Umma harda uban sauri tana gaba ta bata rai Kar a kawo Mata wasa,Kadada tana ganinta tace kin dace da Women leader
Umma harda uban sauri tana gaba ta bata rai Kar a kawo Mata wasa,Kadada tana ganinta tace kin dace da Women leader
kyanki Kawai Yan siyasa su dora ki a saman mota a tafi campaign, Umma bata kulasu ba Kar ma a kawo Mata Wasa,nace Kar Wanda ya kulata ku kyaleta,Safna anci gayu cikin wata Arabian gown me tsada da kyau tayi kyau mashaallah,Umma fuuu ta wuce mu,Safna tazo wuce mu na dafa kafadarta tare da juyo da da ita na jawota baya na tsaidata gabana na kalleta Ido cikin Ido nace local maza ake gani Haka direct hajiya baki booking ba yau ko ke wace baza ki ganshi ba,Safna da rashin kunyarta kin San wace ni? nice wacce Jawad zai au.....Hammatar uwarki nace cewar Tahantsi,Safna Tace what? Kadada tace na badawa Hammatar uwarki gishiri,Safna zagin ma dariya ya bata ta zaci Wasa muke mata ta fara dariya,sai da Tahantsi ta shararo Mata wata doguwar ashariya Mai lafiya,Safna tace kaiiiii ko a tiktok ban taba Jin irin wannan ba,ware....Kadada ta furta tana zaro Mata ido ta tare ta gaba da gaba kamar zata hada kirjinta da nata,Safna tace ke yarinya na fiki iskanci, Safna gaba na ta dawo dama Umma ta nuna Mata nice matar wuyan rigata ta damka ji kake keeeeeeeet....ta tsarge Min riga sai bra a waje Allah yasa nasa tight,Jawad a dole ustaz Wai Subhannallah... Subhannallah ya bude kofa ya koma ciki bazai gani ba,Umma ta Fara dariya kafin ta karasa har taga Safna a kasa an Mata budu budu,Kadada gidan karfi,Tahantsi ta koma daki da gudu ta dakko almakashi sabo da rigar Safna Arabian gown ce za a Sha wahalar tsargeta,Umma sai dukan bayan Kadada take tana saketa wlh, Tahantsi tana zuwa tayi tafiyar ruwa da Umma tayi gaba dama ba karfi sai ta fadi turum a kasa,Ni tuni na koma ciki,su Kadada na bari sai da Suka yiwa Safna fata fata da Riga ga duka,Kadada tace ebo min kasa a wajen bishiyu yau sai taci kasa,sai na tuna Mata wasan Yara,aka ebo Mata kasa Safna tana ta ihu tana bada Hakuri tace wlh bazan dawo ba dama na hakura da shi Umma ce tace zata min hanyarsa sai da suka cike Mata Baki da kasa ga shegen duka taci dan muguntar Kadada har tasa Almakashi zata yanki kunnen Safna kadan,Safna ta fashe da kuka wiwi tana bada Hakuri sai ta fasa tace duk ranar da ko da Wasa Kika dawo gidan Nan sai mun yanke Miki kunnuwa tunda bakya ji
Ina ji kuyi hajuri,Umma tashi tayi tana masifa ta koma palon Jawad tana fada Masa cike da masifa yace please karki dameni ni nace kizo? Me ta miki Ina ruwanki da matata Wai,Mene hadina da ke? wallahi daga yau duk abinda matata ta Miki ba abinda ya dameni tunda baki ja mutuncinki ba haka Kawai kin tsaneta babu dalili Ina ta Miki uzuru bakya gani, Zaki dawo ki kawo min wata gida wallahi ko basu Mata komai ba ta jira sai na sa an daureta har ta Isa tazo gidana ta yagawa matata Kaya, yanzu da a gaban maza ne shike nan an cuceni to ta jira Kiran kotu sai mun zauna a kotu,kina abubuwa da yawa kyaleki nakeyi sabo da Abba,uwata ce ke ko mun hada jini dake karki sake zuwa gidana daga yau,Kuma wallahi duk wacce Zaki gayyato Wai sai kinga bayana kiyi ki gani in kina da riba, Allah yasa Kuma a cikin Iyayen kannena wata tazo karbar yarta ko danta Zan gani,Umma baki bude tace Iyyeeeee Jawad akan wannan banzar marasa asali? Ni kake ci ma mutunci Haka? Jawad yace ki bar min gida Kawai tun kafin na Miki abinda bakya tunani.
Lokacin na canja doguwar Riga na dawo Ina labe Ina ji sai ga Umma ta fito tana kuka na dinga dariya tana fita taga Safna a dunkule kamar wata barewa kayanta fata fata a jikinta kamar daga bakin Kura aka kamota,Umma ta tasheta Suka shiga mota Suka tafi.
Umma a ranta tace Naga alama da bala'i abin nan bazai yuwu ba Bari na koma zagon kasa bazan kashe ficikata a wajen Malam ba akan Najla ko Jawad tuggu ma Watarana yafi asiri,sabo da haka a muslima Zan fito,Najla Kun shiga Uku da uwarki Zan fara,Suka tafi a motarsu,a gidan Umma Suka ya da zango Safna tayi wanka ta wanke bakinta tace ban taba sanin Mata suna da karfi haka ba ta danne Ni na kasa tashi ba ruwana wannan yaran ba Allah a gabansu,Umma ce ta bata Kaya ta canja sannan ta tafi gida,Safna da kuka ta fada gidansu tare da fadawa iyayenta komai,Maman Safna tace wallahi Hajiya Barira sai ta biya kudin lace Dana bata cin hanci bata Isa taci banza ba barni da ita.
Ban koma dakin Jawad ba sai da ya turo me aiki ta kirani,Ina shiga ya fara masifa dole ne Wai sai kunyi fada,kullum sai anyi fada,ki kiyayeni wlh kina sawa ana rubuta min zunubi ko Ina jiki a waje gashi nan ma wa ya sani ko wani me aikin Yana kusa sun kalli jikinki,Kai ya dafe kullum sai kin Sa an rubuta min zunubi zaki jani cikin wuta,idan da ba aurenki nayi ba babu ruwana dake lahirata nake ji,sai da ya gama nace au duk da haka banyi hakuri ba,hakurin me dama ke kina da hakuri ne,tunda Umma ta haukace ba sai ku kyaleta ba,fadan naki ma na banza kina gani aka yaga Miki riga amma baki iya komai ba ke da Zaki maidata kurma sabo da Mari amma kin tsaya har a yaga Miki Kaya ba uwar da Kika iya Dan Allah tafi ki bani waje,da ba su Kadada shike nan sunci banza ke Ni jeki dan Allah,nace ai....jeki nace ni bana son surutu,Yatsu na nasa a gemunsa Ina Masa Wasa sorry.... sorry Saura kadan yayi Dariya yace ba Wanda Kika Raina sai ni an Miki zigidir kina tsaye yau da wasu mazan suna nan da kin dandana kudarki baza ki dinga jawo min zunubi ba ni ba sonki nake ba a'a lahirata nake ji
Ina murmushi Muna zaune a kujera doguwa Ina kallonsa Yana masifa yace kunna min tv ni ya furta Yana shafa gemunsa,Ina kunnawa nakai hausa tv,suna ta saka wakoki tashi nayi na danyi Naira merly dance yace ai ke sai gyaran Allah shi yasa bazan so ki ba,nace naji ai shi yasa nake abinda Naga dama nima ba so nake ka soni ba, kije kiyi abinci yunwa nake ji sabo da magungunan da nake Sha,tashi nayi na fita na iske su Binta suna ta girkinsu ma,Bintu tace ya Kika ji da jarabar matar nan umma? Nace zata Yi ta gama ne duwaiwakana girma garesu dole a zauna dani daram ba ciwo ba wash bayana,babu riba da zata samu sai wahala,miyar kwai nayi Masa da nama Sai ganye da nasa ciki sannan Masa sakwara sharp sharp na Masa Apple juice na wuce na Kai Masa na iske Yana Sallah na ajiye a zaune,da Kansa yayi Alwala da saka jalabiyya,Yana idarwa yace kije kiyi Sallah nace Yau bana yi ai,harda yatsina fuska shine Kika min girki da hannunki, nace hmm su kadada gobe zasu tafi,baza su Bari suyi sati ba? Sunce su sun gaji ba dadi ba a yawo,Allah sarki kice su shirya Hafeez ya fita da su yawo mana suga gari in yaso jibi sai su tafi,to nace da har na basu naira Hamsim nace su dauki ashirin ashirin,son kudi ai babu kamarki Zaki aikata,abincin na zuba yace kije kiyi wanka sai kizo ki bani
Ni bazan ci abinci kina kazama Kuma kinki wanka tun safe,harda bata rai nace bari naje part dina nayi,yace no kiyi anan yanda Zan tabbatar kizo ki min karya,to bari na kwaso kaya ga tsarabarki Nan ta Sweeden sabo da Baki da mutunci shi yasa ban baki ba kin rainani,Dariya nayi nace na gode ajiye min sai ranar da Zan bar gidan nan idan aikina na Gama sai na tafi da abina idan Zan sake auren wani sai nayiwa angon gayu,hmm waye to? ya tambaya nace Salisu,kamar ya sanshi dan wayo yace Salisu Wai na unguwarku marar tarbiyya? nace ka sanshi dama? yace ba shi ya kaiku Interview na biyu ba? Ai lokacin baka Zo ba Ina ka sanshi? yace ai na fiki sanin Salisu ya taba cutata wasu kudade,na rike baki nace Allah? dama Kai ni Wasa nake ba saurayina bane ba sonsa nake ba Kawai bati na gani na Napep dinsa,har nawa ya cuceka? dubu dari biyar,nace amma Salisu Allah ya kwashe Masa Albarka ba gwara da ni ka bawa kudin ba zai ci ubansa bari naje ganin gida har gidansu sai na je a haka kamar mutumin kirki,Jawad yace saurayinki ne dai nace Ni wlh bana sonsa, ko sonsa nake na daina daga yau ya toshe min hanya da idonsa a tsakar kai, Dariya Jawad yayi yace ke amma yarinya ce gashi har na miki wayo naji sirrinki da salisu
Baki na saki Jin Kawai bugar cikina yayi, na Dade Ina kallonsa karshe nace dole ka iya Business tunda ka iya yiwa min wayo sai yau na yarda kana da talent ba ayi asarar kudin tara ba,ai tunda ka iya Yi min wayo sarkin garinmu kafi karfinsa,tashi nayi na koma can kusa da toilet na saka Hijab tare da cire kayana na daura towel ta cikin Hijab din,yace ni Zaki wa wayo kije ki jika Fuska ki zurma hijab kice kinyi wanka, nace da sassafe fa nayi wanka Kuma tunda nace maka zanyi zanyi,yace ban yarda dake ba,Hijab din na cire na ajiye daga ni sai guntun towel,pant Dina na cire na Miko Masa nace ungo shinshina min kaji,ashar ya dura ba shiri Yana dariya yace kutmar..... Allah ya kiyaye,na shinshina abina nace Allah kanshi kaji,Dariya Muka dinga Yi ba shiri toilet na tafi Zan Shige nace Jawad Nawa,yace Ni ba naki bane nace to na waye? Yace na Hafeez ne da Abeed,Saddiq, Nawwara da Meenat,nace to shike nan zamu gani na shige toilet wanka nayi abina na fito na shirya Yana ta kallona Zan zabo kayan yace a haka Zaki bani sai Kaya sunsa kinyi gumi ya bugi can kasa karni da waye da waye sun bigeni,na taho yace koma ki sa turare har cinya zuba turare nace ba matsala a raina zaka sani ne, nayi yanda yace sannan nazo na zauna Ina bashi abinci Allah Allah yake towel ya balle yace dakko min Abeed Wai Dan Abeed ya fisge min towel nace Kai da baka so na dauke shi,Haka nace bana so ki daunki kanina jini na ki dauko min Kani na dinga ganinsa Naga ya lafiyarsa harda bata rai,tashi nayi na saka Hijab har kasa yake ja naje na karbo Abeed,ya ganshi Yana ta bacci yace maida shi yau baida Albarka, Dariya nayi na maida shi na dawo,na iske Yana waya da doctor cewar yasa a wanke ciwonsa a sake sabon bandage yace to,Bayan ya gama yaci abinci Ina bashi abinci Yana ta satar kallona har ya gama ci yasha magunguna sannan Zan tashi na tafi har da bata rai bayan ya gama kalleni Wai jeki to Zan huta bana so a tashe ni
A cikin kayan da Yace Nawa ne tsaraba na dauki wata simple English gown na saka na fita ya kwanta ya fara bacci,Ina zuwa nace Kadada ku shirya anjima 5pm Hafeez zai kaiku Shopping da yawo kunga gobe sai ku tafi da tsaraba nima dai bai ce dani za a je ba amma Zan biku nasan bazai hanani ba,Fara har yanzu kin manta baki bamu labarin aurenki da raino ba ya akayi haka? Nace aikin kudi nake,baki na rufe na tuna zanyi subutar baki sai nace kunji har Ina mantawa bayan aure Umma tace baza ta rike yaran ba sai dai Jawad ya kawo wa matarsa,Ni Kuma na Isa nace kannensa baza su zauna a gidan Dan uwansu ba,Kadada tace to shike Nan koma mene dai Allah ya kade fitina,murna nayi nace Kadada yau Kika Kira Allah?Kadada Murmushi tayi tace ya kike so to na muku Addua irin taku,anyway Allah ya ganar min da ku,Suka Yi shuru,sai yamma Muka shirya na basu sababbin Kaya Suka zaba dogayen riguna masu kyau sunyi kyau,kitsonsu me kyau Suka ki yafa mayafin su baza su yafa ba,kyalesu dake suna da kyau dukkansu wankan tarwada ne ga hanci kyawawa ne karyar mutum ya kushe su, nace yanzu Kadada baza ku saka mayafi ba? Muna garin Yan uwanmu Lagos gidan arna da yawa mu yafa mayafi tab,nace to Tahantsi kije ki gani Hafeez ya shirya tunda Yara sun tafi Islamiyya Kar su dawo bana nan,Tahantsi taje taga Hafeez ansha wankan kana Nan Kaya da key a hannunsa Yana jiranmu, Muna Fitowa na shiga baya ni da Tahantsi Kadada ta shiga gaba,Muka bar gidan sai da Jawad yaga Shuru Shuru gashi Yana son wanka ya fito ya tambayi me aiki tace ai mun fita, haushi yaji wato bazan fada masa ba bai isa ba gashi ban damu da rayuwarsa ba,yace ba ruwanta da rayuwata tasan banyi wanka da Yamma ba gashi Ina so naje asibiti a canja min bandage,Tsaki ya ja yace to hatsari guda ma yarinya mirsisi ko kwalla bare nasa ran zanga hawayenta,haushi ya sake ji yace sabo da taga Allah ya jarabceni ita ke taimaka min dama idan ka laru da danadam ka shiga uku,Tsaki yaja yayi zuciya yace ko hannun zai balle ya balle ai sunyi asara, yayi Fushi ya jawo wata longslip shirt sharara arsh me colar ya saka Yana ta Kara Wai hannunsa, ko Gaban rigar bai kulle ba yace haka Zan tafi ba ruwana, wandonsa Jean black pencil yayi kyau Kamar ba daga bacci ya tashi ba,Driver yayiwa magana ya fito Yana takama Wayar ma bai iya riketa sosai yace Allah yasa na hadu da Ladies Yan Mata gani nan ku tarbeni tunda matar bata so.
Mota ya shiga harda duba Hanya ko zaiyi Karo da wata lady din,Bai ga kowa ba sai arna, motar mu Kuwa open and close Hafeez ya dauka su Kadada Suka ce sai an Mana ta yan India Hafeez ya bude mota Dake unguwarmu kaf ba layin jaga jaga bane,Kadada ta hango Usir na busa kwallo tace mu siyawa Yara nace so kike su hanamu bacci da busa ba me siya to ni a tsaya zanyi sari na dinga siyarwa a Kauye, Hafeez yace to ai sai muje inda ake sauke Kaya a araha Zaki samu,ba inda akace muje ba sai tafiya sarin Kaya nace yawwa idan naga wani Abu Zan siya na baku ku dinga siyarwa a can Kuna turo kudi mu raba riba a sake sarar wasu a tura,ba wani shopping da Muka je Kadada tace kar mu wani kashewa Yan gidanmu kudi mu siya musu garin kwakwi dan Lagos da manja da sabulu me Sanda Sanda sai omo kowacce a gwada mata gongoni Daya da yankan sabulu daya,Ummiya Kuma Ni me za a siya Mata ne,Kadada tace ga lace masu araha ga kyau ga atamfofi Nima a siya min na kaiwa gyatimata data Hantsi tunda dai ai wata kusan tafi wata kusan,nace Ummiyata tafi karfin haka Kadada ki duba mijin da nake aure,ai Zaki bada kudi a bata ga tsaraba nace to.
Wajen Sarin Kaya Muka wuce yanda Muka tsara haka Muka siyi komai na tsaraba,sai dai ni na siyawa Ummiya takalma masu tsada kala Uku da mayafai Atamfa masu tsada kala Uku lace kala biyu ga wani materials,sai omo masu kyau da sabulai Suma su Kadada iyayensu sun musu siyayya dai dai musali haka Yan Gida ma,na bada turaruka masu kyau kala biyu nace a kaiwa Daddy,Kadada tace Babanki fa nace ke rabu da shi,Kadada tace uhm uhm Najla kome iyaye sukayi iyaye ne wlh karki wulakanta daya baza ki ga dai dai ba,watakil ma shi yasa Umma ta tsaneki, nace kin manta abinda Baba ya yiwa Ummiya a gabanmu muma haka tab a kyale zancen Kawai Kuma wlh ban wulakanta shi ba Kawai dai ni bana Shiga sabgarsa,koma mene lafazinki a kansa ba Dadi ki daina ki barshi a ranki,muci gaba da gashi Bari na siyawa Babana gajeren wando na Shan Iska tunda na rasa me ya kamace shi cewar Kadada Muka dinga dariya,Kadada tace ya kaga kaurin Babana a gajeren wando, Tahantsi tace sai kace sandar bishiya kiyi a hankali kin San Babanki Kadada wargajewa yake a tsakar gida ya kwana jikin bishiya Karki silar da da kunama ko miciji zasu Shige Masa wando mudai ba ruwanmu ato,Kadada tace sai na siya Masa yaji dadin shuka a gona, Gaban wani Igbo taje tace Kai Hafeez ka fada Masa sunan mazantakarka a waje da turanci,Hafeez yace Mene haka Yana dariya,tace gajeren wando buje na manya ai sunansa kenan kana yin sake za aga komai a waje faro, Nace Kadada ke da kin koma wajen Ummiya,ai daga Nan Kauye zamu wuce sai naje ganin gida Zan koma birni,Hafeez ya tsaya ya siyo Wanda Kadada ta nuna kala biyu,aka siyawa ta hantsi sai da muka gama sarin mu sannan aka jibge Mana Kaya a wani katon buhu jumbo me L aka nannade aka sa a mota Muka biya kudi, Muna tafiya Hafeez ya kaimu wani hadadden wajen cin abinci da shakatawa,Muna zuwa Tahantsi tace inzo Lagos banci dodon kodi da tsutsar ruwa ba ai nayi asara,Kadada tace a kawo Kai Hafeez ko Mene Indai da Snail a kawo nace ni dai Banda Ni,baza ki waye ba ai ke cewar Kadada.
Hafeez yasa aka kawo musu shiryeyyen abinci yasha snail wata Miya da wata yellow rice taji kayan lambu,Ni Kuwa Banda Snail nawa,Hafeez ma me Snail ya Saba,Kadada tayi Loma Daya ta dafa min kafada tace baki iya komai ba Dan uwarki shegiyar miyarki sai kace faten garin masara,nace wallahi zamu hadu gobe Zaki bayani,Tahantsi tace rufe Mana baki rannan Haka Kika Mana miyar kubewa Kamar yawun Dan Iska sai kace an wanke Kan dan akuya,Hafeez Yana cin nasa Yana ta dariya yace dan Allah karku tafi gobe,nace zaka Kara kawo mu nan wajen? Yace ae,Kadada tace na yarda da Aljanna gaskiya kukeyi su Fara tunda aka samu irin wajen Nan a duniya ai na yarda a can ma akwai Aljanna,Kuma tunda aka samu Kauye da wahalar rayuwa akwai wuta a can ke Fara karya gwamma take tace Wai bacci akeyi a kabari Kawai a tashi ba hisabi,Allah Ina zuwa sai na nuna Gwamma da yatsa nace karya take tayi magana Kuma na kutuntumata ashar,Tunani tayi tace kai ba yanzu ba sai na sake tabbatarwa, Tahantsi tace karki jawo a tsine miki nace Kuma haka ne ba ruwana kuje da dadin girkinku Fara.
Ni nasan Kadada karya take dan da Tahantsi ce ta fada Zan yarda tafi saukin Kai Kuma da za a samu Kadada ta shiga musulunci da gidan nan sun shiga Uku sai an samu da yawa sun Musulunta sabo da yanda suke sonta sabo da fitsararta da rashin Kunya ko wani aka yiwa Abu a gidan Kadada za a iya turata taje ko Gaban uban waye yasha ashar ba ruwanta,Shi yasa Sam duk haushi suke ji ta zauna a wajen Ummiya amma ba Wanda zai iya Mata dole sai ta koma Kauye nan gani nan bari,shi yasa Ummiya ta janyeta.
Wuri uku Hafeez ya kaimu har dare bayan Isha bamu dawo ba sai 9 pm Muka shigo gida,Muna shigowa Jawad shima motarsa ta shigo bude masa akayi ya fito ya bata rai ko kallonmu baiyi ba ya wuce part dinsa,me aiki zamu sa ya Kai Kaya,Kadada tace matsa ta daga kayan nan zata Yi ciki da shi,Sai ga Farooq ya shigo da motarsa Yana Fitowa yace banyi Niyyar zuwa gidan Nan yau ba sai Kadada tace gobe zasu tafi ko?
Kadada ta jefar da kayan tace Kai irin wannan dirar mikiya haka ba sanarwa Muna can mun tafi cin kayan dadi, Farooq karasowa yayi kusa da mu,ji nayi anyi fito Kamar an busa usur na kalli can inda naji sound din Ido biyu nayi da Jawad yatsansa daya ya daga sama Wai Allah na kallona,Ni Daya na gani dariya nayi na kalleshi,Hafeez ya gani ya kalli Jawad ai sai ya zageshi da Hannu ya Masa dakuwa, wajen ya bari,Ni da Tahantsi ma tafiya Muka yi,Kadada da Farooq Muka bari Kadada tace gobe fa tafiya zamuyi dole Ummiya tana ta fada bai dace ba, Farooq yace to muje mota na baki tsaraba gobe bana gari,tace wasu Yan iskan Samarin Kuwa tab ai ko biyar din rake baza su baka ba,sai zancen banza hauka nake kazo sau Uku na fito ba komai ai Kuwa da yaga harara in ya gallabeni yaji Mari,Farooq ya firgita yace marin saurayin? Fess Kuwa Nawa na mara ai ni duk Samarin da nayi ba Wanda bai tafi gida da yatsuna biyar a fuskarsa ba,Farooq a ransa yace duk zuwa dole na tafi da kyauta wannan jarabar yarinya na rasa me yasa nake nemanta,yace Nima Zaki iya marina? Kadada tace ban gama tantanceka ba tukun amma Kai ai na kyaleka kamshinka yasa na kasa shi yasa ban iya ba amma haushin da ka bani rannan da tuni ban warwareka ba,Kuma yanzu har salo nake a Marin na Marin mutum nace Yi gidan tsohuwarka na juya Ina taku dai dai.
Farooq a ransa yace Allah ya tsare ni tab ,Waya ya dakko guda biyu iri daya amma kowa Kalar tata daban Android din Infinix masu kyau da Leda na kayan sawa kowacce nata daban,baiyi Niyyar bani kudi ba ya irgo dubu ashirin yace gashi kusha ruwa,godiya na dinga Yi nace na gode na gode,ka Dade kayi karko,yayi Murmushi yace golden din ce taki Zaki ga number ta,Kadada ta dura ashar tace samari sai birni Allah idan naje Kauye wani ya kalleni in ba sai naci kaza kazansa Allah yasa ma na koma unguwar su Najla,kamewa tayi ta Sara Masa yanda sojoji suke Yi tace Saura fareti Nan gaba zai biyo baya sai na gama tantanceka,Farooq Yana ta dariya suka yi sallama ya tafi ko ciki bai shigo ba ya wuce abunsa.
Can su Kadada Suka kaure gida da murnar waya,wanka na shiga a room dina lokacin Yara duk sunyi bacci,na iske toilet dina faca faca da jini,raina ya baci matuka nasan Asmau ce ko shakka babu wulakanci ne,Kamar na fashe da kuka haka na danne zuciyata na wanke komai Kal ko su Kadada ban fada musu ba,bayan nayi wanka na fito na Fara shiryawa akwati na bude cikin kayan lefena gaba daya an sharara musu manja,har na ledar an fito da su an zuba,da sauri na bude sauran akwatunan Naga wasu kayan duk an yayyanka su da almakashi wani rigar wani skert din wani wandon,Su Bintu na Kira na tambayesu ko sun ga wani Suka ce basu ga kowa ya shiga ba dake basa zama a part din aiki ke kawo su su tafi,Su Kadada na nunawa Suka ce ki fadawa mijinji mu yanzu wa Muka San yayi da har zamu fara tuhuma,Muka zauna Muna ta alajabi,part din Jawad na tafi da sauri
Ina zuwa part dinsa ban San komai ba ya dauke ni da Mari,sai da idona ya dauke,ciwonsa ya fama tare muka saki ihun,idonsa har ya Kada yayi jajir sabo da tsabar masifar da yake ji,yace ubanwa Kika tambaya da Kika fita? na baki uzini ki fita baki San aure ba? Baki da Ilimin Addini,hannayena na Dora a ka Kar ya sake marina,amma ko kuka banyi ba nace Kaine kace muje fa,kaina yayo da masifa yace ni nace kije? Karya ziki min?
Da sauri nace wayyo Ummiyata karya nake baka ce naje ba Kayi hakuri na rike damatsansa biyu da hannayena biyu Muna facing juna banyi Niyyar bashi hakuri ba amma zuciyata ta kasa dole nace kayi hakuri na fashe da kuka, sai lokacin naji yayi shuru a hankali yace bana son irin wannan ki daina daukan auren nan da wasa addini ba a wasa da shi na fada miki ki daina tunanin lallai sabo da Yara na auro ki,bani da hankali an fada Miki,kin San ba komai nake iyawa ba kin sani in kin San baza ki iya ba ki fada min mana,how dear you da Zaki tafi baza ki fada min ba,ance bazan barki kije bane,sai kin fita baki fada min ba ko ban Isa ki fada min ba,zamana kike ko zaman wasu,Ido na tsira Masa Ina kallon masifa da ruwa ruwanta,nasan nayi laifi nice bani da gaskiya,yatsa ya nuna min wannan ya Zama last warning da Zan miki,da shagwaba Ina dire diren kafafu Kuma Ina rike da damatsansa nace to kayi Hakuri,a raina nace kinyi asara Najla kaddara ta kawoki kowa ubanki yake ci,a garaki ta nan wannan ya garonki ta can na jawa kaina.
Wankan fa yace bana so ya fisge hannayensa yayi tafiyarsa saman bed ya kwanta dake yayi Sallar Isha dinsa,Shuru nayi bai min magana ba Nima ban Masa ba,na gaji da tsaiwa na juya Zan tafi cikin Fushi yace Mene ne Kika shigo da gudu? nace dama zuwa nayi na fada maka kayana na lefe duk an yayyanka rabi wasu an zuba musu manja gashi Nan dai,Yace laifinki ne Allah ne yayi Fushi dake kin fita baki tambayi miji ba shi yasa har wani ya samu dama ya iya shiga ya Miki haka,da kin zauna za a samu a Shiga Kuma wa yace ki bar kofarki a bude Watarana sai anzo an jefa Miki wata masifar a dakinki duniya yanzu ba tsoron Allah ko waye Allah zai tona asirinsa Watarana,Zan siya Miki wasu,sannan kina can Waleed ya bar gidan Nan ya tafi dangin uwarsa masu gadi ne Suka fada min Uwarsa tazo ta dauke shi,nace tab rabu da shi ai wuya ba shegiya bace da ubanta,har Nawwara ta tafi zanje har can na dawo da su idan Suka sake tafiya ba abinda ya dameni,can ma Asif ya ganshi a bayan school shi da Yan iskan abokai suna shaye shaye
Baki na bude nace Allah ya shirya yace ameen ya sake kallona Jawad da naci yace harda yin kwalliya ki shafa su jambaki ke ga kwalluwa ko gashi nan sai zunubi kike tara min Allah ya shiryeki,Dariya nayi ya bata rai yace wannan ba abin dariya bane Zaki jani wutar jahannama ban San hawa ba ban San sauka ba,mutum ko kuka baya Yi sai iskancin banza ya tashi ga abin tausayi baza a tausaya Masa ba,Katuwar mota tayi kuli kuli Dan Niger dani ke Dadi ma Kika ji na mutu ki huta,wallahi ki kiyayi Allah,Dariya na sake yi yaja Tsaki yace in Kinga dama kinyi Niyyar samun lada sai kizo ai kiyi aikinki,Nace ka huce kenan? Ina nan da zafi na turiri nake ma.
Nace Shaddata Fara shike nan, Atamfata wata ja Ina sonta itama an yanka ta,an fama ciwo na yau har kuka nayi gyaran kashin ma Sai da aka sake karya shi aka Dora,nace sannu Allah sarki ni kam lafaya lace Dina idan na tuna sai naji hawaye,Jawad yace a ransa wannan Sam bata tausayina a kasa Zan kwanciyata yau, yace a ransa, bayan na Masa Wanka mun fito nazo Ina shafa Masa Mai Yana lumshe Ido yace hannunki zafi kiyi a hankali sai kace bakya shafa lotion,nasan Kawai fada yayi,a zuciyarsa Kuwa haka yake cewa wayyo wayyo dadi, har ya fito fili nace naji kace wayyo Dadi da sauri ya bude idonsa da ya canja yace wayyo zafi nace ke bakya jin dai dai,kirjinsa nake shafawa na tabo nipples dinsa wani zullo yayi yace zafi wajen ya bugu,,sitiyari ne ya bugi wajen nace sannu yace dakko man zafin can kiyi massaging wajen nan a hankali,ban gane ba na dako nazo na dinga lailaye masa kirji har nipple sai shidewa yake yace zafi.... wayyoooooo zafi....nace tunda wuya kake Sha a bari Mana yace ai bazai warke ba so nake na koma office,Ina ta Abu Daya Yana sheke dadinsa ban sani ba,Ina tayi Yana ta sani Ina wani murjeshi Ina gabansa sai Sannu nake cewa harda hawayen tausayi,ya kusa releasing ban sani ba Naga ya haukace gaba daya duk na rude na zaci ciwon ne yace bani hannunki bani hannunki Yana Shan yaji........Zan mutu Zan mutu Kawai ya damki Boobs dina sabo da rashin wayona nace Yaya ba hannu bane ungo hannuna na Mika Masa ko kulani baiyi ba ya dinga lagude min boobs yace rikeni....rikeni.....Kuma yaki ya bar kirjina ya huta,ni na rude Ina tausayi sai da ya gama kawowa sannan yace Ina hannun? Yaci gaba da rudewarsa na karya,ya rike hannayena na rasa Ina ya samo karfi nace Sannu kasha wahala Yana ta min Dariya a ransa,Yace lullubeni da bedsheet zazzabi nake ji,na lulluba Masa Kansa ne kawai a waje yace dole na koma asibiti gobe a duba,nace gaskiya Sannu Yaya Jawad yau duk kafi bani tausayi yace ashe kina da Imani haka? naji dadi ya yabeni nace Yaya ba Hannu ka rike ba,Yace dan Allah? Wai Ina na rike? Nace kunya nake ji,dama kina da kunya,fuskata na rufe gaba daya,yace to nuna min na gani me na rike idan ba Hannu ba? da gudu na fice Ina ihu wayyoo,Dariya yayi sosai ya sawa kofarsa key ya shige toilet yanzu lafiyarsa ta gudu da kyar yayi wankan tsarki tare da tsarkake jikinsa ya fito Yana ta smiling.
Da na koma bedroom dina na wuce ko su Kadada ban kula ba na wuce na kwanta har bacci ya saceni ban sani ba.
Da sassafe naje part din Jawad Yana ta bacci,na Dan tasheshi ya bude Ido kadan nace su Kadada sun shirya tafiya,da muryar bacci yace da sassafe haka kamar ana korarsu,nace Ummiya tana ta musu waya,yace to bari Asif zaizo ya sasu a jirgi,nace Allah? yace ban sani ba Ina ta murna,jaka ya nuna min me kyau da yake ajiye kudade yace ki Basu dubu dari,Baki na bude yace ae nace to an gode Allah ya Kara budi na dauka naje na basu suka Yi sallama da kowa Hafeez da Ahmad sun Kara musu kyauta,Asif yayi musu komai da kayansu Niki niki suka Isa Kano.
Kafin su Kadada su je gida ma Umma taje wajen Ummiya taje a mutuniyar kirki harda bawa Ummiya hakuri akan farkon zuwanta lokacin kawo lefe,Zama tayi sosai sai da Ummiya ta saki jiki da Umma sannan ta kitsawa Ummiya karya da gaskiya,karshe harda cewa muna godiya wlh yarinya tana reno yanda ya kamata ai bamu taba zato akwai wacce zata iya amincewa a aureta a Bata millions of Naira Kuma a raino,gaskiya kinwa yarki tarbiyya Yara suna can wlh ta musu wanka wanki komai itace ,Munafuki akace idan ya rigaka shiga dakin uwarka sai kaga canji,Ummiya tunani ta lula tana tuna abubuwa da gaggawar auren Yarta da boye boye da ta dinga Yi aka rasa gane Ina ta nufa a Kan auren,Ummiya ranta ya baci wato ni Najla zata yiwa karya,duk abinda nake Mata bata gani,yaran zamani sai a barsu,to Ni na haifeta wannan zaman auren bautar baza tayi shi ba,nikam nayi nawa ya Kare bazan bari a kassara min rayuwar ya ba tunda Najla yarinya ce me ta sani ai Kuwa Bari su Kadada su dawo ai suna hanya Zan bigi cikinsu har can zanje na ganewa idona Kuma na taso yata a gaba, Inshaallah Najla baza ta Kara wata uku a gidan Jawad ba yanzu dai tayi wata biyu bari nayi bincike a nutse lokacin da na gama Zan dakko abata Ina ai Sam baza ta sabu ba bari na fadawa mahaifinta shima yayi bincike haka Ummiya ta Gama sake sakenta,Umma tasan ma tayi nasara sallama tayi tace zata koma dama gidan kawarta tazo ta biyo a gaisa ai an zama daya.
Umma na tafiya Ummiya tace a hankali zanyi bincike ba gaggawa muje zuwa.
Nan na kawo karshen Free pages dina Wanda Suka siya ku jira Update dinku
Masu Sharhi Ina Matukar godiya,a yafeni Wanda Basu da ikon siyen novel Kuma suna min comments amma ban basu kyautar pages ba abin ne sai a hankali
Na gode
AsmaBaffa
08033933642
10/6/22, 22:03 - Buhainat: 🌏JIKAR MAGUZAWA 🌏
51-55
NA KUDI NE
MALLAKIN JIKAR MAGUZAWA PAID GROUP
IN KIN GANSHI A WAJE NA SATA NE.
Official
By
AsmaBaffa
SADAUKARWA NE GA ZAINAB GARBA BUTALAWA
Page naku ne
Ummin Najwa
Nafee
COMMENTS