PAGE 21
PAGE 21
Sultan wani irin kamuwa kuma ,ina nufi sonta kakeyi ,murmushi yarima yayi yace tabbas bakayi karyaba sultan inajin ta araina sosai duk da ban taba ganin fuskarta ba,,,sultan yace to mai zai hana yau mu naimi izini a gurin malaman su musamu ganinta ,yarima yace haka yayi abokinah,,,
Bayan tashi a musabaka ne ,su yarima suka naimi izini ganin leema ta gurin malansu ,,,basu sha wahalaba kasancewar su yaran manya ,,,leema bata kawo kumai a rantaba dan tasaba da jama,a nason ganinta ,,
Da sallama tashiga ofes din da suke ,har kasa ta durkusa ta gaida su ,sannan tace ya shek yace kuna son ganina ,sultan yace eh halima ya karatu da kuma kukary tace Alhamdulilah ,,,,
Yarima yace Allah ya taimaka tace Amin ,,sultan ne yace halema nasan zakiyi mamakin kiranmu duk da dai kinsaba ,abukina ne ya gani ya yaba da halayenki,maana yana sonki ,da sauri lema ta dago kai dan ita ba wanda ya taba gayamata kalmar so,,shuru tayi sultan yace ya kikayi shuru ,sunkuyar da kai tayi ,sannan tace inaga a gurin iyayena zakusamu wannan izinin,,,
Yarima yace haka ne munsu dai kisan da zuwa nmu ne ,,sunana yarima Alamin ,abukina kuma sultan ina fatan mun samu karbuwa ,,,murmushi tayi ,tace zan wuce ,yarima yace to mun gode,, tana fita yarima ya rungume sultan yana dariya ,sultan yace ,naso kace kanaso ganin fuskarta ay ,amma kayi shuru yanzu yazamuyi kaga taki bude fuska kar muje muyi tambaya kuma musa fuskar daban,,,yarima yace kai ni ko ya take inasonta ,ay ita nakeso ba fuskartaba,,,,
Haka umar yatafi gidan kanawar hajiya ya dauku yarta rahama akan zatazu ta ringa kula da hajiya ,,rahama tazo da farko dai tana kula da hajiya kamar gaske amma daga baya abin ya chanza,,,
Hajar kuwa bata zuwa duba hajiya in ta shigo ma haka zatayi ta rufe hanci wai wari ,,,ita kuwa husna tana zuwa kullum ta dubata ,,
Kamar kullum yauma husna ta tattaro yaranta sunzu gaida hajiya suna shigowa hajiya tace,to kaza uwar yaya wai su halema da jamila bazaki auraddah subane ,kullum sai yawo suke agari amma ba mashinshi ni Allah yasa kar su biyu bakin jininki ,,dariya husna tayi tace ,hajiya ya karfin jikin tace ,nakusa warkewa ma ay inma dadi kikeji na zauna yau za a kunce,,,
Husna ta bude baki zatayi mgn saiga sahal da gudu yana hajiya kinga mamana wai sai naje makaranta ba wayyo ,kawai yayi kan hajiya da gudu ji kake kas hajiya ankuma karyewa,ihu tasa tana na shiga uku sahal ka karyani ,sudai husna da yayanta sai sannu suke mata ,melat ce abin yabata haushi ta make sahal aykuwa yasa kuka ,,hajar ce tafito da sauri, tace uban waye ya tabamin yaro,melat tace,take hajiya yayifa ,hajar tace to ayba uwarki ta haifamin shi ba ku kinga irinshi a gidan ku ne yar bakin ciki badake zanyiba uwarki ce saata,,,kafin ta rife baki ,melat ta kaimata mari ,kafin kace me kukawa daker rahama ta rabasu , ,,,husna ta kuri su melat makaranta sannan tacewa hajar kiyi hakuri ,da ne ka haifeshi baka haifi halenshiba ,,,hajar ta murguda baki ,tace karya kike muna muka,, husna tace ni ba saar yinki bace jira melat ta dawo,,,
Hajiya dai bata ba san me akeba dan azaba ,an dada kiran mai gyara ,an gyera hajiya sai kuka da salati take tana sahal ka cuceni,,,
Bayan umar yazo yashiga bangaren hajiya da husna ,,yana shiga bangare hajar yasameta ,tasa waya agaba tayi rub da ciki tana batse cinya tana lumshe ido,leka cikin wayar yayi ,mai zai gani bue film ne take kallo ,yace suba hanallahi hajar ba na hanaki kallon iskancin nan ba ehyee amma baki dainaba ko ,,,kamushi tayi tace washi ahhhh ,yaya zu kayimin man ,wanka mata mari yayi yace yar iska kidawo hankalinki dama nagayamiki in na sake ganinki da bue film abakacen aurenki ,dan haka kije na sakeki,,,,
Manej my fans abin sai a hankali,
*nagode masoyana wanda sukama boyna abakar addua,da wanda sukazu har gida dubashi ,Allah yabar zumunci*
Taku uwar farhana😘
*BRILLIANT WRITTES ASSO*
👱🏻♀👱🏻♀👱🏻♀👱🏻♀👱🏻♀
*YA,YA, MATA*
Abin Alfahari ne
👱🏻♀👱🏻♀👱🏻♀👱🏻♀👱🏻♀
*BY UMMU FARHANA*
*DEDICATED TO MY FANS LOVE U ALL*❤
COMMENTS