kusa dani,idan kuma baya nan zanji kamar na cinyeshi na damu dashi ina ta damunsa da waya Amma da zarar ya dawo gareni to kuma sai naji duniyar tayi min kunci Bazan samu jin dadi ba har sai idan na bar gidan Aayan sai na samu kwanciyar  hankali,d a dare ko Bedroom idan na canja sai na koma jin Kukan Dabbobi iri iri,Aayan ya kasa gane kaina gaba daya mum shiga damuwa babu me kwanciyar hankali a cikinmu,Saida muka kwashe wurin sati biyu muna haka ko Bed bamu hadawa da Aayan,tunda ya gane sai ya dan ja baya da lallabani dole sai mun hada shimfida,abin mamaki kawai yake bashi,ina dakin dana warewa kaina ni kadai 9pm Aayan ya shigo yasha wanka,ina ganinsa raina ya baci kawai naji wani bakin ciki marar misali kuma ni ba shi nake jin Haushi ba bansan me ma nake jin haushin ba,Zama yayi kusa dani Na kara daure fuska,kallona kawai yakeyi da mamaki,Hannu na ya riko na fisge abina,ya kara rukowa da Sauri na boye hannuna Ina shirin yin Kuka,a hankali ya zuba min ido cike da so da kauna nima haka shi nake kallo yana bani tausayi Amma na kasa canjawa ban san dalili ba,Muryarsa naji yace Mufeeda a hankali,Ba tare dana kalleshi ba nace Naam muryata tana rawa zanyi kuka nace dan Allah kayi hakuri wlh ni ban san me yake damuna ba,Karki damu na gane na san lallai akwai Matsala tunda komai baki fasa yi min ba,amma me yasa yau baki yi min abinci ba tunda nine bakya so na rabeki,kin san kuma ke zaki bani abinci naci ko? a hankali na daga kaina kayi hakuri jiya ne banyi bacci ba sai da rana ina ta jin Kukan Zaki dasu Damusa a gidan nan sai da Asuba nayi bacci.

     Ko gida zaki koma wurin Ammah mu gani bana son ganinki a wannan hali Sweetheart,da Sauri nace na gode Na gode dan Allah ka maidani wurin Ammah anan kamar zuciyata zata fashe haka nake ji,Nima Ina da Meeting a Abuja gobe zan wuce sai nan da 2wks zan dawo naso ace tare zamu tafi sai kiga komai nawa na Abuja Sabo da so nake mu koma can da zama na gaji da nan kullum matsala iri iri, bari na dafa ma ko Indomie ce,no ki barshi naci abinci a waje karki damu,gobe ki shirya na maida ke wurin Ammah yana gama fadar haka ya wuce.

    Kuka na saki sosai ina son mijina Amma kuma na rasa me yake damu na,yau ma da kyar na samu bacci sai da Asuba na samu bacci ya kwasheni,da sassafe na tashi bacci a idona na fito zan daura Breakfast,Aayan na gani ya dawo daga Gym room yace kije kiyi baccinki zan siyo mana abinci,Ba tare dana kalleshi ba na juya nace to sai bacci,Shirinsa ya gama yi fes ya jawo Trolley dinsa ya ajiye min take away dina iri iri tare da Short note cewar ya wuce ga Ameer nan zai maidani wurin Ammah karshe yasa I love u My Wife. 

   Sai 2pm na tashi da sauri nayi wanka tare da Sallah sannan na jawo take away naci na koshi ina tunanin mijina,duk naji gaba daya kamar ma ba ni ba,kamar bani da wani amfani a duniya ba tare da Aayan ba,tunaninsa kawai nakeyi iri iri ina jin da a raina wanda da ace yana kusa dani bazan ji hakan ba,Sai dai ma bacin rai,Shiryawa nayi na kulle komai na kashe kayan Wuta na kira Ameer a waya da katuwar jaka ta na hado kayana,Babu wanda yasan me yake damuna,haka Aayan ma ko Daddy bai sanar masa komai ba duk da cewar Daddy ya tafi U.s zai huta kafin bikin su Meenat zai dawo,Ammah ganina da katuwar Trolley sai da gabanta ya fadi,Su Meenat ma haka,Ameer shi kansa tunani yakeyi ko dai ba lfy ba,Sai da muka gaisa dasu  Ammah tace lfy dai ko?murmushin karfin Hali nayi nace lfy lau Ammah ya tafi Abuja ne shine nace ya barni na dawo nan kafin ya dawo shima kuma yace to ba matsala,Ammah ta bata rai shine zaki dawo wajena?ko wacce matar aure ba haka take hakura ta zauna ba,shike nan idan baya nan sai ki bar gidan kema,ke da hakkinki ne kula da gidanki,dukiyarsa da komai nasa sai ki tattaro ki dawo,Jiya ma Aayan Yazo min ni banga Alamar lfy kuke Zama a tare dashi ba,matsala na hango sosai a tare daku,ki fada mana gaskiya ko ki tashi ki koma can gidan mijinki,Ma'eesha tace Haba Ammah ki Bari mana sai anjima ta fada mana,da bana raye ko bana garin nan gidan wa zata koma?dole tana gidan mijinta,Ameer yace nima ban yarda ba Ammah akwai matsala tun wurin sati biyu nake ganin Aayan cikin matsananciyar damuwa,a Office ma kasa komai yakeyi sai ni na koma ina aiki biyu naje nasa nayi a nawa,Har mutane frnds suna tambaya ko lfy? Ma'eesha tace nima Yarima ya tambayeni shi fa ya kasa gane kan Aayan,shuru nayi bance musu komai ba har suka gama cecekucensu,muna zaune a gidan har an kwashe 4days amma bance musu komai ba,tun suna tambayata har sun gaji,Aayan kuwa ko ya kira bana dagawa amma kuma da tuna ninsa nake kwana nake tashi,ina muradin mijina,ina son mijina amma kuma da zarar naga wani abu nasa sai na kasa cewa komai,naji bakin ciki ya addabeni,Meenat ce ta shigo Bedroom inda nake kwance sai tunanin Aayan nakeyi ina jin dadi a raina har Hawaye nakeyi,Sis lfy kike kuwa?da sauri na share Hawayena na Mike zaune nace lfy me kika gani,Ba lfy ba Sis dan Allah ko ni kadai ki sanarwa meke damunki ko za a samu mafita Ammah tana cikin damuwa akanki,kuka na fashe dashi sannan a nutse na sanarwa da Meenat duk abinda yake faruwa da abinda nake ji a raina, amma shine kika ki fada tun tuni ai da ko addua sai a tayaki da ita bari na sanarwa Ammah,bance mata komai ba har ta bar dakin,taje ta sanarwa Ammah komai har Ameer,mamaki ya kama Ameer ya shiga damuwa kowa zarginsa dai bai wuce Su Hajja bane sukayi tsafinsu, addua muka dage da ita,Ammah ta kira Aayan tace a kara dagewa da addua,Ganyyen magariya da addua Ammah ke bani ina sha kullum sabo da yana karya sihiri tare da Habbatussaudat.

   Aayan yana Abuja kamar zaiyi hauka sabo da Missing dina da yayi,ga rashin Kulashi da banyi ko a waya,ga kewata tare da tsananin sona da sha'awata da suka addabeshi,ba yaso ya dawo ma yaga naki kulashi ko yaga na kasa bacci,ya ganni a damuwa shi yasa ma yaki dawowa,ni kuwa Adduar da mukeyi yasa yanzu na samu sauki a raina,ina iya baccina zanci na koshi,Rashin Aayan kawai ke damuna,sai ko gashi na danyi kibata da kyau,Ana gyaran Amarya Ma'eesha Ammah tace a gyara mata da Meenat harda ni ma ayi min,Me gyaran yar Maiduguri ce tazo gidan sai bayan biki zata koma,Meenat sai haushi takeji ita ba Amarya ba sai tsumi ake bata ana gyara mata skin duk sha'awarta ta tashi a banza.

   Ameer yana Office yayi dogon tunani akan matsalata ni da Aayan zumbur ya Mike ya tafi can gidanmu har garden yaje ya koma Jikin bishiyar da yaga Nawwara sanda tazo tana Selfie,kuma yasan sanda tace ita kadai ma zata zaga gidan,a hankali yake kallon wurin da ko ina daga kansa yayi jikin bishiyar mango karaf idonsa ya sauka a saman wata laya katuwa da Zare a jikinta an makaleta a jikin bishiyar, ciro layar yayi yasa a aljihunsa ya koma ya kira wasu tsagerun yaransa wanda yasa suka tare Hajja suka kwace Maganin asiri,tare suka je Har unguwar su Nawwara ta dawo daga unguwa kenan taga Ameer a kofar gidansu,dadi taji ko wajenta yazo zaice  yana sonta ai kuwa da tayi dace,da Mufeeda ba uwar da ta isa ta nuna mata itama,da fara'a Ameer yace muje mota na fada miki abinda ke tafe dani,ba shiri ta bishi mota irin taga me kudi,Sai ko ta shige mota tana shiga taga yan daba ne a ciki gaba daya,ta juya zata fice suka sa lock tare da figar Motar,Ameer kuma ya shiga tasa suka bar unguwar sunci Sa'a ba wasu mutane a layin.

    Bayan sunyi nisa sosai sun shiga daji Nawwara kuka kawai takeyi tana basu hakuri,sai da suka isa inda ba kowa sannan suka yi Parking Ameer ya fito daga motarsa haka ma Guys dinsa suka Jawo Nawwara Waje,Ameer da katuwar waya a hannunsa me kauri da tsayi bai jira komai ba ya fara tsulawa Nawwara ta ko ina tana gunjin kuka ya fasa mata jiki sosai sannan yace Me kika saka sanda Kika je wajen Mufeeda,da sauri Nawwara jiki na rawa tace dan Allah kuyi hakuri wlh sharrin shedan ne,Mijin Mufeeda na ke so sabo da Kudinsa ina bakin ciki Mufeeda ta fini ci gaba,shine kawata ta bani shawara muka je kauyensu can Danbatta Lg wurin malaminsu ya bani laya yace na makale a jikin bishiya ko katangar gidan,shi yasa naje nasa wlh bazan kara ba na tuba dan Allah Ku yafe min karku kasheni.
   Layar Ameer ya Ciro yace itace wannan?da sauri tace ae wlh itace a konata, nan take Ameer ya samu lighter ya kone laya a wajen.
   Lokacin ni Mufeeda ina bacci na farka a firgice ina salati sai kiran Aayan nakeyi,Ammah dasu Meenat suna kaina ina kuka ni a nemo min Mijina,a gigice na dauki waya na danna masa kira,yana Meeting da wasu manya yaga kirana,hakuri ya basu ya dauki wayar, yana dagawa na fara magana ya zaka tafi Abuja ka barni dan Allah kayi hakuri ban san matsalata ba amma ni dan Allah ka dawo ko na biyoka Abj? Cike da Murna yana godiya ga Allah yace bari Ameer zai miki Booking Flight gobe sai ki taho,cike da shagwaba nace a'a ni yanzu nake so nazo wajenka nayi missing dinka,ba yanda baiyi ba kan na bari sai gobe amma naki yarda,Ammah tace ki Bari sai gobe Nace Ni a'a wlh tafiya zanyi ni,Ameer yana Zane Nawwara tana ihu Aayan ya kirashi yana murna yayi sauri yamin booking flight na biyoshi abuja,sai da ya ladaftar da Nawwara sannan ya basu Umarnin su kaita gidan Ammah wajena tayi bayani da kanta, haka naga Nawwara a firgice tana kuka ta durkusa har kasa tana bani hakuri na yafe mata ta fadi abinda ta aikata, bakin ciki da tsanarta ya kamani nace kije dan kanki Amma ni yanzu Bazan yafe miki ba sai ko nan gaba idan na huce Sabo da tuban dole na wahala kikayi bana Allah ba,nace a fitar mana daga gida ko wlh na kara miki wani Dukan, da Sauri tayi waje yaran Ameer suka ce ta shiga mota suka ajiyeta can gefen layinsu,

Ameer kuwa Da sauri yaje ya figi motarsa yayi min komai na tafiya Abuja,Su kuwa Yaran suna zuwa suka korawa Nawwara warning idan tace tasan Ameer ma kashe ta zasuyi,aiko a tsorace ta sa katon hijab dinta tace wlh bazan fada ba yanzu ma a gida cewa zanyi fada mukayi da wasu na musu rashin mutunci suka zanemin jiki,Good for u suka ce tare da Jan Motarsu suka bar layin ko da ta shiga gida kuwa haka tace wasu ta tsokana suka zaneta.

    Ni kuwa ina Zaune an gama zana min lalle hadadde naje Saloon sharp sharp,Ameer yana zuwa ya zayyane mana labarin komai da Nawwara tayi,aiko na dinga tsine mata ba ji ba gani,Aayan ma sai da Ammah ta sanar masa komai yana ta mamaki da Hamdala,wato yanzu kowa Malami,harda yan mata abin yayi yawa,ba a son zama lfy sai haddasa fitina iri iri.
    Ameer yana cin abinci Ammah sai albarka take Sa masa,Meenat tace anyi abin kirki sai wani murmushi kakeyi,Murmushi kawai yayi yace zan rama ne,Lokacin Lallena ya bushe na wanke sannan nayi wanka tare da shirin   Tafiya Abuja ina fitowa da Akwatina na sallami me lalle nace Ammah na tafi ayi mana addua Ameer muje,Meenat tace zan biku Rakiya ta sa mayafinta muka tafi tare,Nace Ohh Nawwara ta Allah ba taki ba,shegiya zata rabamu harda wani Dan Allah kawata ki yafe min,akan me zan yafewa shegiya ai kuwa tayiwa kanta wlh da nayi niyyar bawa Ummanta Atamfa me tsada kyauta na fasa Bazan bayar ba ko unguwar ma na daina bi ta kusa da ita,Dariya su Ameer suke min yanda nake ta mita,Sai da na shiga jirgi suka tafi gida,tuni Aayan yana Airport na Abuja yana jirana,ina sauka ya hangoni da Sauri na karasa cikin takuna na birgewa Nace Nawwarace tsinanniya na fada Kirjinsa ina sheshekar Shagwaba,ya rungumeni tsam a kirjinsa yana lallashina,3wks fa kayi bama tare kuma kace 2wks zaka yi dole nayi Kuka ai,hmm kece bakya so na rabeki ya zanyi dake shi yasa nayi nesa ko zaki fi samun sauki gashi har kiba kikayi da kyau,tausayi ya bani Sabo da ya dan rame kadan,a hankali na rada masa muje yau dadi zamuji abinda ban taba yi ma ba yau shi zan maka ka dage a yau na samu Baby,
Dariya yayi sosai yana jin dadi yace Allah yasa,muje ki fara ganin gidajena na Abuja Amma a Hotel zamuyi 1wk musha Honey moon dinmu,a'a a bari sai gobe ka nuna min gidajen nan Amma yanzu ni nayi Missing dinka abun nan nake so kayi min kawai naji dadi na,Hanci ya lakace min yana dariya yace baki da kunya My Wife me zan miki? Nace hmm ka manta abinda nafi so ma? Allah ya shiryeki nace Ameen muna dariya muka shiga mota Driver ya jamu sai Hotel na gani na fada nan ya kama mana daki hadadden gaske.
    Abinci muka ci da wanka ko gama shiryawa banyi ba yana Saman Bed ya takura nayi Sauri nazo mu kwanta yamma ba dare ba,Light na kashe na haura saman Bed din cikin jikinsa ya sani sosai yana kashe ni gaba daya jikinsa rawa yakeyi ya rude gaba daya kamar yau aka kawoni gidansa a matsayin Amarya,Boobs dina yake murzawa a hankali cike da nutsuwa,inda yake birgeni kenan baya abun Sauri komai da karfi ko ayiwa mace abu da Sauri shi sam baya wannan a nutse yake lailayani kamar kwai duk na gama fita daga hankalina nima haka nake sarrafashi.
   Kwana mukayi muna abu daya,dan hutawa kawai mukeyi muyi bacci mu farka muci gaba da jiyar da juna dadi.
 
   Ameer gida yaje wajen Su Abbi sai mamaki yakeyi yanda suka ki kulashi gaba daya sai fushi sukeyi dashi,wajen Hajja ya nufa sai yaji tana masa zancen aure,tace ka kyalesu Abbi tunda kana son yarinya dole ka aureta karka ji komai,Shi Ameer bai gane kan maganarba tunawa da zancen su Khaleel sunce Aayan ne da Daddy suka yi masa mata sai kawai ya nuna yasan zancen ya lallaba ya bar gidan kafin ya koma gida zazzabi ya rufeshi,Bakin cikinsa bai san wace za a aura masa ba amma tunda yaji ance Aayan da Daddy bashi da damar cewa a'a,haka kuma ya Kira Daddy a waya ya tambayeshi yaji da gaske ne amma Daddy yaki fada masa wacce zai aura,ya kira Aayan ma shima bai fada masa wace Amaryar ba Amma sun tabbatar masa aure za ayi masa,ciwo kansa yakeyi Sabo da bacin rai kawai sai ya wuce gidan Ammah wajen Meenat,tana karatu a zaune taga ya shigo ba sallama yana dafe kansa kamar zai fadi,da Sauri ta mike tana tambayarsa lfy? Yace aure za ayi min Meenat ban san wace Amaryar ba,Meenat gabanta ya fadi sai Hawaye sharrrr da kyar ta share Hawayenta tace wlh baza mu yarda ba,karka taba yarda,ko waye karka yarda da auren dole,wacce tsinanniyace Amaryar taka muje har gida taci ubanta,ai wlh ko ni sai na maka maganinta da kanta zata ce ta fasa,Zauna mu tsara yanda za ayi,Ameer cike da damuwa yace ya za ayi Meenat?Meenat tace kawai zanzo da Driver ranar daurin aure na saceka,sai ace an sace Ango kaga dole a fasa daurin aure ko? Ameer sai da yayi dariya Wai Mace ce zata sace Ango ai ko yace in dai zaki iya an gama kawai ranar daurin aure kizo da Mota ki saceni zan baki yaro daya wanda zai tukaki a mota,Hankalin Meenat ya kwanta tace Alhmdllh ai an kusa bikinma ko?Ameer yace tare dana Ma'eesha fa gashi nan kinga Ammah tana ta hada Lefe Aayan yana shiri,Meenat tace baza a cuceka ba Ya Ameer dole na taimaka maka,Yanzu bari na kawo ma abinci kaci kaji,Meenat ta lallabashi yaci abinci ta bashi paracetamol ya sha tace ci gaba da sha'aninka zan saceka ranar bikin,Ameer ya mika mata Bundle na yan 1k har biyu yace kudin da zaki kamamin Hotel idan kin sace ni Amma ba a Kano ba za ayi saurin gano mu ki kaini Kd,Meenat tace karka damu wlh ba wanda ya Isa yama aure da wata shegiya ina raye.
    Sai da muka kwashe 2wks a Abuja Aayan ya shirya mana zuwa Saudiya tare da Us zamuje hado lefen Ameer wanda ba a siya ba English wears etc,a waya muka sanar musu kawai.
   Bayan mun gama Aikin Hajji 1mnth muka wuce Us nan ma mun kwashe 1mnth biki saura 3wks muka dawo tare da Daddy gaba daya Kano muka sauka,Dangin Yarima sun kawo Lefen Ma'eesha na gani na fada akwati 9,da muka Hada na Ameer shi kuma akwati goma sha Uku Aayan yayi Ammah tace a rage Aayan yace a'a,Meenat tace to wai baza a kai lefen Ameer dangin Amarya ba?Ammah tace sai bayan biki sunce,baki Meenat ta tabe lokacin ana ta gyaran jikinsu gaba daya har ni ma Ammah tace sai anci gaba da yi min Aayan baya daga min kafa sai da gyara.

     Bayan 2wks biki ya matso ana ta shirye shirye Ameer an bashi Iv dinsa yaga Ansa Ameer da Amina bai gane Meenat bace,Su Khaleel sai murna da shirye shirye sukeyi,idan Ameer yace bai san Amaryar ba zaginsa kawai sukeyi wai zai raina musu hankali,Haka Umman Ameer tace tunda Zabin Daddy ne kawai ya karbi auren ba matsala,Aayan yace Ameer a ina kake son Zama? Kano mana yafi min dadi,takardu da mukullan gida ya mika masa na gani na fada yace gashi kusa da gidan Yarima kake Estate daya kuke,Ameer ya karba yana godiya,Aayan yace ga Motoci biyu nan na kara maka kyauta suna gidan,nan zuciyar Ameer tayi sanyi mutumin da yayi maka haka ai bai dace ka bijire masa ba,Amma yana fadawa Meenat ta dinga masifa tace dole sai ta sace shi,Ammah tace tunda Meenat basu sani ba kawai ba sai anyi su Dinner ba,Yarima ya dinga Murna dama ya matsu a kai masa Amarya gwara ana daurawa da yamma a kai masa abarsa zumudi yakeyi su Aayan sai tsiya suke masa yace dama shi dan Izala ne.

   Meenat kuwa Su Haneefa sun dameta da Amaryar Yaya har haushinsu take ji,ranar asabar ranar kuma daurin aure ce,yan Uwa na kusa dana nesa sun cika gida, Meenat da Ameer sun shirya Driver dinsu,driver ya gane shirinsu ya zage ya fadawa Aayan,dariya Aayan yayi yace kayi abinda suka saka kuma karka fadawa kowa bayan ni,shima Aayan yayi shuru da bakinsa, Ameer kamar gaske yasha wanka ya fito Kofar gida inda za a daura aure a masallacin unguwar da Ammah take sai Ko Meenat ta kirashi a waya nan tazo da mota tasha tint Ameer ya shiga suka figi mota Driver na jansu har Kd,Lokacin kuma11:30am aka daura Auren Ameer da Meenat,Maeesha  da Yarima,Aayan ya biya Sadaki har na Yarima dubu Dari dari,Kowa neman Ameer da Meenat yake an rasa hankalin wasu duk ya tashi musamman Ammah da ni,Aayan yace yasan inda suke kawai muci gaba da shagalinmu duk ya bamu labarin komai sai dariya ma da akeyi,har Daddy,su Abbi kansu abin ya basu dariya Amarya ta sace angonta basu san an daura musu aure ba.
   Su Khaleel suka ce shege ashe da gaske bai san wace Amaryar ba ai mun zata wasa yakeyi,Ameer kuwa ya kashe wayoyi haka Meenat ma basu tsaya ko ina ba sai a garin Kd cikin katafaren Hotel,Meenat tace to ni nayi maka me Wuyar bari mu koma Kano,Ameer yace wlh kina zuwa za ace kece kika saceni ko ace kin kaini gidan yan yankan kai gwara mu zauna tare a nan nan da 1wk sai mu koma,Meenat tayi tunani tace tabbas hakane Amma ni Bazan iya kwana a Hotel ni kadai a daki ba,Ameer yace me zai faru sai ki kwanna a Bed ni a kasa just 1wk ne fa,Meenat tace na yarda da kai kai Driver ka tafi gida kace baka san inda muke ba,haka Driver ya tafi kuwa yana mamaki.

    Suna shiga suka biya dakinsu na Sati daya,Meenat tace ban taho da kaya ba Ameer kuwa da yake shiryar abin yayi da kayansa a akwati,Ki shirya anjima sai muje a siyo miki,Kowa da yayi wanka a toilet ya shirya suka fito sukayi sallah abinsu sannan suka fita dagwas dagwas dasu,Ameer yaga Kd ba Uban wanda ya sansu hannu ya mikawa Meenat itama ta bashi suka rike suna Tafiya cike da jin dadi har suka Isa inda ake siyar da readymade kusa da Hotel din,sun siyo su dogayen riguna dasu riga da skert sai take away na abinci da Sauran kayan ciye ciye da suka siyo suka shigo Taxi abinsu har Hotel.

   A room ta sa rigar bacci doguwa ta mutunci wai tana kare mutuncin ta,Ameer kuwa daga shi sai Boxers yana Saman Bed sai mutsu mutsu yakeyi ji yake kamar ya rungume Meenat a jikinsa suyi bacci,Meenat tana saman Sofa tana danna wayarta ta sata a flymode shima haka,wani American film yake kallo a waya Meenat tace dan tura min na rage dare ta zauna gefen Bed din,yace to matso mu kalla a wayata kawai mana mene na bata lokacin,Meenat ta kalli surar Ameer me masifar kyau,wanda take matukar bata sha'awa da birgeta ga kamshinsa me Tafiya da Imaninta,Bata ma san sanda ta matsa ba ta kwanta a gefensa dan nesa kadan,Kamshinta ya cika masa ciki itama haka,wayar ya mika mata jikinsa a mace yace rike mana zata karba Hannunsu ya gogi juna,wani shock suka ji gaba daya,Ameer kasa jurewa yayi.




AsmaBaffa
[2/13, 6:08 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

    KASUWANCI NA





        
           119-120




Official








By
AsmaBaffa

 


     KASUWANCI NA FANS page naku ne Sabo da Sharhi.







     Ameer kasa jurewa yayi gaba daya jikinsa ya fara rawa,tunawa Meenat tayi ba Muharraminta bane sai ta dan matsa kamar zata fada kasa ta wayance da dan karo mana Volume tana basarwa,Ameer waya taki rukuwa a hannunsa kawai jiki a mace ya saki wayar ta fadi kasa idonsa ya koma red sai kallon Meenat yake kamar zai hadiyeta,idonta ta lumshe tare da waresu Ameer ya saki ajiyar zuciya yana wani shidewa a hankali yasa Hannu tare da kashe light dif,Meenat ita kanta shauki kwasar ta yakeyi tace satoka fa nayi taya zaka wani kashe light kuma sai da kace ba abinda zai faru,Juyawa yayi ba tare da yace komai ba ya kifa cikinsa tare da rike Mararsa ciwonsa ya tashi yana nuku nuku,sai nishi yakeyi sama sama,Kawai Meenat tace ni dai ba tausayinka zanji ba idan ma zaka warke ka warke,gani tayi da gaske yake karfa ya mace mata a Hotel da ta shiga Uku ya zatayi ai cewa za a ayi wasu suna Iskanci ya mutu a daki za azo a watsata a radio me zata cewa Ammah,Allah ya taimaka ma ba a Kano suke ba sarakan Sa ido😅👍 da a Kano ne da tuni yan Hisba sun fara zagaye yanzu kaji sunanka a Radio,tana wannan tunanin Ameer masifa ta isheshi kamar zai mutu ga Mara na ciwo ga Masifar Meenat yasan halinta wlh baza ta tausaya masa ba bare ko zafi ya rage,ya rasa ta yanda zai iya shawo kanta,Kawai da Mararsa tayi wani Murdawa sai Ameer ya fara Kuka,kuma munafuncin Ameer ne ciwon bai kai yayi kuka ba,kawai ya fara Kuka kamar mace,Meenat tace kayi ka gama ma ni da me zan taimaka maka ka wani fara kuka kamar yaron goye ya kake so nayi maka dan Allah,Ameer da masifa yace ai ke kika sato ni da ba haka ba ai da kin barni ko banza ina da Mata zanje wajenta kuma dole ta bani abinda nake so,kawai kin sato mutum kina gana masa azaba.

    Dariya Meenat tayi tace au nayi maka rana shine zaka min dare daga taimako,ae wa yace ki taimaka ki maida ni wajen Amarya ta mana ai nasan maybe ma yanzu an daura auren tana can tana jirana ko wace zan yarda na karbi aurena,Kishi Meenat taji ya kamata,haushin Amaryar takeji tace to an sace ka din wlh kayi wasa Amaryar nan kafin ta sanka sai daí ta samu kwancen wata ta samu ragowa,Ameer yace au bayan satar harda raping dina kuma? ki maidani wajen Amarya ta ni ta bani abinda nake so,Allah Sarki My love tana can yanzu a sabon gidana,haushi ya kama Meenat,Ameer ya kara cewa dama ance kyakyawa ce ta karshe ga shape komai yaji,Meenat ta hade rai tare da zuba tagumi,a hankali tace me zan maka to kafin gobe na mayar da kai gida? Ameer yace Kiss ..Sai kuma muyi bacci tare,Baki Meenat ta hangame tace to kai bafa mijina bane taya zan yarda kawai kayi min ciki?Haka ake cikin?daga kiss,ni Bazan miki komai ba am serious pls kawai kwanciya zamuyi kinga ma bani da lfy ina naga wani karfi,Meenat Sabo da kishi ta koma kusa dashi ta kwanta a gefensa,Matsowa yayi sosai ta kasa Motsi gaba daya Sabo da surar Ameer da kamshinsa sun gama Tafiya da ita bata iya hana komai,tana ji Ameer ya jawota jikinsa ido ta lumshe a ranta tana dole mata suyi rubibin Ameer wannan irin Ni'ima haka,Ameer ajiyar zuciya ya saki basu taba zancen soyayya ba ko daya Amma sai ga shauki ya kwashi Ameer yace Beb....My love...u r so Amazing, ki aureni kawai pls,Meenat dadin kalamai yasa tace cike da wata uwar shagwaba hmmm abinda kana da yan mata kana kula mata,Ameer ya narke yace haba da ne fa da dadewa Amma yanzu bana kula kowa kuma wlh banyi komai dasu ba,dan Allah ki aureni wlh nasan Aayan zai yarda,Meenat tace ni ban yarda ba kana kula wasu tunda a gabana kayi waya da wasu,Wayarsa ya dakko tare da nuna mata kalla Beb ki duba contact da text ki gani wlh bana kula kowa,Meenat ta karba ta fara bincike wacece Maryam? bina take wai na aure ta nace a'a taki yarda ko a kirata kiji? Ana haka sai ko Ya manta ya cire flymode sai Kiran Maryam ya shigo,yace Alhmdllh bari ma kiji,Hello ya daga,Maryam tace Darling me nayi maka baka kaunata ina ta binka? Ko wayata baka dagawa,tun daga Niger fa nake kiranka Amma ko Saurarata baka yi,Meenat bakin kishinta ya tashi a lokacin ta maida kanta saman kirjin Ameer tare da yin Mika tana Kukan shagwaba tace Mineeeee....u r so Sweet Common Baby Need some more wai dan maryam taji tace Ameer matan banza yake bi dan iska ne ta fasa,aiko Maryam tace muryar wa nakeji Ameer cikin Dare haka? Yanzu dama abinda kakeyi kenan ,Meenat tace gobe Baby Hotel zamu canja ko? Maryam ta hangame baki tace ai ko ba mutuwa akwai cuta bazai yuwu na aureka ka dakko kanjamau ka kanjama dani lahira ba ditttt ta kashe wayarta tace na fasa yaje dama masu kyau irinsu haka suke da shegen neman mata. Dariya Meenat tayi jin wai za a Kanjama da ita lahira,Ameer yace kin kyauta kin kashe min kasuwa,ci gaba da Searching wayar tayi tana tambaya daya bayan daya saiga kiran Aayan ya shigo,Jiki na rawa Ameer ya daga ,Aayan yace ina ka shiga Ameer?to aure ba fashi an daura in kaga dama ka shekara baka dawo ba,wacce baka so ita aka baka kuma komai dadewa ka dawo Amarya na jiranka,Bai nuna yasan suna tare da Meenat ba,Meenat ce tayi magana ai wlh tunda aka daura baza ka koma ba sai an warware auren nan ko na fasa aurenka ai kace na aureka to ni Bazan zauna da kishiya ba ehe,Aayan yasan Meenat ce sai yace muryar mace nake ji ko me Ameer? Kitt Ameer ya kashe wayar ma gaba daya,Aayan kuwa yana jikina a kwance lokacin ina dariya kasa kasa,Aayan yace lallai yaran nan yan duniya ne yanzu da ba daura ba haka zasuyi,Nace hmm Ai ko da tayo ciki Allah kiyaye, yanzu dai ke zo na miki naki cikin yace ina dariya tare da jin kunyar maganarsa muka fara soyewa lokacin Ameer ya tuna dole fa ya bawa Aayan hakuri nan take ya Kira wayar Aayan lokacin Munyi nisa a harka lokacin Aayan yana so ya kashe waya ashe dagawa yayi Ameer baiji komai ba sai irin Sweet words da Aayan ke furta min yana Kukan Dadi,da Sauri Ameer ya cire wayar a kunnensa,Meenat tace muji ta karba ta kara a kunnenta da Sauri ta kashe tace wlh Mufeeda yar Iska ce,Ameer yace Aayan ne Ya yankewa Iskanci cibi a kasar nan suna dariya,Meenat tace kira Ma'eesha Amarya muji nata kalar,Ameer yace ai kuka zatayi ita First night ne,mu dai kira muji,Nan Ameer ya Kira wayar Yarima lokacin Yarima anyi Sallah da cin abinci an fara baje Kolinsa yaji waya yana dubawa yaga Ameer,tunani yayi ko ba lfy ba tunda baya gida sai ya daga da kyar muryarsa na rawa da kyar ma yake magana,Ma'eesha tuni Hawaye ake gogewa anyi shuru,Yarima yace lfy? Lfy mana ya Amarya dama lafiyarka na kira naji,wani tsaki Yarima yaja yace aikin banza kuma sai yanzu zaka kira dan Iskan yaro,To yi hakuri hadani da Ma'eesha kanwata naji lafiyarta,Zanci kut....Yarima ya dura masa ashar tare da kashe wayarsa,Meenat tana dariya tace bani wayar Allah sai mun hanashi sakewa,Yarima anci gaba da shagali yaji waya ta kara kugi,ya daga cike da masifa Sai yaji Muryar Meenat tace Yi hakuri network ko ta katse bawa Ma'eesha naji muryarta,Ke dai Anty ce wlh cewar Yarima yana datiya,ya kashe wayarsa gaba daya yana dariyar shirmen su Meenat,Meenat ta kashe wayar Ameer gaba daya tace soyayya dadi,wlh mu kara kiran su Mufee Aiko suka kara kiran Wayar Mufee ina dubawa nasa hannun na jefo wayar kasa ta kashe kanta,Meenat tace shu'uma Sis ashe abinda take yi kenan kaima Ameer anyi ma aurenka nice kadai,Baki Ameer ya turo mene haka pls? Gani ai nine mijinki muna komawa za muyi aure ko? Kai kawai Meenat ta daga masa,a hankali ya daura hannunsa saman kirjinta.

     Fara shafa Albarkatun kirjinta yayi Meenat dama ansha Tsumi an gaji nan take sha'awarta ta motsa itama ta kasa hanashi yin abinda yaga dama sai ma taimaka masa da takeyi,ta fara kissing dinsa a hankali,Harshensa ya zura mata a hankali a kunne nan Meenat ta kara tafiya gaba daya,har ya tabbata bata ganewa ya cire mata kayan jikinta bata sani ba sai ji tayi Harka ta kara dadi,Ameer yace kina jin dadi?, Kamar yar maye tace Harka tana tafiya dai dai,Basa iya tuna basu da aure ko a jikinsu Ameer cewa yake kawai Marry me pls Beb,Meenat tana I will...Idan yace will u? Sai tace Must....kawai ba wani Insha'allah kawai Must,sai da Ameer yasa ta daina gane gabas da yamma bata ma san a ina take ba kawai so da Kauna take gwada masa,Har Ameer ya nemi Hanyar yace Beb nayi?Meenat tace ni dai A'a babu kyau idan nayi ciki fa,harda Sa hannu ta rufe wajen ruf,Ameer ya kasa hakura yana Jinta timbir a jikinsa yace Bazan yi releasing a ciki ba Allah,bazan miki ciki ba sai anyi mana aure,Meenat tace Zinafa Allah ya hana,Ina zuciyarsu taki karbar gaskiya ta manta da wani batun rashin aurensu,Yan mata a kiyaye kar so ya kwasheki Namiji yasa ku kebe Sabo da dadin baki so da kuma wani dadi ya sa a kasa tunawa da Allah ana tunanin akwai mafita sai ya faru aga no way out ba mafita me bullewa,a kiyaye kebewa tare da bin son zuciya tsab Shedan zai fi karfinku komai Imaninku kuwa gwara su Ameer su suna da babbar Mafita tunda da aurensu.

    Meenat tana ji tana gani yayi mata abinda yasan ko wa akayiwa shi baza ta iya hakuri ba tare da an shigeta ba,Haka Meenat tace idan kasan da gaske zaka aureni to kayi kadan Amma wlh idan naji da safi Bazan yarda ba,haka kawai kace ni bata gari bace kazo kana zargina bayan anyi aure,Ameer yace haba Meenat wlh nasan Ke Virgin ce kuma zan aureki wlh am serious ina mugun sonki,sonki ne ma yasa har naki yarda da wancan auren,Meenat taji dadi tace da gaske?ae na dade ina sonki a duniya wlh,Meenat ma tace nima haka Allah ina Sonka Amma idan kayi zaka daina ganin mutunci na kace ni yar Iska ce dama,wannan Mentality din bahaushe ne shi yake lalata mace yace mata yar Iska kuma,shi kuma mene?shima dan iska ne ai ko? Meenat tace ae,yace me yasa har kullum anfi ganin cewa mace ce yar Iska kadai shi kuma Namijin da yayi mene sunansa? Ta yuwu ma shi yana yi da mata da yawa macen kuma da shi ta fara Amma sai ya take laifinsa ya hango nata,duk da cewa matan sunfi Laifi a ciki tunda ita ta yarda har akayi Amma wlh Matan ma suna da laifi na fasa yi miki komai ko zan mutu har sai na aureki,Allah na gode ma da ban aikata komai ba kika tunatar damu,Meenat tace to ai ance anayi a tsakanin cinya kawai kayi anan sai kaji sauki,Aiko Ameer yace Allah ya yafe mana ke gyara min cinyar ta isheni,A nan dai Ameer ya samu nutsuwa abinsa shar shar ba tare da ya shigeta ba,Ameer yana cewa aike Baby ko iya cinyar ta ishi mutum ma,Allah ya baki Meenat,Meenat tayi wani likimo a kirjinsa ya kara kankameta a jikinsa suka sha baccinsu,Harda makara yau ba suyi Sallar asuba da wuri ba,sai da Safe Meenat ta shiga jin kunyar banza ta maida kayanta tare da shiga toilet Amma a ranta sai wani dadi takeji tana murmushi ita kadai maimakon taji haushin Ameer ma Amma sai taji ta kara sonsa ma shima Ameer hakan take a wajensa har godiya yake ga Allah da bai yi Sex da Meenat ba da tuni ta daina sonsa,Wanka kowannensu yayi tare da shiri suka zabga kwalliya kowa yana son birge masoyinsa.

    Wasu manyan Igbo christain ne suka zo su biyu tare da bahaushe daya har tsohon gidan mu wanda muka bari Har Ammah ta saida dashi tace kudin suna hannun dangin Abbanmu,Tambaya sukayi ina masu gidan Mufeeda dasu Meenat?Nan aka hadasu da me unguwar layinmu suka yi masa bayani,nan ya shiga gidan su Nawwara yana tambaya ko tasan inda muke rayuwa ga baki sunzo Abbanmu ya basu Sako,Nawwara tace tasan gidan Amma Sabo da abin kunyar data shuka tace baza ta iya zuwa ba sai dai kwatance,Nan ta gwada musu gidan Ammah tare da gidana,tare da ita sukace ta rakasu kofar gida ba sai ta shiga ciki ba,haka kuwa akayi har kofar gidan Ammah sukayi Parking da motarsu,Meenat da Ma'eesha duk basa nan tunda Ma'eesha na gidan miji Meenat ta sace Ango,ni kuma Aayan ya hanani Zama dole yace sai mun tafi gidanmu shi bazai iya kwana shi kadai ba,Waya Ammah ta buga min nazo tare da Aayan da Daddy munyi baki,Haka ba shiri muka zo tare da haduwa a palon Ammah,Suma Arnan kudu gasu a zaune an kawo musu kayan sha,daya a ciki ne yayi magana da turanci yace wace Ammah Matar Abban su Mufeeda? Ammah tace nice,Ga kuma Mufeeda,Suka ce to Abbanku dai Allah ya masa rasuwa sakamakon wata kungiya daya shiga ta yan asiri suna yin kudin Tsafi,dama yace ya gudu ya barku ne tunda Allah ya hadashi da wani abokinsa da yake harkar kungiyar sai akace idan yana so yayi kudi to fa bashi ba aure sannan ba haihuwa,sabo da son da yakewa yaransa da Matarsa yasa ya gudu ya barku dan kar ma dodon tsafi yace yana bukatar jinin yarsa ko matarsa shi yasa ya dinga wulakanta matarsa sannan yace ya tafi neman Kudi Can North ya koma cikin yan kungiyarsu sune suke tsotsewa mutane jini suna satar Yara ana kaiwa gidan tsafi,mu yan sanda ne a kudu asirinsu ya tonu an kamasu kuma kotu ta yanke musu hukuncin kisa shine kafin a kashe su ya bamu wannan sakon sannan yace a fada muku yana baku hakuri ku yafe masa sannan a fada muku yana kaunarku karku rikeshi a ranku dan Allah ku yafe masa yasan ya zalunceku bai kyauta ba,wani Musulmi a cikinsu kuma bahaushe yace kuma ya tuba yayi Istigifari ga Allah yanzu ma da za a kasheshi a gabanmu yayi Kalimatushahad, Allah yasa karshen wahalarsa kenan,Allah ya Amshi tubansa,Hawaye ya kwararowa Ammah tace Ameen Ameen mun yafe masa duniya da lahira Allah yaji kansa da Rahma,Mukace Ameen ban wani damu ba tunda bamu wani shaku dashi ba,amma Mahaifi ne sai da kwalla ta zubo min ina godewa Allah daya tuba kafin ya cika Allah ya amsa,kuma gwara da aka yanke masa hukunci abinda ya shuka ya girba,nan suka bamu wani envelope na pics din Abba kala kala cikin daula yayi kyau jajir dashi,sannan wasu zobe na Gold masu kyau kana kana a ciki da sarkoki kala Uku a ciki,short note dinsa cewar wannan na yarana mata ne Mufeeda,Meenat da Ma'eesha kar ku manta dani yarana karku manta da yi min Addua me kyau,Haka Ammah ma Tata sarkar da bangle tare da zobe du na Gold manya yace ta Matata Abar kaunata,nasan na kuntata miki ba wani abu yasa na daina kusantarki ba lokacin muna tare sai wannan Kungiya dana fada wacce nayi nadama na tuba son zuciya da neman duniya yasa na aikata miki laifi iri iri ki yafe min sarkokin dana baku da kudina na Halak na siya muku ba kudin Haram bane,gonaki na gado na kauye na siyar na siya muku karku ji tsoron komai,ban gujeku dan bana sonku ba sai dan kar na cutar daku Sabo da son duniya,na barku cikin talauci ban baku komai ba cikin dukiyata ba Sabo da nasan da Haram zan ci daku shi yasa nasan halin da kuke ciki na share ku, Alhmdllh nasan inda Yata take aure da wanda su Meenat zasu aura, sannan watarana naga Meenat ido da ido a mota itama nasan ta ganni kuma ta gane nine.na barku lfy ina neman Adduarku.
   Sai lokacin na tuna sanda Meenat ta zo da murna ta fada min wlh taga Abba a katuwar mota ta alfarma yana ja ashe kuwa gaske ne.
    Bayan mun gama karantawa na tambaya nace yanzu an harbesu? Daya daga ciki yace tun lastweek koti tana yanke hukunci aka harbesu shine yace a kawo muku yanzu sai ku sanarwa yan Uwa ayi masa addua.

   Bayan sun gama suka ce zasu tafi haka Daddy yayi musu babbar kyauta tare da godiya suka tafi,lokacin daga ni sai Ammah a Bedroom muna jimami don shi Aayan tausayi yasa ya kasa magana sai Barin gidan ma yayi gaba daya,nace Ammah dama sanda muna Yara mun san kuna fada da Abba shine kika ki fada mana dalili ashe kin san komai,Ammah tace tabbas na sani Sabo da ni ya fara kawowa zancen kan na bashi shawara ya shiga ko a'a naki yarda nace sai dai ya sake ni mukayi ta fada kullum,shi kuma yace bazai sakeni ba ko dan yaransa,kwanaki kadan kuma wani ciwo ya fito min a farji na wanda naki fada muku wanne ciwo ne amma kun san aiki biyu za ayi min a lokacin tunaninku a cinyata yake da kafa,duk a sanadiyar shiga harkar asirin Babanku ya shafa min ciwon,Dodon tsafi ya bashi magani idan zai sadu da matarsa ko wata mace ya zuba maganin ba tare da macen ta sani ba,tunda ya zuba min ban sani ba kawai na tashi da gabana da wani Katon kurji guda me ciwo da zafi ga tauri kuma yaki warkewa kin san magani har na Hausa ba wanda banyi ba Amma baku san mene ba,kawai ciwon dake kafata kuka sani shima duk sanadiyar Abbanku na samu cutar Amma Alhmdllh Allah ba azzalimin bawansa ba gashi na warke sai tarihi,Duk wannan shine asalin fadan da mukeyi,kuma ni naji labari yana raye yana zuwa Kano ma,Karshe bakwa gida duk kun fita ya Aiko min da takardar yana nemana mu dawo mu zauna tare dashi zai min maganin cutar dake damuna,shine ma da Aayan yace zasu fitar dani waje nace kawai ace na rasu dan kar ma yasan ina raye,ga kuma dalilina na kisan me rayuwa take ciki,kinga tunda yana bibiyarmu yasan bana raye daga baya kuma yasan ina raye na dawo tunda gashi har sarka ya siya dani.Daddy ne ya Kira mu har Aayan nan ya kara yi mana nasiha me shiga Rai karshe yace ya samu matar aure shima watace yar Katsina state zai aura Dattijuwa ta kirki kyakyawar gaske ga iya wanka.
   Aayan ya mike yabi bayan Daddy wai shi sam bai yarda ba sai dai ya Auri Ammah ai Allah ya halatta,Abba yace ina sam shi kunyar Ammah yake ji bazai iya da na auren yarta shi kuma ya auri uwar ba,duk da Allah ne ya halatta shi bazai iya ba,Aayan shi kuma yace wlh bai yarda ba,Daddy yayi dariya yace ji min yaro kaine zaka zauna min da matar,Aayan yace Allah ko ka auri matar nan sai na koreta ya bar gidan a fusace.

    A waya na kira Ma'eesha na sanar mata da komai sai kuka takewa mutane a waya,nace ke dalla wai mene haka addua zaki masa,Maeesha tace ta Abba ai ta kare Sis ni ta kaina nakeyi dan Allah kizo Sis,Ba inda zanzo sanda kike fitsararki za ayi miki aure wa kika nema yanzu kuma me zan miki,Sis wlh ya gama yi min dugu dugu dan Allah kizo tana kuka tana rokona,Aayan na kira a waya nace kazo ka kaini gidan Ma'eesha ko ka turo Driver ya kaini bata da lfy,Ke...mene haka ina ruwanki mijinta ya dauki wahalarsa ki kyalesu ke wa yazo ya taimaka miki ai ni nayi wahalata ba inda zakije bare wasu su dinga kalleki a kan hanya,gasu nan a titi mutum na Driving yana leken motar wasu idan yaga me kyau,kice zaki zo kawai ki share ta,to kawai nace masa Amma kaga su Meenat fa basu dawo ba,yace af ki kyalesu dan Allah duk na fadawa kowa idan sun dawo kar ace suna da aure ayi musu shuru a Saurayi da budurwa suke idan ya mata ciki zamuga yanda zasuyi da cikin,Nace kar su zubar a boye ba a sani ba?ido zan Sa musu ai zansa masu kula dasu,ai Meenat ma tana da tarbiya baza ta bari ya mata ciki ba sai ta tabbatar suna da aure,dariya Aayan yayi yace dake a Hadith aka rawaito su ko a Qur'ani aka fadesu ko?ke anan harkar babu wani Uztaz komai tsoron Allah dinka nasan Ameer fa Sarai dan ma ya tuba ne karfin sha'awa gareshi wlh zai wahala su rabu da Meenat baiyi komai ba,To Allah yasa ma an daura musu auren cewa ta,Anjima zan dawo na daukeki ki zauna wurin Ammah Ok nace Allah ya kaimu,I love u nace yace Love u much more Dear tare da sakar min Kiss ta waya sannan ya kashe.

    Hajja ce zaune tayi jugum tana tunanin rayuwarta ta baya taga fa tunda ta taso a rayuwarta da yawon Malamai ta saba Amma har yau dai ba abinda ya canja babu wani ci gaba data samu,yanda ake da haka take har yanzu sai ma abubuwa da suke lalace mata kullum,gashi ta raba kan yayanta ta tarwatsa su,amma ta godewa Allah da Mutum dayane aka ware wato Daddy,Su Abbi da take so gasu nan tsiya tsiya kullum sai ma rayuwarsu da ta dakushe ta sanadiyyar tarbiyyar data yi musu,jikanta daya da aka ware ba a so shine komai dinsu,shine gatansu,duk da abinda sukayi musu ko aka basa kawosu,basu fasa yi musu komai ba wanda suke so din ne ma basa taimaka musu da komai Sabo da mutuncinsu ya zube a gaban yaran,sun san duk abinda suke kullawa kuma ba me kyau bane, ita kadai take tunaninta iri iri nan ta tabe baki tare da yin kwafa ko ta mene oho.
    Khaleel ne ya shigo yana Bouncing ya kalli Hajja yace yane?Ya akayi kuwa gayu cewar Hajja tunda yan iska ne itama haka zata mai dasu,Yayane ya akayi ne ta gidana?Hajja tace Hakan akayi Baba sai akayi Yaya ne eh? Dariya ce ta kama Khaleel shi tsokanarta yayi kawai shine itama wai ta canja murya ta rama,Mujaheed ya shigo suka tafa da Khaleel yace Guy Beb din nan tana yawa wlh aurarta zanyi Amma ka gane sai wani raina min wayo take,Khaleel yace har yau baka gane mata ba kai banza ne na fada ma yanda zakayi ka yaketa sosai kaki ji,Mujaheed yace hmm an zuba mini Kaye wlh Amma nifa aure nake so wlh idan na kara shekara ba aure to fa yaro zai lalace,Khaleel yace ai kai shekara kace ni na kara 6mnths ko kamar Hajja na samu kwamusheta zanyi kawai,Hhhh suka dinga dariya,Hajja tace wlh baku Isa ba Allah ya fiku yan iska wlh ni uban Babanku ne dai dai ni,Kakanku shine kuma da gashi wlh na rufe kofa,dariya suka dingayi Mujaheed yace yo ke Hajja me za aci dake wai kinyi expired me zaki tsinanawa wani ke da kika iya ma irin na da na yan kauye bana zamani ba,Haja ta kwalla tafi ai wlh karya kuke me na yanzu zasu fada mana duk abinda kuke ji dashi kafin kuyi anyishi,Matan su Sajeeda sai dariya suke Hajja ta zage ana ta musu da ita ita bata yadda ba bata tsufa.

   Su Abbi ana ta neman matan da za aura Amma an kasa samu sai na banza,da kyar suka samu wasu Zawarawa ko wanne ya fito da ita zai aura,abinka da auren Manya sati biyu tsakani Suka sanarwa Daddy ya musu komai aka daura aure tare da tarewar Amare marasa mutunci na karshen gari ne,ko wacce da kalar nata rashin mutuncin,Su su Khaleel suna ta bakin ciki,Hajja kuwa Murna takeyi sun auri mataye na gari,da Daddy yazo gaisheta harda gori ta masa cewar saura kai tsohon gwauro an kasa aure,ka daure ka ajiye mata ko ka
Samu nutsuwa ga yan uwanka su Uku sun dallo mata matasa., Daddy yace na kusa ai Aayan ne yake bani matsala shi sai wacce yake so,wai cewa yayi na auri Maman Mufeeda,nan take Hajja ta fashe da kuka su Mufeeda gaba daya sun mallake mata zuri'a yanzu har uwar ma so ake Danta ya aura kuma abin haushin duk masu kudi,masu halin kirkin dangin Mufeeda suke aurewa takaici ya kama Hajja tace yanzu har Uwar tasu gososo da ita itama aure take so kuma ta rasa wanda zata aura sai kai,Uwa gososo da ita katuwar banza tana Tafiya kamar wahainiya da Duwawu kamar tukubar tsire tana mirginasu sai shegen iyayi da kisisina duk tabi ta koyawa yaranta suna ta mallake Jama'a nan Hajja ta dinga masifa,Daddy yace bafa aurarta zanyi ba Aayan ne yake so na aura,ai abinda yace shi kakeyi tunda yace ka aureta nasan sai ka aura,da kamar ba kai ka haifeshi ba Sai abinda yace sai yanda yayi da kai tirr da halinka.
 
    Meenat kuwa bayan sun karya tana saman Sofa Ameer na Bed Amma hankalin kowa yana kan dan uwansa,tana tunanin daren jiya yanda Ameer yasa taji mugun Dadin da baza ta manta ba shima tunanin da yake kenan, kallonsa tayi shima haka yace dawo nan Muyii bacci,Meenat anji dadi jiya batayi musu ba ta koma jikinsa ta kwanta,yana shafa gashinta me santsi da tsayi a hankali ya rada mata ko mu kara sati daya a Hotel kinga sai muyi 2wks ko?Meenat ana shagwaba tace ae mu kara yanda kaga ya dace,Nan ma basu bata lokaci ba Ameer ya fara rabata da kayan jikinta.












AszmaBaffa
[2/14, 11:57 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

    KASUWANCI NA





           121-125




Official




By
AsmaBaffa






          AsmaBaffa wannan page nawa ne na kaina sabo da dadin Typing😍.







      

   Ameer ya fara rabata da kayan jikinta kenan Meenat ta fara karbar Dadinta zam zam firgigit ta dawo hayyacinta ta tuna basu fa da aure Allah ya tsinewa me yin haka,ita bata damu da wani dan Adam ba wai ko zai mata gori nan gaba kawai sabo da Allah ta tuna ba kyau fa,nan take Meenat ta maida kayanta tana Hawaye ta tattara nata ya nata,Ameer yana tambaya lfy?ta bari da yamma sai su koma Kano,Meenat dama ta Kware wajen iya masifa nan ta hayayyako masa da masifa tana Galla masa harara,zaka lalatani dama haka kake wlh bazan aureka ba kaji na rantse na fada ma bazan taba aurenka ba har abada,Hannu Ameer yasa tare da riko kafadarta da sauri ta fisge kanta tace matsa Malam bani ba kai anyi min tarbiyya ta zaka batata dama Ku gidanku baku gaji tarbiyya ba,maganar nan da ta fada tayiwa Ameer ciwo matuka ko ba komai ai tayi masa kara amma ba komai shi ya jawo daya kula yarinya haka amma ya zaiyi wlh yana sonta da gaske sosai ma,shanye bacin ransa yayi tare da cewa kiyi hakuri da nasan abinda nayi zai bata miki rai bazan taba ko rike miki yatsa ba,kiyi hakuri karki ce bazaki aureni ba,wlh ina Sonki kamar raina,da farko ban gane hakan ba sai da za ayi min aure na gane ke nake so Meenat,Da ace ba ke bace bazan bari ma na biyoki nan ba,karki manta ni ba yaro bane amma na biye miki muka zo nan,dan Allah ki aureni Ameer ya furta tare da dire gwiwoyinsa biyu a kasa yana rokon Meenat kamar almajiri,sai hakuri yake bata bayan ita ma ai da laifinta amma Still hakuri yake bata.

    Meenat idonta a rufe kamar bata San Ameer ba bazan aureka ba tunda dan Iska ne kai wa ya sani ma ko gado kayi ,Meenat da kuruciya ma magana da dama idan tazo mata gani take dai dai ce, wannan maganar ta Meenat itace ta batawa Ameer rai ai ko ba komai ta daraja iyayensa wato a wajen iyayensa ya gaji iskancin,idonsa ne ya canja yayi jajir jikinsa yana rawa sabo da bacin rai,shi da ba Meenat bace ta fada masa haka ba da sauki,kuma duk da haka bai ji haushinta sosai ba amma ai iyaye iyaye ne ko me suke yi,a fusace ya Mike ya shirya tsab ya hada nasa ya nasa ba wanda ke kula wani,da sauri ya ajiye mata Key din room din ya ja akwatinsa karama yayi waje,a nan ta zauna gefen Bed tayi tagumi tana tuna irin maganganun da ta yabawa Ameer gaskiya bata kyauta ba duk irin mutunci da abinda yake musu musamman Ita Meenat ma komai shi yake mata,ta dade a haka amma girman kai yasa tace bai isa na bashi hakuri ba wlh ta Mike ta bar Bedroom din itama da kayanta,Ameer yana jiran Taxi itama haka gasu nan a titi kowa a gefensa kamar ba wanda yasan wani,Meenat sai kallonsa takeyi a ranta tana gaskiya Ameer yana da kyau carkwadi,Ya tsaida Taxi dinsa sai tayi sauri ta rigashi shigewa ciki,ya jawota waje yana fushi ba tare da yace komai ba,ta makale ta rike kujerar mota kam,ya fisgota amma taki jawowa dake hannu daya yasa,Driver na taxi yace Subhanallah Mallam bafa a garin arna muke ba,baka sani ba ko tana da aure kawai kazo kana rike mace kuma baza kayi mata magana ta fita ba sai ka dakumi mace ku fara kokawa,Driver bai gama magana ba yaga Meenat itama tana ta kokawar kwacewa a hannun Ameer ba ruwanta da wannan namiji ne,kokawa suka fara driver yana kunga Innalillahi kai..kai...ku bari mana...ke macece ki kyaleshi,kai malam kaci girma mana ka hakura,ba wanda ya kula me taxi a cikinsu Ameer yasa hannu da karfi yayo waje da Meenat har tana bigewa kadan a kanta,Ta Dafe wajen ta jawo rigar Ameer tace ai na rigaka tsaida me Taxi din zaka raina min hankali ka wani ce kai ka tsayar,yayi yayi ta sake masa riga taki,me taxi yana baiwar Allah ke kuwa kiyi hakuri mana ki sakeshi kina mace,Meenat tace ai wlh sai dai a kasheni,Ameer yace ina zuwa me taxi ya juyo yana kallonta yace sake ni,Meenat sai taji tsoro ta sakeshi taga ba fuskar wasa,amma sai ta kuma fadawa motar da gudu,Ameer ya dakkota kamar jaririya kowa yana kallo yayi tafiya me nisa da ita sannan ya ajiyeta ya dawo motar da sauri ya shiga ya kulle yasa lock,sai ta glass take kallonsa yana kallonta yace Driver muje Airport,Meenat ma da sauri ta tare taxi tace bi bayan waccen motar karka bari su tsere mana,haka suke tafiya suna bayan su Ameer,Sai da Ameer yazo airport abinsa yana fitowa yaga Meenat itama da sauri tace wlh nima sai ka hau dani jirgin ai ta dalilinka nazo garin,bai kulata ba yanda ya siya ticket haka Meenat ma tayi har suka shiga jirgi,Nan ma tace kujerar Ameer ce tata sukayi ta ture ture ana kallonsu,mintuna suka iso Kano suna zuwa Meenat ta shiga Taxi Ameer ya shige motarsa Driver yazo daukansa Direct gida ya wuce,itama Meenat gidana ta taho sabo da tasan bata isa taje wajen Ammah ba me zata mata gwara ma ni Mufeeda na rufa mata asiri,Ameer naga ya shugo a fusace yace Anty na dawo ina yini?Harara na aika masa na hade rai nace yanzu abinda kayi ka kyauta kenan Ameer?am so sorry Anty dan Allah ki bawa Yaya hakuri wlh bazan sake ba,nan Ameer ya dinga bani hakuri Aayan yana jinsa bai San yana gidan ba daya palon,Nace Yana wancen palon kaje ka bashi hakuri,sai dai ki rakani dan Allah Anty,nace muje to mun fara tafiya sai ga Meenat ta shugo ita dama bata San ma za a mata aure ba kawai Hakuri ta fara bani wai na roki Ammah a yafe mata barayi ne suka sace ta da kyar ta gudu daga gidan yan Mafiya,Nace wannan kuma ke ya shafa ke da Ammah kuma ki tafi gidanku nan gidan mijina nane Allah bazan tafi ba cewar Meenat,Ameer nasa a gaba yana rabe rabe muka shiga Aayan dama yana jin komai da muke cewa haka dai kawai Meenat take gani kamar a Tv ana film.

   Ameer ya fara bada hakuri yana kasa da kai,Aayan yace kanka kayiwa Ameer ba ni ba Amarya tuni tayi aurenta sai ka zuba ruwa a kasa ka Sha ka nemi wacce kake so na aura maka,ko Kunya Ameer yace Allah yanzu tayi aure?,ta auri wani?,kai amma Alhmdllh naji dadi dama ina da wacce nake so Yaya,Aayan kawai Murmushi yayi yace jeka ka bawa Abba hakuri,Ameer haka yaje wurin Daddy ma ya bashi hakuri Daddy yace ba damuwa,firgit na farka tsakiyar dare daga Dogon Mafarki na Amma sai bacci ya kwashe ni again.

     Meenat tunda ta dawo naki kulata ko kallonta bana yi,haka ta tafi wurin Aayan shima tace yan Mafiya ne suka saceta,Aayan yace Allah sarki alhmdllh Allah ya auna mana arziki da kika kubuta,Meenat tace wlh kam kai kaga yara manya da tsofaffi,baka Ga wani tsoho ba abin tausayi suka yi masa aski tare da yankashi gunduwa gunduwa,Aayan yace sannu kunga tashin hankali,Meenat tace dan Allah ka bawa sis hakuri fushi takeyi dani kuma ba laifi na bane Ammah fada zata min idan Mufee bata goya min bayana ba,Aayan yace ke da yan Mafiya suka kama ta ya za ayi miki fada.

    9pm na dare na shiga Bedroom din Meenat tana zaune ta zuba tagumi tana tunanin Ammah me zata yi mata,ga Ameer da sukayi fada yaki kulata shine damuwarta,a hankali na bigi hannunta ta gyara zamanta sai kebewa takeyi zatayi kuka,a hankali nace Meenat Ashe baki da tarbiya ban sani ba?Ashe dabba ce ke? Ke inba dakikiya ba mace da kike me daraja da kima amma shine kika biyewa zuciya kika zuga Ameer wai kina mace kece me sace Namiji,Meenat kanki kalau kuwa? Ana tunanin kinfi kowa Sanin duniya Ashe Dabba ce kawai bamu sani ba,kika bi Ameer Har Hotel,Hotel fa Meenat yaushe kikayi wannan wayewar ban sani ba,Sis wlh...yi min shuru makaryaciya abinda kun kira mu da dare jiya ko kin manta ne na tuna miki,tarbiyar da aka bamu kenan?Ina muka san wani Hotel ma?to bari na fada miki wlh wlh kinji na rantse ko Meenat kina da aure,rana daya aka daura miki aure da Ma'eesha Ameer ma ranar aka daura masa,Kinci Amanar mijinki,ga Azabar Allah kuma ki shirya nan da 3days za a kaiki gidan miji shashasha wacce bata San inda kanta yake mata ciwo ba,idan ma kinsan kunyi wani abu gwara ki fada tun wuri idan ya miki ciki ke kika jiyo kuma,Kuka Meenat ta barke da dashi tana wlh bazan yarda ba bana sonsa Allah sai na gudu na bar gari,ficewa nayi na kyaleta nan tana sharbar kukanta,ina fita ta Mike tayi part din Ameer da Daddy tana Kuka,Bedroom din Ameer ta nufa tare da bankawa ciki tace Ameer Ashe an daura min aure nima gaban Ameer ya fadi yace ashe za ayi yaki wlh wlh ba wanda ya isa ki hada shimfida dashi bari mu tabbatar da gaskiya za a kwashi yan kallo,Meenat tana kuka tana kayi wani abu dan Allah an min aure,Harara Ameer ya zuba mata me zan miki ni da nayi gadon Iskanci nake dan Iska kuma tunda Aayan yace matar da aka bani tayi aurenta ma ai shike nan na huta kije ki rungumi mijinki wanda ba gadon Yan Iska ba,ai in ka isa Allah ya tsine min ka gama tabe min jiki kace naje wani wajen mijina gwara ma ka canja tunani ko wlh naje na tona ma asiri wajen Aayan da Ammah,Ameer yace jeki mana ya juya mata baya Meenat haushi ya kamata ta  karasa Jikin mirror na Ameer ta dinga watsi da kayan kai ta gama fashe turarukan tas da komai,bai kulata ba ta samu Bedsheet din da yake kai ta dinga ja iya karfinta,Ameer yana dariya a ransa wannan masifa ta Meenat mutum ya mata ciki ai ya shiga uku a duniya,tashi yayi daga saman Bed ya Mike tsaye,Meenat kamar mahaukaciya ta cire bedsheet din ta jefar dashi ta dage kafiyar dake saman Bed din gaba daya,Wayar Ameer ta fadi kasa ta dauke wayar ta fasata a kasa ta tsage kwatsa kwatsa,Tayi waje da sauri tana kuka tayi wajena Mufeeda ina wajen Aayan ta buga mana kofa na bude tare da Galla mata harara nace lfy? Marar tarbiyya ya akayi? Shuru tayi tana tsiyayar da hawaye dan Allah Sis wlh zan fada miki gaskiya,kizo kiji da kyar nabi bayanta muka zauna a palo nace ina Jinki ina da aikin yi,Meenat ta fara ina...Ina...sis Allah bamuyi Babban Iskanci ba wlh ba abinda ya min,kinga..uhm....kawai Romancing dina yayi wlh kuma ni sace shi nayi mu gudu ina sonsa za ayi masa aure,ai shine dan Iska daya min tunda ai ni ban tayashi ba kuma ni...yi min shuru yanzu Meenat da ba ayi muku aure ba da shike nan ba ruwanki haka zaki sakarwa namiji jikinki,ni duk gwagwarmayar dana sha a duniya ki duba yawon dana yi da neman kudi har gidajen manyan yan siyasa lokacin kun fini sanin duniya ma Amma banyi komai Bad ba ban saida mutuncina ba sai ke,ki duba irin dadewa da zaman da mukayi tare da Ameer gida daya same palo dakinsa kusa da naku Amma duk bakiyi komai ba sai yanzu,mutumin da bai ce yana sonki ba yanzu idan wata yake so ba ke bafa?Idan Allah ya canja masa ra'ayi ya auri wata fa?wannan mutuncinki ne,ai kuma kuna da laifi me yasa baku fada min za ayi min aure ba,mene abin boye boye a fito a fada min mana sai kuyi kunbiya kunbiyarku kawai kuma kuce zaku ga laifina,Ai kun san ba dutse bace ni ku fada min gaskiya mana,ai har waya mun bugo muku me yasa baku ce anyi min aure ba wlh ba ruwana alhaki a kanku,baki na saki ina kallon Meenat nace to ai kinyi ta banzar ke aka Yiwa gata so ake yace yana sonki da kansa shashasha sannan a fada muku shine kika wani dauke Ameer kuka tafi yanzu idan an kaiki me zaki kai masa dakin mijin da zaiyi zumudinki? Meenat tace to ai da saura a abunda mukayi me mukayi ma ai ba aje wajen ba,wa aka yi min aure dashi? Ni yanzu kin fara bani tsoro Meenat Amma Ameer ne dama aka daura muku aure tare,Da Sauri Meenat ta buga tsalle taja gefe tace yanzu dama shine?Amma baku fada mana ba? Kun cuce mu wlh bakin Meenat yaki rufuwa,nace banza saura kije ki Bada kanki da duk kin fimu class Meenat ashe na banza ne dama,Meenat tace ke nifa ba irinki bace Amma dan Allah ku kyale Ameer ku nuna ban san nice matarsa ba ai wlh sai na yi masa rashin mutunci da ya zage ya taba min jiki na, baki na tabe nace banza a banza Man kare bayan shi ya miki 1-0 me zakiyi masa kuma ki godewa Allah mijinki ne gwara ma da aka miki auren ashe, fari Meenat tayi da ido tace wlh gwara da kuka yi min ni halittar mu ba daya bace na fiku lfy kuma ai da laifinku domin haka Ammah ta dinga dura min tsumi ba wanda yace ni Amarya ce,kuna ta min gyare gyare ba dole na kasa tsare kaina ba,ba shi yasa yanzu ake lalacewa da yawa yan mata ma yanzu maganin mata suke sha ki fadi ta inda zan zauna lfy,ai wlh kune ma masu laifi tunda kune kuka ki fada mana yanzu kun bata mana lokaci.

    Mikewa nayi na barta nan ban kulata ba,gani Meenat tayi an nuna mata Aayan ya samu Ameer yace ka shirya babu me kai ma Amarya ka dauki Abarka kuje ku cinye junanku,Ameer kai a kasa yace wacece wai Yaya? Wacce ta saceka kuka tafi Iskanci Hotel Meenat,Ameer da Sauri ya wani rungume Aayan yana ihun murna da godiya,amma baku fada mana ba ai wlh da mun san hakane baza mu dawo daga Honey moon ba kawai Kd zamu koma sai mun gama cin Amarci zamu dawo.Allah ya shiryeka sai kuje ku bawa Ammah hakuri.

      Sai Meenat taga Da wuri Ameer yazo Sabo da Ammah data koma gida bata mata fada ba sai Nasiha tace Laifinsu ne da basu fada Musu ba,kuskurensu ne amma suma sunyi gaggawar daukan mataki basu tsaya munji dalili da wace Amarya ba muka tafi,dama duk me bin shawarar wasu matan to zaiyi nadama karshe Sabo da wasu basa tuna me zaije ya dawo kawai sai su yanke hukunci,da Ameer yazo ma haka Ammah tayi masa nasiha da fada ba ji ba gani Ameer yana hada zufa ina gefe tana rusa Kuka,a cikin dogon Mafarkinta tana ta kuka wiwi tana Bawa Ammah hakuri

     Ammah ce ta tashi Meenat tana bacci sai kuka take wiwi ta hada uban zufa tana fada tace Meenat yaufa ake daura aure wannan wanne Iskanci ne sai ki kwanta tun jiya kike bacci kinki tashi in baki sani ba ki sani Kema Amarya ce yau za a daura miki aure,a firgice ta tashi yanzu duk auren data ga an daura,da zaman Hotel dinsu da Ameer,da fadan da sukayi da kuma auren Ma'eesha gaba daya mafarki ta shiga yi duka gaba daya,dariya tayi data tuna duk a mafarki wai suka kira Mufee a Waya suna making love da Ma'eesha suna first night,kai Mafarki karya ne ashe ko auren ma ba a daura ba bare har ma su hadu da Ameer,Lokacin ma Ameer tuni ya sha wanka Aayan ya rikeshi, Meenat mamakin mafarkinta takeyi yanzu duk wannan dadin da suka ji da Ameer a mafarki ne?Abinda take iya tunawa shine ana gobe daurin aure sun tsara da Ameer zata sace shi kafin daurin aure,ta kwanta bacci da dare kuma ta fara mafarkin harma ta saceshi,sun gudu ga abinda ya faru kuma.
    Da sauri tayi wanka me kwalliya ta shiryata sosai tasha kyau kayanta irin shaddar Ameer fara,Maeesha kuma irin na Yarima light blue,Tana fitowa palo aka saki guda ayyiri yiri ga kawayensu da yawa yan schl sunci kwalliya,gasu Humaira,Auta,Maman Meenat,Seeyah Ibrahim duk a mafarki Meenat ta sace Ameer ga yan biki na gaskiya shi yasa ashe bata ga su Flower ba,Hadiza Mukhatar,Oum Farouq,Maman Khairat,Mum Suhail gasu nan dai Ko ina yan AsmaBaffa fans club,Kasuwancina fans,taskar surayyarms,taskar fiddausi sodangi,House of Hausa Novel,latest Novella,Uwargida gp da Sauran yan gps duk gasu nan kowa yaci wanka ya cakare yana jira yaji daurin Aure,Ameer kuwa Aayan ya ja shi ya sanar masa wa zai aura sai Murna yake,haka Meenat ma Ammah ta fada mata har wata yanga takeyi.
    Ameer tunda yaji Meenat ce yace sai anyi Dinner da yamma lis,Yarima yace ba a Isa ba baya so kamar yanda Ammah tace Amma Ameer yace shi wlh sai sunyi dan ya gayyaci frnds na kusa dana nesa ma, su Khaleel sune a gaba kusa da Ango,haka Yan Mata su Haneefa an tsege a gidan Amare sai hararar su Humaira sukeyi Sabo da shishigi da sukeyi a bikin musamman Flower data sauka da akwati guda,Auta ce me kaiwa da kawowa,Ga Sameeran gaya dasu Jannat ma,Nafi ana ta iyayi,su Hanan sai karairaya akeyi,Zainab atiku salama Sabo da iyayi har gidan kwalliya itama taje kamar Amarya,Suby sai turanci akeyi ba a Hausa, kida ke tashi Dj a tsakar gida su Aliyu da Sabeer ne suka kawo Dj suka ce ayi ta sakin kida har sai an gama biki An kai Amarya sai zagawa suke suna kallon yan mata,Maeesha ce Yarima ya kirata Princess yanzu za a daura fa muna masallaci,Maeesha anji kunya tace to kawai ta kashe wayar jiki a mace,sai ko aka ji Masu speaker sunce An daura Auren Ameer Mustapha tare da Amina Abubakar Saddiq akan Sadaki Naira dubu Dari da Hamsim sabanin na mafarkin Meenat dubu dari kuma wai Aayan ne ya biya wannan kuwa Ameer ya biya da kansa,Akace again An daura Auren Ma'eesha da Usman  Yarima akan Sadaki dubu dari da Hamsim shima,mata sai guda da shewa Meenat bata murna tunda Ameer ba soyayya sukeyi dashi ba,amma da ace wani aka bata ai gwara Ameer din, ana kida maroka na rokonsu angwaye da abokai suka shigo gidan Amare Aayan yana cikin abokai Barin Yarima,Yanda naci uban kyau da kwalliya ka rantse nima Amarya ce nasha Material color din yard din Aayan,Aayan fadar kyansa bata lokaci ne kawai ya haska ko ina,sun gaishe da Dangin Ammah tare da Amma da Dangin Abbanmu shima,ashe ba a mafarki Abba ya Aiko da sakonsa ba kafin a harbeshi Amma sai Meenat ta ganshi a Marfaki ashe ma kar da kar bakin Abba suka zo Meenat da Ma'eesha suna wajen Amma sai tayi Mafarki har Ma'eesha sai waya aka buga mata tana Kukan first night gaskiya mafarki shirme ne amma dana fitsari tayi sai taga ta tsula fitsarin,Sai yanzu komai yake dawo mata abinda ma ya faru tana wajen sai ta kara mafarkin abun..tana wannan tunani Yarima yaja Amaryarsa suka fita da frnds suna kashe pics,Sai ga Ameer ya shigo yana zuba kamshi kamar a sace shi bakinsa baya rufuwa banyi zaton zaiji dadi ba,Kusa da ita ya zauna Humaira ta mike ta bashi wuri sai aka rufesu da wayoyi ana pics Ammah tace ku fita waje can ta koresu ni kuma na daure Fuska gaba daya da kyar nake dariyar yake kawai mafarkinta take tunawa na daren jiya,mamakinta tana wajenfa Nawwara ta kawo bakin da suka kawo sakon Abbanmu har Ammah ta karasa mana labarin komai Amma sai ta sake Mafarki hakan ta faru Amma babu ita a wajen Ma'eesha ma buga mata waya akayi,a takaice dai duk mafarkinta nata  akan bikinsu ne ya tsaya mata a rai shi yasa ta kwana mafarkai iri iri film guda Allah ya kyauta,inda ya bata dariya fadansu da Ameer a Taxi da jirgi ana basu hakuri a fili na fara murmushi ana pics Ameer sai kallonta yakeyi cike da so yace lfy? A kunyace tace wlh jiya kwana nayi ina wani Mafarki me ban haushi da abin dariya,amma gwara da Allah yasa ba da gaske bane hakan ta faru da na shiga Uku,kaga yanda har Sis Mufee nayiwa rashin kunya fa,wai naje room dinka na farfasa maka turaruka na cire bedsheet tare da dage katifar ina kuka,Dariya Ameer yayi yace lallai kinsha aiki to ni kuma me nakeyi?Meenat tace dariya ma kake min na zama mahaukaciya,kasan maganar da mukayi jiya nace zan sace ka a mafarki wai har na saceka mun gudu Kd,Ameer yayi dariya yace wa zai yarda da wannan shawarar taki sai kace wani yaro ni kuma sai na tsaya sototo ki saceni ashe kece ma Namiji,Nace a Kd har fa kuka kayi min wai na saceka ina gana ma azaba,dariya Ameer ya dinga yi yace kawai dan daudu na koma ashe taya zan miki kuka Meenat abinma baiyi making sense ba,ai dana tafi na kwanta na huta tuni nayi watsi da shawararki,kin san idan Munje wani waje wani abun ya faru tunda mu lokacin bamu san mune mata da mijin ba to duk abinda muka aikata Haramun ne tunda ni nasan ke ba Matata bace kema kin san baki da aure har sai an sanar damu mun sani,haba Meenat taya zan biyewa shawararki nifa ba mace bane ina da tunani me zurfi,matukar muka kebe tare to dole sai nayi Sex Allah ya gani Bazan iya kyaleki ba wlh ko me zakiyi sai nayi,Kunya ce ta rufe Meenat tace abar zancen dan Allah,Khaleel ne ya janye Ameer bayan sun gama pics suka tafi gidan da suka sauki baki maza frnds su Meenat ma suka koma cikin frnds ana ciye ciye ana cashewa.

   Ameer kamar ba Ango ba haka ya dinga taka rawa su Aayan da frnds suna ta dariya su Sabeer dasu Haneefa ba irin rawar da basuyi ba,Maeesha ma Amarya sai Jinta akayi a filin rawa can Compound suna taka rawa da frnds dinta harda Ameer,Meenat kuwa duk ta damu kanta har ta fara ciwon kai sai Bedroom din Ammah ta koma ta kwanta tana ta bacci.
    Ameer ne yake matukar fushi da ita  akan taki yarda dashi ya kwashi gara,da kyar ta dan yarda tace zo kayi to Babyna a nutse ya rungumeta ya shiga kissing dinta so deeply nan take suka rude sai mirzar juna sukeyi ba tare da kaya a jikinsu ba,nishi kawai suke da Kukan dadi,Ni Mufeeda ce na fara buga musu kofa su bude su fito Sabo da za a kai Amarya Amma Ango ya riketa suna Holewa a Bedroom din Ammah,ango ya fara neman hanyarsa Meenat sai nishi takeyi nazo tana bacci na daka mata uban duka firgigit ta tashi daga baccin da takeyi tana mafarki suna Making love da Ameer,idonta cike da bacci ta tashi nace ke wai wacce banza ce? Kin zauna sai nishi da kuka kike ma mutane yamma tayi kizo kiyi sallah kin san anjima za ayi Dinner kuma yau za a kaiku gidan miji,Kaina na dafe ina mamakin jarabar mafarkin da nakeyi akan Ameer kullum kuma sai na Sharholiya,tashi kiyi sallah na kara fada mata,wlh Sis Period nakeyi yau yazo da Safe,Amarya kice Ango yaga ta kansa yau,wai ke Sis mene haka dan Allah ni bana so wlh sai kace ni yar Iska ce, kazar hadi tasha tsumi na kawowa Meenat tare da Maltina nace ta cinye du,haka na kaiwa Ma'eesha Tata Amma taki ci a waya na kira Aayan nace ya bawa Yarima waya Aayan ya mika masa nace Yarima kazo ka bata abinci taki ci rabonta da abinci tun jiya,haka kuma ta dinga rawa ba komai a cikinta dan Allah kazo,Ma'eesha ta fashe da kuka Sis wlh bana son auren nan ni Bazan iya kula da namiji ba,t ausayi ta bani tabbas Ma'eesha tayi yarinta da yawa kuma miji kamar Yarima sai gwarzuwa jajirtacciya,dalla rufe min baki kin gama rawarki zaki fara Yiwa mutane kuka,Kowa haka akayi masa ashe ni jaruma ce gaskiya yanda baku sani bama nayi aure ba kuka ba komai,Kuka Ma'eesha takeyi wiwi kamar zata mutu har lallashinta na fara Amma taki hakura ba yanda banyi ba,waya na kira Aayan nace pls kacewa Yarima yayi sauri,15mnt sai ga Yarima yazo na jata can palon da ba kowa nace lallasar min ita Ango taki yin shuru,Yarima yayi murmushi yace jeki nasan kayata yanzu zata dawo normal,ga abincin ka bata ta cinye, na koma wajen Meenat sai na tarar itama tayi tagumi tana Kuka nace wai ya kuke so nayi Ammah tana fama da Jama'a ni nake kula da frnds dinku da ku yanzu ga Aayan kin san Nemana yake fa dole sai naje Guess house dinmu naji me yake so,Mene ne? Just tell me ke kuma me yake damunki? Sister nifa ba soyayya muke ba taya zan Sa Ameer ya so ni? Meenat wahala...har sai na koya miki idan abu ya wuce miki duhu ki kirani a waya ko Ammah,Wayar Aayan ce ta shigo na daga yace Dan Allah ga Mujaheed nan yazo zai kawoki wajena daya gidan nawa,wai me zanyi ma? Kin san nifa bacci nake so nayi kafin aje Dinner kizo ki tayani bacci,yau daya dan Allah ka hakura kayi kai daya,kin san sharadina Baby kawai kizo bana bacci kin sani sai da abu a bakina,Nasan me yake nufi kamar yaro jariri shi baccinsa sai da Boobs a bakinsa,banyi musu ba nacewa Ammah zanje na karbo wasu dinkuna,tace ki dawo da wuri Mufeeda nace to,da Sauri na shiga motar Mujaheed ya kaini gidan ya tafi,Har yayi shirin bacci kayana kawai na cire Aayan ya daura ni saman Bed ba abinda Yamin sai kirjina da yake sha yana murzawa har bacci ya kwashe mu.

    8:30pm akayi shirin zuwa hadaddiyar Dinner wacce ba kara min kayatuwa wajen yayi ba,Ansha wanka anyi kyau,Amare sun hadu,Ni da Aayan kuwa ba a magana irin kyan da mukayi,wajen ya cika anyi watsi da kudi,anci an sha anyi rawa an girgije,ana gamawa dole sai washe gari za a kai Amare,washe gari ma sabon shagalin Dj aka sha wurin Magriba motocin kai Amare suka jere dama unguwa daya layi daya gidan Ameer da Yarima suke kawai sai aka tafi da Amare gaba daya aka kaisu gidan Mazajensu, gida na gani na fada yasha kayan alatu da birgewa fadar tsarin gidanma bata baki ne Aayan ne ya zuba Musu Furniture yan kasar waje,harka iya harka mun kaisu tare da garar su wanda nice da kudina nayi kayan gara.
   na koma wajen Ammah tace Mufeeda Maza tashi kema ki tafi gidan mijinki Dangina dana Babanku zasu tsaya mu gyara komai.






AsmaBaffa
[2/19, 11:06 AM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

    KASUWANCI NA




          126-130





Official






By
AsmaBaffa








           


      Ammah ta damu lallai sai na koma gida yau da daren nan amma na dage sai na tsaya na gyara mata Bedroom da sauran abubuwanta shi yasa ma dole ta hakura ta kyaleni haka na kwana zuwa gobe sai na tafi, mun danyi abinda za muyi na kwanta baccin gajiya ya kwashe ni a bedroom din su Meenat,Driver din Aayan ne yazo daukana Inna tace ai tace baza ta koma ba sai gobe tayi bacci ma,Driver ya kira Aayan a waya tare da Sanar masa,Aayan ya kira wayata amma na kasheta ma baki daya sabo da nasan zai Dameni sai na koma gida,Driver yayiwa Magana cewar ya dawo gida kawai shi zai zo da kansa ya dakkoni,Almost 10pm Aayan ya iso gidan da kansa daga shi sai armless da 3qrt,har ciki ya shiga da Sallama yana jin kunyar Ammah da danginta amma ba yanda zaiyi haka suna hira Sama sama wasu ma sunyi bacci wasu suna gyangyadi ya shiga palon yana kasa kasa da kai,Ammah tasan me ya kawoshi  dama haka ta guda shi yasa tace na koma amma naki ji,da fara'a ya Gaishesu cikin ladabi da biyayya kafin yayi magana Ammah tace tana dakin can shiga ciki,Kunya ta lullubeshi amma ya maze yace to ya wuce sum sum,ina cikin bacci naji kamar ana shafa min kunne.

    Sosa wurin nayi ina baccina ya sunkuya a hankali ya shiga kissing dina da sauri na kara turo masa lips ban san me yake ba,Hanci na yaja kadan a hankali na bude ido na jajir dashi sabo da baccin dake cikinsa,mika nayi me Jan hankali gashin kaina ya Barbaza wani ma ya rufe min rabin fuska,a hankali ya sa Hannu yana gyara min gashina yana maidashi baya,wuyana ya shiga shafawa sannan yace sannu Sweet wife kin gaji ko?a hankali tare da shagwaba gami da kisisina na daga kai sama kadan sai kuma na koma jikinsa na lafe ina niyyar ci gaba da bacci na,tashi mu tafi gida,Yau kadai baza ka iya hakura ba My Man? Na furta kamar yar maye ina kara makalewa a jikinsa,na so na barki amma bazan iya ba kinsan ba wani abu zan miki ba kawai bazan iya bacci bakya kusa bane kin San Karatun ba sai na kara biya miki ba,just Silently tashi mu wuce,ga gida ga gida amma kice zaki kwana,Shagwaba na ajiye masa..haba My Man bikin nan na 2sisters dina fa baka barni na kwana ko daya bafa sannan kuma kullum da rana ma sai na tayaka bacci har an gama biki yanzu daka barni ai da sai na huta zuwa gobe amma yanzu ko munje gidan ma baza ka bari muyi baccin ba.
    ae naji kawai tashi mu wuce ni bazan iya ba, mayafi na ya hango cikin kayan su Meenat da yawa da suke gefen Bed za a kai musu gobe yace laa ga Mayafinki ma ya zaro shi tare da mika min na karba,yana karewa dakin kallo yace wannan kayan kika sa da safe ga wanda kika sa da yamma ma bari na hadasu mu tafi,da mamaki nace ya akayi ka sani?hmm kamar bani na siyi kayan da hannuna ba kuma ni dinki ma indai nakine ina gane shape dinki ne,bare kin manta kin tura min pics din ta WhatsApp, sauran kuma da kika sa duk ba bawa me wankin ki ta wanke wannan ne kawai na yau ba a wanke ba,wancan ma har na shirya miki su a Wardrobe dazu,ina kallo ya hada kayan kaf da kansa ya zuba a jakata takalmi na ya dauko ya sauka tare da tsugunuwa a kasa kamar me neman gafara ina zaune a gefen gado ya saka min takalma da kansa jakar da Mayafi suna hannunsa ya mikar dani tsaye tare da cewa let's go,ina turo baki Nace ka goyani to kaji,no su Ammah suna Palo akwai kunya,doka kafafu na farayi ina kukan shagwaba na bude kofar na fita yana Bina a baya,munci Sa'a ba kowa a palon yanzu duk sun tafi Bedroom sai kawai na zura hannuna ta cikinsa nasa tare da kwanciya a jikinsa,kansa ya juyo a hankali tare da zuba min kyawawan idonsa masu tafiya da Imanin mace sannan yayi murmushi nima Murmushin nayi muka fita zuwa Compound wurin motar ya bude baya ya zuba kayan,ya bude min na shiga ya rufe sannan ya zaka ya shiga shima muka bar gida sai waya na kira Ammah nace mun tafi gida gobe zan dawo Addua ta zuba mana sannan na kashe wayar.
     Hannu Aayan ya miko min a motar na sa hannuna cikin nasa ya shiga murzawa nima ina murza nasa shidewa yayi ya dan kalleni idonsa har ya canja launi sabo da rabonmu da juna tun kafin bikin su Meenat ko mun hadu ma a gajiye muke babu nutsuwa a tare damu bare muyi wani abu ni kaina nasan nayi missing din mijina.
    Sakon Kallo muke aikawa juna a hankali nace I love u,Murmushi me Sauti yayi sannan ya maida hankalinsa wajen Driving dinsa daga bisani ya juyo yace Mene yafi love a soyayya? Nace Kauna ce I think yace to ita nake miki ni kinga na fiki,Allah ban yarda ba sai dai na fi sonka da kaunarka,Hmm haka kike cewa amma ni nasan na fi Sonki ni da nakeji kamar na maida ke cikina,nima nace to ai ni so nake na cinyeka na lashe ka kaga ai na fika,dariya ya shigayi cikin sigar wasa da tsokana yace kurwata Kur tafi karfinki Ki cinyeni ki lasheni a kaina zaki gwada maitarki? Dariya nima na fara yi baccin nawa ma ya gudu gaba daya muna hirarmu har muka isa gida.

    Ango Yarima bayan an kai masa Amarya an watse ba kowa a gidan sai Ma'eesha Amarya dake sheshekar kuka kamar zata kashe kanta tana ta kiran Ammah da Mufeeda,Haka Yarima ya shigo ya isketa da sauri ya karasa Bedroom din tare da ajiye ledar da ya shigo da ita,saman Bed din ya zauna a hankali tare da Zare mata Mayafin da ta dukunkune kanta a ciki tana kuka,Lallashi ya fara Princess kiyi hakuri ki daina kukan ya isa haka ya rungumeta a jikinsa kamshin turarensa da Laushin fatar Yarima yasa Ma'eesha bata San ma sanda tayi shuru ba, a hankali ya rada mata Ya isa haka kukan Ba dai akan Ammah da Mufee bane?a hankali tace ae tana ajiyar zuciya yace to gobe ma zan kaiki wajensu can zaki yini idan ma naga dama na barki ki kwana kullum sai na kaiki can,Maeesha ta yarda tace da gaske?yace sosai ma,idan ma kuka zaki dinga yi sai na koma gidan Aayan tare da ke ya bamu part guda muyi zamanmu kusa da Mufeeda ko?sai ga Ma'eesha tana dariyar Jin dadi ita  da gaske ta dauki zancen,Yace amma da sharadi sai in baza ki kara yin kuka ba amma idan kika kara kuka ko Hawaye ne to na fasa,da sauri tace bazan kara ba na daina,kiss ya Manna mata a goshi da saman hancinta sai lips dinta,muje na baki abinci sai muyi wanka da Sallah muyi bacci bazan iya jira ba bacci ne sosai a ido na,jin yace bacci ne a idonsa Ma'eesha sai ta kara sakin jiki ba abinda zai mata ai bacci kawai zasuyi abinsu,nan ta saki ranta fess yana bata kaji tana dan tayashi hirar sama sama suna dariya cike da shauki Masoya burinsu ya cika anyi aure,Yarima yana kallonta yace ji nake kamar bani ba princess am so so Happy Alhmdllh da Allah ya mallaka min ke,Ma'eesha wani sanyin dadi take ji tace hmm ai na fika My Heart Ashe haka ake ji idan an daurawa mutum aure Ashe gaskiya ne da ake cewa an daura wa mutum igiya,kaji ana ma Nasiha to fa Girma da Nauyi ya hau kanki sai hakuri,Ammah tace Ma'eesha Nauyi ya hau kanki sai hakuri ai ko ana cewa an daura Aure sai naji kaina yayi wani Nauyi gingirigim nace laa ashe kuwa haka ake ji wlh Nauyi ya hau kan mutum,Wata dariya da Yarima yayi wacce bai taba yin irin ta a duniya ba sai yau sabo da Ma'eesha ta bashi dariya Kuruciya bata gane me ake nufi ba da ake cewa Nauyi ya hau mutum ita da gaske jin nauyin akeyi a ka,amma bayan ya gama dariyarsa itama tana dan tayashi kadan yace ashe kema kinji kamar ni? Ai kin bani dariya ne da kika ce gingirigim,Ma'eesha tace kai dai bari Angona naji wani dimmm duf Wutar kaina ta dauke gaba daya shi yasa ai kawai nayi ta kuka to ni naji duniya tamin Zafi kaina yayi nauyi sai da kazo ka lallasheni,shedan ne kawai yafi tasiri a wajen mata shi yasa kuke jin bacin rai in an daura cewar Yarima,Aiko aiki yaganshi dan baza a warware ba tun ranar fa nace wa Ammah na fasa auren tace ai shike nan ba a warware wa bare wani shedan yasa a warware shi da ba saninsa akayi ba nima ba aji maganata ba sai tasa wa yake ganinsa can ta matse masa.
    Shi dai Ameer dariyar ta isheshi har tayi yawa ma kuwa lallai zai sha kuruciya Raino kawai zaiyi duk ba ma wannan ba tunaninsa yanda zai Kusanci Ma'eesha tayi yarinta da yawa duk da cewar tana da girman jiki da tsayinta itama ba ramammiya ba bame kiba ba duk haka muke amma Age din Ma'eesha sunyi karanci a kusanceta just 16yrs amma haka zai gwada ya za ayi yasan dai zai sha jinya kawai shi yasa ma ya fadawa Ummansa tunda Doctor ce ta bashi magunguna dasu ka kamata tace idan kuma yaga da matsala kawai ya kirata da wuri tazo gidan again gaggawa.

   Bayan sun gama cin abincin wanka Ma'eesha tayi tare da Brush shima Yarima ya shiga kafin ya fito ta shirya ta gyara wajen ta kai komai kitchen tana dawowa ta kara fesa Roomfreshner ta shimfida musu Sallaya tasa Hijab tana jiransa ya fito,yana fitowa shima ya shafa lotion ya shirya sosai yasa jallabiya tare da jansu Sallah raka'a biyu sukayi addua sosai ya mike ya dakko mata wata yar matsiyaciyar rigar bacci ba kowacce zata iya sawa ba a ranar da aka kaita gidan miji ba sabo da zata ji kunya da yawa,Amma ba wasa ya mika mata yace sauri kisa muyi bacci ina so bacci ya isheni yau,Maeesha ta duba rigar tace amma wannan zan Sa? tana kwabe fuska da shagwaba,lallashinta yayi da kyar ta shiga toilet ta sa haka ta fito sabo da yace Allah zai tsine mata idan taki yin abinda yake so,tana fitowa sai kare jikinta takeyi sabo da yanda yake kallonta abin ya bata tsoro,hannunta ya rike duka biyun yana kallon kirjinta sosai a hankali ta zame kasa ta dunkule waje daya tana murmushi cike da tsoro,Light ya kashe cike da zumudi jiki na rawa ya dauketa sai bisa Bed shima ya haura duk wayon da yake tunanin hada mata ganin surar ta me kyau yasa ya mance da komai ya rude ya gama zaucewa, ita kuwa har ta fara Kuka a hankali ya rada mata My Princess ba abinda zan miki kawai Romancing pls,ni dai ban yarda ba tsoro nake ji,kyaleta yayi kawai ya shiga Murzata cikin Kwarewa da wayewa sai ko ta manta da wani tsoro ma tana dan Jin dadinta Har Allah yasa tace ta yarda yayi, tunda ya shigeta take tsala kuka tana surutai na wahala sai Mufeeda take kira amma ina baya jin kira kalamai masu Zafi yake rada mata ya Haukace kawai sai da ya dan jima sannan ya samu nutsuwa,Maeesha Kuka take da taga Jini yaji mata rauni kenan a fili tace ni dai bazan yafe ba gashi nan jini na zai kare wa ya sani ma ko jijiyata ce tsinke tana shesheka dan mungunta kaji min ciwo a wajen nan duk tsaronsa da nakeyi murmushi yakeyi na jin dadi da nishadi ga wani sonta da yake kara shigarsa,mugani ciwon idan da yawa sai na kira Ummata,tana kuka tace me ka sani da zaka gane ciwo yayi yawa ko baiyi ba da kyar ya lallabata suka yi wanka ya gasa mata jiki sosai,nan ma ansha kuka da tabara kafin ta bari ya shirya ta suka koma baccinsu.

    Ameer Ango bai shiga gidan ba sai 10pm su Khaleel suka rako shi yace to ba sai sun shiga ba su koma suka ce sai sun shiga amma Ameer yace basu isa ba Sam dole suka hakura suna tsokanarsa suka tafi gida.
    Yana shiga cikin hadadden palonsu bai samu Meenat ba sai a Bedroom dinta tana zaune ba ko mayafi tayi tagumi gaba daya tsoro ya kamata,Sallama yayi mata tare da tsayawa a jikin kofar ya harde hannaye yana kallonta yanda tayi kyau tana walwali ta ko ina, zuciyarsa ce ta shiga bugawa cike da jin dadi Meenat ta Zama mallakinsa a ransa yace Alhmdllh Alhmdllh,Karasawa yayi dauke da Sallama a bakinsa,a hankali Meenat ta dago ta kalleshi a ranta taji sanyi sabo da dama tsoro take ji,ga wani uban kyau da yasha cikin wani yard hadadde milk dinkin yan gayu,alama ya gani tsoro take ji an barta ita kadai a gida, cikin muryarsa me dadin ji yace Tsoro kike ji ne? Kai kawai ta daga masa sannan ta tace kaina ke ciwo kuma Ya Ameer,Eyya sannu ya kai hannu zai taba wuyanta tayi sauri taja baya wai bazai taba mata jiki ba,mene kika wani ja baya zama kisa wlh nace sai na nayi tabe tabe,Meenat ta cuno baki gaba tare da kara boye jikinta wai kar ya taba ta ai kuwa Ameer ya haura saman Bed din yana cewa naga kin rainani bari nayi maganinki,hakuri Meenat ta fara bashi yace to bude wuyan na taba naji,da Sauri ta cire hannunta ya taba yaji jikinta da zafi alamar zazzabi ne,tashi kije kiyi wanka kici abinci sai kisha magani ki kwanta ya furta zai bar dakin yace Good night ina zaka je ni ban saba kwana ni kadai bafa tsoro nake ji kasan tunda muka taso bama kwanciya mu kadai ka zauna pls,ae jeki yi wankan nima wanka zanyi first zan dawo yanzu kiyi alwala,to kawai tace har ya bar dakin ita kuma ta shiga Toilet tayi wanka tare da Alwala ta zauna duk da jikinta ba dadi haka ta shirya sosai tare da shafa turarukanta lungu da sako, rigar Bacci ta dauka Gown yar karama marar nauyi pink color tasa tayi kyau matuka skert tasa a saman kayanta tare da Hijab sai ga Ameer ya shigo cikin jallabiya Brown ya jasu sallah Raka biyu tare da adduoi na sunna,kaji da Hanta masu ruwa ruwa tare da kayan sha ya bude musu yayi yayi taci taki haka ya jawota jikinsa tana so ta kwace yace Bana son jayayya fa kawai ki karba dole ya dinga bata a baki ta danci ba da yawa ba sai Fresh milk tare da Fruits paracetamol ya bata ta Sha sannan ya kaita Toilet sukayi Brush ta kwanta a saman Bed,shi kuma ya cire Boxers dinsa kenan Meenat tace ni Allah a'a ni baza ka kwanta min a bed a haka ba,kalleka ba riga sai guntun wando kallo yabi Meenat dashi sannan yace kin rainani da yawa amma zanyi maganinki,Meenat wai dan kar ma yace tana sonsa shine take masa hakan,kawai taga ya juya ya fice abinsa,ga Meenat ana tsoron kwanciya ita daya amma dan kar ta zubar da ajinta tayi kwanciyarta haka a tsorace dama shi Ameer tausaya mata yayi amma da badan haka ba yasan Meenat yar rainin hankali ce sai ya dauki mataki a kanta wanda baza ta rainashi ba dole ta dinga Respecting nasa idan ya tsaya to yana gani zata fi karfinsa.
  
      Meenat tsoro bacci ya hanata da ta sani bata kori Ameer ba,1:30am ta fito daga dakinta ta shiga neman na Ameer har ta je jikin kofarsa da take tunanin dakinsa ne tayi knocking da karfi da kyar ya bude idonsa yasan itace amma ya share Sunansa ta shiga kira Ya Ameer ...ya Ameer amma yayi banza da ita,da kyar ya Mike tare da bude mata kofar yana tambaya lfy cikin dakin zata shige yasa jikinsa ya datse mata hanya,tabi ta daya barin nan ma yasa kafa ya tokare hanyar yace lfy wai?Tsoro nake ji Allah dan Allah muje Bedroom dina ko ka barni na kwana a nan ko a kasa ne, Bata rai yayi sosai ba wasa yace ni bana iya kwana da mutum a daki daya dama naje taimaka miki zaki min iyayi ba sai ki kwana ke daya ba,to kayi hakuri bazan kara ba,Matukar zaki nemi rainani wlh baza muyi shiri ba,ban son raini a rayuwata kin sanni tun tuni muyi respecting din juna is better, kai ta daga da to sannan yace shiga ki kwanta,dama shi Ameer haka yake da son a girmamashi bai son ya raina wani shima kuma baya daukan raini yaga Meenat dole sai ya gyara mata Zama,tana shiga tace Ya Ameer Zanyi Fitsari,da kyar ya amsa mata yayi kwanciyarsa tare da kashe Light,tana fitowa daga Toilet tace Ya Ameer a ina zan kwanta to? Yace inda kika ga dama,cike da shagwaba tace to ka matsa min mana,Shareta yayi kawai ta hau Saman Bed din amma tsokanar Meenat yasa ta fara tura Ameer gefe ta kasa dole ta haura ta samansa ta koma ta gabansa ta kwanta sabo da yafi fili,tana zuwa data kwanta sai kawai ta jibga masa kafarta daya a cikinsa tana dariya a ranta,Ameer shi wai kar a rainashi baiyi magana ba ta kara dora hannunta wuyansa da karfi wai bacci takeyi,Ameer ya dauke kafarta ya jefar saman Bed,Hannunta ya cire a jikinsa tana cirewa ta kama dariya a fili yana jinta shima boye dariyarsa yakeyi yanda yake so ya share amma ya kasa sai boye fuskarsa yayi a saman Pillow,Meenat ta sa hannayenta biyu tare da dago da kansa ta karfi tana dariya kuma wai sai ta sa Masa yatsanta na tsakiya a bakinsa Ameer kamar ya samu Lollypop ya fara tsotsarsa Meenat har jikinta ya fara canjawa ya cijeta da sauri ta zare hannun tana kukan shagwaba,ta danyi shuru sai taga tuni Ameer bacci har ya kwashe shi ba wahala light ta kunna ta sunkuya a samansa tana karewa fuskarsa kallo yana baccinsa cikin nutsuwa,jijjigashi tayi da karfi wai bazaiyi bacci ba ita bata yi ba,da sauri ya bude idonsa tace ni ka tashi,idonsa ya lumshe Meenat ta ja masa gashin ido ni ka tashi,cikin mayen bacci yace Meenat zan miki abinda zaki raina kanki gwara ki lallaba muyi bacci Meenat jin haka yasa tayi shuru har yaja bargo ya rufe kansa Shi kadai amma Meenat ta yaye masa Bargo ya rike ta rike ya ja ta ja itama ya fisge ya rufa musu gaba daya shi Ameer baya so Meenat ta raina shi ne kawai,shi yasa yake sharewa bayan haka ma yaga tana masa kallon ko iya jikinta yake so shi yasa ya danne zuciyarsa kawai ya kwanta amma Meenat ba ruwanta tsokanarsa takeyi kawai wanda nan take Ameer ya fara canjawa jarabarsa ta fara motsawa yanaa dannewa ne kawai,gaba daya yanzu ma baccin yaki zuwa masa sai juyi yakeyi lokacin kuma Meenat ma bata yi bacci ba,ganinsa ba love suke ba me zaisa ya nemi wani abu a wajenta ta rainashi ma kawai sai ya tuno da iskancin karyarsa da yakeyi yace ciwon Sha'awarsa ne ya motsa.

    Murkususu ya fara yana rike mara yaje jikin Kunnen Meenat yana juyi da sauri ta dawo daga dogon tunaninta da takeyi ta rude tana lfy ya Ameer kamar zatayi kuka,yace ciwon ne ya tashi,me ya dace nayi maka wayyo ni Meenat na shiga uku bari na kira Ya Aayan,da sauri yace no..no ki Bari zanji sauki ma idan kuma lokacina yayi na rasu shike nan,Zaro ido tayi taji ance lokacin rasuwa hannunta ta daura saman kansa taji normal ba Zafi ta cire hannunsa da ya rike Marar tana nan ne?ta fara murza masa a hankali,Ameer yayi ajiyar zuciya tare da shidewa yana fitar da wani numfashi,Meenat ta rude tunaninta ciwone yayi tsanani sai ta fashe da kuka ta koma tare da manne bakinsu waje daya wai ya daina shidewa,Ameer sabo da abinda yaji a jikinsa bai San sanda yace wash Dadi ba ya kara Manne Meenat a jikinsa,ciik Meenat ta tsaya ta gano gaskiya Ashe wayo ya hada mata amma ta kasa tashi a jikinsa yanda taji laushi da kamshin Ameer jikinta ya Zama weak sai ma itama tace nima ta Anty Mufee zanyi kawai nayi masa wayo nima sis Mufee Method,sai tayi luf tana shafa masa kirji a hankali tace kaji sauki Sannu,Wayyo bana son ka Mutu Ameer dina,u r my Best frnd duk da ba soyayya muke ba ai ina ji da kai dan Allah karka Mutu ta kara kankame Ameer tana shafa masa gashi,tace da sauki? Ameer a nan ya gano Meenat muguwar Makira ce sabo da yasan ta gane shi Amma tana raina masa hankali kuma bai gano cewar dadi take so taji ba tayi masa tunaninsa raina masa hankali takeyi,Sai shima a ransa yace lallai dole na nade borin kunya ta da hauka kar ta gano naga yar rainin wayo ce,Sai ya birkice kawai yace Bakina baya gajiya da Kuka matukar ba ki rufeshi ba irin dazu,Meenat a ranta tace dama ta samu ko ba komai nima sai na gwada yanda nake gani a film din turawa ko zan iya,Sai tace a fili sannu kaji tana shafa masa Mara a hankali Ameer ya fita daga hayyacinsa tace ni ka daina Kukan nan Ajiyar zuciyar ta isa haka ta furta tana hade bakinta da nasa Ameer bai ma san ya fara tsotse Lips din Meenat ba itama haka.

    Hajja ce zaune ta zuba uban tagumi Halayen matan da su Abbi suka auro ya ishe ta,kowacce ta tashi rashin Mutuncinta sai ta taso ta zazzagewa Hajja shi,Matar Abbi Sani ma har bangaje Hajja takeyi,gasu da asiri kowacce a cikinsu su uku Asiri ne aikinsu sun gama mallake su Abbi sai abinda suka ce,haka Hajja ma suna gani matansa suna wulakantata amma basa cewa komai,Yaran gidan kuma kowa harkar gabansa yake suna Jin haushi anki dawo da Iyayensu mata shi yasa suka ce Amare su kashe su baki daya ba ruwansu,matar Abbi Mustapha ko ina bata barinsa yaje kullum tana wajensa bata iya hakura ita ko yaushe sai ya mata Sex ba adadi shi kuma Abbi ba haka yake ba Sam yayi kokari sau biyu a rana amma ita kawai ba adadi nan Abbi ya fara ramewa kullum sai tumburewa yakeyi kamar me cuta sai dan ciki, ta Abbi Sani kuwa duk neman matan nan ya daina shi yanzu taci kwalarsa ta zare masa ido a daki magana idan tayi masa haka jikinsa yake mazari sai yanda tace. ta Abbin Yara kuwa aiki kawai take sashi har gyaran Bed da wanki etc,Hajja duk son yaranta sai dai ta shiga daki tayi kuka taci kuka ta godewa Allah sabo da tana magana zasu mata kaca kaca bata da yanci kullum idonta Hawaye basa tsayawa,ba wani kudi take samu ba bare taje gidan Malamai itama baya ga haka ma taga malaman gaba daya karyar banza ce abun baya dorewa yake karyewa sai dai ka kare a neman Malamai ba ci gaba,Daddy kuma tunda ya gano hakan ya daina zuwa ko gaida Hajja ya fadawa Ameer da Aayan lallai karsu sake su je gidan su kyalesu tunda ana basu ci sha da sutura,Khaleel ma suna matukar yiwa Daddy biyayya ya kara basu shawara kar su sa musu baki su kyalesu kawai su dandana ko zasu gane gaskiya.
   Hajja babu me kulata bare aji matsalarta tana zaune a Palo ita daya Matar Abbi Sani ta fito ta kira sunan Hajja na Yanka Khadija Kin Haifo jarabar duniya kin Haifo Bala'i taja tsaki ta koma Bedroom,Hajja tana goge Hawaye na bakin ciki Matar Abbin Ameer ma ta kawo mata tuwon shinkafa miyar taushe tana sani sai ta ajiye saitin kafar Hajja tare da tura kwanon miyar ya zube a kafar Hajja gashi da zafi sosai Hajja ta Mike a zabure zata arce ba karfi tsufa ya kamata sai ta gice ta fadi kasa nan take Kafarta ta karye Baras sannan ta fada saman tuwo da miyar ya kone mata Mazaunai sai Kuka da Neman agaji,duk yaran gidan basa nan cikin matan su Abbi dasu Abbin ba wanda ya leko Hajja su Abbi suna ji suna gani kuma suna son uwarsu Amma matan sun hanasu fitowa haka Hajja ta kangare a kasa tana Kuka,Abbin Yara yafi tausayi sai Kuka yakeyi uwarsu tana wani Hali amma matarsa tasa key a daki bazai fita ba.

  Abbi Mustapha kuwa sai ya tashi da sauri zai fito sai ta Sha koshi ta zare masa ido tare da daka masa tsawa sai ya koma ya zauna,Abbi Sani bai ma san me akeyi ba yana can toilet yana ta wankewa Amarya kayan sawa. Aayan ne yazo gidan da niyyar dubo wasu takardu nasa a tsohon Part dinmu sai ko yaga idan ya wuce bai gaida su Abbi ba baza suji dadi ba kawai sai yayi hanyar part din tun a hanya yaji kukan Hajja,da sauri ya karasa ya hango Hajja ranga ranga yashe a kasa ga kafa a karye ta kone kuma,Dama suna da labarin yanda matan sukeyi a gidan,Hajja ya kalla duk tayi baki ta rame skin ta kara yaushi abin ba dadi,Cak ya dauki Hajja kamar tsinke dama to an tsofe bayan mota ya sata cikin daya daga jerin motocin da yazo dasu Escort kawai ya bawa Umarni asibitin da zasu kai Hajja,da sauri ya debo takaddun da yazo dauka yabi bayan su asibiti tare da Sanarwa Daddy dasu Ameer dan gaban goshin Hajja.
  
    Sameera yar daba bata an dan yi nadama kadan sabo da kudi tasa Senator saurayinta ya kashe sosai sabo da a fito da ita tare da yaranta ai kuwa sun samu Nasara yau Monday aka fitar da ita zuciyarta cike da mugunta iri iri,wasu kuwa cikin yaranta duk sun tuba sunyi nadama itama ba laifi tayi dana sani da Nadamar halinta kadan,Tana mota duk tayi duhu ta dawo wata kazama da ita kamar mahaukaciya ,driver dinta ta ba Umarni ya tsaya a shagon saida wayoyi ta aika Driver da kudi tace ka siyo min iPhone 7 ya shiga shagon kenan wasu gungun yan tasha yan daba ne kawai a tsakaninsu fada ya sarke suka taho rudududu da gudu kawai wasu a ciki suna gudun tsira sunga motar da key a jiki kuma kamar a bude ma kawai da nufin su shiga ciki su gudu in yaso sa ajiye motar a gaba kawai suna budewa ta bude daya ciki yace kai kaga da mahaukaciya a ciki kawai a jefarta da sauri basu jira me ba suka jefo Sameera waje ta fado gefen titi su kuma suka figi motar suka kara gaba sai da suka hau titi ma sannan suka rufe murfin motar sabo da saurin da suke,Su kuma wanda suka biyosu bakin cikin sun gudu suka sauke haushinsu a kan Sameera suna ke kika jawo mana ubanwa yace kizo da mota nan wajen dan Me ae suna dura zagi na gaske kawai suka shiga sassaranta ta ko ina a jiki Allah ma yasa Police sunzo unguwar an kirasu yan daba suka gudu ba wanda aka kama sai Sameera jiki ko ina duk jini nan Driver ya fito yana Salati suka kwasheta sai asibiti,Rigar Sameera sai yanke ta akayi in to pieces sabo da ta jike da jini ta manne a jikinta,Da kyar aka ce to ranta har aka samu ta farfado,a hankali tana numfarfashi yan Uwa du suna kanta tace alhakin wasu ne da na sa akayi musu,bazan..kara....ba....Na..hakura da daba....aure zanyi...idan...Allah yasa...Na ..samu...Lfy..Ban...san...haka..ake..ji...ba..naci zalin...mutane..nasa anyiwa wasu fin abinda akayi min...sabo da..Ina...da kudi..danginta suna zagaye da ita ana lallashinta tayi hakuri ta warke kawai ayi maganar amma taki ji sai taci gaba ma da...haka..ma...nasa...aka Sassari..Hafiz wlh..Ni nasa kuce ya yafe min...Ni ce...Allura akayi mata ta bacci kawai sannan aka samu tayi shuru.

    Ango Ameer suna kissing din juna Meenat ta tuna fa baice yana sonta ba haka kawai zai rainata,a hankali ta zare bakinta a nasa ta matsa can gefe yace ya akayi yana rawar jiki duk ya canja gaba daya,Meenat tace bacci zanyi jin haka yasa yace Ok sabo da bai son ya takura mata a daren farko da aka kawota gidansa kuma bai son raini shi,sai taga ma ko jikinta yake so,a hankali ya kwanta yana tunani cike da jaraba har Meenat tayi bacci a hankali ya lallaba zuwa jikinta ya shige jikinta sosai yana shakar kamshinta da yan tabe tabe da yake mata a hankali ba tare da ta sani ba tana baccinta sai da ya kwashe lokaci me tsawo kafin Allah ya taimakeshi bacci ya daukeshi.

    Aayan sai naci yakewa Daddy a waya sai ya Auri Ammah idan ba haka ba shi ko wa za aura baya sonta,Daddy har yau Bai bashi amsa ba,yau ma still Har Office din Daddy ya sameshi yana damunsa,Daddy dan Allah pls kaji Ni bana son wancan matar dan Allah kar ka aure ta,Baki Daddy ya rike yana mamaki yace ikon Allah kaine zaka zauna min da matar ko me?kana fa takura min,Aayan ya bata rai yana wata shagwaba Daddy kyakyawace fa na San tafi wacce kake so kyau ma,murmushi Daddy yayi jin rashin kunyar Aayan ma tayi masa yawa hannu ya daga masa ok..ok Son jeka zanyi shawara ka daina takura min na fada ma,Zan daina zuwa Office din nan tayaka aiki dama sabo da kai nake zuwa,Daddy indai ka auri Ammah to har Hutu zan baka kuje Honey Moon Allah yasa ta Haifo min Kani ko kanwa ma na samu abokan Shawara nima ina da yan Uwa ko,Kwalin tissue Daddy ya jefowa Aayan da niyyar ya makeshi amma Aayan da sauri ya goce yana dariya,get out Aayan da sauri Aayan ya fita yana dariya,shi kanshi Daddy dariyar Manya yayi kuma fa Aayan da gaskiyarsa Ammah ta hadu sosai shi kadai ya ayyana hakan a ransa.




Kuyi hakuri Fans kwana biyu ina busy ne shi yasa kuka ji shuru,sannan masu yi min text ta pc yayi yawa da kyar idan zan iya reply ma duka akan lokaci kar aji nayi late reply aji haushi na pls ayi min Uzuri sabo da abubuwa da yawa sunyi yawa dan Allah a dinga Uzuri a daina saurin jin haushi ko ana fassara magana,nafiku son na gama Novel din nan da wuri Uzuri pls bana so fans dina suyi fushi.love u All.







AsmaBaffa
[2/20, 10:00 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

    KASUWANCI NA




          131-135





Official





By
AsmaBaffa









       Daddy shi kadai yake murmushinsa idan ya tuna maganganun dan nasa Aayan,Ma'eesha kam anji jiki komai sai dai Yarima yayi mata tana kwance daga an dan taba ta sai kuka dama kadan take jira,Umman Yarima ce ta aiko Driver da abinci iri iri aka kawo musu amma Ma'eesha taki ci idan ma ya matsa sai kuka zata fara,gajiya yayi ya kira Aayan a waya ya hada shi da Mufeeda ko zata dan lallasheta,lokacin kuma Mufeeda ta tashi gaba daya zuciyarta tashi take,jikinta ya dau Zafi suna kwance da Aayan ta Mike da sauri ta shiga toilet da Sauri ta danyi Amai ba dai me yawa bane Aayan yace dama baki da lfy ne? Wlh ban sani ba ko Malaria ce yau 1wk kenan kullum haka haka nake jina jikina ba dadi,Ido ya zuba min na dauke kaina gefe tare da dariya ina mene haka kuma,Aayan yace ko dai nayi miki ciki? Jibeshi ko kunya baka ji wai kayi min ciki ba wani ciki kalleni da kyau ni daya ce,Aayan yana murmushi yace ni naga abinda na gani sannan kuma ni naji abinda na ji a tare dake kawai ki yarda kin Zama Mum...kirr wayarsa tayi kara yaga Yarima dauka yayi tare da Sallama,ko gaisawa basuyi ba yace Man hadani da wife dinka pls,Baice komai ba ya bani wayar na karba tare da cewa My in-law ya kk ya Babyna Ma'eesha? Gata nan tun jiya take kuka taki cin komai nayi har na gaji,bani ita kawai,Yarima ya mikawa Maeeshah waya nace Hello.

    Cikin muryar Kuka ta fara magana Sis kizo ki daukeni dan Allah azaba kawai yake gana mini,lallashinta na shigayi da kyar ta hakura sannan mukayi Sallama,Aayan yana murmushi ya karbi wayarsa tare da ce min Maman Fadila ko Maman Fhudal,kana waisting time dinka ba komai a cikin komai amma duk kabi ka damu,lips dinsa naji saman nawa yana tsotsa a hankali tun ban fara biye masa ba har nabi nima.

    Ameer bacci sukeyi sosai su garin Bacci Meenat ta dauki kanta ta aza saman nasa fuskarsu Manne data juna face to face, suna ta bacci Har rana ta fito ko Sallah basuyi ba,Meenat ta kara kankameshi bata sani ba shima haka Ameer yaji laushi a jikinsa sai ya kara nadewa a jikinta ba tare da ya sani ba,Meenat ce ta fara farkawa da sauri ta Mike zumbur tunaninta Ma'eesha ce sai ta tuna fa an musu aure,Da sauri ta fada toilet tayi Alwala sai da tayi Sallah da Azkhar sannan ta bar masa dakinsa ta koma nata ta shige wanka abinta,Ameer sai da ya dan jima yana bacci sannan ya tashi shima ya fesa  wanka da Brush tare da sallah,Cikin wata Shadda arniya ya shirya silver ba karamin kyau yayi ba kamar a sace shi a gudu palon kasa ya sakko Kamshin girki ya cika ko ina Meenat tana kitchen Ashe sabo da tasan Mufeeda baza ta kawo musu abinci ba sabo da mayyar mijinta ce sai abinda yace bazai ma bari ta wahala ba, Ammah kuma bata so ta daura mata aiki,Ameer kuma Ummansa tana can gidansu itama ci da ita akeyi tunda ya kai Meenat har sau uku ta gaida Ummansa kuma bikin ma da Umman akayi komai,a hankali ya karasa kitchen din sai da Numfashinsa ya dauke zuciyarsa ta buga ganin yanda Meenat ta hade cikin Riga da skert na lace dinkin zamani hips din nan  ba a magana, kamshinsa taji kawai tasan yana kusa a hankali ta juyo sukayi Ido biyu,Wani kallo yake mata yanda tayi kyau ba zai iya dauke kansa ba,itama ya tafi da ita wannan wanka haka kamar yau ne daurin Auren,da ace bata San Ameer ba da sai tace shike nan fita zaiyi wani waje amma tasan shi ko a gida yake sai yaci Uban wanka,dan kar ta rainashi ya dauke kai ya fara duba fridge da niyyar daukan abu yazo,Meenat tace uhm...Ina kwana ka tashi lfy,yace lfy Alhmdllh ya share,itama taci gaba da aikinta yana ta dube dube a fridge yana fito da abubuwan da jiya aka zuba su a ciki na kayan sha da marmari da kuma Kaji da sauran kalolin Nama ne kawai bai fito dasu ya mayar ba,Meenat ta gaji da karaf karaf da yakeyi tace wai me kake nema haka? Baki san inda yake ba ajiyar wani bata wani bace,Bayan ya mayar da komai mazauninsa ya Mike yace kiyi Sauri yunwa nake ji,Harara Meenat ta zuba masa,ke ni kike Harara sa'anki ne ni?Meenat ta tsorata tace a'a yi hakuri,Matsowa yayi kamar zai shige jikinta tuni har ta lumshe ido sabo da dadin kamshin turarensa facing din juna suke yana kallonta kamar me da sauri ta juya baya zata ci gaba da aikinta taji ya sata a tsakiya gabanta Sink bayanta kuma shine jikinsa gaba daya a jikinta yake,Hannayensa Biyu ya aza saman cikinta yana shafawa a hankali har zuwa wuyanta, kansa ya daura a saman dokin wuyanta yana shakar kamshinta tare da sauke ajiyar zuciya,luf Meenat tayi ita tasan me take ji kawai a jininta a hankali ta juyo ta jingina da sink,fuskarsa ya daura saman kirjinta zuwa wuyanta yana murza kansa,a hankali ta ajiye Wukar dake hannunta gefe ta rungumeshi gaba daya a jikinta,kansa ya dago a hankali tare da matso dashi zuwa fuskar ta ya daura lips dinsa yana dan shafawa da lips nasa cike da nutsuwa tare da salon kwarewa ya fara kissing din lips dinta,Harshenta yake tsotsa tare da labbanta Meenat ta sakalo hannayenta ta Saman wuyansa tana shafa wuyansa ta baya zuwa sumarsa me matukar kyau da laushi tare da Santsi ga yawa sosai.

     Zip din rigarta yaja kasa a hankali ba tare da Meenat ta sani ba ma rigar da ta sa ya zame kasa, da Hakoransa ya balle mata Bra din dake jikinta Hannayensa ya daura Saman Boobs dinta ya shiga murzasu a hankali,Meenat ta manta ma girki takeyi Allah yasa ta gama soye soyenta ruwan tea ne kawai ke saman wutar Gas din,Kafafunsu baza su iya daukansu ba Ameer saman Kujerar dake kitchen din ta girki ya zauna dake doguwa ce, Meenat ya jawo ta zauna saman Cinyarsa kowa yaji kunya ba wanda ke magana sai nishi da shidewa da sukeyi,hannu yasa da niyyar janye mata Skert sabo da har ya zage zip din tuni,Dan hankalinta ne ya dawo jikinta kadan ta ja baya tana kokarin Maida kayanta,Ameer sumarsa ya sosa idonsa kwalla ce ciki yayi Red kayansa duk ya yamutse yana gyarawa ya harari Meenat dake daura dankwalinta yace kin bata min kaya da Powder jiba jambaki,Meenat ta murguda baki ni nace ka Sha min lips ko kazo jikina ka gama duniyancinka zaka zo kace waye waye,Murmushi yayi tare da cewa bakinki ne dan Duniyar ai,Meenat har yau a diririce take ta kasa karasa aikin sai dube dube take tana kwance dankwali tana gyarawa,Ameer ya sheke da dariya yana kallon abinta takeyi har ya gaji yace ki kwantar da hankalinki Meenatuna zan kwashe tarkacen dake Tekun taki tsab,Kunya ta kama Meenat da sauri ta dauki ludayi,yace ajiye ko tea din ake Eba da ludayi? sai ta ajiye ta dauki spoon na cin abinci,Ameer yace wannan katon spoon din fa? Nan ma bata ce komai ba ta ajiye ta sauke tukunyar dake neman tafasa,Ameer yace lallai Meenat Karamin kai ne da ke dan wannan abin duk kin birkicice koma Dining ni zan karasa,Bata ce komai ba yaga kuwa ta fice abinta,lallai da gaske dama irinsu Meenat Karamin kwakwalwa garesu ba wahala ka cakar dasu,a ransa yace Meenat idan ace yar shaye shaye ce to kanta bazai dauka ba.

    Ameer ne ya karasa komai ya shirya a Dining Meenat ta zauna a Dining room tayi shuru kawai tana kallonsa sai wasa take da hannayenta,Allah sarki Meenat an dura mata maganin mata na tsumi dama yaya take lallabawa,shi ya zuba mata komai ya hada Mata tea ya tura mata gabanta sabo da kar taji kunya ta fara ci badan tana so ba ita yanzu ba shine a gabanta ba,Kowa yayi shuru yana tunani har suka gama ci,shi yayi wanke wanke ita kuma ta gyara ko ina banda Compound akwai masu aiki da tuni ma sunyi aikinsu,Ameer sarkin tsabta har ya cire kayansa ya shiga wanka zai sake shiryawa wai yayi girki kayan sun baci jikinsa na kauri,Meenat bata ma San yana toilet ba ta gama gyara Bedroom,ta bude toilet sai da ta kulle taga Ameer daure da guntun Towel yana kuskure bakinsa da liquid toothpaste tare da mouth Freshener bai fara wanka ba,Da sauri ta juya zata fita,taku daya ya kamota ya rungumeta yana ina zaki kuma ai tunda Allah ya kawo ki kuma sai ki min wankan,Meenat kamar zatayi kuka ta fara kokarin karbe kanta,harshensa yasa yana mata wasa dashi a kunne Meenat ta Zama Weak tuni sai yanda Ameer yayi da ita ya riga da ya gama gane lagonta,tana jinsa ya rabata da kayan jikinta tas maimakon yajata suyi wanka sai ya shiga Shan Boobs dinta yana wasa da daya,Meenat tana shidewa bata ma San ta fara shafa kirjinsa ba tana kissing dinsa sosai,Ameer cinyarta ya dan buda ya kalli kasanta mamaki ya tafi dashi ganin yanda Meenat ta Zama wet har ma yayi yawa Bai taba ganin irinsa ba shi kam yayi sa'a sai kawai ya fasa wankan sabo da shi yanzu bazai iya komai ba,Ya dauki Meenat cak suka fito waje,lokacin Meenat tana cikin bukatuwa ko wasa ne yayi da ita sosai amma ganin ba soyayya suke ba ta cuci kanta wajen kwace jikinta ta koma toilet tasa key tana maida numfashi,wanka tayi tare da wanke toilet din ta maida kayanta daya cire mata ta fito,Ameer kuma anyi Flat a saman Bed ji yake kamar ya mutu ya huta da irin wahalar da yake sha,Idan har bai rage zafinsa ba to yanzu cutarsa ta gaske zata dawo sabo da ya fara Jin alamarta,Meenat Zata fice da sauri a hankali ya kira sunanta,ta dawo ta zauna a gefen Bed din,kansa ya daura saman cinyarta a hankali yace Meenat me yasa bakya so na ni?Ban gane ba ta tambaya,me yasa kika tsaneni yanzu? Hmm ni fa ban san me kake nufi ba,me nayi maka?ko magana fa bakya yi min sai dole bare muyi Hira,nifa mijinki ne Meenat ai fa da ba haka muke dake ba,ni ban tsaneka ba taya zan tsaneka,da na tsaneka ai bazan bari na aure ka ba,Kina sona ya tambaya yana kallonta,Kai kana so na ne itama ta tambaya?ae ai shi yasa ma na yarda akayi aurenmu kuma kinga yanda na dinga murna da naji kece sai da nayi rawar da ban taba yi ba a duniya Saura kadan na cire kafata sabo da rawa,Dariya Meenat tayi tana Jin dadi a ranta dama ta fahimci Ameer yana sonta itama kuma haka,a hankali yace ke fa?,ni bazan kwaikwaiyeka ba ka bari nan gaba zan fada da kaina,Murmushi yayi me Jan hankali sai da Meenat tayi kasa da kanta,kansa ta ture gefe ta tashi tare da bar masa Bedroom din ranta kwal kwal fes da farin ciki da gudu ma ta fada dakinta tana murna,Ameer kuma dadi yake ji ya fadi  abinda ya dade a ransa yana damunsa,lallabawa  yayi wanka yasa kana nan kaya marasa nauyi ya kwanta cikinsa na masa ciwo kadan kadan.

   Hajja tana asibiti tana jinya dangi da jikoki ke sintiri a kanta ana jinyar ta amma banda su Abbi da matayensu ba wanda ya leka ta,ni kuwa Mufeeda nafi kowa zuwa dubiyar Hajja da kula da ita ko yaushe ina hanya da lafiyayyan abinci,Hajja mamaki takeyi sosai yanda ban taba nuna naji haushinta ba kuma duk abinda tayi min bai Dameni ba,yau ma zazzabi nake ji da Amai amma haka na samu Aayan dole muje duba Hajja na kai mata abinci,Na gaji kin sani Mufee na amma ke kullum rigimarki kenan kullum fa sai munje,rungumeshi  nayi yana jikin Mirror pls My Man ko dan Daddy mana harfa nayi abincin na shagwabe kamar zanyi kuka it's ok zamuje ba sai kinyi kuka ba,da Murna na karasa shiryashi na dauko Manyan kaya zan sa masa,ya make kafada kamar yaro a'a banda wannan ni bana son manyan kaya yau,dariya nayi na dauko masa wani Jean black da Riga Milk and Blue nan ma yace no banda dogon wando, kallonsa nayi to fisabilillah wanne kake so na sa ma na dauko kace banda wancan ko wanne an baka kace no ya zanyi da kai,Murmushi ya saki ba tare da ya shirya ba me tsada yanda na masa maganar kamar Uwa da dan karamin danta,ya kara narkewa sabo da yaga ina biye masa,3qtr na dauko Fari nace wannan fa?ya girgiza kai banda shi bana sonsa, dukan wasa na masa a kirji sannann nace Allah kaji na rantse sai kasa shi,Saman Bed na turashi da karfi muna dariya na kamo kafarsa na sa masa Boxers tare da 3qtr sannan nasa masa rigar, wai sai ya kama zai cire da sauri nace wlh idan ka cire yau baza mu kara shiri ba,mikewa yayi ya karasa gyare gyarensa nima na shirya cikin  wani kayan India riga da skert masu matukar tsada da kyau kamar a saceni,ta baya naji yamin wata Zazzafar Runguma tare da maida hannayensa saman Boobs dina zaka fara ko dan Allah Yanlabai ka saurara mu tafi,a haka muka fito har palo sannan ya gyara min mayafina ya dauki Basket din kayan muka fito da jakata a hannu takalmina me tsini ka rantse Balarabiya ce da Bature,muna zuwa Hajja da fara'a yau ta amsa ina gaisheta ta amsa da murna,Aayan ma  ya gaisheta yana mata sannu da jiki,Nace Hajja ina mutan gidan ban gansu ba? Baki ta tabe tana dan nishi tace yau kwanansu uku basu zo ba daga ni sai masu kula dani dattijan da Aayan ya kawo yan aiki su biyu sune suke jinyata,daga ku sai Daddy sai Ameer dan Albarka jiya ma yazo da Amaryarsa Alhmdllh naji dadi wlh Allah dai yayi albarka,jiya ma Ammah tazo ta dubani mutuniyar kirki,Haka Hajja ta dinga yaba mana,nace Hajja na zuba miki abincin?da murna tace ba dole ba yar nan wannan girki naki me dadi ai dole ki kwace min miji,dariya mukayi gaba daya na zuba mata iri iri gasu nan sai da ta Zaba,mun dade a wajenta sannan Aayan ya bata Kudi masu yawa yace sai gobe zamuje gidan Yarima da Ameer, Allah yayi albarka Ashe ziyarar Amare zaku je,tunda Aayan yake wa Hajja abin alheri bata taba masa godiya ba sai yau.

   Dama unguwa layi daya Ameer suke da Yarima,Gidan Yarima muka fara zuwa 5pm Ma'eesha tana Palo yana bata abinci a baki mukayi Sallama,tana jin muryarta ta tashi daga saman cinyar Yarima ta fado jikina da gudu tana ihu,ta kankameni ta ko ina,Aayan yana dariya yace sake min ita haka mana sai kin ballata kuma, sannu da zuwa ya Aayan Sister Oyoyo ina ta cewa ya kawo ni wajenki yaki yarda Ma'eesha harda kwalla,zama mukayi ina kusa da Aayan amma Ma'eesha ta manne a gefe na,Yarima yace Madam ya gari nace lfy alhmdllh Ango muka gaisa da wasa da dariya,Maeesha ma haka dan Allah Sis Mufee Muje daki dama ina nemanki na kira ki a waya baki dauka ba,nasan Complain ne akan me zan dauka,to ai gashi kinzo Muje kiji.

    Yarima ya mata signa da Ido wai tasan me zata fada,itama ta wani kashe masa ido daya sannan muka wuce dakinta,Aayan kuwa tafawa sukayi yace kan mage ya waye Yarima ko waya babu kai ga me Amarya,to dan sa ido kai kayi lokacinka ni so kake na kashe kaina ko?a'a bance ba dan iska yarinya karama kanwata ko kunya babu,a wannan fa ba wani kunya guy ba wani kanwa suna hirarsu dai.
     Ma'eesha ce ta rike Hannuna Sis Wahala kullum yake bani,da sauri na rufe mata baki da tafin hannuna karki sake ki fadawa kowa sirrinki da mijinki duk yanda kuke da shi ko kin manta Islamiyya ne,kuka ta saki Min Allah Sis sau uku yake min a rana,na fada miki ban son irin maganar nan zan bar miki gidanki,to yi hakuri Sis tana goge Hawaye tace me zan dinga dafa masa to?Baki na bude ke baza kisan wanne abinci mijinki yafi so ba,ba kinga yanda nakewa Aayan ba haka kema zaki dinga masa Abinci masu dadi kalar da yake so,kwalliya tsafta duk nasan baki da matsalar komai zaki iya ki dage ki Kula dashi sosai,abincin a ina kike samu tunda baki fara ba?Ummansa ce take aiko mana kullum,to daga yau kice ta daina gobe ki fara yiwa mijinki komai,duk fa na karanta miki komai kin sani to mene ne,karki sake ki nuna masa bakya so ya sadu dake kinji duk sanda yazo ki daure ki bada hadin kai,sai amfani da ruwan Zafi da tsumin da Ammah ta hada miki,na gane sis yawwa ki kara hakuri zaki saba da komai,kuma nan gaba zaki ji dadin abinda yake miki kike cewa da zafi,kai ta daga min,sau nawa kike fesa kwalliya da wanka? Tace uku ko hudu ai yayi ko?nace ae Good bari muje gidan Meenat,Haba Sis da wuri dan Allah bafa na son haka Ma'eesha so kike yace kin gaji dashi zai yo miki kishiya,jin nace kishiya zai mata sai tace a'a zan barki ki tafi ba damuwa ni,dariya nayi muka fito tare da ita nace Ranka ya dade tashi mu je gidan Meenat da Ammah idan kun gama,yace dama ke nake jira let's go,Maeesha tace Sis abinci,nace a koshe muke kin San bana barin kaina da Mijina da yunwa,Yarima yace itama haka bata barina da yunwa ko My Dear? Ya furta yana Maida Ma'eesha jikinsa a haka suka rako mu har mota muka wuce su kuma suka koma ciki.

    Meenat tana kitchen tana hada Abincin dare,Ameer yana gefenta kowa na zuba son girmansa, na danna Door bell tare Murda Handle,Aayan yace a'a jira malama a bude so kike muje mu samesu a wani yanayi muji kunya kin San Ameer fa Maye ne bare yau 3days kacal,Ameer ne ya bude kofa yana fushi Meenat tace Ya bude kofa yana Babba kuma mijinta ai a kasansa take,Aayan ya kalleshi sanye da farar Jallabiya wata Fitted sosai yayi kyau,kai kuma lfy kake ta wani shagwaba a jikin kofa kaje kayi mata ba mu ba,Dariya yayi Ya Aayan Sannu ai dole nayi fushi dan Allah Sis kato dani da shekaruna Meenat take aikena ni kin San ban son Raini,Dariya mukayi Aayan yace bani Hanya muka shiga gaba daya,Meenat tana Jin muryarmu ta fito da sauri tana murna Tana mana sannu da zuwa,da sauri ta kawo mana kayan sha iri iri sabo da tafi Ma'eesha wayo dama ance duk tsiya wanda ya girmeki ya girmeka,mun gaisa da juna cike da girmama juna ana wasa da dariya Meenat tace ina zuwa Sister,Ya Ameer danzo kitchen na ganka,Aayan yace iyye Meenat anyi aure har anfi son ayi sirri da miji,Dariya mukeyi,Ameer ya turo baki kunji ko Sis Mufee nafa girmeta ya Mike ya bi bayanta yana kunkuni,Kallonsa Meenat tayi tana dariya tace dama shawara ce a basu snacks din da nayi ko kuma a bari sai na gama abincin? Ki basu mana tunda ba dadewa zasuyi ba idan kuma suna nan sai aci duka tare dasu ai da yawa,Snacks masu dadi ta hado a wani plate kato me kyau ta mikawa Ameer tace karba ka
kai musu bari na dan karasa wannan aikin,Karba yayi tare da cewa dan dai kece kawai Allah,abinda kullum ko tausayina bakyayi kina gani da dare sai ki wani hanani ko Kiss nayi Allah kiji tsoron Allah 3days kin hanani,Nace ai dai zan baka watarana idan naji zan iya ko? ta furta tana murmushi,kallonta ya tsaya yi yace Ina Sonki da yawa ne Meenat amma da watace da tuni ko raping dinta nayi dole,amma ke kike juya ni Hajiyata sai abinda kike so ke kuwa naga bakya sona,Tausayinsa Meenat taji tace Ina Sonka Allah sosai Ameer dina ban taba son kowa ba sai kai kayi hakuri zan Yarda kayi ne tunda nace,yana rike da Plate tasa hannayenta ta wuyansa sannan ta hade bakinsu waje daya suna tsotse junansu Saura kadan ya jefar da Plate din ta kyaleshi tace au mun manta da baki fa,Ameer yace ni dai I need more,ka bari sai dare Promise yau duk inda kake so sai ka taba a jikina,are sured?,tace yes Sir, fita yayi zuwa Palo Ya kawo mana abinci amma duk munga ya canja kawai mun gane me sukayi muma ai suna shiga kitchen sai da muka danyi Kissing din juna ni da Aayan dina,munsha Hira dasu Ameer sai da mukayi Sallar Magrib sannan muka wuce gidan Ammah nan mukayi Sallar Isha sannan muka mata Sallama ita da Inna wacce har yau bata koma Kauye ba Ammah ta hanata wai sai tayi ko 3wks ne.
  Su Khaleel ma Aayan ya musu fada su dinga zuwa duba Hajja kuma sunji maganarsa,Sajeeda tana nan tana soyewa da tsohon saurayinta yanzu da gaske Aure zasuyi,H aka Meenal ma da Haneefa duk sun samu samarinsu tsayayyu na gari,Khaleel da Mujaheed suna zuwa zance yanzu ko Allah zai sa a dace.
 
    Bayan tafiyarmu Ameer yaje Sallar Isha sai ya dawo da Zazzabi sosai jikin Meenat ya kwanta kawai tana zaune tana karatun Qurani,jin jikinsa da zafi tace Honey Lfy tana taba kansa zazzabi nake ji Darling ki bani abinda nake so dan Allah Meenat bazan iya jira ba,har Zazzabi kakeyi a cutar taka dama?kai ya daga mata,idanunsa na tara kwalla duk sun koma red sabo da bala'in da yake ji a jikinsa,Zafi Darling ance da zafi,a hankali Ameer ya janye jikinsa ya kyale Meenat ya koma Saman Bed ya shige Blanket sabo da ta fara bashi haushi, yana rawar sanyi sosai,yasan Meenat baza ta bashi abinda yake so ba,yau kwana uku yana cike da matsananciyar bukatar matarsa Meenat bai San me yasa Meenat kadai yake sha'awa ba,Shirin bacci Meenat tayi sosai cikin wata rigar bacci me tayar da hankalin da namiji,Kamshi kawai takeyi ta shigo Bedroom din tare da haurawa saman Bed din da Ameer ke kwance a kai, cikin Blanket din ta shiga yana ta tunanin Mafita yana addua sai ga Meenat ta shige jikinsa bata bata lokaci ba ta kwanta suna facing juna ta sa hannayenta biyu tare da tallafo kan Ameer tace Sannu Mijina,bai ce komai ba,tace dan san min Lips dinka da Tongue dinka Babyna na dan Sha,Kafada ya make wai yayi fushi,ni din?kai ya daga mata wai ae,Rigarsa ta cire masa a hankali daga shi sai Boxers, a hankali Meenat ta shafa kasan Mararsa ta fara tsotsar lips dinsa tana rada masa love u Mijina,ta ja boxers dinsa ta sakeshi das duk so take Ameer ya daina fushi yau ta bashi Hakkinsa ko mutuwa zatayi bata damu ba,Ameer tuni ya daina Jin zazzabi ya gigice,da Zafi zafi  ya fara kissing dinta a haukace yana lashe mata jiki musamman kirjinta da kanta tace na cire ma rigar? da kyar murya a sarke yace yeah Sweetheart,Meenat ta cire masa,yace Babyyyy tace Naam ya akayi itama da kyar take iya magana,Ki fada min Sweet words,Meenat sambatun da take ya girmi a rubutasu sabo da Meenat daban ce wajen maita ko ya Ameer ya taba ta zata haukace bare yau da taba da Himma da kanta ta yarda,Ameer yaji dadi abinda Meenat tayi masa babu wani iyayi na Amare wai su sababbi Virging ko romancing baza su bari ayi ba su dinga kukan harda Karin karya dan ace su basu San komai ba,bayan suna kallace kallacen film din turawa,wasu ma kafin mijin ya auresu suna Shan Romancing tun a waje suna mirje juna tare da karanta Novels etc wasu ma Bf suke kallo amma Sai ana pretending,Meenat kam a hankali tace na gwada ma Sucking Down ko zan iya idan na koya sai na dinga ma,Haka ta gwada idan baiyi ba yace kaza zakiyi kar kiyi kaza,duk inda zata taba masa yaji dadi sai da ya fada mata kuma ta dage ta gwada masa wasu da dama,shima yace sai ta fada suna Romancing abinsu tana fada masa shima haka,Har yazo yana lalubar Hanyarsa Meenat ta fara nokewa zata gudu,Ameer ya riketa kam ta fara wutsil wutsil zata gudu,ya riketa yana lallabata Meenat ta fashe da kuka wlh ni bana son wannan,ta bude Blanket ta fito da sauri Ameer ya rikota sosai tare da jawota ya rufesu a blanket,ni wancan nake so banda wannan Zafi ne zanji tana kuka,Yana lallashi ki kwantar da hankalinki dan Allah bazan miki da zafi ba,Meenat tana kuka tace wannan abun naka Allah tayi girma ni bazan iya ba,Gani Ameer yayi Meenat zata haukatashi in ya sake kawai ya riketa tare da bankareta ya bajeta Kuka take kamar za a yankata tana zan tsaya,zan tsaya karka min da karfi,yace Ok to Dole Meenat ta tsaya tana Wayyo Ya Allah tana ji Ameer ya nemi hanya ta fara Subhanallahi..yace kiyi shuru dan Allah ba da zafi zanyi ba yana marairaicewa,Meenat a rude tace to..to..to..to..to kuma taki tayi shuru ,tana Jin Bakon abu ta fara dan kukanta amma bada yawa ba,Ameer sai yaji kamar na dadi ma takeyi yaci gaba da baje shagalinsa,Meenat taji jiki yau Sosai Kusan kwana yayi tun a daren sai yayi sau biyu ba yanda ta iya,iya wahala ta gama Shanta,Sai dai kuma fagen lallashi da sa albarka ta Shashi wajen Ameer,Tana shesheka yana shafa gashinta yace ya isa haka ai kin huta an wuce wajen yanzu shike nan an bude Hanya baza ki kara Jin hakan ba kinji,Meenat a ranta sai da tayi dariya gashi kalamansa suna sata farin ciki da jin dadi a ranta,a mma idan ta tuna wahalar da ya bata sai ta fara fushi har sukayi wanka ya gasa ta sosai suka koma bacci,Ameer kamar yayi me sabo da farin ciki ya rasa inda zai sa kansa yasa Meenat ma.








AsmaBaffa
[2/28, 10:46 AM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

    KASUWANCI NA








         136-140




Official



By
AsmaBaffa




  

      Page din Flower ne wannan dan jin dadinta.



   Ba a Yarda wata tayi Poster Din Wannan Novel ba na KASUWANCI NA.wacce tayi kuma na kamata sai na kona mata Mazaune me gidanta yayi asara😍😍😍😍😍😘😘🙈🙈👍👍love u all fans.

   Kwana biyu fans kuyi hakuri na rashin jina,Rasuwa akayi mana me zafi,masu kirana ta waya ana tambayata lfy nake kuwa ina matukar Gode muku sosai Allah ya saka da alkhairi.masu tura min text through WhatsApp da Phone na gode Allah ya bar zumunci.

Page dinku ne wannan Fans gaba daya da wanda na sani da wanda ban sani ba.
           




       
    Daddy ne ya samu Babban Amininsa Ahmad Naira Bola suka yi shawara kawai zai auri Ammah yanda Aayan yace, Sunyi Shiri tsab suka tafi neman yardar Ammah kafin aje danginta,Driver na parking a gidan Ammah lokacin Aayan yaje gidan da yamma shima zai kwashi gaisuwa,Karaf yaga Daddy harda abokinsa,Farin ciki ya kamashi amma Bai tsaya ba yayi sauri ya karasa palon Ammah domin ya fada mata taci kwalliya sai yaga Ammah ta hade cikin wata dakakkiyar shadda Maroon tasha kyau,bai taba Sanin Ammah nada kuruciya haka ba sai yau,abinda Aayan bai sani ba kafin Daddy yaje sai da ya nemi Number din Ammah a hannun Ameer sannan ya sanar mata sabo da haka tare da Inna yar uwarta suka shirya girki tasan Daddy bature ne dama kuma baya cin abincin Hausawa sabo da haka na turawa tayi masa irin su Snacks duk Ameer ne munafikin da ya fada mata ta waya wasu ma bata iya ba amma ya tura mata Masu yi ma Daddy girkin na gida suka koya mata da yawa a ciki,ta kuwa yi kuma yayi harma yafi nasu.

    Ammah na ganin Aayan kunya ta kamata sauri take ya tafi amma yaki tafiya har Daddy Me aiki tayi musu Iso suka shigo,Aayan sai washe baki yake harara Daddy ya watsa masa da Ido ya nuna masa ya fita amma yace ni matata nake jira tace na jira ta a nan gidan sai dai na koma Bedroom din can ya furta tare da komawa Bedroom,Ammah ta gabatar musu da kayan abinci ta zauna a kunyace Daddy a ransa yace Allah yayi Halitta a nan,da naso na tafka kuskure Allah yayiwa Aayan albarka,nan abokin Daddy ya Sanarwa Ammah meke tafe dasu,itama dai tace ita kunya takeji gaskiya a kyale maganar,Aayan yana labe yana ji a daki,yana why Ammah wacce kunya kuma kai Hausa People,da kyar Abokin Daddy ya dage tare da Inna da ta zauna a wajen yanzu tace Allah ya halatta baza ki Haramta ba kinfi so ki zauna a haka,nawa kike da kuruciyarki,Ammah dai tace to Allah ya tabbatar da Alkhairi na Amince amma da sharadi bazamu zauna a gidan suruki na Aayan ba,Daddy yace Ni kaina yanzu ba a gidan nake ba dama lalura ce tasa amma tuni na koma gida na,Aayan ma kwanan nan zasu koma Abuja da zama tare da zaga kasashe mu kuwa muna kano sabo da Mahaifiyata,idan ma Abuja kike so sai mu zauna can ki zabi gidan da ya miki,Ammah tace a'a nan ma yayi abincin suka dan ci kadan sannan suka musu Sallama tare da zube Kudi masu yawa suka tafi,sai da Aayan yaga Daddy ya fita sannan ya fita da Sauri yana Ammah na tafi tace na gaidaki dariya ma ya bawa su Ammah dama sa ido ya zauna Ashe.

   Yana fita lokacin Daddy zai shiga Mota Aayan ya rungumeshi yana Dariya Daddy Ashe zance kazo da ka fada min nine dan rakiya,Abokin Daddy Alhaji Ahmad Naira Bola dariya yake musu shi dai rayuwar Daddy da dansa tana birgeshi,Duka Daddy ya kaiwa Aayan Yanda Aayan ya dage yana gwada yanda Daddy yayi,Mota suka shiga suka barshi yana dariya sai lokacin Shima ya shiga motarsa Driver ya jashi sai gida,ya shigo da Murna ya tarar na kafa kaina a cikin wani Vaseline ina shakar Kamshin kwanan nan dadin Kamshinsa nake ji ban san me yasa ba.

    Kallona ya tsaya yi ko Sallama na kasa amsa masa sai a zuciyata hancina yana cikin robar Vaseline,lfy kuwa? Na fada miki ciki ne da ke kinki yarda,gobe asibiti zamuje ko bakya so,Vaseline din na lakuto tare da laftawa a saman Hancina wai na dinga jin kamshinsa ba ruwana,Ina zuwa nace masa na fice can garden jikin bishiya na samo Kasa a dan karamin Kwano na dawo na tankade abata luwai na dan kwabata da ruwa ina dan ebowa da cokali ina shanyewa,a kitchen ya sameni tunaninsa wani abin nake Sha me dadi,tsoro ne ya kamashi ya kwace kwanon ya zubawa kasar ruwa ya wanke dan Plate din, mene haka dan Allah?karki kara sha ko bana gidan nan kashe min jaririn zakiyi da kasa,idan ta tsotse miki jini fa ko ta miki illa ko akwai kwayoyin cuta ke kika ci fa,Kuka nasa masa nace Ni ba a sona sai jariri tun bai zo duniya ba tunda haka zaka dinga nuna banbanci to indai ciki ne zubarwa zanyi,Wasa nake miki Baby haba ni na isa ai kinfi Jariri shin din Banza,ya isa ina ruwana dashi,sai lokacin to in dai ka kara nuna ya fini wlh sai nayi ta Shan kasa da kanwa ko nasha gayyen darbejiya daci yasa cikin ya zube idan shine kawai wani yazo sama ta kai a nuna ya fini,Aayan yace ni ai ban isa wani fiki ba,waye ma ya isa na daina sonsa tuni yaje yasha zamansa,Hannunsa na rike nace wayyo..yace Mene Allah jiya naji ana min Usha Usha a cikina,ka gani yanzu ma,dariya Aayan yayi yanda nake gwadawa da Hannu kamar Yar China,cikina na rike nace wash..wash..Allah na Yau Kungfu ne ake min idan kuwa jariri ne wannan to dan kasar China ne zan Haifo shi a nan kasar.
    Aayan yace shine ma yasa kansa a gefen cikina yace kai jariri ka daina kuka kana wutsil wutsil bazan taba sonka kamar matata ba,nafi sonta itace gaba da kai,Dariyar jin dadi nayi na zauna tare da cewa woo...ba a sonsa,Aayan dariya yake sha abinda nakeyi na kuruciya.

    Meenat ce ta bude idonta daga baccin wahala da takeyi While Ameer yake shakar na dadi abinsa,a hankali ta zare jikinta a nasa ta fada Toilet,wanka da duk abinda ya dace tayi ta fito sosai ta gasa jikinta,Sallah ta gabatar tare da azkhar sannan ta shirya sama sama ta canja New night Gown me dan sauki saukin tsaraici ta kwanta a gefensa again kwanciyar da tayi ne ta tashi Ameer,da sauri Meenat ta rufe idonta amma ya rigada ya ganta,yaga alamar tayi kokarin yin wanka ta shirya kanta Jarumace Meenat,shima toilet ya fada ya gama komai ya fito ya gabatar da Sallar asubah tare da azkhar daga shi sai boxers ya koma Bed din tare da shigar da Meenat jikinsa sosai yana kissing dinta a wuya da gashinta zuwa gashin kanta dake kamshi baccinta takeyi kawai abinta.

   Bacci suka ci gaba da yi ba su suka tashi ba sai wurin 11am hakan ma shi ya takura sabo da bata ci,Ameer waya ya buga min lokacin zanyi shirin zuwa schl sabo da muna shirye shiryen fara Waec da Neco, Sister Mufee dan Allah do me a Favour Meenat Bata da lfy ne abinci muke so,Ok zan bawa Driver ya kawo muku,kitchen na kara shiga na dan musu masu sauki,Dama nayi farfesu sai kawai na soya Chips da kwai tare da ruwan tea na shirya komai sharp sharp na bawa Driver ya kai musu,Meenat ya matsawa dole sai ta tashi taci abinci, Da kansa ya kaita ta kuskure bakinta sannan ya zuba musu abinci a Bedroom din ya dinga ciyar da ita shima yana ci har suka koshi,duk abinda yakeyi Meenat taki bude idonta bare ta masa magana wai kunya takeji ita har suka gama cin abincin ya bata Mouthfreshner  ta kuskure bakinta shima haka,zata koma ta kwanta ya riketa tare da cewa dan zauna kadan ba kyau ana gama cin abinci a kwanta,Kayan da suka bata ya maida kitchen ya gyara Bedroom din sannan ya hau Saman Bed din tare da cewa kwanta Sweetlove ya sata cikin jikinsa suka kwanta ya fara kokarin cire mata yar rigarta,da sauri ta bude idonta cike da muryar kuka tace shike nan tunda kashe ni kake son yi sai ka dauki raina,Murmushi yayi tare da cewa ba abinda zan miki nafi so kawai najiki a jikina ba kaya kiyi hakuri My Meenat,Kai kawai ta daga mishi yana lashe mata hawaye da harshensa,tana shesheka tace ka..ka..kira min Ammah na gaisheta dasu Sisters kwana biyu bamuyi waya ba,Jiya fa ne kawai bakuyi magana ba Babyna amma bari na kira Sis Mufee,Yana Dialing Number din Mufee Aayan ne ya dauka yace tana schl sai anjima zan dakko ta ya akayi? Ameer yace kai ya Aayan wayar ma Tata idan tana schl tana hannunka kamar wani P.A,idan ta dawo kace ta kira Meenat back,ok cewar Aayan ya datse kiran,Ameer kuma ya Kira Ma'eesha wacce yanzu ta dan saba da harkar Yarima da sukeyi tana jin dadi kadan,Suna murza juna Kiran Ameer ya shigo Amma Yarima yace baza a daga yanzu ba sai sun gama tukun zasu kira back,Ammah kadai aka samu a waya sukayi Hira ba tare da ta gane komai ba,suna gamawa Meenat ta makale a jikin Ameer tana masa magana kasa kasa Allah ka bani wahala Honey jiya ko tausayina baka jiba,Am so sorry My love Bazan kara ba kinji yana lallashinta tana shagwaba .

     Alhmdllh Daddy ya yaje Dangin Ammah  Sati daya aka daura auren Ammah da Daddy ko su Aayan basu sani ba Hajja kawai ya fadawa tana asibiti har yau ba a sallameta ba, ina fitowa daga class an tashi naga Ma'eesha tana daga min hannu ita ta tafi Yarima yazo daukanta,ina daga mata hannu kawai naji an daga ni sama nasan Aayan ne ina jin kamshinsa,ana kallonmu fa zaka Sa  ace bani da kunya,thts y nake so ai mu koma Abuja dagani sai ke babu me Sa mana Ido jira nakeyi ku gama zana last Exam ta Neco,Murmushin dake kara min kyai nayi tare da rike Hannunsa nace Muje Mijina,Office dina zamuje ki jirani na gama sai mu wuce gida ko,amma fa kasan bani da wata lfy kasala,ga saurin jin yunwa kuma ina tashin zuciya kaga kuwa akwai Matsala kar nayi maka Amai a Office,ba damuwa muje haka gobe baku da schl asibiti zamu je kar Babyna ya girma ba a fara dura masa kwayoyi ba,biyu da Safe biyu da dare,dariya na farayi shima haka nace kamar kasan yaran yanzu duk yan kwaya ake haifowa,sabo da tun a ciki ake dura musu kwayoyi.
    Muna ta hirarmu har ya bude min mota na shiga shima ya shige Driver tare da escort suka ja sai Office katafaren building.

   Tun a hanya nace a tsaya a siya min Doya da kwai haka yasa aka siya min,ya kwanto dani jikinsa yana tambayata sai me kike so Babyna?Nace Coconut da Alkubus,Ina zan samo Wani Alkubus ni kiyi hakuri na fadawa Ammah tayi miki idan zamu tafi gida sai mu biya mu karbo,banyi musu ba nace masa to Allah ya kaimu yace Ameen Sweetyna, ina jikinsa muka karasa Office yana signing da Sauran ayyuka ni kuma ina saman Cinyarsa a zaune kamar yarinya karama motsi kadan idan nayi sai yace min ya akayi ina ta ciye ciye na hankali Kwance,Duk abinda nace ina son ci da Sauri yake Bada Umarni lallai a kawo min naci rashin kunyar da yake zubawa kuwa na caring sai dai idan baza ka kallemu ba ka tafi.

    Yau kwana Uku da Angwancewar Ameer jinya yakeyi har yau Meenat taki ta daina lango kullum tace bata warke ba ta wani narke zatayi kuka,amma a fagen Romancing itace kan gaba, 9pm Meenat taci uwar kwalliya sanye take cikin English Gown iya rabin cinya light blue and White sai kamshi takeyi gashinta yasha gyaran gaske kamshi ke tashi kawai ta ko ina,palon Angonta Ameer ta nufa tana Tafiya cikin nutsuwa tare da jan Hankali yana Palonsa sai chat yakeyi a waya yana Jin kamshin ta da Sauri ya fita daga WhatsApp din ashe Meenat ta gane me yayi,cikin takunta na kasaita ta karaso inda yake zaune Saman 3seater kafin ta zauna ya jawota jikinsa saman cinyarsa ta zauna yana shafa mata wuyanta da kafadunta ta baya,cikin muryar da ba a san Meenat da ita ba tace Ashe da ka shirya nan ka dawo? Yeah Princess ya furta yana Jan zip din rigarta kasa baya har yayi Zipping dinsa, Bra ya balle mata tare da janye rigar ya jata kasa ta koma kasan cikinta,Dukiyar Fulaninta masu matukar kyau da sheki suka bayyana juyowa tayi gaba daya a jikinsa ta kwanta Saman kirjinsa tare da rungumeshi tana rufe ido wai Kunya,Na shanunta ya shiga wasa dasu tana masa shagwaba,a shagwabe tace Husband ya amsa da Naam cikin dishewar murya,nuna min Chat dinka na WhatsApp na gani,Murmushi yayi tare da cewa gaskiya sai dai kiyi hakuri bazan iya nuna miki ko Contact dina ba, Ni Din?tana kallonsa kamar zatayi kuka,yace to me zaki gani in ba neman rigima ba,ni...Ni...Allah sai ka nuna min,am sorry to say gaskiya bazan iya ba,Fushi tayi a fusace ta kwace jikinta tare da maida Bra da rigarta tana niyyar tashi ga Kwalla na shirin kwararo mata,Ba shiri ya fisgota ta fado jikinsa me laushi da kamshi nan take ya mika mata wayar gashi kalla kuma nima sai naga naki murmushi tayi kyawunta ya kara bayyana ta karba tana me dauke da murmushi a fuskarta ta fara duba Contact,tana tambayarsa kowa taga Number din mace,haka WhatsApp nasa ma sai da ta bincika tas taga babu mace da suke chat,farin ciki ta shiga yi mijinta baya kula wata,Shi kuwa ko duba nata baiyi ba don baya zargin Meenat da komai.da kanta ta ja Hannunsa zuwa Bedroom dinsa sabo da tasan tayi masa laifi wajen danne masa hakki yayi hakuri da ita har ta fara Jin kunyar Ameer din nata,Rigarsa armless ta zare masa a hankali itama sannan ta kashe Light duf duhu ya gauraye dakin sai karar ac da kamshi kawai ke tashi,Bai ma san ta cire kayan ta gaba daya ba sai jinta yayi a jikinsa ta rungumeshi sosai Albarkatun kirjinta suka sashi ya saki ajiyar zuciyar ba tare da ya shirya ba ya dauki Meenat zuwa saman Bed,a nutse cike da wayewa suke gudanar da harkarsu har ya samu abinda yake so ba tare da tasha wahala ba,Gaskiya Ameer karshe ne hakan Meenat ke ayyanawa a ranta tana Jin dadi,bangaren Ameer ma hakan yake ji a ransa tana manne cikin jikinsa suna hira Sama sama har sukayi bacci abinsu.

   Kwanci tashi yau Sati Uku kenan da auren Su Ma'eesha Sameera Yar daba taji sauki Sosai ta warke inda ta fitar da Alhajinta me kudi zatayi aure itama ta saduda da al'amarin duniya,an sallami Hajja daga Hospital Ta samu Lfy amma matan su Abbi basu canja ba,su Khaleel ne ma watarana suke dan tarewa Hajja sabo da su Abbi sun koma abin tausayi sun koma rakumi da Akala,Kullum Hajja kuka take sharba musamman idan taga danta Abbi Mustapha yana wanke wanke da shara yayi duhu ya rame,yau kamar kullum matar Abbi Sani ta sashi wankin kayanta sai zufa yake hadawa,Hajja ta fita tana dingisa kafarta da bata gama warkewa ba,tana fada kan ya daina wankin haka ya isa,suna haka sai ga matar ta fito babu bata lokaci ta shiga Zagin Hajja Munafuka,Karuwa sannan ta ture Hajja ta fadi rim again akan kafar data karye nan take kafa ta kara samun matsala dama bata gama warkewa ba aiki ya lalace ya dawo baya,Hajja yau tayi kukan da bata taba yi ba,ba shiri ta fara Allah na tuba ka yafeni,Na jawowa kaina,na cuci kaina da yarana na ruguza farin cikina na tarwatsa kan yarana,Hajja tana ta tuba tana tona asirinta,Khaleel da Mujaheed ne suka hango me ke faruwa da Sauri suka karasa kan Hajja suka sata a mota sai asibiti tare da sanarwa Daddy,Aayan da Ameer abinda ke faruwa,Ameer bakin ciki ya kamashi Key din mota ya dauka kawai Meenat lokacin tana kitchen ya leka da Sauri yace na fita ana kira na Babyna yanzu zan dawo har ya tafi ya dawo da Sauri ya rungume Meenat tare da kissing dinta a lips yace take care of ur self for  me Wifedina,same too u Darling banda tukin ganganci kaji mijina,ya fita yana daga mata hannu ta kwalla da karfi am gonna Miss u Sweetheart kar ka bari a kalle min kai,shima da dan karfi yace Already started Missing u SweetMeenat ya fice dauke da murmushi ya manta ma da fushin da yakeyi Meenat ma murmushi take bazawa kawai.

   Bai zarce ko ina ba sai gida wajen Su Abbi,yana zuwa a fusace Ameer bai kula kowa ba ya fara shigewa Bedroom din Abbi Mustapha Baban Ameer kenan ya fara watso kayan matar anci sa'a Abbi yana bayi yana wanka,kasan Bed din ya dage katifar sai ga Wata yar tukunya dauke da tarkacen tsafi a ciki tare da ruwan rubutu,Ameer bai jira ba ya fito ya jefota ta saman Bene tukunyar tsafi ta ragargaje,haka ya fita ya shige dakin Matar Abbi tana cikin gyara kaya taga Ameer ya fado da zureriyar Sandarsa tunaninta dukanta zaiyi ko Ya haukace sai ta fita da gudun tsiya,Abbi na ganin haka ya rufa mata baya dama sai abinda tace Kan tace ne kafin tace ya aikata,nan Ameer ya kulle dakin da key ya shiga bincike a dakin ya dinga samo guru,laya,ruwan rubutu,ya duba kasan bed din ba komai cikin pillow ya duba tare da Sa wuka ya tsarge pillow din ta ko ina ya fito da soson da suke ciki sai ga layu iri iri a Cikin pillow an hada dashi an dinke pillow tsab baza ka taba ganewa ba,yanzu mata abinda sukeyi kenan za a kai Amarya kafin a kaita sai an yanka pillow da razor a tura kulunboto sannan a mayar a dinke yanda ba Uban wanda zai gani sai kaga pillow normal ashe da tarkacen tsafi a ciki,miji yana ta kwanciya a kai,wasu har katifa ake yankawa asa sai a Sa zare da allura a dinke ba me ganewa Allah ka shirya mu.

   Ameer yana fitowa ya fada dakin Abbin Yara Duk ya fita a hayyacinsa matar ta sashi sai ya goyata ya dinga zaga Bedroom da ita,gata wata me kiba katuwar gaske suna ganin Ameer da shegiyar wuka suka saki ihu ta fisgi Hannun mijinta suka gudu nan ma haka ya dinga kwakwulo kayan tsafi,sabo da Ameer duk irin wannan harkar ta malamai ya santa tunda suna zuwa da Hajja kafin Allah ya shiryeshi sannan Hajja tana sasu suna yin irin wannan abun wajen iyayensu mata,haka ma da Matar Daddy da kuma Matan Aayan duk irin wannan yasan su shi yasa yake da saurin gane irin wannan harkar,a leda ya kwaso komai ya fito dasu yabi ta baya duk ya warware layun sannan ya yayyaga komai da almakashi into pieces ya konesu tas,Sai ga su Abbi nan take sun dawo hayyacinsu,Hajja kawai suke nema da yaransu,Matar Abbi Mustapha kuwa taci duka hannun Abbi kamar jaka wai ta rabashi da Uwarsa,a wajen duk suka rubuta musu saki dai dai na musulunci Ameer da kansa yasa Securities sukayi waje dasu suna kuka tare da nadamar halayensu.

   Da su Abbi tare da Sauran Yara suka dunguma zuwa asibiti wurin Hajja da take fadawa su Khaleel ku taimakawa iyayenku da addua su dawo cikin hankalinsu su dawo da iyayenku mata yan albarka masu biyayya,ni na jawo da nace sai sun sake aure,banyi adalci ba ko a baro sai an turani naje har gida na basu hakuri da kaina zanyi bikonsu ko da kafar katako ce,Mufeeda tare da kannenta suma zan nemi gafararsu,Daddy ne ya shigo a birkice nan Hajja ta damki hannunsa tana bashi hakuri tana kuka ka yafe min ni na jawo nice....Hajja na yafe tuntuni ni dama ban rikeki ba kuma aike Mahaifiya ta ce ba komai ya wuce ki bari kiji sauki ko na fitar dake kasar waje?Hajja tana goge Hawaye tana Allah ya maka albarka Ka yafe min dana,na maka abubuwa suna haka sai ga Aayan da Mufee duk ta kara wani fari tayi kiba da kyau Sabo da cikin dake jikinta,Hajja ta shiga bawa Aayan Hakuri da Mufee,Aayan yace shi ya hakura ta ma daina bata bakinta,Su Abbi su Ukun tare da Ameer suka shugo suma nanfa Hajja bata boye ba tace da kanta ta lalata zumuncin yaranta,To Allah yasa su Abbi sunyi Nadama nan suka shiga Yiwa Hajja fada da nasiha sannan sukace duk itace ta cucesu Amma tun da Allah ya ganar dasu sun yafe suma a yafe musu,a asibitin aka shiga yafewa juna anyi wa'azi tare da Nasiha wa juna an tunatar sosai dama wasu Iyayen da kansu suke bata zumuncin yaransu suna raba kan yaransu,a karshe Hajja tace da kanta zata je bikon iyayen su Ameer babu wanda ya kai su Abbi Murna za a dawo musu da matayensu yan kirki

   Su Abbi sai gafarar Daddy suke ta faman roka sai lokacin ya fada musu ya auri Ammah kuma a satin nan zata tare a sabon gidansa daya tsantsara na fitar hankali,sun tayashi murna sosai har Abbi Mustapha na tsokanarsa an samu dangin kyau,Hajja kuwa Allura akayi mata anci sa'a ashe bata kara karyewa ba ta dan bugu dai a wajen Amma Dorin bai lalace ba,Aayan sai murna yakeyi shi da Mufee ashe Daddy ya auri Ammah basu sani ba,nan Mufeeda ta fita waje ta kira Meenat da Ma'eesha ta sanar musu Ammah ta auri Daddy ta labarta musu yanda Daddy ya basu labarin har yanda aka daura aure,Sunyi farin ciki Ammah ta samu me kula da ita,Meenat tace Sis kicewa Darling yataho gida haka na gaji da jiransa,Dariya Mufeeda tayi tace idan yazo me zai miki sarkin jaraba Bazan fada masa ba,dan Allah Mufeen Ammah ki fadawa Ameer dina na kira wayarsa a kashe,tana cikin haka sai ga Ameer ya fito, na mika masa waya nace ga Meenat tana magana,da Sauri ya karbi wayar yana murmushi yace Hello...tuba nake ranki ya dade kaina bisa wuya gani nan yanzu ki bani 15mnt Insha'allah ,Meenat sai Kukan shagwaba take masa ita yayi Sauri ya barta ita kadai.

     Yarima da Ma'eesha saura 1wk zasu wuce Us sannan suje saudiya za a kwashi Amarci,dama anan ma Yarima baya daga mata kafa ko kadan,itama ta zama irinsa mayyarsa ce bata zuwa ko ina kullum tana gidanta kusa da Mijinta Office ma kusan kullum da ita suke zuwa,yauma 1pm yana Office ya kasa aikata komai kawai matarsa yake so yaji kusa dashi suna ta faman waya Amma bata gamsar dashi gaba daya,sai kawai yasa Driver  ya dakko masa abarsa,ta gama shirya abincin da ake kai masa Office kenan tayi wanka tana shiri ya kirata a waya lallai tabi Driver suzo tare,zatayi Musu Yace dama ai ba sona kike ba yana narkewa kamar mace dole ta hakura ta shirya a mutunce tabi Driver tare da basket din Abincinta,tana zuwa yasa key a Office dinsa yace ya tashi daga aiki yau ko uban waye ya dawo gobe ko knocking kar ayi Masa suka shiga Soyewa da abar kaunarsa Ma'eesha itama ta gama gogewa da rashin kunya biye masa takeyi shi yasa yake kara sonta.

    Kwanan Hajja Hudu aka sallameta tana dan digishinta haka tasa Driver ya kaita gidajen matayen su Abbi na farko tare da Daddy suka Bada hakuri da kyar suka amince aka sake daura aure tare da tarewa gaba daya,Daddy ya Mayar da Su Abbi kan aikinsu na da,tare da siya musu motoci na alfarma, Su Ameer da Sauran Yara sai murna iyayensu sun dawo Alhmdllh,lokacin kuma bikin Khaleel da Mujaheed,Sajeeda da Haneefa ya matso tunda ansa rana tuni,Saura Meenal,Sabeer da Aliyu nan gaba,gidan yanzu ya Zama gidan masu tarbiya da hankali kowa ya nutsu yasan mene rayuwa ba wulakanta dan Adam ba komai,mutanen unguwar ma yabonsu sukeyi yanzu sosai ana zaman lfy da mutunci da makwafta ba irin da ba,Su Haneefa gayu ya dawo yaci uban na da Amma yanzu na mutunci akeyin shigar mota sai wacce suka ga dama.
    Yau Sati guda cif Sunday yaune kuma Ammah ta tattara nata kaf dama an shirya komai kamar wata budurwa,da wasu dattijai yan matasan iyaye kawayenta su Uku tun na tsohuwar unguwarsu tare da yan uwanta guda biyu sune suka kai Ammah dakin mijinta Daddy cikin lafiyayyun motoci guda kusan biyar,Ammah ba a ganeta sam Sabo da Su Mufeeda sun takura an kaita gidan kwalliya anyi mata,ga gyaran jiki ko ina kamshi fata na sheki gashi etc tasha tsumi iri iri abin ba a magana gata dama Ammah matashiyar Uwa me ji da kuruciya dai dai gwargwado tasha kyau an kaita duk an maida kowa gida lfy sai ita kadai a katafaren gidan sai yan aiki masu kaiwa da kawowa ko ina kamshi na tashi.
   8pm Daddy ya shigo Bedroom din Ammah tana gefen Bed suna waya da Inna,tana ganinsa tace zan kiraki gobe Insha'allah ta kashe wayar, ta kalli Daddy dauke da lafiyayyen Murmushi yasha farar Shadda sai yau ta hango tsan tsan kuruciyarsa shima hakan dan sai yau ya tabbatar Ammah ta hadu ta ko ina,Gefenta ya zauna da ita suna shakar kamshin juna jikinsa na gugar nata,kunya ta lullube Ammah ta sunkuyar da kai kasa,Daddy irin Aayan ne sai zumudi yakeyi Da kyar ma ya Umarceta sukayi Sallar nafeela suka ci kayan makulashe Ammah da kyar ta karba Daddy yana bata a baki,Suna gamawa suka sake brush tare da wanka kowannensu yayi shirin Bacci suka haura Saman Bed,Ammah kunya take ji ta kasa sakin jiki,yana janta da Hira Amma da kyar take bashi amsa,Daddy cike da kulawa tare da tausasa murya yace Kin san nifa Bature ne kin sani asalin Bature ne mu ba haka muke rayuwarmu ba,ban saba da hakan ba,Mun zama daya ai ke matatace mene ne abin jin kunyata matsalar Hausawa kunya gaban me gida,am serious ni bana son kunyar nan ki tsaya mu nunawa juna so tare da kulawa shi muke bukata. murmushi tayi tare da juyowa suna facing juna tace na gane me kake nufi ta furta tana me rufe fuska da tafin hannunta,wanne suna kike so na fada miki? Ko wanne ma cewar Ammah,tunani ya shiga yace Honey?dariya tayi tace ai zanji kunyar yarana,yace to Maman Aayan? Taji dadi irin karar da Daddy yayi mata baice ta Mufeeda ko Meenat ba sai dansa ya nuna dansa nata ne nan take Ammah tace kai Kuma Daddyn Mufeeda ko? farin ciki ya lullube Daddy nan labari ya canja Salo suka koma soyewa suka lula duniyar ma'aurata abinsu.

    5pm Mufeeda tana zaune ta baje kasa saman Center carpet na gaske Madara da sugar ta hada take faman lasa tana jin dadi Aayan yana gefenta sai cike takaddu yakeyi,Ba tare da ya kalleta ba yace Queen yau kinsha maganinki kuwa na rana wanda Doctor ya baki kafin mu koma Next wk?fuska na hade ina shagwaba tare da tirje tirje ina kuka a hankali nace ni na tsani magani ka sani bana sha sai kana takurawa sai na sha lafiyata kalau,Queen ki taimaka min Dan Allah kisha ya kike so nayi da raina idan baki da koshin lfy kuma kin san akwai Baby na a cikinki,ni dai Bazan sha ba na furta tare da fashewa da kuka,Da kansa ya tashi ya dakko maganin a leda da ruwa ya ballo kala wurin Uku yanda akace a sha ya mika min da ruwa dan Allah kisha My Queen kinji ya shiga lallashina Amma naki sha,yace zan siya miki mota fa sabuwa dal me tsadar gaske,sai lokacin na kalleshi da Hawayena nace da gaske?Yace kin san ai idan nace bana canjawa,Kasuwancinmu zamu dawo dashi idan nasha magani zaka siya min wani abu ko ka bani kudin?Aayan ya dinga dariya  yace lallai me hali baya fasa Halinsa ashe har yau da ragowa,Ni ka amsa min kawai pls,yace ae to min dawo da kasuwancinmu kisha magani na baki kudi idan kin sha wannan mota ce guda gobe kudi jibi wani abu haka har ki sauka lfy,Murna ta kamani na karbe na shanye magani tas sannan ya ci gaba da aikinsa,yana farawa nace ni tausa nake so dole ya ajiye aikin ya shiga yi min tausa me dadi ina kwance saman Sofa.

    Ma'eesha yau jirginsu ya lula zuwa Us a jirgi ma suna manne da juna ana kissing din juna,Ameer yau ya gaji a Office sosai Meenat kuma ta koma schl University dinta tana zuwa tana tashi daga schl ta wuce Office wurin Ameer tunda Driver ya turo mata wai su biyo su daukeshi su koma gida tare ya gaji,amma tunda yaga Meenat bata kansa yake ba ta Meenat yakeyi wai ta gaji sai lallaba abarsa yakeyi,Suna cikin mota ya kwantar da ita a jikinsa bacci ya sace ta har suka Isa gida tana bacci,Sai daukanta yayi kamar Jaririya suka shiga ciki kana ya kwantar da ita Saman Bed shi kuma ya shiga toilet da niyyar yin wanka,
  Ya kusa gama wankan yaji Kukan Meenat da karfi karfi ya firgita da Sauri ya ya daura Towel ya fito,baki ya bude tare da rafka Salati.



    


AsmaBaffa
[3/4, 11:23 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

  KASUWANCI NA





        141-150





Official






By
AsmaBaffa






      

     a kasa ya hango Meenat Dafe da Mara jini na bin kafafunta,mamaki yakeyi wata daya da sati Uku da bikinsu Meenat tana da shigar ciki Ashe da Alama bai dade a jikinta ba ya zube,da Sauri ya kamata ya kaita toilet tare da yi mata wanka  still jinin na zuba da sauri ya bata pad, Meenat tana kuka tace jini na zai kare zan mutu,duk Ameer ya rude da sauri yasa boxers tare da zura jallabiya a jikinsa ya koma toilet inda Meenat ke zaune Jini na fita a jikinta sai kara karfi ma yakeyi kaya ya sa mata ya dan shirya ta sama sama yanda jinin bazai batata da yawa ba sabo da dankwalinta na atamfa ya linka ya mata kunzugu dashi haka,mota ya sata ya zauna gefenta tana cikin jikinsa sai kuka takeyi tana Salati zata mutu,Ameer yana aikin lallashi Driver na tuki da gaggawa suka isa Katafaren Private Hospital akayi ciki da Meenat wacce ke jin mararta kamar zata balle,Emergency aka shiga da ita,nan likitoci suka rufa a kanta,Ameer yana    gefe daga waje an hanashi shiga Kawai zaga wajen yakeyi hawaye ya zubo masa na tsoro karfa Meenat dinsa ko ta mutu,Wurin 3hrs Nurse ta fito tayiwa Ameer magana shiga tana nemanka,Ameer da sauri ya shiga har an canjawa Meenat daki ta warke kamar ba ita ba a zaune ma ya sameta gefen Bed,Ameer yaje da niyyar rungumeta amma taki yarda wai batayi wanka ba,likita ne ya shugo ya musu bayani ciki ne ya shiga baifi 1mnth ba ya zube kuma tunda har wankin ciki anyiwa Meenat,Magunguna ya rubuta musu har na Karin jini da shawarwari ya basu sannan ya rubuta musu Sallama,Ameer daukan Meenat yayi kamar yar Baby ya kaita mota Driver ya jasu suka tafi gida ba tare da kowa yasan me ya faru ba tunda ko a waya Ameer yaki sanarwa kowa.

    Suna komawa gida shi ya gyara toilet din da kansa sannan ya hadawa Meenat ruwan Zafi ya gasa ta sosai sannan tayi wanka,tana fitowa ya shirya mata jikinta har Makeup shi yayi mata kana ya bata abinci taci tasha magunguna ta kwanta bacci ya kwashe ta,shi kuma ya kara wanke toilet tare da gyara Bedroom din komai yana kamshi shima yayi wanka ya shirya kayan Meenat daya zuba a washing machine su ya kwaso ya shanya su tas sannan ya wanke nasa Suma a washing Machine ya shanya yana danna system gefen Meenat dake bacci kayan suka bushe ya goge su ya adana su dama Ameer akwai tsafta bai son kazanta.
   Ammah ya kira a waya ya sanar mata Meenat tayi bari amma ta warke ba matsala,ya sanarwa Ummansa,ya kira Mufeeda lokacin ina jikin Aayan dina yana shafa dan cikina da yanzu ya turo ana iya jin tudunsa,Ameer yace Anty Mufee Meenat ce tayi Bari yau dazu muka dawo daga asibiti amma ta warke lfy take, cike da tsoro nace yaushe zatayi wani cikin da har zai zube 2mnths fa da bikin,Ameer yace ai Doctor yace watansa daya ya fita bafa wani abu da aka gani kawai Blood ne,Mufee tace to tunda da sauki Alhmdllh zamuzo da dare,Aayan ne yace me ya Samu Meenat din?bari tayi wai na cikin 1mth,Murmushi Aayan yayi yace shege Ameer ai dole ma ya barar da cikin da kansa baya saurarawa yarinyar nan ga ciki dan karami an dameshi da jaraba, na masa hararar wasa tare da cewa kai ai kafi Ameer zaka ce Ameer kai baka ganin me kakeyi,Aayan yace Saura dan duniya Yarima,wasa nakeyi da Kirjinsa ina zaga yatsana a kai,yana shafa min dan cikina.

   Maeesha ma an sanar mata da barin Meenat tayi mamaki,da dare duk munje har Ammah Daddy da kansa ya kaita suka duba Meenat,Ammah ta sanarwa Ameer yanda zai kula da Meenat har ta warware sosai,Ni kuwa kawai dariya ma Meenat take bani har yanga takeyi ita ta samu ciki har da bari ga shagwaba da take uban zubawa musamman idan taga Ameer a wajen shike lallaba ta,Muna zaune saiga su Hajja dasu Hanifa kusan gaba daya gidan sunzo Duba Meenat,Daga baya su Abbi suka zo da matayensu harda Umman Ameer sai da ta kawowa Meenat Soyayyun Zabbi cikin wani Bowl.

     Bayan mun watse Ameer ya matsa jikin Meenat dinsa yana murmushi tare da zuba mata kallon so kana yace Meenat dina ni kadai sai lokacin ta kalleshi itama dauke da shauki a fuskarta ga wani son Ameer dake Karuwa mata a ranta ko dan yana da kyau ne oho ta kasa ganewa, bakinsa ya shigar cikin nata ya shiga tsotsa,Meenat ta lumshe ido itama tana mayar masa da martani sun dauki tsawon lokaci a haka Meenat ta janye jikinta taga Ameer din nata duk ya hargitse kuma baza ta iya bashi abinda yake so ba bata da lfy,Idonsa jajir ya kalleta da kyar ta iya magana murya a dishe yace pls Baby ba dai hanani zakiyi ba? Hannayensa ta riko da hannayenta a nutse cike da Ladabi tace Honey am so sorry yau kaima kasan baza ka samu ba ko ba komai Yau nayi Bari fa ai yakamata ko ba komai ka bani hutu ko na 1mnth ne tunda shima ai kamar Haihuwa ne yama fi haihuwa wahala ance,Marairaicewa yayi kamar zaiyi kuka yace Dan Allah kin ga fa ba jini kike ba har sallah kinyi dazu,kamar fa haihuwa ce Prince,Ni dai ban yarda ba yana shagwaba kamar jariri,Meenat tace yanzu ni danya ce fa?hakan nafi so ai danyar sharaf,dariya tayi kawai tace kama daina Sa Rai ka bari zan baka labs dina thts all,Ameer yace ni dai ba haka naso ba Amma ya zanyi dake Amma ki min alkawari yaushe zaki bani gobe? 1mnth nace fa,Ameer da kalar tausayi yace dama ance Mata Bedding dinma sai sunga dama zasu baka,kasa kasa Meenat ke dariyar mitar Ameer,mikewa tayi ta barshi ta nufi Sama,Kamar Ummansa haka ya bita a baya kamar jela yana roko Harda komawa bara irin ta almajirai Yara yana Iya... ko dan kanzo...Almajiri bara iya..,Iya ni ban samu ba iya...Meenat tana dariya ta shige Bedroom Amma Ameer bai daina ba Sai ma cewa yayi Iya ni ban samu ba...ko ni Mijinki ki san mini Iya....Meenat tana dariya tace Allah ka daina ce min Iya kamar wata tsohuwa,to kice zaki bani yau ko gobe sai na daina shuru ta masa yace zanci gaba Wahidin Iya....da Sauri Meenat tace gobe  ka kawo Kwanonka dan anace,Murmushin dake kara masa kyau ya saki ba tare da ya shirya ba,Dan sajen nan tare da gemu firit suka kara kawata fuskarsa, Dimple dinsa ya loba,Meenat ta saki baki tana kallon haduwa kamar tayi yawa da Aayan kamar Babansu daya,jikinta ne ya mutu Sabo da ta dade tana kallon Ameer musamman da taga ya tube daga shi sai Boxers tana son Surar Ameer matuka,a hankali ta mike ta Isa gabansa sosai suna dan gogar juna kadan a hankali ta zagayo da hannayenta ta cikinsa ta rungumeshi a jikinta sosai,suna kallon juna kowannensu da salon iya kallonsa da suke Aikawa juna,a nutse tace ina Sonka da yawa Mujina,Kara matseta yayi a jikinsa yana rada mata wasu zafafan dalasaman so a kunnenta karshe yace muje muyi wanka muyi bacci ko Sweet Princess? Kai kawai ta iya daga masa ya gama Tafiya da imaninta.

     Ma'eesha da Yarima cikin Sweeming Pool na alfarma suna wanka a katafaren gidan su Yarima dake Us,idan kunga Ma'eesha baza ku gane ta ba,kamar baturiya daga ita sai Swimming Dress Kalar Bra da pant,Yarima dan short ne a jikinsa a Cikin Pool din suke shagalinsu kawai,Yana ciki ta shiga saman Bayansa ta makale suna wankansu tare sai dariya sukeyi cike da so,gabansa ya dawo da ita Sabo da Ma'eesha bata iya ruwa ba koya mata yakeyi a tsorace take duk tabi ta makalkaleshi, peace kibi a hankali duk kin wani Tsorata,ni kasan ban iya bafa ta kara manne masa,Kanta ya dago cike da nutsuwa ya tura harshensa cikin bakinta ya shiga tsotsa,Maeesha ta kara matseshi a jikinta tare da maida masa da martani,kasa ta zame a hankali ta nutse a Cikin ruwa ko second bata yi ba ta dago kamar ranta zai fita wai ita ta koyi Swimming,tace Baby kalla na fara iyawa kamar kifi ta kwanta saman ruwa sai ko tayi kasa kamar an jefa dutse ta dago da Sauri tana facal facal da ruwa ita bata yarda ba ta iya ruwa,Yarima dariya yake ya riko ta tare da kunna uban nutso da ita suna kasan ya riketa ya shiga murza Boobs dinta,dago da ita saman ruwa yayi Ma'eesha ta fara tari zatayi kuka za a kasheta a ruwa wai,Sun dade suna murza juna a Cikin ruwan nan sannan suka fita tare da kwanciya saman kujerun hutu suna kora Juice da kayan ciye ciye.

   Bayan 3wks Dan cikina ya girma ba laifi har ana iya hangoshi kadan muna mota tare da Aayan Driver na janmu yau gidan Ammah zamuje mu gaishesu,sallama mukayi a palon Ammah na zaune gefen Daddy tana yanke masa farcensa suna hirarsu ta masoya,Har kasa muka gaida su suka amsa da fara'a na koma jikin Ammah na makale Aayan yana hararata,shima ya koma kusa da Daddy suna maganganunsu na aiki,Daddy ne yace Aayan yaushe zaku tafi ne? Sai ta Haihu Bazan yarda ta shiga jirgi da dan cikin nan ba ya zube,Kunya ce ta lullubeni kamar na nutse,shi kuwa ko a jikinsa,Daddy ne ya tabe baki tare da cewa shashasha to ai inda zakuje suke da Doctors manya ka kaita kawai taga dangin kakanka sai ku zauna a can idan Allah ya sauketa lfy sai ku dawo,Ni Daddy ya barmu anan muje kawai mu dawo,Ammah tace to yanda kuka ga dama mu cikin satin gaba zamu tafi Saudiya da Us Insha'allah,farin ciki ya mamayeni Ammah fa an waye an san gari, addua mukayi musu mun dade har dare muna gidan tare muka shiga kitchen da Ammah,Sai bayan Aayan da Daddy sun dawo daga Sallar Isha mun ci abinci muka bar gidan abinmu,Ammah ta bani wasu tarkacen na mata da turaruka na kwanciya.
   Kullum muna waya dasu Ma'eesha yayin da Bikin su Hanifa ke matsowa ana ta shirye shirye sosai.
  Ammah da Daddy su zasuyo order din kayan lefen mazan da Furniture na mata kaf shi yasa ma zasu bar kasar,Sameera yar Daba anyi bikinta itama da gwaninta suna can suna shan Amarci da katuwar muryarta kamar ta Maza.

     Hajja zaune take tayi tagumi tana Jan carbi sai Istingifari takeyi bata gajiya da Nadamar Halinta ga ciwon kafa ya hanata sakat duk kayan dadi an hanata ci a Hospital ba cin jan nama,kaji ma sai dafaffiya ba kullum ba,Yanda take mutunci da Ammah ba a magana kamar zata goyata haka kaf jikokinta ta kara rikesu musamman Aayan sai yanzu take nuna masa so tasan Muhimmancinsa,Matayen su Abbi girmamata dama can basa gajiya bare yanzu,itama ta rikesu da mutunci,Sai yanzu take so ta gyara zumuncin tana kokarin hada kan su Abbi da Daddy Amma sai dai ayi Amma basu shaku ba,ta rigada ta raba,sai dai komai suyi sama sama duk da cewar ba wata matsala Amma abinda take nema bazai samu ba a yanzu.
    Sabeer,Aliyu da Meenal ma sun gama University dinsu yanzu saura Yara yan Secondary da Primary kawai.

     Ameer ne ya shigo a gajiye yau ya dade a Office yasha wahala,lokacin Meenat tasan lokacinsa yayi na dawowa wanka ta dauka Cikin kana nan kaya Wando Short Jean blue ko Mazaunai da kadan ya rufe mata su da yar riga karama ko cibi bata rufe ba,Ameer tunda yayi tozali da ita hankalinsa ya tashi,kamshi kawai ke tashi ta ko ina a gidan sabo da yasha gyara ga matar gidan ta cakare,cikin salon tafiyarta ta jan hankali ta karasa wajensa a hankali kafin ma tace ko a ya fisgota jikinsa ya kankame abarsa yana sakin ajiyar zuciya,nan take ya birkice mata kissing dinsa ta fara cikin kwarewa Meenat ba sanya fa,Daukanta yayi zuwa Bedroom da kyar Meenat ta kwaci kanta wajen lallabashi ya bari sai yayi wanka yaci abinci sai ma yayi ko me yake so,yaki yarda Meenat tace haba mana dan Allah so kake yunwa ta kama min kai?Ka rufa min asiri kaci first abun nan ba guduwa zaiyi ba yana jiranka ai naka ne,ta dade tana lallashinsa sannan yace sai dai ita ta masa wankan idan yaci abincin,Abincin kuwa ya fara ci, da kanta ta ciyar dashi ya koshi sannan ta kaishi toilet tare da taimaka masa yayi wanka da Brush,mai ta shiga murza masa kafin a gama Ameer ya kasa jurewa ya shiga wani Salon na daban.

    Hankali kwance muke shan Amarcinmu,Kwanaki suna shudewa Ma'eesha da Yarima sun dawo daga turai da dan karamin cikinta na wata 3, ciki na ya shiga 7mths muka sha bikin su Khaleel da kyawawan Amarensu Aayan ne ya bawa Khaleel da Mujaheed gidaje dankarere ,Haneefa da Sajeeda suma da angwayensu ya musu kayan daki na fita kunya,saura bikin Sabeer da Aliyu Sabeer Meenal zai aura,auren zumunci za ayi musu suna son junansu,Aliyu kuma yar kanwar mamansu zai aura an Sa bikinsu cikina yana 9mnths dai dai ba wani girman ciki gareni ba,kullum addua mukeyi tare da Aayan Allah ya saukeni lfy, ba sosai yake fita ya barni ba Sabo da cikin ya girma ko Haihuwa zata taso min,Ammah ta turo min Dattijuwa guda bayan yan aikin da suke gidan zata dinga kula dani Sabo da Haihuwa, Baba nake cewa da ita Sabo da bata girmanta,da kyar na lallaba Aayan kan yaje Office tunda Haihuwar taki zuwa,cikin rashin Sa'a ya samu Tafiya ta kamashi zuwa Turkysh wani Meeting kan harkar Business dinsu,a gurguje ya shirya na hada masa kaya yace 1wk zaiyi ya dawo Sabo da cikin da nake dauke dashi.
   Na damu matuka ban so tafiyar tasa ba Amma sai ban nuna a fili ba na boye nasan idan yasan ban so zai fasa Tafiya kawai,Nace Zan bika airport yace a'a yamma tayi sosai ga Babyna zai sha wahala ki hakura kinji,Hawaye ne ya shiga sintiri a fuskata gani nakeyi kafin ya dawo ko na mutu ma Maybe,Fuskata ya leka Oh...Common Sweetheart mene abin kuka zaki Sa na fasa tafiyar nan ko me zai faru ya faru,Da Sauri na shanye Kukana tare da share hawayena ina murmushin Dole,Nasha Lallashi kafin ya yarda zaije da kyar muka rabu da juna ya tafi cikin zugar motocinsa,suna zuwa jirgi ya kusa tashi kawai yaje da Sauri ya wuce ciki,ba a dade ba jirginsu ya daga.

    Ina nan ina kewar Mijina,ranar kuma na fara ciwon Mara sama sama,yana sauka ya kirani a waya yaje lfy,cikin dare ma mun dade muna waya dashi,tunda Aayan ya tafi kullum sai munyi waya har ya cika 4days a can duk da haka ina dan jin Ciwon marar sama sama,yau tun asuba bayan nayi Sallah kafata ta rike na kasa tashi,Baba na shiga kwalawa kira iya karfina ta fado dakin da gudu tana lfy Hajiya? dake ta manyanta sai ta gano Haihuwa ce nan ta fita ta sanarwa Driver,Ita da Abu me aiki suka kamani zuwa mota Driver ya kaimu Private Hospital din da muke zuwa da Aayan,Sunce na kira Aayan nace a kyaleshi kar hankalinsa ya tashi,ciwo sai gaba yake yi Baba tana a fadawa yan uwanki da mijinki sai nace a'a bana son hankalin Mijina ya tashi,ciwo yana ci gaba duk na fita a hayyacina ban ma san me nakeyi ba nace a kirashi din Hankalinsa yayi ta tashi ina ruwana,ban dade ba Allah ya taimakeni na Haifo dana katon gaske Namiji kyakyawa, bayan an gyarani har wanka Baba me aiki tayi min na shirya,shima Jariri an shiryashi tsab cikin kayan sanyi farare masu tsada da kyau, Ameer na kira nace kar ya fadawa Aayan komai,Ameer na fadawa Yazo asibiti na haihu,15mnt sai gasu Shi da Meenat,addua da komai shi yayiwa jaririn,nima nayi masa Meenat ce ta koma gida ta shiryo min girki iri iri ta kawo lokacin anyi min Allurai ina bacci,Sai yamma lis na tashi naji karfi sosai a jikina ga yunwa na ci na,Abinci naci na koshi kamar ciki na zai fashe,Doctor tazo ta bamu takardar Sallama muka tafi gida gaba daya tare dasu Meenat,gidana muka je na kwaso kayana akwati guda dana jaririn da muka tara har gadonsa muka tafi gidan Ammah baki daya, sai ganinmu tayi da jariri,Murna takeyi kamar me,Daddy yana dakinsa ta kirashi ya dauki Jariri shima sai murna ga yaro kyakyawa kamarsa daya da Aayan,Nan Ammah ta dinga min fada ban fadawa mutane ba,har Aayan ta kirashi da kanta tana sanar masa yace Ammah shi yasa nayi ta kiranta tun jiya bata shiga Ashe bata da lfy bata fada min ba,Murna Aayan yace shi tahowa gida zaiyi ya fasa kaiwa sati guda,da kyar Ammah ta bashi baki ya hakura,su Hajja,Abbi da matayensu duk sai gasu,Maeesha me dan karamin ciki ita da Yarima sun zo suma,Su Hanifa Amare tare dasu Khaleel duk sun cika gidan Ammah ana ta hira ana Jin dadi.
  Bamu muka samu Saukin mutane ba sai dare suka tafi sannan Ammah ta hada min ruwa na sakeyin wanka da kanta ta gasa min jikina shima Jariri anyi masa wankan an shiryashi cikin kayan baccinsa yana dan bed dinsa yana bacci,lotion na shafa me kamshi na shirya nima cikin kayan baccina lokacin masu aiki sun kara Gyara ko ina,zan kwanta Ammah tazo da abinci lafiyayyu tasa dole sai da naci da yawa nayi Brush sannan na kwanta,har bacci ya fara daukana Ammah ta shigo tana fada wai Mufeeda baki da hankali ne ko me kin kashe wayarki mijinki yana ta kira bata shiga kuma ke baki kirashi ba ko laifi yayi miki ko wani abu ne ya faru?bafa na son irin wannan ban son neman rigima,yanzu baki tambayeshi ba kin kwaso jiki kin dawo waje na,idan baya so fa? Da bamu  dawo daga kasar waje ba wajen wa zaki?ai dole ki zauna a gidanki,bana son ki zubar min da mutunci a gaban suruki ki kiyayeni,kiyi Hakuri Ammah mantawa nayi yanzu zan kirashi,tsaki taja ta fice daga dakin,Da sauri na jawo wayata na kunna kana na shiga kiran Aayan na kira yakai sau biyar sannan ya daga Cike da bacin rai yace ina jinki ya akayi?

    Naji haushin maganar amma ai nice da laifi sai nace barka da dare Yanlabai Allah ya taimaki ranka ya Dade Baban Baby,tuba nake nayi laifi Mijina uban dana a yafe min,duk wani fushi da Aayan keyi nan adtake ya yaye baki daya sai ma farin ciki da ya shiga yi na gama kashe masa jiki,yace ba wani kinyi laifi zaki min dadin Baki dama ai haka kike min kullum sai ki dinga cutata dan kin San ina da hakuri,Dariyar jin dadi nayi nace Hakurin da ka saba yi dani shi zakayi Dad din Baby, Hmm to ya jikin?dana ya fito lfy ko?cike da shagwaba nace da sauki bayan ya bani wahala kamar zan mutu ai ni fushi nakeyi dashi,Aayan yace dan Allah? Nace sosai ma dan kawai baka ji bane aka ce sai nayi nishi na daddage nayi daya yaron nan dake bashi da kunya yaki tahowa sai ya makale kafada yace bazai fito ba wai,Aayan ya sheke da dariya yace a ina kika ji sanda ya makale kafadar? Ina dariya nace a cikin cikina naji wani bangare yayi min bake bake wani kababa a nan na gano me yayi ai ko nace zanyi maganinsa na kara yi da karfin tsiya yaji na shakeshi da yawa yace zan dan fito shine ya taho kadan,Ina yin na hudu yaji wuya ba dadi sai ya fito yana tsala uban ihu,Dariya Aayan yayi tare da cewa to Alhmdllh tunda kin sauka lfy ai ba matsala,Duk abinda kuke so Na fadawa Ammah baki da prob nima jibi zan dawo Insha'allah,Ina Baby Boy dina da wa yake kama?nace gashi baccinsa yakeyi ma ko Na mintsineshi kaji Kukansa,da sauri yace a'a ko da wasa Karki fara,Dariya nayi nace kamarku daya baka ganshi ba wlh na iya haihuwa zukekene yan mata zasu dinga rubibinsa idan ya girma,Allah yasa ya samo min suruka ta gari kyakyawa kaga ya gaji Ubansa,dariya Aayan yakeyi sosai yanzu daga haihuwa har kin fara zancen Suruka,nace ae idan Meenat ta haihu nasan kyakyawa zata haifo ko Ma'eesha sai a bashi matarsa,Aayan yace baki isa ba babu me yiwa dana auren dole, sai ya Zaba ya darje, haka muka dinga musu,kaji yana motsi,Ko Nono yake son sha? Ya tambaya, hannu nasa na daukeshi ya fara kuka Aayan yana ji ta waya sai murna yakeyi baki yaki rufuwa nace bari na kara masa waya a kunne kayi masa magana,Jariri na kuka ni kuwa na manna masa waya a kunne Aayan kuma ta waya yana Hello My Son,Dad dinka ne,Abbanka ne Be quite yaro bai San me akeyi ba,na shiga bashi Nono yayi shuru kuwa muna waya da Aayan.

   Yace muyi video call haka na kunna light na kirashi ta Skype muka fara Video call yana ganinmu ni da jariri,muna ta hira cikin Jin dadi mun dade sannan muka rabu da juna muka fara baccinmu cikin nishadi,washe gari ma haka gidan ya cika da yan Uwa da abokan arziki,kamar ba ni na haihu ba haka nake shiga cikinsu muna hira  ga waya Aayan ya Dameni da ita muntuna kadan zai kira yaji ya muke muna haka har na kwashe Kwana hudu da Haihuwa tunanina ma sai bayan suna Aayan zai dawo tunda naga an kusa, 8pm Ammah tayiwa Jariri wanka tare da shiryashi tsab cikin kayansa masu kauri da kyau nima na bashi Nono ya koshi yana yin Bacci na kwantar dashi saman Bed dinsa nima nayi wanka nayi shirin bacci kamshi ne kawai muke zubawa ni da jaririn,Sallamar Aayan naji ya turo kofar bayansa kuma mata masu aiki ne suka shigo da Akwatuna har uku suka fita,wani sanyin dadi ya kamani naga Rabin raina ya dawo yanzu zan na ganin abina a kusa,Cike da murna ina zaune tsakiyar Saman bed nace Oyoyo ina murmushi ga wani Mashahurin kyau dana kara sabo da samun kulawa,Kallona yakeyi tun daga sama har kasa kamar ba nice na Haihu ba sai ma kyau da na kara,Saman Bed din ya hauro ya bani zaffafar Runguma da Kiss sannan ya Koma gadon Jariri dake bacci ya daukeshi yana zuba masa adduoi,Sai da ya gaji sannan Ya kwantar dashi daga bisani ya shiga wanka,Ammah ce ta kirani a waya wai naje kitchen na dauko masa Abinci,Mamaki nayi wai Ammah Ashe tasan Aayan zai dawo shine ba wanda ya fada min har ta masa Abinci da kanta,Kitchen na shiga abinci na Alfarma na gargajiya dana zamani Ammah ta gama shiryawa na dakko masa komai da kayan sha masu sanyi, bayan yayi shirin bacci ya zauna dirshan yaci yasha,yace shine baza ki bani a baki ba?nace na sani ko zakayi kyankyami na kasan wasu kyankyamin matarsu sukeyi idan ta haihu,Fuska ya bata ke ni zaki bata min rai ke zanyi kyankyami?kin Zama jinina fa bana son irin maganganu nan ko ni Bahaushe ne? Yi hakuri na daina,Brush yayi yasha Ruwa sannan ya kashe Light ya kwanta gefe na,Nace Ammah fa zatayi fada,wa yace ki dawo nan? Kin fada min zaki dawo ko kin nemi Izinina? Kince nan da can dayane to mene ko dan kin haihu sai akace miki kar na kwanta Bed daya da matarsa? a'a amma ai ni dai Allah tsoro nake ji,shuru yayi min da kaina naga kamar baiji dadin maganar ba sai na juya na rungumeshi kamar jira yake ya makalkaleni a jikinsa muka Sha baccinmu.

    Kwanci tashi yau ranar suna Ammah ba taron Suna Aayan dan Ahlul sunna ne ba  a taron Suna yace a masallaci yaron yaci Sunan Abbanmu Abubakar Saddiq Aayan yayi min kara naji dadi,haka Ammah dasu Meenat har godiya muka yi masa,Fhadeel muke ce masa.

    Bayan 1mnth Aayan ya kaini Hospital aka bamu shawara na family planning shi baya son Haihuwa kamar tattabara duk mace ta ragargaje ta fita daga hayyacinta sabo da kwanika a samu ciki kafin a yaye daya ya Kamu da cuta ga na ciki ba a da tabbas zaizo da rai,Da kyar ya barni muka zaga dangi yan Uwa da abokan arziki munje har Maiduguri da Kauyen su Ammah,gidajen frnds duk munyi Zumunci tare dasu Meenat.

    Gidanmu gaba daya ya canja komai na gidan da kyar ake ganewa ya kara tsarashi,Direct mukayi Sallama da kowa muka dage zuwa Us daga can zamuje aikin Hajji mu kuma zaga wasu kasashen tare da jaririnmu Fadeel.
  Ma'eesha ciki yana ta girma ya shiga wata Bakwai,Yarima da Ummansa suna ji da ita kusan ma a gidan su Yarima ta tare gaba daya tare dashi suna soyewa watarana Umman ta koresu idan suka dameta,Abban Yarima kuwa Bai cika Zama a kasar ba sai lokaci lokaci yake zuwa ko matarsa ta bishi can, yanda Yarima ke Lallaba Ma'eesha har yayi yawa ta gama sangarcewa dake ya nemo mata Wata Private University tana karatu kusan tare suke karatun ma har ta gama level 1 idan sun dawo Hutu zata shiga level 2,Yayin da Meenat ta gama level 2 zata shiga 3,ni kuwa ina Zero level sai mun dawo Aayan zai kaini wacce yaga dama komai a karatu jaraba nice a karshen baya ina takaicin wannan abu amma haka Allah ya tsara ya zanyi.

      Meenat ce kwance saman Bed tayi shirin bacci Ameer yana kasa jikin Bed yasha shirin bacci sai rubuce rubuce yakeyi na Office kafin gobe sabo da Aayan ya bar masa aiki,juyi Meenat tayi ta kara juyi ta matsu yazo su kwanta,y ana jinta sauri yake ya gama yasan Halin Meenat yanzu zatayi zuciya da kyar zai lallasheta ta hakura,bai karasa ba ya hakura ya Mike tare da kwanciya a gefenta gani yayi har tayi baccin karya wai dan kar yace ta damu dashi,Shuru kowannensu yayi kawai shima yayi baccin karya kamar da gaske,Meenat taji shuru ko hannunta bai rike ba,fuskarsa ta leka ta shiga mamaki ganin yana bacci a fili tace bacci yayi a wannan situation din da ni Meenat kamata ina kusa dashi bai ji komai na feeling ba ya fara bacci,Kwanciya tayi a fili ta kuma cewa ko Hannu bai iya rike min ba ina kusa dashi wannan me ya faru ko ya daina sona ne?wayyo karfa ko wata ya hango Ameer yana jin Meenat tana surutunta dariya ta cika masa ciki,shuru tayi ta rufe ido ta bude taja dan tsaki sannan ta kara rufe ido itama,cikin nutsuwa da muryarsa me dadi taji yace ya akayi My love?  Na isa Hamshakiya tana kusa na kasa tabata a hankali ya sa hannunsa cikin nata ya juyo tare da hayewa samanta a hankali ya shiga matsawa da fuskarsa hancinsa yana Gogan nata ya hade bakinsu waje daya ya fara tsotsa kamar zai cinye bakin ya huta,hannayenta ya rike da hannayensa ya maida su saitin kanta ya bankareta kamar me shirin yi mata fyade Meenat dadi yana ratsata a hankali ta zare masa riga tana shafa shi ta ko ina musamman kirjinsa Nishi kawai sukeyi Sweet words na tashi daga bakunansu,Basu gama gigicewa ba sai da ya shiga Murza Albarkatun kirjinta yana shansu Meenat kamar wata me shirin hawa Bori Gogan kuwa ka rantse Aljanune bakake dashi masu Zafi suka motsa kusan raba dare sukayi suna jiyar da juna dadi kafin su sararawa Kansu basu ma San sanda bacci ya kwashe su ba.

   Cikin Ma'eesha ya shiga wata tara Haihuwa ko yau ko gobe,Wata ranar Juma'a ta fara Nakuda aka kaita asibiti kamar zata mutu Yarima ya dinga Kuka ana bashi hakuri yan Uwa da abokan arziki jiki yayi Sanyi asibiti ya cika ana tunanin da kyar Ma'eesha ma zata tashi,muna Can  Russia dama Saura 1wk mu dawo Nigeria Meenat ta fada min tana kuka,da sauri Aayan ya hada mana komai muka sauka a Nigeria,Asibiti muka wuce muna zuwa tana Haihuwa ta santalo Danta Namiji katon gaske kowa ya kalli jaririn yasan ansha wahala kafin a haifeshi,sai ga Ma'eesha ta farfado aka gyara ta da jiriri tare da canja musu daki,Yarima ya riga kowa shiga yana kuka idonsa ya koma red sai yaga Ma'eesha tangargar abinta,Munsha murna muka koma gidanmu mukayi baccin gajiya,gaskiya Aayan yana kashe min kudi a duniya ba abinda na nema na rasa,sutura kuwa ko matar shugaban kasa sai ta jinjina min, Fadeel ya girma yayi wayonsa gwanin sha'awa kamar dan Bature jajir dashi.

   Yarima bakinsu daya da abokinsa Aayan shima ba a bikin suna dan ma kar a damesu sai ya dauke Ma'eesha da Jaririn suka hau jirgi zuwa Cairo wai sun tafi hutawa suna can akayi yanka aka radawa yaro Suna Ashman,acan Cairo sukayi jegonsu yana kula da abarsa,basu dawo ba sai da suka kwashe 3mnths lokacin Meenat a fara laulayi sosai,cikinta wata hudu,Duk inda Ameer yayi tana tare dashi Har masallacin juma'a tare suke tafiya tayi sallah cikin mata ta jirashi a mota,Ko taki binsa sai ya matsa sun tafi tare wai kar ya barta ita daya a gida tana laulayi,Ammah tayi fadan har ta gaji,ni ko Aayan ya samomin private university a Abuja can zamu koma dashi gaba daya mu da kano sai dai muzo Hutu,Daddy yace bazai yuwu ba sai dai mu dinga zuwa akan lokaci baya so mu tafi mu zauna ba zumunci.

    Na fara lecture da wata biyar matan su Khaleel duk suna da ciki haka Su Hanifa ma an kusa Haihuwa, tuni anyi bikin Sabeer da Meenal,Aliyu da yar uwarsa shima, Meenat ta Haifo yarta mace kyakyawar gaske, Su Ameer har Dinner akayi hadaddiya a katafaren waje yan AsmaBaffa Fans club duk sunzo,Kasuwancina true fans duk gasu nan anci an Sha an cashe yarta taci Suna Fadeela.

     Bayan Sunan Meenat  muka koma Abuja ni da Aayan sai ga Kiran Ma'eesha wai Ammah ta samu ciki,Kunya ta kamani na saki Salati Aayan ya sameni na zuba tagumi.
   Meenat kuwa harda rawa Ammah zata haihu,Hajja ma taji labari sai murna takeyi,Ammah kunya takeji wai Yayanta na haihuwa itama haka,Daddy yafi kowa kamar zaiyi hauka Sabo da Murna ya rasa inda zai Sa kansa.




  Kwana biyu bana muku posting kuyi hakuri kawai gajiya nayi sam ban son Typing din shi yasa bana yi akan lokaci kun san Jiki da jini dan Adam ajizi ne sai Hakuri.








AsmaBaffa
[3/6, 10:54 AM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

   KASUWANCI NA



       151-160









Official





By
AsmaBaffa








           FINAL








        Daddy murna tasa ya rasa inda zai sa Ammah yace sai ta zabi abinda takeso a duniya yayi mata taki fada wai ita kunya,Hajja tunda taji cikin nan ta kara son Ammah kusan kullum sai tasa an kawota a mota ta duba lafiyar Ammah,h aka ni dasu Meenat ko yaushe muna hanya nice ma ban cika zuwa ba sabo da nayi nesa dasu ina Abuja,Aayan ya Kira Daddy a waya yace Congrat Dad, Daddy ya shiga dariya yana godewa Aayan da ya matsa lallai akan a auri Ammah gashi ya Zama alkhairi.

   Meenat yarta Fadeela tayi dan wayo kadan,Yarta ta shirya ta kawo mata ita gaskiya Fadeela tana da kyau ta hadu karshe,tsakanin ita da Fadeel dina ban san ma wa yafi wani kyau ba,Ameer ne ya fito cikin takunsa yasha wankan wani farin yard ba karamin kyau yayi ba,mikewa tsaye Meenat tayi tare da cewa Ina kuma zaka fita da yamma haka? Sarkin kishi ba inda zanje Aayan ne ya aikeni gidanmu yanzu zan dawo,to muje tare mana ba musu yace shi yasa kika shirya kema kenan dakko mayafin mu tafi,Ba musu ta dakko harda jaka da takalminta me tsini ta bishi  suka tafi shi ya dauki Fadeela yana mata wasa,bayan sunje gidan suka ji Matar Mujaheed ta haifi mace,sunje sunyi barka suka wuce gidan Ma'eesha a can har dare suna gidan,sai 9pm suka dawo gidansu Meenat ta shirya Fadeela tare da lallabata wai tayi bacci lokacin Ameer ya fito daure da dan Towel fari a kugunsa yana goge jikinsa da wani karami gefen Bed jikin Meenat dinsa ya zauna wacce ke aikin jijjiga yarta,ki bata tasha Milk dinta mana sai ki ta wani mata wayo a haka yarinyar nan bata wani koshi da Nono kike hanata,ko na baka ita ka bata naka ne maybe zata fi koshi,Murmushi yayi tare da cewa ba sai kin fada min baka ba,kuma kema kin san da ina dashi har amai sai ta dinga yi yanda zan na cika mata ciki,ga Fadeel nan Har ya fita kiba,ai dama to ya girmeta yaro zaka ce wani abu,Nine yaron? Kalli yata katuwa,Fadeela taki bacci kawai ta zuge zip na rigarta ta fara bata Nono tana sha,Ameer har ya tashi ya nufi Wardrop ya dawo ya zauna shi burinsa yaga ana bawa jariri nono yana sha abin birgeshi yakeyi,Sai kallonsu yakeyi kamar maye,A hankali shima ya kwanta saman cinyarta ba shiri ta matsar da jaririyarta shima ya kwanta kadan,tana taje mata gashinta bata san me yake ba babu zato taji shima yana zuke daya Breast din kamar maye,da Sauri ta gama bata ta gyara rigarta tasan Halin Ameer sai ma ya shanye du ya zuke mata nutrients dinta.

     Bayan wata Uku cikin Ammah ya girma sosai zama da kyar Sabo da cikin yana bata wahala, ina gidan Ammah Aayan yazo daukana muna cikin mota ya bani shawara Honey tunda naga kinyi dan nisa a karatun kuma gashi an kusa yaye Fadeel me zai hana a daina planning din kafin ki samu wani cikin kinga an yayeshi tuni,sai mu kara Haihuwa Allah shi ke rayawa Amma baza mu zauna ayi ta planning ba tunda bamu ke da kanmu ba ya kamata ace nima na tara Yara ko Uku ne sai ki huta da yawa,ko dan lafiyarki ma idan mace tana Haihuwa tafi lfy ko? Fuska na bata nace banfa gama karatu ba,ni gaskiya ko zan haihu sai na kara 3yrs sai na daina planning kaine fa kaki kaini schl da wuri yanzu kuma ga schl ga ciki ni Bazan iya ba,Baki ya bude Yanda yaga ina masa masifa daga kawo shawara yace Iyyeee lallai kinci abinci Mufeeda ke kike aurena ko ni? Kinga ina biye miki zaki rainani dama ance mata basu san kadan ba idan kana biye musu sai su fara rainaka suna takaka,Shawara fa na bayar baza ki fada min direct ba kema a shawarce zaki fada min sai a gane a dauki wanda ya fi dacewa yanzu ma Umarni kika bani sam ga abinda zakiyi ke kinje University ko?kuma ni zaki ma shouting kamar danki? Ransa ya baci sosai Amma zuciyata bata kawo komai ba sai ma cewa nayi Oho ni dai Bazan yi wani ciki yanzu ba,duk wahalar da na sha,kasan zafin haihuwa kuwa dole kace haka,a hasale yace Ok to zamuga me iko tunda kikace haka na fasa shawarar Haihuwa nake so kuma dole a daina Planning ai ni naga dama.
  Ni da jikina sanda zanyi ma ka sani ne,har muka karasa gida cacar baki mukeyi har ya shareni kowa ya fita daga motar a fusace,ko dakinsa banje ba nayi kwanciyata a dakina,shima haka Amma gaba daya tunaninsa nakeyi kuma nasan shine da gaskiya kawai neman fada ne irin nawa,Kowannenmu da kyar ya samu bacci ya daukeshi,ba abinda yafi damuna irin yanda ya daina cin abincina,ya daina kula ko kallo ban isheshi ba har muka kwashe 1wk a haka kullum sai nayi kuka na godewa Allah,yau nayi niyyar bashi hakuri naga ya sakko yana jan Trolley yasha kana nan kaya masu tsada da mugun kyau,ba karamin kyau yayi ba kamar a saceshi,sai dai da gani yana cikin damuwa,bai ko kalleni ba ya nufi wajen Fadeel dake kwance yana wasa yana wutsil wutsil sai dariya yakewa Aayan yaga Babansa,ina kallo ya daukeshi suka danyi wasa sannan ya kwantar dashi ya sa masa farar takarda a hannunsa ya rike kam sannan yaja akwatinsa ya tafi,gabana ya fadi sosai yana fita na karbe takardar da Sauri na bude an rubuta gabana yana faduwa nasan ko bai sakeni ba to sai ya ci min mutunci a ciki ga abinda na gani a rubuce:
        Na tafi Saudiya Nextwk zan dawo Insha'allah Bazan dawo nan ba Abuja zan wuce idan kun gama sanda kika ga dama ki koma schl,ke wato baki da kunya tsagera ce ke ko? ki tabbatar kin Daina planning din nan kafin na dawo ciki zan miki Sabo ki Haihu,Yarinya ba a Isa da ke ba sai rigima iri iri.
    Love u,am gonna Miss u Darling bae.

   Ina gama karantawa ban san sanda Hawayen farin ciki ya zubo min ba,ina dariyar jin dadi Kaji fa manya,masu Ilmi da wayewa,ba a fada ayi ta gaba ana fushi a kullaci mutum a zuciya,komai cikin ilimi akeyinshi ba irin mutanenmu ba,a fuska mutum ya nuna baya jin haushinka ko ka bashi hakuri yace ya hakura sai ya dinga gana ma azaba iri iri sai ya rama abinda ka masa,wasu kuma abu kadan sai a maida shi babba ayi fushi,baza a danne zuciya a hakura ba,ga Aayan duk yanda na bata masa naki bashi hakuri na daina zuwa dakinsa bai Sa yayi fushi dani ba,sai ma ya maida abin wasa,ni da kaina naji kunyar kaina,naji ban kyauta ba,kuma ko yanzu nasan Aayan ya gama wayewa ya nuna shi me Ilmi ne ba irin wasu ba ga Ilmi Amma Jahili ya fisu hali me kyau,gaba daya naji Bakin cikina ya yaye,nan take na jawo wayata da Sauri na danna Number dinsa,lokacin yana Airport ana screening bai samu damar dagawa ba,sai Text na tura masa ga abinda nace:
        Allah ya kiyaye Hanya Mijina,Allah ya kaika lfy ya dawo mana da kai lfy,kayi hakuri ka yafe min a bisa bijirewa Umarninka da nayi,na tafka kuskure dan Allah ka yafe min My Man,Fadeel yana gaishe da Abbansa.
    Love u much more Dear,already started Missing u My Husband.
   Yana ganin sakon ya cika da farin ciki marar misaltuwa gashi har anyi solving case din,dama fushi ko masifa ba lallai su kawo gyara ba.
  Tunda ya tafi yaki yarda muyi waya dashi sai text kawai kullum ba adadi,Kwanansa biyar nayi booking flight muka koma Abuja na shiga gyaran jiki ba ji ba gani zan tarbi Ango na.

      Sajeeda ta Haihu da sati Biyu matar Khaleel me sabulu ma ta sauka lfy duk Maza suka haifa,yayin da su Sabeer suke kwasar Amarci,Sameera ma ta haifi mace tuni.
    Lokacin kuma Daddy da Ammah sun tafi Us wai acan zata Haifa masa dansa ko yarsa.
    Meenat uwar yan shiga kitchen yau ma tana kitchen tana girki Fadeela na Rarrafe ta biyota kitchen din Ameer ya shigo cikin 3qtr da yar t-shirt yau a haka ya fita ya dawo Sumar nan ta kara yawa yanzu ma yake ji da daukan wanka,Fadeela tana ganinsa ta dinga washe yan hakoranta wai ya dauketa tana mika masa hannu,Meenat tace wane ke yarinya sai ya fara da Uwarki tukun,dariya Ameer yayi ya fara Huging din Meenat tare da dagata Sama ya direta suna dariya har Fadeela kamar ta san me suke itama ya dauketa yana mata rawa tana dariya gwanin sha'awa,
    Ameer Tafiya yayi da yarsa har wanka shi yayi mata ya shiryata cikin kaya kanana masu tsada da kyau har kwalliya yayi mata harda jambaki,shima yayi wanka ya dakkota suka fito Meenat tana ta dariya yanda ya mata kwalliya harda Jambaki kuma tayi kyau,Meenat tace Babyn Fadeel ce ai wannan,Ameer yace na bashi ita ma sukayi dariya,suna cin abinci na kira Meenat a waya nace zan kawo Fadeel yaye wajenku,Meenat tace Sister Kukan dan yaye nake tsoro wannan yaron naku miskili ga masifa yazo yana hanamu bacci wlh wajen Hajja can zamu maida shi,dariya nayi nace koma ina ne ku kaishi kawai,kwana Uku na sanarwa Aayan na masa text baiyi musu ba na shirya Fadeel da kaina nabi Flight na kawoshi gobe Aayan zai dawo,lallai aka tsantsara min gashi naci gyaran jiki ina sheki na koma Abuja da dare,washe gari na shirya abinci iri iri ina jiran isowar Aayan dina,Meenat ta kirani tace abin mamaki Sis ko kuka Fadeel baiyi ba kamar nice Mamansa kuma yana cin komai ko nono sau biyu ya nema na bashi milk shike nan Amma fa Fadeela tana cin duka a hannunsa,Dariya mukayi gaba daya tana bani labarin Fadeel.

   Wanka nayi na shirya cikin fitted Gown Black and Golden color Ready made ce tayi kyau,kamar Wata balarabiya haka na fito,Gidana da jikina kamshi kawai yakeyi ina cikin gyara fuskata naji dirin Motoci nasan ma Aayan ne ya dawo,palo na sakko na tsaya jikin kofa ina jin Door Bell na bude da murna,dukul na tsaya ganin Ma'eesha da Yarima tare da Ashman dinsu,Daga ina kuke haka yanzu ko waya babu ku shugo ina murna,suna shigowa sai ga Aayan ashe yana bayan Yarima ban san dashi ba na juya baya naji ya rungumeni kamar zai maidani cikinsa,cike da murna na juya na kara makaleshi ina murna na bashi kiss a lips mun dade a haka yana kare min kallo,ga Lallena ya tafi da Imaninsa,a kunne ya rada min Abban Yarima ne ya turo shi Abuja zai masa Wani aiki na 1wk anjima zasu tafi gidansu ziyara suka kawo mana,a kunne nima na rada masa na gane yanzu muje kayi wanka kaci abinci,Yarima suna Palo basu san ma me mukeyi ba,Maeesha tace yunwa mukeji mu dan Allah kizo ki bamu abinci,Hanyar Sama Aayan yabi ni kuma na shiga kitchen na shirya Dining komai da Komai Yarima yace to mu baza mu jira ku ba ci zamuyi,dariya nayi nabi bayan Aayan lokacin ya shiga wanka.
    Da kaina na shirya Mijina na bashi yaci ya koshi nima haka,bayan munyi Sallar Isha Yarima ya dauki matarsa da dansa suka tafi masaukinsu,Suna Tafiya Aayan ya jawoni jikinsa,nace jibi Allurar da akayi min date zai cika kaga ba sai mun kara yi ba tunda Haihuwar kake so,Murmushi yayi sannan yace ai ba yanzu nace ba daga yayewa sai an kara kamar ta 3mnth sai a bari,dadi naji sosai ina masa godiya ina bashi hakuri, bakinmu ya hade waje daya muka shiga sarrafa juna kamar ba gobe,kusan kwana mukayi muna abu daya gaskiya baza mu manta da daren yau ba mun jiyar da juna dadi wanda bazai misaltu ba.
    Bayan wata Uku Ammah Haihuwa ko yau ko gobe tana shan wahala a Us Daddy kuwa ji yake da ita kamar itace wacce ya fara aura a duniya,Wata ranar asabar Ammah ta tashi da Nakuda suka tafi asibiti tare da Daddy kamar jira akeyi suna shiga da 5mnt ta Haifi Namiji kato kyakyawa 15mnt tsakani wata sabuwar nakuda ta kama Ammah ta Haifo Mace ta biyu,Yayanta biyu ta Haifa manyan gaske Namiji da Mace abin sha'awa,Tunda labari ya iske mu muke faman Murna,Babu wanda bai taya Ammah Murna ba,sai a Pics da video call muka gansu gwanin birgewa,ranar suna Aka Sa musu Hameed da Hameeda.
   Sai da Ammah suka kwashe 2mnths yaran sunyi wayo sannan suka dawo gida,tattarowa mukayi da Aayan muka zo Kano munsha kallon kyawawan yan biyu,Aayan yayi kanne muma munyi kanne abin murna Fadeel dina ya kara girma da wayo yana yawonsa ko ina,Haka Fadeela ta Meenat tana Tafiya Ashman din Yarima sun saba Sosai da Fadeel.
    Su Khaleel dasu Haneefa duk da yaransu dagwas dagwas kowa na ji da gayu,Matan su Sabeer ma sun kusa Haihuwa abin ba a cewa komai Zuriyar Hajja tana yaduwa Babban abin farin cikin Family din duk sun gyara halayensu,Hajja tafi kowa Murna da hakan sai dai lfy bata isheta ba jikin tsufa yau fari gobe baki.A mmah ta dakko Inna da wata Kawarta sun dawo Kano gidan da Yarima ya siya mata tace su zauna a ciki suma.

      Bayan Shekara Biyu tuni Meenat ta gama Degree dinta ita da Ma'eesha,nima ina daf da gama nawa,lokacin Na kara Haihuwar yata mace sunan Umman Aayan taci Amma muna ce mata Royal Angel,haka Ma'eesha ta Haifi Namiji again Fhudal,Meenat ciki ne da ita kawai bata haihu ba,Su Hanifa ma daga me ciki sai wanda suka kara Haihuwa.
    Bayan 1yr na gama Degree dina mun dawo kano yanzu hutawa muke zuwa Abuja kawai lokacin Ammah ta kara Haifo Namiji kato  sunansa Muhsin.
    Meenat ce kwance ita da Fadeela da Danta Ahmad dan karami sunyi rubdugu a jikin Ameer yana aikinsa a System duk sun Hanashi yi har bacci ya kwashesu duk suna saman cinyarsa,Meenat tayi matashi da kafadarsa Allah yasa sunyi shirin bacci,Saman Sofa ya kwantar da Meenat sannan ya dauki Fadeela ya kaita Bedroom ya kaita tayi fitsari sannan ya sa mata sabuwar Pampers Sabo da tsaro ya kwantar da ita saman dan Bed dinta dake jikin nasu,Jariri dan 4mnths ya dakko shima a shirye yake kawai dan Bed dinsa shima dake jikin nasu ya kwantar da shi,Wasu suna gangancin saurin Barin Yara su kadai a dakinsu wai gayu ko ace haka turawa sukeyi wani abu ya samu Yara kina can kuna bacci,ya kamata ana dan bari Yara suna kara dan girma da wayo,  ko kuma a hadasu da Nanny suna kwana tare wannan duk bai dace ba a dinga  bari Yara suna wayo kafin.
  Ameer wajen da  Meenat ke kwance ya je ya koma ya dakkota kamar Jaririya itama ya kaita saman Bed din su kato ya shimfidar da ita zai bar saman Bed din yaji hannayen Meenat ta sakalosu ta wuyansu tare da jawoshi ya fado kanta ciki mayen bacci tace Dan Allah mu kwanta ka hakura da aikin nan tunda kayi shirin bacci,Ok ai dama yanzu time dinki ne sakeni na dawo,Kayan wuta ya kashe ya dawo suma ya kashe musu light suka kwanta bayan yayiwa yaransa adduar bacci,Meenat ta shige jikinsa Ameer ya canja Salo na daban,bata san sanda ta biye masa ba suka Tsunduma a tafikin so addua dauke a bakinsu.
  Ammah dai tun daga wannan Haihuwa guda uku Allah ya yaye mata bata kara Haihuwa ba.

    Ma'eesha tana kitchen tana shirya girkin dare Ashman shuru ko motsotsinsa ba a ji ashe yana Palo Computer din Ma'eesha yake wasa da ita ya fasata yayi mata kaca kaca,ya dakko Handrier ma nata ya fasa,Body Cream ya kwaso yayi faca faca dashi a jikin kaninsa dake kwance wai shafa masa yayi,Maeesha ta fito kenan tayi arba da abinda yakeyi,takaici ya rufe ta tama rasa me zatayi masa, ai kawai sai ta fashe da kuka taga ta kanta zai gudu yasan yayi laifi ta cafkoshi tare da cire takalminta daya ta masa Flat ta Zane masa Duwawu yana ihun Kuka sai Dad yake kira,Suna haka sai ga Yarima ya shigo da Sauri kamar zai tashi sama yana masifa ya karbe Dansa yana tambaya lfy? Ma'eesha tace kalli kalla pls abinda yayi min gwara ka bani shi na ballashi,Harara Yarima ya zabga mata kuma shine zaki dukar min yaro karki kara taba min dana,ki fadi kudin na biyaki,ban hana ki masa hukunci ba ko ki masa fada Amma ban son duka kina masa kuka so kike ya lalace Uwarsa na zubar da Hawaye a kansa,yaro ai ba a masa fada ta haka,Nasiha zaki masa,ko zaki dakeshi ba irin wannan ba,kaima idan ka kara lalata abu a gidan nan Tiger zan siyo ta cinyeka Oya bata hakuri,da Sauri Ashman ya durkusa kasa yace kiyi Hakuri Mummy na daina,Maeesha bata ce komai ba ta dauki Danta ta sake masa wanka ta shiryashi,me aiki ta gyara wajen da komai,Maeesha yau sai fushi takeyi sai da Yarima yace zai siya mata duk kayan da dansa ya fasa sannan ta dan hakura kadan,Da dare ma fushi takeyi kuma da Yarima take fushin,Suna kwance da yayi niyyar riketa sai ta matsa gefe,da Sauri ya fisgota ya hade bakinsu ya shiga Tsotsa yana lallashinta tare da fada mata Sweet words har ta sakko ta Bada kai Bori ya hau.
  Alhmdllh Family da kowa ana zaune lfy cikin so da kaunar juna,ba wani fada etc,ga zumunci anayi ana zaman lfy da kowa,Haka kawaye da abokan arziki lfy ake rayuwa dasu,gaskiya kowa ya gammu sai yayi sha'awa bamu da wata matsala.

     Wanka Aayan yasha cikin wata Shadda light blue me matukar kyau da tsadar gaske dinkin zamani fitted na Maza,sai kamshi yake ba karamin kyau yayi ba kamar a saceshi yaro yake kara dawowa,fitowa nayi daga Bedroom dina sanye cikin wasu kana nan kaya ba karamin kyau nayi ba,jean Black da t-shirt white and Blue gashina yasha gyara sai sheki da kamshi ke tashi a jikina,Magan nayi cike da Salo na lankwashe Murya kana nace My Man ba dai fita zaka yi ba? a hankali yace ae gashi ma almost 9pm,Dan Allah ka fasa muyi hira ka dan jira na gama abinda nakeyi na dawo na kula da kai bana son fitar nan taka kaji My Man na karasa cike da shagwaba,tsigar jikinsa ta tashi yaji wani yarrrrrrrr wanda yasashi komawa sama kawai ya fasa fita,Baba Me kula da Yara ta kawo minsu ta gama shiryasu gwanin sha'awa yan gayu a gidan yan gayu,iyayensu ma yan gayu,Fadeel yana bina a baya ina dauke da yata mace muka haura Sama,Fadeel da gudu ya fada jikin Aayan ya wani kwanta mala mala sai tumurmusa Aayan yake yana Ihun wasansa,Bari Fadeel bana son shirmenka sauka ka tafi dakinku wurin Baba sai tsalle kake min a Bed sai ka lalata min Bedsheet,Aayan yace kaji Me Mummy tace,Kafada ya makale shi a nan zai kwana dama da gadonsa kawai na dakko na danna abu sai ga Bed din Fadeel ya bude ya Zama gado na Yara hadadde, jeka kwanta kuma kayi bacci ban son wasa,kwanciya yayi itama Kanwar Fadeel  Angel na kwanta na daura ta saman cikina tana bacci,Aayan duk hankalinsa ya tashi shigar dake jikina da kamshina ya gama ruda shi,matsowa yayi jikina a hankali ya rada min a ajiye Baby girl din nan a bani lokacina Honey,Nima a hankali nace kasan dai Fadeel baccinsa baiyi nisa ba,dan Allah tashi ki duba idan yayi bacci ki kaishi dakin Baba,Kwantar da Royal Angel nayi saman Bed dinta,Aayan yace tsaya na kaishi da kaina ya furta yana dauke da Fadeel ya kwankwasawa Baba ta karbeshi tare da kwantar dashi,har dakin ya shiga da kansa yayiwa Fadeel adduar bacci sannan ya fito yana Yiwa Baba sai da Safe.
    Kafin ya dawo nayi shirin bacci na Angel tana bacci abinta nayi mata addua shima Aayan yazo yayi mata tasa sannan ya hauro Saman Bed,Direct Samana ya haye ya sani a corner ya shiga Kissing din Goshina,saman hanci na,zuwa lips dina da wuyana,duk ya rude ganin Albarkatun kirjina sai kara kyau sukeyi basu da alamar zubewa kamar ban taba shayarwa ba,muryarsa na rawa yace I love u My life,kullum sabuwa kike dawowa Darling,Kaima haka Darling Bae Bazan daina Sonka ba bana gajiya da kai,ajiyar zuciya muka saki a tare lokacin da yake shigata dauke da addua a bakunan mu,Ba abinda mukeyi sai Nishi da Kukan Dadi Kalamai masu sanyi da gardi suna fita ta ko ina sai da muka tabbatar mun raya wannan dare wajen daffaka Sunna.
    Aayan sai addua yake min yana Sa min Albarka nima haka a zuciyata ina alfahari da samun miji irin Aayan samun irinsu sai an tona,ba abinda na nema na rasa shi yasa ko aiki bama yi na Gomnati ko Company komai mazajenmu suna mana kuma muna godewa ba hadama da son zuciya.
    Mun kara gogewa mun zama matan attajirai masu ji da kansu kowa ya kallemu sai ya koka musamman ni yanda ba a magana ma,fadar yanda na koma bata baki ne,ko yaushe mune Abuja,Saudiya,Us da Sauran kasashe muna zaga duniya,M otoci sai wanda muka ga damar hawa Ameer mota har biyu ya siyawa Meenat,Maeesha ma haka ni kuwa sai yanda nayi da motocin Ogana,yace zai siya min nace motocin sunyi yawa haka iya na gidan sunfi kala goma na alfarma.
   Muna taimakawa na kasa damu da dangi abokan arziki sosai muna taimaka musu har Alummar Musulmi indai munga wani a wani Hali sai mun tallafa musu, gaskiya Allah ya zuba mana baiwar kyau gaba dayanmu dasu Meenat sai ka rasa wacce ce tafi Haduwa ma,muna kashe wanka.

   Bayan wuya sai dadi haka Allah yake ikonsa baka zama wani sai ka sha wahala,idan akayi hakuri komai sai ya wuce kamar ba ayi ba,dama rashin hakuri shike jawo barna iri iri,wani kullum cikin rana yana neman na Halak bai samu ba,wani sai kaga Bai shiga ranan ba Allah ya bashi ya kara masa,kyauta ce ta Allah,wani kullum addini yana bin dokokin Allah sai ganshi bashi da cin yau bare na gobe Ammah sai kaga me sabon Allah gashi attajiri na gaske,Sai ayi Hatsari kaga Malami me tsoron Allah yayi kaca kaca ya rasu ka Hango Karuwa a gefe can tana cin chewgum dinta ko rauni bata ji ba😅😅 haka Allah yake ikonsa,duk halin da ka tsinci kanka ka gode masa,sannan aci gaba da addua karki ga Mufeeda da Aayan tare dasu Meenat kamar Allah ya basu komai na duniya kice kema sai kin dawo haka,kowa da Kaddarar Sa kowa da jarabawarsa kuma questions na kowa daban ne idan kikace zaki copy jarabawar wasu to zaki fadi Zero Katon kan jaki zaki ci 😅Sabo da ba questions dinku daya ba kowa da kalar nasa wani yafi wani,kuma bawai Su Mufeeda za ace shikenan baza a kara jarabtarsu ba no zasu ci gaba da karbar jarabawa daga Allah sai ko in su samu me sauki.

   Aayan karki ga me kudine da lafiya ga kyau kice kema dole irinsa zaki samu ko mijinki sai ya dawo Ameer ko Yarima 😅duk Halittace ta Allah sai kiga dan Mummanki yafiye miko ko wanne namiji a duniya Halitta ce ta Allah kuma kowa yana da tasa baiwar ta musamman,mata a kara hakuri da juriya sannan mu kara jajircewa wajen kula da mazajenmu tare da tarbiyyantar da yaranmu.
   
   NAN ZAN AJIYE ALKALAMINA NA KYALE SU MUFEEDA HAKA.

   ALHMDLLH  da Allah ya bani dama da ikon kammala wannan Novel,ina matukar Godiya gareku masu kaunar wannan Novel,ina jinjina ga masoyana kaf duk a inda kuke ina kaunarku da wanda na sani da wanda ban sani ba,Masu kirana ta waya,text etc na gode Allah ya bar zumunci.

     Ina neman Afwarku na rashin karasa muku Novel da wuri da banyi ba na samu kaina da rashin son Typing  da fatan zakuyi hakuri ni kaina ban so hakan ba.

    Naso ace duk masoyana dana sani na baku kyautar page ko na kwala muku kira na gaishe daku a Cikin Novel dina😍😅 Amma hakan Bai samu ba,ayi hakuri ina kaunarku fans.

    Groups wanda suka fi kowa birgeni wajen yin Sharhi Har na Samu na gama typing ina jinjina da godiya:
ASMABAFFA FANS CLUB
KASUWANCINA TRUE FANS
HOUSE OF HAUSA NOVELS
TASKAR SURAYYARMS
TASKAR FIDDAUSI SODANGI
LATEST NOVELLA
UWARGIDA da Sauran Gp na gode Allah ya bar kauna.

    Sai kurakurai dole za a samu da yawan gaske wanda ku masu karatu zaku fi gane hakan,da su Typing error ayi min Afwa wannan Halayyace ta dan Adam wanda ya Zama dole tunda dole za a samu wani abin da bai muku ba,ga kuma halin mantuwa shima sai anyi mana Uzuri.

    Kuskurenmu a ciki Allah ya yafe mana,darasin da muka koya Allah ya bamu ikon yin aiki dashi Ameen.
   Fans Allah ya biyaku ya saka muku da alkhairi baki daya.❤❤😘

   Sai mun sake haduwa a sabon Novel dina nan gaba Insha'allah idan Allah ya kaimu da rai da lfy zan sake Sambado muku Sabo idan na huta da dan yawa.😍😍😍❤❤❤❤❤❤😍😍 Kar naji an tambaye ni sabon Novel da wuri👊👊👊sai na huta da yawa.

Zanyi Missing dinku fans musamman masu Sharhi yanda muke rakashewa muna wasa da dariya😍😍😘😘😘😍🤣wayyooooo.

   AsmaBaffa loves u all.....





AsmaBaffa
COPY BY ZAINAB BUTALAWA


COMMENTS

Name

ADSENSE,4,Airtel,1,ANDROID,9,AQIDARMU Book 1 Complete Hausa Novel,1,AQIDARMU Book 2 Complete Hausa Novel,1,Arbitrade,4,Arbitrage,1,AUREN MU Complete Hausa Novel,1,Babban Yaya Hausa Novel Complete,1,Babu So Complete Hausa Novel,1,Bakar Inuwa Complete Hausa Novel,27,Billyn Abdul Novels,7,BLOGGING,13,Business online,10,Crypto currency,17,Dare Daya Hausa Novel Complete,1,Daudar Gora Book 1 Complete Hausa Novel,48,Daudar Gora Book 2 Complete Hausa Novel,95,DOWNLOAD,2,Duk Karfin Izzata Book 2 Complete Hausa Novel,34,Education,3,Email,1,Facebook,4,Finance,1,Furar Danko Book 2 Complete,9,Furar Danko Complete Hausa Novel,31,fyade hausa novel by maman teddy,1,fyade hausa novel Complete,1,Gidan Haya Hausa Novel Complete,6,Gidan Haya Complete Hausa Novel,4,Gidan Haya Hausa Novel,1,Gidan Kwarata Complete Hausa Novel,1,Glo,1,Google,1,GURBIN IDO Complete Hausa Novel,1,Hamshakiya Hausa Novel Complete,25,JARABABBEN NAMIJI Complete Hausa Novel,1,Jikar Maguzawa Complete Hausa Novel,23,Job,7,KASUWANCI NA Complete Hausa Novel,1,Layikan waya,2,Loan,8,MA'AIKACIYAR GOMNATI Complete Hausa Novel,1,Makauniyar Kaddara Complete Hausa Novel,70,Mufeedah Complete Hausa Novel,25,Namijin Zuma Complete Hausa Novel,26,nihaad complete,62,Nihaad Complete Hausa Novel,62,nihaad hausa novel,62,Npower,13,Pc Tools,2,Qamshi Hausa Novel Complete,14,Raina Kama Complete Hausa Novel,29,Sakayyah Book 2 Hausa Novel Complete,30,Sakayyah Hausa Novel Complete,60,SHAKUWAR YARINTA COMPLETE HAUSA NOVEL,20,Support,26,Tabarmar Kashi book 2,7,Teach and guide,8,TUMFAFIYA Complete Hausa Novel,1,TUMFAFIYA Hausa Novel,50,TUMFAFIYA Hausa Novel Complete,19,UNCLE DATTI Hausa Novel Complete,1,Watsapp,3,Waye Mijina Hausa Novel Complete,5,WEB LANGUAGE,1,WEB TUTORIAL,2,Yar Aikin Karuwai Book 1 Complete,1,Yar Aikin Karuwai Book 2,1,Yar Aikin Karuwai Hausa Novel,1,Yaya Mata Complete Hausa Novel,22,Zafafa Biyar Novels,7,
ltr
item
NAGARTA24 || job || npower || crypto currency || arbitrade || loan || teach and guide || support ||: KASUWANCI NA Complete Hausa Novel
KASUWANCI NA Complete Hausa Novel
https://blogger.googleusercontent.com/img/b/R29vZ2xl/AVvXsEg84Aup7QU7ErlA1a7jlcCUfPYou52963_CHffk41jfwz_9Qd-uffE87Xm4Cos6olBEnsElNFbe7csxwnBXjCuMd8s_df0QW4-Idr_TPIeqt08n05vSBiT0otbh2lpe6o1xpVePdelwZLNlPIjOboB9EZyqfKieLBM7RNaxaEHdld4DPfUxyTdNT2IKJiFw/s320/img_1696842016094.webp
https://blogger.googleusercontent.com/img/b/R29vZ2xl/AVvXsEg84Aup7QU7ErlA1a7jlcCUfPYou52963_CHffk41jfwz_9Qd-uffE87Xm4Cos6olBEnsElNFbe7csxwnBXjCuMd8s_df0QW4-Idr_TPIeqt08n05vSBiT0otbh2lpe6o1xpVePdelwZLNlPIjOboB9EZyqfKieLBM7RNaxaEHdld4DPfUxyTdNT2IKJiFw/s72-c/img_1696842016094.webp
NAGARTA24 || job || npower || crypto currency || arbitrade || loan || teach and guide || support ||
https://www.nagarta24.com.ng/2023/10/kasuwanci-na-complete-hausa-novel.html
https://www.nagarta24.com.ng/
https://www.nagarta24.com.ng/
https://www.nagarta24.com.ng/2023/10/kasuwanci-na-complete-hausa-novel.html
true
1779421581242976301
UTF-8
Loaded All Posts Not found any posts VIEW ALL Readmore Reply Cancel reply Delete By Home PAGES POSTS View All RECOMMENDED FOR YOU LABEL ARCHIVE SEARCH ALL POSTS Not found any post match with your request Back Home Sunday Monday Tuesday Wednesday Thursday Friday Saturday Sun Mon Tue Wed Thu Fri Sat January February March April May June July August September October November December Jan Feb Mar Apr May Jun Jul Aug Sep Oct Nov Dec just now 1 minute ago $$1$$ minutes ago 1 hour ago $$1$$ hours ago Yesterday $$1$$ days ago $$1$$ weeks ago more than 5 weeks ago Followers Follow THIS PREMIUM CONTENT IS LOCKED STEP 1: Share to a social network STEP 2: Click the link on your social network Copy All Code Select All Code All codes were copied to your clipboard Can not copy the codes / texts, please press [CTRL]+[C] (or CMD+C with Mac) to copy Table of Content