PAGE 10
PAGE 10
Rarrashin ta yakeyi yana bata hakuri ,,husna nima auren nan bason shi nakeba kinsan ba yadda zanyine amma kisawa ranki hakuri insha Allahu ba abinda zai faro ,,,tace hammm kuma yanzu daga ta haifi namiji shikenan ko,kaima zaka juyamin baya,, tasake fashewa da kuka mai tsuma zuciya ,,shima umar sai yasa kuka ,,,da sauri husna tayi shuru tace ,,,haba umar kuka kuma kayi shuru Dan Allah ,,,,yace to yazanyi husna ya kikeson inyi babu inda zanji sanyi sai gunki kekuma sai kuka kike habah,,,take tafara kuka kuka dariya dariya,,,shima yayi shuru yace ko kefa ,,,ya dada rungumeta sosai a jikinshi yana kissing dinta ,,,yace oya muje muyi wanka mu kwanta maza,,,a shagwabe tace ni bazanyi wanka ba fa yau ,,,yace ni zan miki maza ,,sidak ya dauketa sai bayi ,,,
Washe gari da safe dayake lahadi ce umar yana gida da yaranshi da matatshi suna ta wasa da dariya bakajin kumai sai ihun yaran suyi guje guje yayi musu doki ,,,haka dai suke ta dariya , ,,,
Lami ce tafito ta gaida hajiya ta zauna suna Dan taba hira ,,,hajiya tace na dauka bacci kike ,,lami tace ina naga bacci uban ya,ya, mata yana musu wasa dariya da ehu yacikamin kunne ,,,hajiya tace wa kenan tace wa in banda umar sai wasa suke da yayanshi suna dariya har uwar ,,,,hajiya tace ay munafukar yarinyace kinga tasan ta mallake shi zancen auren ko a jikinta ,,,hammm ay zai fito yasameni ,,,
Umar ko saida ya hada gumi sosai yace to ya isa kuje kuyi wanka muje yawu maza ,,sai suka diba da gudu ,,,shima wankan ya shiga,,, bayan ya shirya yace husna har kefa zamu fitah ,,,tace to ,,yace bari mu gaisa da hajiya kafin nan ke shiya ,,,,
Shida yaran suka fita daya a kafada daya baya yana Jan saura haka sukashiga dakin hajiya,,,da slm ton kan ta amsa tace sannu jakin ya,ya, mata eyye ji yadda ka goyusu sai sun kassaraka yau ni rabi naga fitina ina ita gimbiyar ta haduka da annuba ,,,maza kuyi waje, sum sum suka fice,badan ranshi yaso ba,,,
Bayan sun gaisa ne hajiya tace ,,to mgnr hajar kawu kudade aje akai ,,kuma batun gidah a sabun gidah nakeson a ajeyeta,,,shuru yayi yasan abun da kamar wuya husna ta yadda ,,,take yasamu mafita yace ay akwai saura aiki sosai ,,kuma kudin sun karemin ,,,na dakata da ginin ,,,
Tace ,,to badamuwa ay sai a gyera sashen chan nakusa daku tazauna kafin ka kara ,,,nan ma shuru yayi shi so yayi tace abari ya gama,,,,haka dai sukayi ta tattaunawa ,,,an tsayar da magana akan zataje tasamu baffanshi zaije gidansu hajar naima mishi auren hajar ,,,husna ce tayi sallama a nutse ta gaida hajiya ,,,hajiya tace to husna dana dai zaiyi aure nan da sati biyu nan da wata tara umar zai samu da namiji ,,,husna Allah ya tabbatar da Alheri ,,,hajiya tace Amen in da gaske kike , ,,
Suna tfy a muta suna hira haka sukayi ta yawu guri guri sun shakata sunyi siyyah ,dan yanzu umar yana samu sosai a gurin aikin shi ,,,ya jidawa yaranshi kayan wasa sosai haka suka dawu gida shidai duka kukarinshi ya farantawa husna rai ,,ya kuma tabbatarmata shi wan nan aure tasa a ranta dole ne kawai ba yadda ya iyah,,,,
Baffan umar sunje gidansu hajar an basu auren hajar kuma ansa rana kamar yadda iyayen suka shirya sati biyu ,,,,
Lami da hajiya ne suke ta rangada buda wai murnar auren umar sukeyi ita dai husna tana jinsu aikin ta kawai takeyi tana adua akan Allah ya kawumata sauki a rant,,,
Kasancewar hajiya tanada kudi kuma ita takeson umar yayi aure ,,,bata bi takanshi ,kashe kudinta take sosai tagama kumai harsu kayan laife ita tayi,,takera umar yagani yagani kuma ya yaba,,,, sannan yace hajiya ita kuma husna fah ,,,staki tayi tace bata dubu guma ya isheta,,,yace haba dai ,,,tace toh sai kayi yadda kakeso bari ma da kaina zan bata,,,
Haka ko hajiya ta dau cingam da guro da dubu guma suka shiga shashen husna bayan sun zauna ne lami ta cellah mata goron a cinya tace to ansa rana hajiya kuma tace kashi kisai kayan fadar kishiya ,,,husna hawaye kawai take ,,, haka suka ta habaicin su suka fita,,,
Haka sai yinin ranar husna tayi shi ba dadi har zuwa dare tukun umar yadawu ,,,tunda ya shigo ya gane yau husna ranta a bace yake, sai da yabari yara sukai bacci tukun ya janyu husna jikin shi yace matata meye tamuwar ki ne,,,,
Kuka ne ya kufcemata tace umar anamin wulakanci a gidan nan ,,kumai daya danganci aurenka sai dai inji a wurin hajiya ,,nan tabashi labari,,,sannan tace yamata alfarma tunda yara suna Hutu ta tafi yobe gurin surayya ita bazaata iyah jure wan nan wulakancin ba,,,,,
Hakuri bata yakumace shi bai Masan sun kawumata kudiba amma dama ya turawa surayya dubu Dari biyar taimata siyayyah ,amma tunda tanason zuwa to ta shirya gobe ya kaita ,,,godiya tamishi sosai ,,,,
.
Washe gari su hajiya da lami anata shirye2 ana habaici sai ganin husna sukayi da akwatuna,,, ta gaishesu tace ta tafi damaturu ,,,hajiya tace umma ta gaida aysha ,,,lami tace keko husna meye na yaji ba akanki aka fara kishiyaba kiyi zamanki man tanayi tana dariya,,,hajiya tace gayama ta dai aure ba fashi taje tayi duk yadda zatayi,itakan husna uffan batace ba ,, ta mike tace to mun tafi,
Awaje tasami umar har sunshiga mota da yara ,,suka kama hanya sai yobe,,,,
Nave Allah ya kiyaya,
Taku ummu farhana😘
*BRILLIANT WRITTER ASSO*
👱🏻♀👱🏻♀👱🏻♀👱🏻♀👱🏻♀
*YA,YA, MATAH*
(Abin Alfaharine)
👱🏻♀👱🏻♀👱🏻♀👱🏻♀👱🏻♀
*By ummu farhana*
*DEDICATED TO BRILLIANT WRITER ASSO*
*NA GODE DA ADDUUIN KO MASOYA NAJI SAUKI SOSAI ALLAH YABAR KAUNA*
*INA TAYA ALUMMAR MUSULMI BARKA DA SALLAH ALLAH YA MAIMAITAMA NA*
*SANNAN INA BAWA MASOYANA HAKURI NAJINA SHURU,UZIRI NE YA DAKATAR DANI*
*INSHA ALLAHU ZANYI KUKARIN KAWUMUKU AKAI AKAI*👏👏👏
COMMENTS