Makauniyar Kaddara 69

 *Page 69*

 *Page 69*



...........Rayuwa ta cigaba da tafiya cikin farin ciki gasu Zinneerah, babu abinda zatacema ALLAH dasu Hajiya iya sai godiya, dan itakam sun bata ƙyauta da har abadan bazata daina alfahari da tutuiya dasu ba. Kwananta goma dayin arba'i su yaya Gajeje suka shirya komawa Danya, duk da dai Inna bata warke bane sarai Alhmdllh jikinta yayi sauƙi sosai, dan kullum sai Dr Mahmud yazo safe da dare ya sake dubata. Tana ɗan magana da motsa jikinta, tafiya ce dai babu kam kafafun zuwa gidan malamai sun mutu.

     A ɗan zaman nan gidan Zinneerah babu fashi kullum sai tayi kuka. Musamman idan AK ya shiga ya gaisheta ko aka kawo wani lafiyayyen abinci aka bata, ko Zinneerah ta shiga da yaranta abin sha'awa gaisheta. Balle ta zauna dan su ɗanyi hira ta dinga haɗiyar zuciya kenan kamar budiddigin ƙwaɗo. Little kam baya minti goma bai shiga ɗakin ba inhar yana gida. Dole kuma take kulashi saboda shi babu ruwansa haye mata jiki yake, sai ma idan Zinneerah ta ganine taita masa faɗan karya ƙarisa mata uwa, daya faki ido kuma zai sake komawa, ko ganinta a zaunen ne shike ɗaukar masa hankali oho😂..

           A dalilin zaman Inna maman sadiq kuma tazo gidan sau kusan uku dubata ita da mmn halima. Na kusan ƙarshene sukazo harda mmn sakina da matar naziru da ayanzu suketa zuminci da Khalipha, dan sun zama abokai tunda ba wani girman Khalipha ɗin yayba shima auren gata ne Abba dama yay masa.

    Shatara ta arziƙi AK da Dr Mahmud suka haɗa musu, sannan kuma suka tafi gaba ɗayansu musu rakkiya harda AK da Dr Mahmud dan sunason zuwa su gaida Baba duk da baima jima da zuwa ya dubata ba shi da ƴan uwansa, sai su Meenal da suka maƙale. Tarba suka samu mai ban mamaki daga amaryar baba da dangi, kowa yana sambarka da ƴan biyun Zinneerah dan hada yawon arba'in duk ta haɗa tazo. Ga Sa'a ma na fama da nata laulayin cikin sai fatan sauka lafiya.

      Anan su AK suka barsu zasu kwana biyu, ya juya shi dasu Jamal da Dr Mahmud kowa na kewar matarsa. Da farko little ya maƙale binsu zaiyi, mi kuma ya gani harya shiga motar tama ɗakko masa kayansa sai cayay kuma zai zauna wajan su Anam indai badasu za'a koma Kano ba.

        

      Kwanansu huɗu a Danya Zinneerah da Sa'a suka shiga lungu da saƙo gaida ƴan uwa da abokan arziƙi, duk inda suka gitta sha'awarsu ake ana san barka dan sun zama abin kwatance ga kowa. Alkairi kam duk inda suka shiga sukan ajiye gwargwadon ƙarfinsu su wuce ana saka musu albarka. Baba kansa yana cikin farin ciki da kasancewar ƴaƴansa cikin kwanciyar hankali. Mutane nata zuwa ganin Inna ana yadda mata habaici akan ga wadda ta tsana da gallazamawa nan ta zama silar samun lafiyarta ai.

      Babu bakin magana ga Inna Asabe danya musu murus, sai kukan zuci da haɗiyar zuciya kawai. 

    Randa suka cika kwanaki huɗu babu daɗi babu ƙari sai ga Moos'ab yazo kwasarsu. Zinneerah bataso hakaba dan catake zaiyi haƙuri sukai 1week ɗin data roƙa. Amma hakanma sun gode dan batai zaton zai bari ba. Aiko data dawo tasha mitar shi an barsa shi kaɗai a gida kamar mara gata.

         Dariya ta dinga masa da bashi haƙuri. daga ƙarshe tabi hanyar data dace wajen lallashin abinta. Gaba ɗaya gidan yanzu sai take jinsa wani iri da duk suka tafi, sauƙinma ta taho da ɗiyar Yaya gajeje zata ɗan mata hutu mai suna Saliha. Yarinya ce ƙyaƙyƙyawa kuma nutsatstsiya, shekaranta goma kwata-kwata. Tarbiyan yarinyar yasa ta shiga ran AK yace makaranta zai nema mata dan tazo kenan bazata komaba. Sosai Zinneerah taji daɗin hakan kuwa taita masa godiya.

         Bayan sati uku da dawowarsu daga Danya da ƙyar ya barta taje Minna wajen Gwaggo Maryama. Aiko taji daɗin wannan zuwa harda ƴar ƙwallarta. Kwanansu biyu acan suka dawo, Hajiya iya ta sake jajubarta suka tafi bauchi. AK nata fushi batabi takansaba tace yawan arba'in Zinneerah keyi dana aure daya hanata yi. 

                Yama zai yi da tsohuwarnan inba yay gum da bakinsaba. Dan yana tankawa zatama iya ƙwaƙulo wasu dangin a wani garin tace Zinneerah taje. Satinsu ɗaya a can suka dawo. Shima kuma sai ya fara musu shirin zuwa Morocco daga can zasu wuce London su ɗan huta tunda little sun sami hutu. Fatansa kuma ya tarkato su Mammah su dawo a maida aurenta da baffah tunda yaga sun sakko an daina faɗan masoya saita waya idan sun kira juna da nufin gaisuwa. Mahma kuwa gida zai saya mata tai zamanta kusa dasu.


  *_MOROCCO_*


   Wannan shine karon farko na zuwan Zinneerah dangin kakarsu AK, tako sami tarba ta mutunci ga mutanen har taita mamaki, yaranta kowa yana nuna musu so da ƙauna abin birgewa. Yaran Mahma kuwa kamar sun santa dama can, dan janta suka dingayi a jiki ita dasu little. Magana kuwa sai da turanci, waɗanda basaji sai larabci sai dai ake musu tafinta da Zinneerah dan ita dai ba iyawa taiba sai abinda ba'a rasaba na islamiyya, wanda bai wuce gaisuwa ba da kalmomi.

     Satinsu ɗaya cif suka wuce london cike da kewarsu, inda acanma suka sami tarba ga Mahma da Mammah. Kwanansu biyu da isowa Adilah da Huzaifa suka iso suma. Ai fa sai gida ya kacame da farin ciki bakin Mammah tamkar zai yage dan farin ciki. dan itama Adilah fama take da ciki harya fito abinsa.


    Sunsha hutu da soyayyarsu a london kafin su tattaro kuma su dawo gida dansu little sun koma school. Satinsu biyu da dawowa aka maida auren Mammah da Baffah.

        Zo kaga farin ciki wajen yaran gidan, dan koba komai AK ya cancanci su girmama mahaifiyarsa su kuma sota dan shima yana girmama nasu. Ba'a wani tsaya ja'inja ba Mammah ta tarkato kayanta ta dawo Nigeria gidan masoyinta bisa rakkiyar dangin mahaifinsu.  

           Aiko sai ga baffah da mammah an ƙara shimfiɗa sabuwar soyayya, ita da abokan zamanta kuwa sai dai sambarka. Dan tana ƙoƙarin danne kishinta kamar yanda suma suke danne nasu kodan yara da nasihar da hajiya iya ke musu kullum babu gajiyawa. Dan babu abinda zatace da UBANGIJI sai godiya na sake haɗe mata kan family ɗinta da yayi, bayan gwagarmaya da jarabawar data sha a shekarun baya wajen ganin ta haɗesu waje guda hakan bai samuba sai da iyaka tazo.

    Mahma kuma AK ya saya mata gida anan kusa dasu, da yake mutumce maison jama'a saita tarkato ƴaƴan dangi daga kaita dansu tayata zama.


★★★


        Daga haka rayuwa ta cigaba da turawa Zinneerah na cigaba dama AK naci akan dawowar Farah. Duk da yana ɓata mata rai haka take sake dawowa ta ƙara masa maganar.

     Sai gashi a wasa-wasa dai sai da Farah da Zakiyya suka cika shekaru biyu cif da maimartaba ya basu. Zuwa lokacin ƴan biyu babu inda basa zuwa da kafafunsu, yara sunyi ɓul dasu masha ALLAH ga wayo dan sun hau karatun little.

     Naci Zinneerah ta cigaba da masa akan dawowar Farah ɗin yana basar da ita har sai da ta ƙara wata uku akan shekara biyun mai martaba sannan yace mata zaije. Amma babu rana.

    Wannan maganar tasata tunkarar hajiya iya da batun da Baffah a karo na farko. Albarka suka dinga saka mata. Uncle Ahmad yace insha ALLAH da kansa zaije ya ɗakko Farah ɗin.


★__________★


     Aiko kamar yanda Uncle Ahmad yay alƙawari bayan sati guda da wannan zance batare da sanin AK ba sai gashi tare da Farah. Lokacin suna a barandar gidan su duka da yammaci iskar la'asar na kaɗasu. Boss na zaune yana harkar business ɗinsa a lap-top duk da ma su Anam na hanashi, dan sai hawa masa jiki suke suna ƙirniya. Zinneerah na gefensa tana koyama Little homework.

        Duban Zinneerah yay yana nuna mata Anam data haye masa dokin wuya. “Mami kizo ki ɗauke kakarnan taki kona jehota ƙasa ta isheni ALLAH, ta hanani aiki”.

     Dariya Zinneerah tai saboda yanda yay maganar a marairaice tana kallon uban da ƴar. Tace, “Idan ka jeho Granny ƙasa aiko ka koma Morocco da ƙafa dan takwararta ba ɗaga maka ƙafa zatai ba”.

     Murmushi yay yana sauke Anam ɗin da faɗin, “Madam rikici ba, ai saita saukemin Nigeria a kaina wlhy. Inaga dai bara na haƙura da aikin nan kawai dan ba barina zasuyi ba, shi baffah ma neman rikitamin system ɗin yake”.

     Little daketa tunzura baki gaba ya gaji da homework ɗin yace, “Daddy na ɗakko ball muyi?”.

       “Kokuma kakan ball ɗin ba”. Zinneerah ta faɗa tana nuna masa littafin gabansa. sake tunzura bakin yay yana kallon AK kamar zai kuka. Yanda yay ɗin ya bama AK dariya. Shima sai ya duba zinneerah yana marairaicewa kamar yanda little yayi. “Mami a tausaya mana a barmu mu huta. Itafa bokon nan iyakarta duniya, kuma mu ba dangin mango park ba”.

          Ta buɗe baki zata bashi amsa motar Uncle Ahmad dake tare da Khalipha da Farah ta shigo gidan. Shi AK da farko ma ya zata ko Suhail ne babban ɗan Uncle Ahmad ɗin dan nan ɗin gidan zuwansa ne sosai tunda ya baro Turkey. Dan haka yayma Zinneerah nuni da hijjab ɗinta dake gefe dama ajiye. Sai da yaga Khalipha ya fito da Uncle Ahmad ɗin ya sashi miƙewa tsaye babu shiri. Yana ƙoƙarin nufarsu Farah ta fito a motar. Ta rame sosai ta canja tamkar ba itaba. A take fara'ar fuskar AK ta ɓace ɓat. Sai dai babu damar magana saboda Uncle Ahmad.

        Sannu da zuwa Zinneerah taketa musu fuskarta ɗauke da murmushi. Uncle Ahmad ya ɗauka little yana faɗin, “Uhm babana zoka samin albarka”.

    Shima Khalipha sai ya ɗauka Amaan yace, “Nima taho samin tawa albarkar babana tunda abin hakane”. Dariya aka sanya musamman da Anam taje jikin AK itama ta maƙale. Shi dai ko murmushi baiyiba.

     Ita dai Zinneerah nufar Farah dake kallonsu tamkar tana hawayema tayi tana mata sannu da zuwa cikin fara'a. Yanda ta amsa mata kamar a kunyace sai ta bata mamaki, ta kama hannunta sukabi bayan su AK ɗin da har sun shige ciki.


     Sashen AK suka nufa, sai da ta raka Farah sannan ta dawo ta koma sashenta tasa Saliha haɗa abin sha da motsa baki takai musu, ita kuma ta ɗauka abincinsu na dare da aka girka gaba ɗaya ta nufi sashen nasa. Ta iske Khalipha nata tsokanar Saliha dan mutuniyarsa ce sosai. Bayan ta gama zata wuce ta kirata tazo ta tattara yaran suje. Ɗaukar Anam tayi da tisa ƙeyar little da Amaan suka fita. Itama ta gama shirya abincin a dining zata fita Uncle Ahmad ya dakatar da ita.

       “Dawo ki zauna Inno ai maganar ta shafeki kema”. Dawowa tai babu musu ta zauna.

         Bayan Uncle Ahmad ya buɗe taron da addu'a ya fara musu da nasiha mai ratsa jiki, kafin ya duba AK da yay kicin-kicin da rai. “Abdul-Mutallab ayi haƙuri, a cigaba da haƙuri a ƙara haƙuri. Ita ƙaddara haka take babu abinda ya isa tsaidata ga bawa. UBANGIJI ya riga ya hukunta faruwar hakan a garemu tilas. Hakan jarabawa ce. Maganar tone-tone bama ta tasoba tunda anyi komai ya wuce sai ayi haƙuri kuma a sake kafa sabuwar rayuwa. Ga Farah nan ta dawo cikin iyalinka. Ina fatan zaku manta da komai ku ringumi junanku kuyi haƙuri. Darajar haƙurin da zakuyi sai ALLAH ya ƙara muku kwanciyar hankali da farin ciki kaji”.

       Kan AK a ƙasa yace, “Dady taya zan zauna da wadda bata amshi laifinta ba, girman kai ya hanata neman yafiya ga wadda suka zalunta duk da rawar gani data taka wajen hana katsewar igiyar aurenta”.

     Shashshekar kukan Farah ne ya fito, tace, “Wlhy ba girman kai ya hanani neman gafarar Zinneerah ba kunya ce kawai da nauyin girman laifin da aka aikata mata, duk da ALLAH shine shaidata ban sanma wadda aka sakama ciki ba. Amma inajin nadama da kaico da kawunanmu saboda son zuciya. Zinneerah ki yafe mana domin ALLAH badan halinmu ba. Duk da nasan munzo a makare ga neman gafarar taki. Amma dan girman ALLAH ki gafarcemu, gwiyawunmu bisa ƙasa........”

      Sauron katseta Zinneerah tai da faɗin, “Haba aunty Farah, wlhy ni ban rikeku ba tun a waccan ranar komai ya wuce a gareni. Sai dai muyi fatan ALLAH ya yafe mana baki ɗaya. Ya kuma bamu zaman lafiya da haƙuri da juna”.

      Da amin duk suka amsa. Yayin da AK ya ballama Zinneerah harara. Murmushi kawai tayi ta ɗauke kanta. Shima AK ɗin gafararsa Farah ta nema, duk da dai bai kulataba bai kumace uffanba. Uncle Ahmad dai ya ɗora musu da sabuwar nasiha data ƙara sanyaya jikinsu.

    Da ga ƙarshe ya rufe taron da addu'a suka tattara suka tafi aka bar Farah anan. 

       Tashi Zinneerah tai zata barsu AK ya dakatar da ita wai ta haɗa masa ruwan wanka. Kafinma ta nufi ɗakin shi ya shige. sai taji duk babu daɗi ga Farah zaune ko kallonta baiyiba.

      Tayi tunanin Farah zata ɓata rai, sai taga kawai ta bisa da kallo tana murmushi da share hawaye a kaikaice. Ta maido dubanta ga Zinneerah datai shiru kanta a ƙasa ta kasa tashi. “Mamin Abdul kije karya ga kin ɓata masa lokaci, sai dai ki sake roƙamin shi gafara dan ALLAH, da kuma keys ɗin sashena”.

       “Kiyi haƙuri dan ALLAH aunty Farah komai zai wuce. Kinsan dai halinsa kinma fini sani. Keys kuma suna wajena ma bara na ɗauka miki”. Tai maganar tana nufar hanyar ƙofar fita. Da sauri Farah ta dakatar da ita tana miƙewa. “A'a kinga jeki ki cika umarninsa zanje na jiraki a general falo”.

        Kai Zinneerah ta kaɗa mata kawai cike dajin nauyi ta nufi ɗakin nasa. A cike fam ta iske AK da haushi. Kamar jira yake tana shigowa ya balbaleta da masifa wai ta wulakantasa bayan ya faɗa mata bukatarsa. Hankalintane ya tashi dan faɗa sosai yakeyi. 

       Ganin abin karya juye mata yasata faɗawa jikinsa ta manne bakinsu waje guda ta shiga lallashi ta hanyar da yafi buƙata. Ai ko saigashi yay bulum harma yana neman zurmawa. Da ƙyar ta ƙwace kanta ta na masa dariya. Ƙwafa yay da fadin, “Zan kamaki ne ai, zakimin bayani dalla-dalla tunda na fara zama abokin wasanki”.

    Ita dai shigewa toilet tai tana masa dariya.


     Da taimakon su Saliha Farah ta gyara sashenta, Zinneerah takai mata abinci da kanta tana sake mata sannu da zuwa. Dan harda yara taje mata. Jawosu Farah tai jikinta ta rungume ƙwalla na cika mata ido. Little kam daga jikin Zinneerah ya makale yana gaisheta. Duk yanda taso yazo gareta yaƙi dole ta haƙura. Anan ta bar mata Amaan da Anam suka fita ita da little tana masa faɗa.

        Buɗar bakin yaron nan sai cewa yay, “Mami ni bana sonta...”.  Baima rufe bakiba ta make bakin har yana fashewa. Ta shiga masa masifar da ta kai har AK dake falonsa fitowa dan suna a general falo ne tsaye.

       Kallon yanda bakin little din ke jini yana kuka yayi. “Lafiya? miya miki haka harda fasa baki?”.

       Ranta a ɓace tace, “Idanma ya sake maimaita abinda ya faɗa wlhy haƙwaran zan zubar ƙasa. Dalla matsamin na wuce mara mutunci”. Ta faɗa tana turesa tai shigewarta sashenta.

      Da kallo AK ya bita ransa a ɓace, dan ya tsani ana dukar masa yara itama kuma ta sani, yakance ko laifi sukai ta zaunar dasu ta musu nasiha bawai dukaba dan baya magani. Hannun little ɗin ya kama suka shige sashensa yana tambayarsa miyayi mata?.

     Abinka ga yaro saiya maimaita abinda ya fadama Farah ɗin. Faɗa shima yay masa da nasiha akan karya sake itama Momy ce. Yaron sai yace bazai sakeba ya kuma bashi haƙuri. Tare da cewa bara yaje itama Mami ya bata haƙuri.

     Cayay ya barta idan sun dawo salla saiya rakashi ya bata.


Haka kuwa akai bayan sun dawo salla sashen Zinneerah ɗin suka shiga shi da little. Acan ɗakinta na ƙurya suka sameta ita da Saliha suna magana. Saliha ta gaishesa ta fice. Zama yay bakin gado little kuma yaje gabanta ya durƙusa. “Mami kiyi haƙuri bazan sakeba dan ALLAH”.

    Shiru tai masa tamkar batajiba sai da AK ɗin yace tunda ya baki haƙuri ba kuma sai ya wuce ba.

      “Yayanmu so kake na haƙura gobe ya sake kenan? Shi ɗan karamin nan dashi har yasan wani cewa baya son mutum?”.

      Kuka little yasa mata yana ƙara bata haƙuri hannayensa riƙe da kunnuwansa. Nanma dai baki AK ɗin yasa harta haƙura. Little ya fita ya barsu a ɗakin saboda aikansa da tayi wajen Saliha.

      Mikewa tai tana ninke abin sallar da take kai zaune, AK dake binta da kallo yace, “Kemafa masifanki yayi yawa”.

     Baki ta kumbura gaba amma batace komai ba. Hakan yasa AK kamota ta faɗo jikinsa. Lips ɗinta ya ɗalla da yatsunsa yana faɗin, “Dan wulakancin kin fasamin bakin yaro harda jini”.

    Murmushi tayi tana cusa kanta a ƙirjinsa da faɗin, “Kaga gobe idan zaima wani rashin kunya sai ya tuna da wannan ai”.

      “Uhmyim, to ai ba ƙyaleki zanyiba sai na rama masa”. Yay maganar yana ɗaura lips ɗinsa kan nata. Daga hukunci aka zarce soyayya. Daga karshe dai sai da aka kai gayin wanka...........✍

     


*_Dan ALLAH ku saka ɗan uwana addu'oinki na yinin yau, ya ɓata an rasa inda yake kuma babu labarinsa. ALLAH ya bayyanashi, ya karama mahaifiyarsa damu nutsuwa. Ya kuma tsaresa a duk inda yake. Ya bashi kariya daga abokan banza ko miyagun mutane. Tare da sauran al'ummar musulmi baki ɗaya_*😭🙏🏻



*_ZAFAFA BIYAR  NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*


Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.


*_★ AL-ƘIBLA_*💘

_Na Safiyya Huguma_


*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖

_Hafsat Rano_


*_★ DALAAL_*💝

_Na Miss xoxo_


*_★ UBAYD MALEEK_*💓

_Na Mamu gee_


*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔

_Na Bilyn Abdull_


Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.


Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300

Biyu____400

Uku_____450

Huɗu____500

Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


*_08085405215_*


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


  0903 234 5899


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍


*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*


*_TYPING📲_*



*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*



_______________________


COMMENTS

Name

ADSENSE,4,Airtel,1,ANDROID,9,AQIDARMU Book 1 Complete Hausa Novel,1,AQIDARMU Book 2 Complete Hausa Novel,1,Arbitrade,4,Arbitrage,1,AUREN MU Complete Hausa Novel,1,Babban Yaya Hausa Novel Complete,1,Babu So Complete Hausa Novel,1,Bakar Inuwa Complete Hausa Novel,27,Billyn Abdul Novels,7,BLOGGING,13,Business online,10,Crypto currency,17,Dare Daya Hausa Novel Complete,1,Daudar Gora Book 1 Complete Hausa Novel,48,Daudar Gora Book 2 Complete Hausa Novel,95,DOWNLOAD,2,Duk Karfin Izzata Book 2 Complete Hausa Novel,34,Education,3,Email,1,Facebook,4,Finance,1,Furar Danko Book 2 Complete,9,Furar Danko Complete Hausa Novel,31,fyade hausa novel by maman teddy,1,fyade hausa novel Complete,1,Gidan Haya Hausa Novel Complete,6,Gidan Haya Complete Hausa Novel,4,Gidan Haya Hausa Novel,1,Gidan Kwarata Complete Hausa Novel,1,Glo,1,Google,1,GURBIN IDO Complete Hausa Novel,1,Hamshakiya Hausa Novel Complete,25,JARABABBEN NAMIJI Complete Hausa Novel,1,Jikar Maguzawa Complete Hausa Novel,23,Job,7,KASUWANCI NA Complete Hausa Novel,1,Layikan waya,2,Loan,8,MA'AIKACIYAR GOMNATI Complete Hausa Novel,1,Makauniyar Kaddara Complete Hausa Novel,70,Mufeedah Complete Hausa Novel,25,Namijin Zuma Complete Hausa Novel,26,nihaad complete,62,Nihaad Complete Hausa Novel,62,nihaad hausa novel,62,Npower,13,Pc Tools,2,Qamshi Hausa Novel Complete,14,Raina Kama Complete Hausa Novel,29,Sakayyah Book 2 Hausa Novel Complete,30,Sakayyah Hausa Novel Complete,60,SHAKUWAR YARINTA COMPLETE HAUSA NOVEL,20,Support,26,Tabarmar Kashi book 2,7,Teach and guide,8,TUMFAFIYA Complete Hausa Novel,1,TUMFAFIYA Hausa Novel,50,TUMFAFIYA Hausa Novel Complete,19,UNCLE DATTI Hausa Novel Complete,1,Watsapp,3,Waye Mijina Hausa Novel Complete,5,WEB LANGUAGE,1,WEB TUTORIAL,2,Yar Aikin Karuwai Book 1 Complete,1,Yar Aikin Karuwai Book 2,1,Yar Aikin Karuwai Hausa Novel,1,Yaya Mata Complete Hausa Novel,22,Zafafa Biyar Novels,7,
ltr
item
NAGARTA24 || job || npower || crypto currency || arbitrade || loan || teach and guide || support ||: Makauniyar Kaddara 69
Makauniyar Kaddara 69
https://blogger.googleusercontent.com/img/b/R29vZ2xl/AVvXsEgDgHDniA3YGcYeEScpYkrv8OVBgucHl9MUbm5z3lwZU_K7qqgU6ZPiWB4wE-7aWZC-I6d-cxXOHaunvvaPOpyTng19J5vfSTqvK6T_bMussypIOdh35HXj9VFjJJOE2FCFZKZM8elxOhq61axKw3AYFr56NygW5wicb1Lf4pxBZ0f-Z405fkao94_AfTTL/s320/img_1696965128975.webp
https://blogger.googleusercontent.com/img/b/R29vZ2xl/AVvXsEgDgHDniA3YGcYeEScpYkrv8OVBgucHl9MUbm5z3lwZU_K7qqgU6ZPiWB4wE-7aWZC-I6d-cxXOHaunvvaPOpyTng19J5vfSTqvK6T_bMussypIOdh35HXj9VFjJJOE2FCFZKZM8elxOhq61axKw3AYFr56NygW5wicb1Lf4pxBZ0f-Z405fkao94_AfTTL/s72-c/img_1696965128975.webp
NAGARTA24 || job || npower || crypto currency || arbitrade || loan || teach and guide || support ||
https://www.nagarta24.com.ng/2023/10/makauniyar-kaddara-69.html
https://www.nagarta24.com.ng/
https://www.nagarta24.com.ng/
https://www.nagarta24.com.ng/2023/10/makauniyar-kaddara-69.html
true
1779421581242976301
UTF-8
Loaded All Posts Not found any posts VIEW ALL Readmore Reply Cancel reply Delete By Home PAGES POSTS View All RECOMMENDED FOR YOU LABEL ARCHIVE SEARCH ALL POSTS Not found any post match with your request Back Home Sunday Monday Tuesday Wednesday Thursday Friday Saturday Sun Mon Tue Wed Thu Fri Sat January February March April May June July August September October November December Jan Feb Mar Apr May Jun Jul Aug Sep Oct Nov Dec just now 1 minute ago $$1$$ minutes ago 1 hour ago $$1$$ hours ago Yesterday $$1$$ days ago $$1$$ weeks ago more than 5 weeks ago Followers Follow THIS PREMIUM CONTENT IS LOCKED STEP 1: Share to a social network STEP 2: Click the link on your social network Copy All Code Select All Code All codes were copied to your clipboard Can not copy the codes / texts, please press [CTRL]+[C] (or CMD+C with Mac) to copy Table of Content