TABARMAR KASHI Book 2 Page 64

 "HUGUMA*

 "HUGUMA*




*_TABARMAR KASHI_*


Book 02 Page 64


Dukkansu suka mige sanda sukaj| qarar bude gate din gidan tare da qarara shigowar ayarin motocinsu su

MT JARMA. Kallo sosal hajiya mansura ta mayar kan labiba


"Wannan karon babu sauqi babu sassauci,babu kuma daga qata,fatatawa ce ta gaske,yaqin sunquru za'a yi tsakaninmu da duk wanda zai hana mana cikar burinmu,ni dake kowa yayi amtani da damarsa ya samawa zuciyarsa abinda takeso" kai labiba ta jinjina cike da gamsuwa


"In sha Allah mama" tare suka fara takawa suna fita zuwa harabar ajjiye motoci na gidan, don zuwa yanzun sunsan duka motocin sun isa can.


Lissatinsu ya basu dal dal, sanda suka isa din duka suna qoqarin fitowa daga motocin, banda toufeeq, da säahar dake zaune cikin tasu motar kamar basu shirya fitowar ba,ya tsareta da fararen idanunsa yana Kalionta bayan ya dauke kallonsa daga duk jama' ar dake farfajiyar gurin, kama daga ma'aikatan gidan da haseena dake riqe da hannun hajiya qarama dake qogarin fitowa da mota,har labiba da ke isowa gurin.



"SAHR…...bana buqatar.....


"Shshshsh" tace dashi tana dora yatsantsa kan labbansa fararen idanunta masu wani irin haske ta zubesu a cikin nasa


"Kada kace komai,duk wadan nan tarkace nima bana bugatarsu,for now ya kamata su nisanci rayuwar mijina ko? idan ba haka ba zasuy nadaman cusa kansu ga rayuwarka,am new version of saahar, ba tsohon version din da suka sani bane" a hankali ya kama yatsanta dake kan labbansa ya tura bakinsa yadan tsotse kadan. Da sauri ta fuse hannun tsigar jikinta na tashi tana masa nuni da fadeela dake zaune gaban motar, kafadunsa duka biyun ya daga sannan ya rausayar da idanunsa ya maidasu waje shi da ita duka suna ci gaba da kallon wajen.


Cikin takun kissa da jan hankali hajiya mansura ke takowa zuwa gurin har ta iso bakin motar dr jarma


"'Barka isowa,marhaban da......." Qafewa kalaman bakinta sukayi suka tsaya mata a wuyanta,su basu fita ba su basu koma ba,wani irin abu ya tsarga mata wanda ya haifar da tsatstsafowar gumi daga kowacce kafa ta jikinta sakamakon ganin maji da tay na fitowa a motar mazauni daya da Dr din. Duk wata walwala tata ta janye kaff!. Bata taba zaman kishi da maji ba, amma tayi imani zaman kishi da matar bazai taba yi ma kowacce macce dadi ba,duk wadda kuma tayi gangancin aikata hakan tabbas zata iya kwasar kashinta a hannu.



Da boka da malam cakude da tuggu da makirci amma tsahon shekarun da tayi da Dr din basuyi nasarar cire maji dari bisa dari daga zuciyarsa ba,ta wahala ta wannan fannin da tsantsar baqin kishi, wanda ta dinga ji inda tare suka rayu da maji babu abinda zai hana zuciyarta bugawa fes.


Murmushi hajiya qarama ta saukewa fuskar hajya mansura,ta tabbatar a yau boom na farko da zai fara tayar mata da kan mansura batun maida auren mijinta ne da tsohuwar matarsa da tayr imanin mansura din bata sani ba,kuma tasan itace mutum ta farko da zata fara aje zarginta a kanta,to ko hakan ma yayi mata,wannan zai qara mata tsoronta cikin zuciyarta hadi da shakkarta,zai kuma sake dasa mata cewa ita din ta isa da yayanta kuma kome tace ya aikata zaiyi din,duk da lamuran sun fara sauyawa.


Murmushin da ta gani a fuskar fauziyya shi ya sanyata hanzarin maida nata murmushin saman tata fuskar itama,ta sani murmushin fauziyya irin wannan ga abokin takun saqa ba alkhairi bane,sai ta sake matsawa tana yi masa maraba,fiye da rabin hankalinta nakan maji.


Ko sau daya majin bata dubeta ba,saboda bata qaunar kishin dake ranta ya motsa a kanta,abu daya ta sani,ranta yana baci da yadda Mahmud din ya buge da auren mansura. Tasan mansura farin sani tunda tana daya daga cikin qawayen da fauziyya ke tara mata suna keta alfarmarta har cikin gidanta a wancan lokacin.



Ta gefansu ta wuce abinta tana migawa nadeeya

Jakar hannunta,sannan suka wuce zuwa sashensu.


Idanun Dr yana kan maj,yayin da idanun mansura yake kan Dr,har zuwa sanda maji tayi nisa ya maido hankalinsa ga mansura. Fuska ta bata sosai baqinciki yana ciciyar zuciyarta,babu ta yadda zata yarda ta bari matar nan taci gaba da zama a qasar nan,idan ba haka ba kuwa tayi imanin tata ta kusa qarewa.


Juyawa tayi abinta saboda bacin rai,sai yasa hannu ya kamota


"Yaki mana,ya zaki tafi?" Ya fada a tausashe. Dole yabi a sannu, saboda yasan a yau din Allah ne kadai yasan kalan tashin hankalin da za'a yi a gidan idan taji maida aurensu, amma hakan ya zama dole ya shelanta kowa ya sani saboda fidda zargi da kuma sake shaidar zamantowarsu miji ga mata din ga family dinsa.


"To me yayi saura kuma?"


"Muje" kawai yace da ita. Gaba tayi tana qoqarin hadiye fushinta, tanason taci ribar yau din,ta kuma kwashe dukka nasarorin da malamin tsubbun ya gaya mata, tasan tushi kuma ko tashin hankali bazat sanya ta tsira da komal ba indar Mahmud ne.


"Ki koma suna cikin motar, ki tarbeshi ki nuna damuwa da kulawarki a kansa" hajiya qarama tace da haseena wadda ke shirin shiga sashenta. Bata cewa uwar komai ba ta juya din da sassarta, ya qaguwa tayi da son ganin toufeeq din, tunda ya tafi ko sau daya bataji muryarsa ba bare ay zancan ganinsa.


Tana dab da isa ta hangi labiba a tsaye a gurin,wani bacin rai ya taso mata,itafa ba labiba da suke takara tare ba,hatta da saahar din ta tsaneta.


Ya gama karantar takun kowa a cikinsu, sai ya janye idanunsa cikin ransa yana raya kowacce zataci qaniyarta. A nutse ya bude motar ya sanyo qafafunsa waje. Cak kowacce ta tsaya daga inda take, kwarjininsa cikar haiba da kamalarsa yana dukan fuska da zuciyar kowaccensu.


Hannu ya miga ma saahar dake zaune cikin motar, idanu suka hada ya sakar mata murmushin nan nasa me tsada,sai ta mayar masa da martani, ta miga masa nata hannun tana jin qaimi cikin zuicyarta,wani sashen na zuciyarta yana sake cika sosai da kishinsa.

Tamkar wata da zara haka suka fito, sunyi want irin mugun kyau da matching da junansu, koda maqiyr idan ya gansu a lokacin sal sun burgeshi.


Daga labiba har meenal kowacce sai data hadiye wani yawu mai tauri, a take dukka wani qwarin gwiwar da labiba ta debo ta tsiyaye ta kuma tarwatse a gurin, kallon sãahar kawai na farko taji ta raina kanta gaba daya,tako ina bata isa ta gwada kanta da ita ba, koda silin yatsanta guda daya tasan bata kamo ba,sãahar din tayi wata muguwar gogewar da ko ke diya mace sai ta burgeki bare d'a namiji,duk da wanna kuma idanuwanta sun gaza daukewa daga kallonsu.


Yawun bakin meenal gaba daya ya dauke da wani irin mahaukacin kishin saahar, tabbas inda ace akwai bindiga yanxun a hannunta babu abinda zai hanata harbawa saitin zuciyar saahar, tako ina ita dimma tasan zati da cikar haiba nutsuwa da kamalar säahar ta zarta tata,saidai kuma bata jin ko kadan wannan Karan zatay giving up, ba zata sassauta ba wajen farautar toufeeq har sai taga abinda ya turewa buzu nadinsa,don haka ta tattara dukkan qwarin gwiwarta tayi taku biyu zuwa inda suke takawa,cikin fari da ido, lanqwasa harshe da yauqi tace


"'Barka da dawowa yaa mohanmu.....


"'Wayy!" Säahar ta datsin maganar da meenal ta debo tana lanqwashewa, abinda ya maida dukkan hankalin toufeeq kanta


"Yaya? me ya faru?" Cikin wata muguwar shagwaba data shigeshi gaba daya cikin jini da julya tace


"Qafafuna,na gaji,nidai ka daukeni"


"Angama" ya furta yana nannade hannun tsadadden yadin jikinsa. A tausashe sannan a hankali ya tsugunna yasa hannunsa ya dagata cak ya fara takawa da ita zuwa sashensa idanunsa cikin nata yana tambayarta


"Are u comfortable?" Kai ta jinjina masa sannan a sace ta dubi sashen da su labiba sukayi mutuwar tsaye,cikin sa'a suka hada idanu,ta aje musu wani kallo na baku isa ba sannan ta maida kanta saman qirjinsa ta kwantar a shagwabe.


Dariya labiba ta qyaqyace da ita sanda taga haseena da tayi mugun shaqa,ta kuma gaza boye shaqar da tayi  din ta hanyar binsu da kallo, duk da cewa sun bacewa ganinta


"Ashe dai duka burga ce,ashe dai ba'a isa din ba,ashe duk kwana da tashin da akeyi gida daya duka suna ne,ah wai" labiban ta furta tana tura dauninta gaban goshi,duk kuwa da cewa ita dinma ta shaqi bacin rai har kusan fiye dana haseena.


A mugun fusace haseena din ta waiwayo

'Ke, ki saurara malama, koda giwa ta fadi tafi qarfin wawa, ni ba sa'arki bace,don nafi qarfinki har abada" sosai labiba ta sanya dariya harda shewa


"Mu gani a qasa mana,wai inji kare ana biki a gidansu yace mu gani a qasa,ashe duk wani cika baki da fankamar uwar taki na banza ne, tunda ta gaza mallaka miki mutum daya tal a rayuwarki,wannan ma ya isheku hasara da kaico, bayan kaicon da a wunin yau kafin faduwar rana yake shirin samunku, ku shirya zuwarma gagarumar FALLASA wadda zata cimma rayuwarku" daga wannan sai ta juya tana taku d'ai d'ai, cikin ranta tana jin FALLASAR da zata auku a yau din, tamkar mabudin nasara ne a garesu.


_to maji ma gani wai an binne tsohuwa da ranta_


A bisa bigire daya suke takawa,saidai kowacce zuciyarta cike take da alwashi da kuma mugun tanadi ga ‘yar uwarta,wani irin kallo a sace wanda bakuna basu furta komai ba sai fatan cikan burika, a haka har suka iso mararrabar sassan guda biyu,dr jarma yay gaba. Daga Mansura har fauziyyar kowaccensu tsawa tayi "Ina miki barka da isowa qasarki ta gado,ina miki barka da isowa bigiren da zaki fahimci bakin rijiya ba wajen wasan makaho bane,ina kuma yi miki jaje da kalar qaddarar da yau din tazo miki da shi, ina miki fatan samun juriya a bisa hakan" sai da gaban hajiya qarama. yadan fadi, amma kuma tayi gaggawar ture wannan daga ranta da tunaninta,don kuwa a kaf tarihinta bata taba yarda kalaman barazana sun tsoratata daga bakin abokin adawa ba. Jifanta tayi da murmushi duk da zuciyarta na cike da kokwanton yadda mansura ke magana kanta tsaye cike da qwarin gwiwa


"Ke ya kamata ki riqe wadan nan kalaman kiyi bitarsu da kyau,domin a yau kadai zaki fahimci ni fauziyya nike sanyawa a auro a kuma saka sannan ayi kome a duk sanda naso hakan, baya ga wanna kuma..…... Tarantin

nan da kike shirin taka gefansa, kina gab da gain asarar da bazaki iya qidanya adadinta ba" murmushin ta jefa mata Itama


"Ni dake shege ka fasa"


"Dan halak sai kallo" sai kowannensu ya juya yana nufar sashensa, saida dukkansu zukatansu cike suke da fargabar yagewar zaninsa a tsakiyar kasuwa,saboda gaba dayansu sunsan sunyi birniya me zurfi da kowa a cikinsu yasan da mummunar ajiyar dan uwansa,amma cikar da zukatansu sukayi da daukan fansa da samun cikar burin diyoyinsu ya sanya suke jin komai zasu iyayi, komai ta fanjama fanjam.



*_turqashi, kuzo kuyi kallon dinkin gadar zare zai tsinke_*



Da hanau gwara mannau inji hausawa * ,ku yimin uzuri,jiya dama ta bayar,yau kuma sal a hankali, na gode qwarai_*




Zafafabiyar

COMMENTS

Name

ADSENSE,4,Airtel,1,ANDROID,9,AQIDARMU Book 1 Complete Hausa Novel,1,AQIDARMU Book 2 Complete Hausa Novel,1,Arbitrade,4,Arbitrage,1,AUREN MU Complete Hausa Novel,1,Babban Yaya Hausa Novel Complete,1,Babu So Complete Hausa Novel,1,Bakar Inuwa Complete Hausa Novel,27,Billyn Abdul Novels,7,BLOGGING,13,Business online,10,Crypto currency,17,Dare Daya Hausa Novel Complete,1,Daudar Gora Book 1 Complete Hausa Novel,48,Daudar Gora Book 2 Complete Hausa Novel,95,DOWNLOAD,2,Duk Karfin Izzata Book 2 Complete Hausa Novel,34,Education,3,Email,1,Facebook,4,Finance,1,Furar Danko Book 2 Complete,9,Furar Danko Complete Hausa Novel,31,fyade hausa novel by maman teddy,1,fyade hausa novel Complete,1,Gidan Haya Hausa Novel Complete,6,Gidan Haya Complete Hausa Novel,4,Gidan Haya Hausa Novel,1,Gidan Kwarata Complete Hausa Novel,1,Glo,1,Google,1,GURBIN IDO Complete Hausa Novel,1,Hamshakiya Hausa Novel Complete,25,JARABABBEN NAMIJI Complete Hausa Novel,1,Jikar Maguzawa Complete Hausa Novel,23,Job,7,KASUWANCI NA Complete Hausa Novel,1,Layikan waya,2,Loan,8,MA'AIKACIYAR GOMNATI Complete Hausa Novel,1,Makauniyar Kaddara Complete Hausa Novel,70,Mufeedah Complete Hausa Novel,25,Namijin Zuma Complete Hausa Novel,26,nihaad complete,62,Nihaad Complete Hausa Novel,62,nihaad hausa novel,62,Npower,13,Pc Tools,2,Qamshi Hausa Novel Complete,14,Raina Kama Complete Hausa Novel,29,Sakayyah Book 2 Hausa Novel Complete,30,Sakayyah Hausa Novel Complete,60,SHAKUWAR YARINTA COMPLETE HAUSA NOVEL,20,Support,26,Tabarmar Kashi book 2,7,Teach and guide,8,TUMFAFIYA Complete Hausa Novel,1,TUMFAFIYA Hausa Novel,50,TUMFAFIYA Hausa Novel Complete,19,UNCLE DATTI Hausa Novel Complete,1,Watsapp,3,Waye Mijina Hausa Novel Complete,5,WEB LANGUAGE,1,WEB TUTORIAL,2,Yar Aikin Karuwai Book 1 Complete,1,Yar Aikin Karuwai Book 2,1,Yar Aikin Karuwai Hausa Novel,1,Yaya Mata Complete Hausa Novel,22,Zafafa Biyar Novels,7,
ltr
item
NAGARTA24 || job || npower || crypto currency || arbitrade || loan || teach and guide || support ||: TABARMAR KASHI Book 2 Page 64
TABARMAR KASHI Book 2 Page 64
https://blogger.googleusercontent.com/img/b/R29vZ2xl/AVvXsEhUFO9kjD1Urakmch6xkgrRfE3Yc6c1XVPjhn_68P7_8VHsei6ycB_bIF2P95TaByI_V1xrfcgUlck1LirmDQT7wRWQZtfosiOaeV-9qCGQ7eQPndluNTevnjPSJ1T755-8AStFczGbCpFmhRwNFhHG7fTZeTq2DZqH1WCkG3rUWeXlUolmsDN1S-gkSqqt/s1600/img_1696515891961.jpg
https://blogger.googleusercontent.com/img/b/R29vZ2xl/AVvXsEhUFO9kjD1Urakmch6xkgrRfE3Yc6c1XVPjhn_68P7_8VHsei6ycB_bIF2P95TaByI_V1xrfcgUlck1LirmDQT7wRWQZtfosiOaeV-9qCGQ7eQPndluNTevnjPSJ1T755-8AStFczGbCpFmhRwNFhHG7fTZeTq2DZqH1WCkG3rUWeXlUolmsDN1S-gkSqqt/s72-c/img_1696515891961.jpg
NAGARTA24 || job || npower || crypto currency || arbitrade || loan || teach and guide || support ||
https://www.nagarta24.com.ng/2023/10/tabarmar-kashi-book-2-page-64.html
https://www.nagarta24.com.ng/
https://www.nagarta24.com.ng/
https://www.nagarta24.com.ng/2023/10/tabarmar-kashi-book-2-page-64.html
true
1779421581242976301
UTF-8
Loaded All Posts Not found any posts VIEW ALL Readmore Reply Cancel reply Delete By Home PAGES POSTS View All RECOMMENDED FOR YOU LABEL ARCHIVE SEARCH ALL POSTS Not found any post match with your request Back Home Sunday Monday Tuesday Wednesday Thursday Friday Saturday Sun Mon Tue Wed Thu Fri Sat January February March April May June July August September October November December Jan Feb Mar Apr May Jun Jul Aug Sep Oct Nov Dec just now 1 minute ago $$1$$ minutes ago 1 hour ago $$1$$ hours ago Yesterday $$1$$ days ago $$1$$ weeks ago more than 5 weeks ago Followers Follow THIS PREMIUM CONTENT IS LOCKED STEP 1: Share to a social network STEP 2: Click the link on your social network Copy All Code Select All Code All codes were copied to your clipboard Can not copy the codes / texts, please press [CTRL]+[C] (or CMD+C with Mac) to copy Table of Content