Furar Danko 74

  𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲   🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗

 


𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗




           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻



𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 7️⃣4️⃣




.........Haka abubuwa suka cigaba da tafiya a gidan Smart da ɓangaren kwallonsa. Dan matuƙa ya dage da training da kuma kiyaye cin abubuwa tare da miƙama UBANGIJI al'amuransa, harda azumin kwana uku yayi da sadaka. Maganar shaƙuwa ko hirar arziƙi kam tsakaninsa da Lulu babu. Babu mai shiga sabgar wani ta ɓangaren lalama, garama shi wani lokacin yakan ɗan tsokaleta ita kuma tai masifa. Idan lokacin salla yayi kuma ko baya gidan zai tura mata text message akan tayi dan ALLAH, tai ma mahaifiyarta kuma addu'a. Sosai yake karya lagonta da hakan shiyyasa a yanzu kam Alhamdullah da wahala kaga lokacin sallar ma ya shige bata tashi tayi ba, daya turo saƙon ko batai niyya ba zata tashi taje tayi. Idan kuma yana gidan zai mata magana nan ma tayi. Girki ma dai kullum da rigima ake yinsa na safe dana rana idan har yana gidan, idan kuma ya fita na safen kawai akeyi ita dama ba damuwa tai da abincin ba, da dare kuma shi dama ba damuwa yay da cin abinci ba balle yanzu da yake sake ƙoƙarin daidaita jikinsa. Kayan shaye-shaye dai duk da ya toshe ko'ina da samunsu hakan baisa zuciyarsa ta samu nutsuwa ba, a duk motsinta kaffa-kaffa yake yi, ita kuma duk da ta daure kwana biyu a cikar kwana na biyar sai da yanayinta ya canja saboda matuƙa take buƙatar su, ta rage kulashi suyi faɗa, ta zama shiru-shiru, wani lokacin ma yakan shigo gidan ko ɗakinta ya ganta zaune a lungu ta takure kanta cikin damuwa koma tana kuka, sosai take bashi tausayi, dan haka a duk sanda ya ganta a yanayin sai ya zauna yayta mata nasiha ne cikin tausasawa, yana kuma ƙoƙarin bata ruwan addu'oin da malam ya basa a ɓoye batare da ta sani ba, magani ma na nan zuwa da malam ɗin yace zai haɗa mata inasha ALLAH akan shaye-shayen dai. A ɓangaren karatu da suka fara duk da dai suna ɗan kai ruwa rana wasu lokutan kafin ayi, Alhamdullah ya fahimci tana ganewa, dan a ɗan tsukun kwanakin a ɓangaren salla abubuwa da yawa Lulu ta gyara, tana kuma ƙoƙarin riƙe addu'oi. Nacin fita aiki kuma bata daina ba, shi kuma bai kulata ba. Washe garin da suka cika kwana biyar ranar asabar Aunty Bilkisu da Hawwah da Maryam da Asma'u sukazo gidan, ranar yana gida bai fita ba, dan dama fitar tasa dai ba ko yaushe bace ba, ba kuma ta wuce zuwa gidansu, stadium training, sai ɗan kaikawo akan case ɗintan nan na yarinyar nan da yake mata bincike tunda su Uncle Yousuf sun shigar da ƙara court da mahaifiyar yarinyar da kuma taimakon ƴan sanda. Duk sanda ya fita kuma baya yarda ya daɗe idan yayi tunanin ya barta ita kaɗai dan a ɗan zaman sun nan ya fahimci bata son kaɗaici, sai kuma sauran kai kawon da suke da su Coach akan batunsa na abubuwan da suka saura dole da kansa zaiyi. Tarba suka samu ta muntunawa ga Lulu irin wadda su kansu basuyi zato ba, sai suka ji ƙaunar matar ɗan uwan nasu ta ƙara mamayesu. Fargabar da suke ta wataran zai iya aure matarsa ta rabasu da shi ta fita fit a zuciyarsu. Yana ɗaki yana barci hayaniyarsu ta tada shi, bai san kosu waye ba dan haka ya tashi badan barcin ya ishesa ba ya fito, turus yay yana kallonsu, sai bin Lulu daketa faman murmushin yake da kallo, a zuciyarsa kuma yana wani tunani, musamman akan maganar malam da yace tana da ɓoyayyun halaye masu ƙyau, to amma miyasa masu aikin gidansu su take musu duk yanda taso? Kodan su suna a ƙarƙashin ta ne take gani, na biyu ya fahimci bata son kaɗaici sam, dan koshi idan zai fita gidan sai ya ga yanayinta ya canja zuwa damuwa koda bazatace komai ba. Maryam ce ta fara hangosa, cike da jin daɗi ta ce, “Yaya Hydar sannu da fitowa”. Da kai ya amsa mata, yayinda sauran ma duk suka juyo harda Lulu, sai dai kallo ɗaya ta masa ita ta ɗauke nata idon. Falon ya ƙaraso ya zauna, cikin girmamawa ya gaida Aunty Bilkisu, su Hawwah ma suka gaida shi. Daga haka aka ɗan cigaba da hira sai dai basu yarda sunyi wani abinda Lulu zataji a ranta kamar ita barece a cikinsu ba. Wannan abu yayi matuƙar tasiri a zuciyarta, sannan yanda suke girmama juna da shaƙuwarsu da soyayya mai ƙarfi ya matuƙar sata jin kewa da jin inama itama haka take da nata ƴan uwan. Ta kasance cikin farin ciki a wannan yinin, dan ko abinci Maryam da Hawwah ne sukayi basu barta tai komai ba sai Asma'u data gyara gidan, dan wannan shine kema Lulu wahala kuma duk da bata ƙaunar ƙazanta. Ta masa maganar mai aiki yaƙi ce mata komai, shi kuma ba mai aikin ce baiso ba duk da yasan kuɗin biyanta ma a garesa wani abu ne daban, tsoron kar mai aikin ta zame mata ƴar aikar sayo ƙwaya yake shiyyasa yay mata shiru. A lokacin da su Hawwah ke kitchen suna girki Aunty Bilkisu kece masa. “Hydar baka ganin ya kamata kayi haƙuri Hawwah ta koma ɗakinta, mijinta na sonta sannan yana ƙoƙarin sa a kanta, mahaifiyarsa kuma shima tafi ƙarfinsa ne. Tunda su Abba sun bar komai a hannunka ya kamata ayi haƙuri ta koma haka nan ai anja masa kunne, ALLAH tausayi yake ban kullum yana cikin zaryar zuwa gidan nan, ga Nasreen dake damunta kullum ita Abbanta Abbanta, ita kanta Hawwah dauriya kawai takeyi da kuma bazata iya ƙetare maganarka ba, kayi haƙuri ka duba ta koma gidan mijinta kodan halin Umma da bata gajiya da abin faɗa kullum ta ALLAH a gidan nan kan Hawwah, haƙurin shi yafi komai ko ya kikace Mawaddat?”. Ta ƙare maganar tana duban Lulu da ke saurarensu. Jin jina kai Lulu tai da faɗin, “Hakane Aunty, to amma miya kawo matsalar har haka? Sa'id ɗin bashine na gani a wajen bikin nan ba anata kai da kawo da shi?”.

      “Shine fa.....” nan ta kwashe komai ta sanarma mata. Sosai Lulu tai mamaki, sai dai kuma hakan baizo mata baƙoba dan sun sha cin karo da irin waɗan nan case ɗin wasu ma sai iyayen mijin sun illata yaran saboda ƙiyayya, wasu ko yaranne fitsararru, sannan kakarsu Dada ita kanta fitinanniyar mace ce da tasan tana ƙuntatama matan kawun nanta matuƙa. Duban Smart tai da faɗin, “To amma shi miyasa bazai zauna yay magana ta fahimta da mahaifiyarsa ba, ko kuma yabar gidan nake ganin hakan zai basu masalaha idan basa ganin juna ai Aunty, ko za'a dinga samun matsalolin ba kamar suna zaune waje ɗaya ba”.

       “Kowama haka yake faɗa Mawaddat, to amma maman ce taƙi yarda wai zasu barta a kaɗaici. Shi dai mijinki shi ya kamata yay haƙuri a duba kodan Sa'id ɗin” ta ƙare maganar da kallon Smart.

         Shiru kamar bazaice komai ba sai kuma ya ɗan nisa. Cikin ɗage kafaɗa ya ce, “Aunty Bilkisu bawai zaman nata nima namin daɗi bane, sai dai kuma bazan barta ta koma ba haka salin alin, inada shiri nima dan dolene sai mahaifiyar Sa'id ta fahimci kuskurenta ko kuma ya raba musu gidan, inada hikimata na tsaiwa akan hakan dan har mahaifinsa ya dawo sannan”.

      Cikin gamsuwa Lulu ta ce, “Hakan da yayi ɗin shine dai-dai, inba hakaba komawar tata haka nan babu wani mataki zai cigaba da bada damar faruwar fiye da haka a tsakaninsu......”

      Haka suka cigaba da tattaunawa har su Hawwah suka kammala girki. Wani abu daya saka Lulu farin ciki lokacin da su Aunty Bilkisu sukai zaman cin abincin da suka zuba a tray ɗaya sai ta tsaya kallonsu musamman da Smart ya ɗakko nasa spoon yazo tsakkiyarsu ya zauna yana faɗin “Ni sai a ware ni”. Abune da bata taɓa gani a gidansu ba, itama saita tura baki gaba tace, “Ni baku so naci da ku saboda ba Ammah ta haifoni ba”. 

      Da sauri aunty Bilkisu ta kamo hanunta ta zaunar kusa da ita kusa da Smart kuma ɗan shine a gefenta, har suna haɗa baki ita da su Hawwah wajen faɗin, “Karkisa Ammah ta dafamu a tukunyarta da jin wannan kalamai”. Murmushi tayi kamar yanda shima Smart ke kallonta ta ƙasan ido yana yi, sai tana mai jinta kamar sabuwar halitta a yau. Lulu da bata damu da abinci ba yau kam saita saki jiki ta ɗan ci. Da son neman magana Smart ya ɗauki naman gabanta, hararsa tayi da tura baki itama ta ɗauki na gabansa batare da tace komai ba, kallonta yay yana ɗan zaro ido ya ce, “Miye kuma na ɗauka min nama Madam?”.

        “Nawa daka fara ɗauka naka ne”.

    Itama ta faɗa cikin ɗam murguɗa baki kaɗan. Kai kawai ya jinjina alamar zan rama, su dai su Hawwah sai gimtse dariya suke. Can Lulu ta sake ɗaukar naman gaban nasa ta rufe da abinci, sarai ya ganta sai baiyi magana ba sai da ya shammaceta ta ɗakko zata kai baki caraf ya ɗauke sa daga spoon ɗin nata ya lunƙuma baki.  “What!” ta faɗa tana kallonsa, miƙewa yay da mata gwalo yabar wajen dan ya ƙoshi daman. Da gudu su Maryam suka tashi suna dariya. Lulu ta dubi Aunty Bilkisu kamar zatayi kuka ta ce, “Aunty kin ganshi ko? Shi baiso a zauna lafiya kullum sai anyi faɗa yake jin daɗi”.

      Aunty Bilkisu dake danne dariya da ƙyar ta harari Smart da dafa Lulu da itama ke hararsa ta ce, “Kinga ƙanwata barsa zamu rama. Tsarabar dana kawo takine ke kaɗai nama fasa bashi”. Murmushi tai da sake hararar Smart itama ta masa gwalo da faɗin, “7-6”. Ƙwaɓe fuska ya ɗan yi shima da yin ƙwafa ya ce, “Ki jira game over. Aunty kuma gaskiya ba haka akeyi ba”.

     “To ni haka zanyi”. Cewar Aunty Bilkisu tana hararsa. Sai kuma ta kalla Lulu, “Kin san wani abu shi fa dama Hydar akwai zura tun yana yaro, idan aka zuba abinci aka bashi sai yace shi bashi yake so ba na Ammah yake so, idan aka bashi sai kuma yace (Ni wannan ina co) ya sake nuna namu, nan ma a bashi sai ya sake nuna wani nanma yace shi wannan yana co, hankalinsa bazai sake kwanciya ba sai yaga kaf abincin an tara masa gabansa zai bar kunnen kowa ya huta kuma fa ba ci zaiba.

       “Kai aunty miye na faɗa mata kuma” Smart ya faɗa cikin shagwaɓa. Aiko mi Lulu zatai inba dariya ba. Sai ta kallesa tace “Ni wannan ina co” ta ƙyalƙyale da dariya. Sai da takai ya kwashi filos ya fara jefa mata ta tashi da gudu tana cigaba da faɗa. Dole aunty Bilkisu ta dara itama tana sake jin ƙaunar Lulun a ranta. Waɗan nan abubuwan sun matuƙar ɗauke ma Lulu kewa da sakata a farin ciki a wannan yinin, yayinda gefe ɗaya ta takurama Smart da faɗin ‘Ni wannan ina co’ har bayan tafiyarsu. Shima sai abun ya koma bashi dariya dan ya fahimci ta samu abin yi.........✍️

      


         


_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_


*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*


FURAR DANKO

Billyn Abdul


-ZAFIN KAI

Mamuhgee


-TABARMAR ‘KASHI

Safiyya Huguma


-BAKON MUNAFIKI

Miss xoxo


Duka hudu 1k

Uku 800

Biyu 600

Daya 400


Pay at👇


1487616276 

Access Bank

Bilkisa Ibrahim Musa

Sai katura shedar biyanka anan👇


09032345899


Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇

09033181070



*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


*THANKS FOR CHOOSING US*🥰


Zafafa🫶🔥




*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*

COMMENTS

Name

ADSENSE,4,Airtel,1,ANDROID,9,AQIDARMU Book 1 Complete Hausa Novel,1,AQIDARMU Book 2 Complete Hausa Novel,1,Arbitrade,4,Arbitrage,1,AUREN MU Complete Hausa Novel,1,Babban Yaya Hausa Novel Complete,1,Babu So Complete Hausa Novel,1,Bakar Inuwa Complete Hausa Novel,27,Billyn Abdul Novels,7,BLOGGING,13,Business online,10,Crypto currency,17,Dare Daya Hausa Novel Complete,1,Daudar Gora Book 1 Complete Hausa Novel,48,Daudar Gora Book 2 Complete Hausa Novel,95,DOWNLOAD,2,Duk Karfin Izzata Book 2 Complete Hausa Novel,34,Education,3,Email,1,Facebook,4,Finance,1,Furar Danko Book 2 Complete,9,Furar Danko Complete Hausa Novel,31,fyade hausa novel by maman teddy,1,fyade hausa novel Complete,1,Gidan Haya Hausa Novel Complete,6,Gidan Haya Complete Hausa Novel,4,Gidan Haya Hausa Novel,1,Gidan Kwarata Complete Hausa Novel,1,Glo,1,Google,1,GURBIN IDO Complete Hausa Novel,1,Hamshakiya Hausa Novel Complete,25,JARABABBEN NAMIJI Complete Hausa Novel,1,Jikar Maguzawa Complete Hausa Novel,23,Job,7,KASUWANCI NA Complete Hausa Novel,1,Layikan waya,2,Loan,8,MA'AIKACIYAR GOMNATI Complete Hausa Novel,1,Makauniyar Kaddara Complete Hausa Novel,70,Mufeedah Complete Hausa Novel,25,Namijin Zuma Complete Hausa Novel,26,nihaad complete,62,Nihaad Complete Hausa Novel,62,nihaad hausa novel,62,Npower,13,Pc Tools,2,Qamshi Hausa Novel Complete,14,Raina Kama Complete Hausa Novel,29,Sakayyah Book 2 Hausa Novel Complete,30,Sakayyah Hausa Novel Complete,60,SHAKUWAR YARINTA COMPLETE HAUSA NOVEL,20,Support,26,Tabarmar Kashi book 2,7,Teach and guide,8,TUMFAFIYA Complete Hausa Novel,1,TUMFAFIYA Hausa Novel,50,TUMFAFIYA Hausa Novel Complete,19,UNCLE DATTI Hausa Novel Complete,1,Watsapp,3,Waye Mijina Hausa Novel Complete,5,WEB LANGUAGE,1,WEB TUTORIAL,2,Yar Aikin Karuwai Book 1 Complete,1,Yar Aikin Karuwai Book 2,1,Yar Aikin Karuwai Hausa Novel,1,Yaya Mata Complete Hausa Novel,22,Zafafa Biyar Novels,7,
ltr
item
NAGARTA24 || job || npower || crypto currency || arbitrade || loan || teach and guide || support ||: Furar Danko 74
Furar Danko 74
https://blogger.googleusercontent.com/img/b/R29vZ2xl/AVvXsEhKApn83ujA5DRafnyIfov6ovfV76fmkFe1YdjfEKqjAWj3lFrfxNZDYRq7sesCNhuJs3xhcZxHkfCa8ACXujGIDlHvcJSMYFL9UvDzQQLFzgsvR1RS1g1GStejGGx-lM6VHKE5oUPi9WMPpRbZplO2YPTsh8I-3WbgKS3Q1Y0vAq_7ZnyXBp2G0cKjnZqD/s320/img_1696029890866.jpg
https://blogger.googleusercontent.com/img/b/R29vZ2xl/AVvXsEhKApn83ujA5DRafnyIfov6ovfV76fmkFe1YdjfEKqjAWj3lFrfxNZDYRq7sesCNhuJs3xhcZxHkfCa8ACXujGIDlHvcJSMYFL9UvDzQQLFzgsvR1RS1g1GStejGGx-lM6VHKE5oUPi9WMPpRbZplO2YPTsh8I-3WbgKS3Q1Y0vAq_7ZnyXBp2G0cKjnZqD/s72-c/img_1696029890866.jpg
NAGARTA24 || job || npower || crypto currency || arbitrade || loan || teach and guide || support ||
https://www.nagarta24.com.ng/2023/10/furar-danko-74.html
https://www.nagarta24.com.ng/
https://www.nagarta24.com.ng/
https://www.nagarta24.com.ng/2023/10/furar-danko-74.html
true
1779421581242976301
UTF-8
Loaded All Posts Not found any posts VIEW ALL Readmore Reply Cancel reply Delete By Home PAGES POSTS View All RECOMMENDED FOR YOU LABEL ARCHIVE SEARCH ALL POSTS Not found any post match with your request Back Home Sunday Monday Tuesday Wednesday Thursday Friday Saturday Sun Mon Tue Wed Thu Fri Sat January February March April May June July August September October November December Jan Feb Mar Apr May Jun Jul Aug Sep Oct Nov Dec just now 1 minute ago $$1$$ minutes ago 1 hour ago $$1$$ hours ago Yesterday $$1$$ days ago $$1$$ weeks ago more than 5 weeks ago Followers Follow THIS PREMIUM CONTENT IS LOCKED STEP 1: Share to a social network STEP 2: Click the link on your social network Copy All Code Select All Code All codes were copied to your clipboard Can not copy the codes / texts, please press [CTRL]+[C] (or CMD+C with Mac) to copy Table of Content